Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta shiga aika mata dasu tana ce mata yar baqin ciki haka zata qare tana gani suna abin arziqi banda ita.

Wai ya Hajia Balaraba ta qare da maganin Malam Wizy ne?? 😂😂😂🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 7

A bangaren Hajia Balaraba kuwa cike da farin ciki ta bude gida ta shiga ganin har sannan Kishiyarta bata dawo daga gurin aiki ba, cikin sauri ta fito da rubutu ta huda leda tareda guntsa ta feshe kofar dakin Amarya tana cewa “Shegiya maza ki dawo ki taka ni Alhaji yaiyo waya daga kasuwar ma yace ya sake ki base ya jira ya dawo ba” ta qulle ragowar gudun kar ya zube ta qarasa qofar ta.

Mayafinta kadai ta ajiye ta shiga kitchen ta hau kicikicin dora girki qarin farin cikinta ita ce da girki dama kai yau koda ba itace da girki ba ai dole tasan yanda za’ayi ta aiwatar da aikin nan tanayi tana tuna irin cin mitunchin da Alhaji yai mata dazu da safe kafin ya fita kuma ta tabbata duk Amarya ce ta zugoshi har yana iqirarin tabar ganin sun tara yaya da jikoki tsaf seya yanka mata tikitin zawarci.

Itadai tunda Malam na kan Tudu ya kwanta dama kamar ya tafi da duk ayyukan da Tayi akan Alhaji ne komai ya karye shekara da shekaru tana cin duniyarta da tsinke se yanzu da tsufa ya kusa cin mata ne zata fara karbar taskun namiji ina bazeyuwu ba ai.

Tsaf ta gama hada lafiyayyar Miyar taushenta kafin ta dakko qaramar tukunya ta sare wata wadda zata ci, nan da nan dakko ragowar rubutun Malam Wizy ta kurbe tas ta kuskuro dattin bakinta da komai ta watsa musu a miya ta sake kurbe ragowar ta zuba ta juyata dakyau ta rage wuta ranta fes dan gani take kamar ma aikin gama ya gama.

Tana cikin malmala tuwan autarta me suna Ruqayya ta shigo ta dawo daga makaranta dan tana shekarar ta ta qarshe ne a GSU da mamaki ta kalli maman tata kafin tace “Hajia kece dakanki yau a kitchen ina Baba Zulai din”

Bata ko dago ta kalleta ba tace “Taje gida Sa’adenta batada lafiya ina ga se gobe zata dawo”

“Kai dukda haka da mamaki ace Hajia kina girki lallai yau zamu kwashi dabge bari nayi sauri nayi wanka nayi Sallah muzo mu kwashi ganima”

“Zaki kwashi ganima dan uwarki duk zan kulle bakinku ai na ga ta inda zaki ringa kaiwa uban naki gulma idan na taba kudinsa” ta fada bayan Ruqayyan ta fita daga kitchen din

Oho bata ma san tanayi ba dakin ta ta nufa a ranta tana ayyana tabbas akwai wata a qasa dan ita dai tafi shekara Goma rabonda taga Hajia tayi girki da kanta Baba Zulai ce take yi musu ko kuma ita idan taba gida. Ita zata iya cewa ma idan kaga Hajia a kitchen to an gama Abinci ne idan harda na Baban zatayi barbade daga baya ma daya gane yai Allah ya isa yama zo kuma ya dena cin abincin kwatakwata se baya bayan nan taga ya dawo yana ci.

Ita kuwa Hajia tana sauke tuwo ruwan Tea ta mayar ta saka lipton dinta da kayan qanshi sannan ta zuba jiqon Wizy, bata matsa ko ina ba seda ta kammala tsaf ta hada komai ta kai kan Dining sannan tashi ga dakinta tai wanka ta fara jero Qara’in salloli.
Seda akayi Isha Alhaji ya shigo, kai tsaye part din Amarya ya shiga dan akwai kayan daya manta da safe da ze tafi kasuwa yana so ya dauka kar gobe ya sake mantawa. da mamaki ya kalleta dan ya zata ta tafi aiki tunda tace masa Night Duty ne da ita. tana ganinsa ta miqe

“Yawwa Alhaji dama kai nake jira tun dazu”
“Lafiya Abida baki tafi aikin ba? Jiran me kike mun?” Ya fada yana kallonta. Seta miqa masa wayarta kawai ba tareda tace komai ba, karba yayi yana duba screen din sega video Hajia Balaraba tana kici kicin zuge jaka, baya jin me take cewa amma fes yaga sanda ta ciro leda ta guntsi rubutun ta feshe kofar dakin Amarya ta tafi”
Se ya miqa mata wayar dason jin qarin bayani.

“Wallahi Alhaji yanda ka gani dinnan kasan ka fita ka barni kaina yana ciwo dan haka sena kwanta dan ban ma samu zuwa Barkar Haula da nace maka zan fita ba, se bayan La’asar na ma idar da sallah na tashi zan leqa na karbo Kati se naji motsin a bude qofa, in duba ta window fa shine naga Maman Suhaila na wannan ta tsaya tana maganganu tareda bude jaka wayata na hannuna ni kuma shine na kunna video saboda kar a maimaita irin ta wancan karan data zuba magani akace qarya nakeyi yanzu dai ga Hujja ka gani da idonka, nidai ban fita ba koma na menene kai kadai ka tsallaka shi se kasan yanda zaayi azo a karya dan bazan yi ta zama a daki ba kona fita a sabautani a banza”.

Wani irin tuquqin baqin cikine ya rufe Alhaji har huci yakeyi, wato duk Allah ya isar dayai wa matar nan bata daddara ba kenan? Shin wai se Yaushe Balaraba nutsu tasan Annabi ya faku ne ita dai duniya ce kawai a gabanta to kuwa Insha Allahu Allah baze sake bata ikon maidashi halin data jefa rayuwarsa a baya ba shi wallahi badan kar duniya ta zageshi ace ya saki matar sa auren shekara Arba’in ba da rabuwa zeyi da ita ya huta amma yanzu babu wand ze dubi abinda ta aikata masa shedai a dora masa laifi ace Ya wulaqanta Uwargidansa.

Cikin fushin daya gaza boyewa ya fita, mintina kadan ya dawo tareda wani yaro ya shigo palour ya bar yaron a kofar dakin tareda nuna masa gurin yace ga inda zeyi fitsarin nan yaro kuwa ya tsula abunsa Alhaji ya fita ya nuna masa famfo ya taro ruwa suka sheqe a gurin nan da nan ya wuce daman tiles ne. Ciki ya dawo yace da Abida ta biyo shi yai gaba tana baya se palour Hajia Balaraba.

Tana zaune ta hakimce akan kujera ta sheqa kwalliya ta garari ta kuwa yi kyau sosai dan Hajia Balaraba akwai kyan jiki da gayu kai bazakace tabawa Hamsin baya ba. Tana ganin Alhaji ta miqe da fara’a da nufin tarar sa sedai ganin Amarya a bayansa yasa ta gintse fuska a ranta tana tunanin meya faru kuma dan ita bata ma lura da yanayin fuskar Alhajin ba.

“Balaraba me kika zuba a qofar dakin Abida?” Ya tambaye ta cikin kaushin murya. Qirjinta ne ya fara luguden daka zuciyarta kaman zatayi tsalle ta fito saboda razana, ya akayi ya sani to ko wani ya ganta ne? Ita dai a hasashenta babu kowa a gidan dan Tunda da zata fita seda ta saka muqulli ta kulle haka data dawo dakanta ta bude kofar, koma menene bazata bare a gano ta dole tasan yanda zata kare kanta.

Qoqarin daidaita nutsuwarta tayi tana daure fuska tace “Bangane me kake nufi ba Alhaji wani sharrin kuma aka sake qullomin yau ma? Ni duk yau ma ban fita daga part dina ba bare har naje qofarta na zuba abu”.

Kallon takaici da tsana yake binta dashi, se ya miqawa Abida hannu tayi saurin miqa masa wayarta. Video yayi playing ya miqawa Hajia Balaraba dake ta taraddadin me nene a cikin wayar Abidan, ai seda ta kusa Sakin fitsari a gurin saboda kidima nan danna zufa ta shiga keto mata.

“Wane La’anannen ne ya dauki wannan video” ta fada bakinta yana rawa tsabar yanda ta rikice, zata sakw magana ya miqa mata hannu ta bashi wayar yana cewa

“Kici gaba Balaraba sharri dan aikene ki sani duk nisan indai kika aika shi watarana seya dawo miki, tunda har kin raina Allah ya isar da nayi miki akan in kika sake yimun wani abu ko wani daga cikin iyalaina shikenan na barki da Allah kuma matakin qarshe dazan dauka shine wallahi Balaraba idan kika sake zuwa gidan wani malami kika aikata wani abun sihiri a cikin gidan nan kai na ko kan wani nawa, na sani ko ban sani ba to ki sani a bakin aurenki”

Cikin tsananin razani ta dago ta kalle shi dan bata taba zaton tsaurin hukuncin ze kai haka ba, ta bude baki da niyyar neman sassauci yace “Karma kice komai dagaske nake kuma ba igiya daya ko biyu ba dukka ukun nake nufi idan kuma kika aikata a bayan idona ba tare da na sani ba muka ci gaba da zaman aure dake wannan kuma na barki da Allah shi ze bimin haqqin zaman zina da kika sa nayi ba tare da sani na ba” yana kaiwa nan ya shige dakin sa da yake a part din nata, Abida ma jiki a sanyaye ta juya ta fita aka bar Balaraba da dora hannu aka tama tasa kuka zatayi ko ihu?

Wannan shi ake kira da An bata biyar goma bata gyaru ba (Dama ai duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba tabbas tashi ko dumi kuwa ba zatayi ba).


Lagos
Seda Ma’u ta cike satin nan daya raya cif aka sallameta, da safe bayan Bashir da yara sunzo sun tafi tacewa Dr ya sallameta haka. Da kanta ta karbi Discharging later ta hada yan kayanta kafim ta kira Uber ta cale gida (tsiyar garin da baka da dangi kenan).

Koda ta isa gidan bata zauna ba seda ta gyara ko ina tsaf ya dawo mata yanda take so sannan ta shiga hidimar dora girki kuma, aikin ya jata da yawa dan har bayan La’asar sannan ta kammala komai ta jere akan Dining kafin ta koma dakinta kuma ta fada wanka. Tsaf ta shirya cikin wani hadadden cotton lace Army green da akayiwa dinkin Fitted gown datai bala’in yi mata kyau ta fito mata sauran quruciyarta. Indai gayune dole a cirewa Ma’u hula wannan ko a zamanin yammatancinta babu kamarta a kaf qawayenta tana da kyau ta kuma iya daukar wanka ga farin jini Allah ya mata abinda ya sa ta zama ta daban kenan da sauran.

Daurin nan ta kawo shi gaban goshi bayan ta fake gashinta qasa qasa sannan ta saka cogenta ta qara feshe jikinta da turaruka ta shiga juyi a gaban mirrow dan ta burge kanta da kanta ballanta na Kuma Bashir ya ganta tasan duk yanda yake qyashin ya yaba kwalliyarta yau kam se idanunsa sun fado qasa qilan a garin kallo.

Mint flavored chewing gum ta jefa a bakinta kafin ta fito palour ta samu kujerar dake facing kofar shigowa ta dora daya kan daya tana girgizasu tana danna waya ba koyi minti biyar da zama ba ta jiyo tsayuwar motarsu, seta qara gyara zaman ta dakyau tana sauraron shigowarsu.

Aliyu ne a gaba dauke da Laptop bag din Bashir se school bag dinsa daya goya a baya se ga sauran a bayansa. Gaba daya suka nufe ta cike da murnar ganinta a gidan, Aliyu ne yace

“Mami this house can never be complete without you Allah Mami da baki nan ji nake kamar a kango muke kwana amma yanzu tundaga qofa kawai naji it feels like home again ashe kece kika dawo ciki”

Dukan wasa ta kai masa tana cewa “Oh Ali yammata kam se sun bani da dadin bakin nan naka Allah dai ya nuna mun lokacin” se ya rufe fuska wai shi kunya yana cewa “Kai Mami ki dena kunya nake ji”
Gaba daya suka saka dariya, se a sannan ta daga kanta ta kalli inda Malam Bashir yaci burki tunda ya shigo, seta qara fadada murmushinta tana cewa

“Aa Baban Ali yane ka tsaya ka shigo ka zauna mana ko ka qara sa ciki”.

Bashir
Numfashinsa ne ya dauke na wani lokaci sanda yai arba da fuskar Ma’u, tayi masa kyau matuqa gaya da har ya kasa iya cire idanunsa daga kanta. Maganar da tayi ce ta fargar dashi kamar dama me jiran umarninta kuwa se ya taho, kusa da ita inda Farida ke zaune ya daga Faridan cak ya zauna a gurin tareda dora ta a cinyarsa kafin ya maida kallonsa kan Asma’u yace “to naga ne hankalin ki yana kan yaranki kamar ma ni baki ganni ba” ya fada yana kafeta da kallon nan nasa me saka Yammata fadawa soyayyarsa ba tare da sun shirya ba.

Irin kallon da shi ya ringa qara rura garwashin soyayyarsa a zuciyarta har ya tada gagarumar wuta da hauyau ba’a samu ruwa ko iskar da sukayi nasarar kashe ta ba.

Seta tsura masa nata kyawawan idon tana hango abinda zuciyarta ce kadai take da tafsirinsa, a cikin idanun Bashir kadai take iya hango tsabtatacciyar qaunarta wadda babu Algus ko digo a ciki amma ginshiri da baqar izzar sa suke hana bakinsa iya furtawa. Har gara gangar jikinsa takan gaza bashi hadin kai gurin boye sirrin zuciyar tasa dan a duk sanda suka hadu gangar jikinsa na sarrafuwa ne kawai bisa umarnin zuciyarsa bawai kwakwalwarsa da take nan kamar wadda akeyiwa hayaqin wiwi ba, yanzu yai abin arziqi an jima ya tafka na tsiya.

Ganin irin kallon qudar da Abbi da Mami sukewa junansu ya saka Amna kama hannun twins manyan kuma suka tashi gaba daya kowa suka shige dakinsu, miqewar Farida daga kan qafarsa ta ankarar dashi, seya janye idanunsa cikin son basarwa shima ya miqe yana ce mata

“Zan samu abinci kuwa? Gaba daya yau coffee ne kadai a cikina”

“Ai fa ga Kuku ta dawo dole ka nemi abinci babu tambayar ya akai na taho ni kadai ban kiraka ba balle jin ya jikina” ta ayyana a zuciyarta, a fili kuwa seta ce “kayi wanka first, ga abinci nan yana jiranku” se ta miqe ta nufi dakin su Amna.

Se ya rakata da ido kuwa kamar zasu fado din, yanda take juya qugunta da ya fito sosai saboda yanda rigar ta bawa komai haqqinsa ga qarar takalmin qafarta da yake ji kamar qararrawa a cikin qwaqwalwarsa. Wasu busassun yawu ya hadiye tareda lasar lips dinsa da suka bushe kafin yace “Hmmm” (inji me ciwon haqori 😂😂😂) karaf a kuwa a kunnen Asma’u daidai sanda take tura qofar dakin su Faridan

“Idan baka chanza hali ba Bashir wata rana sedai ka farka ka ganka a kabari Maganganun da kake dannewa sun shaqe maka wuya, ayi mutum bakin na son magana amma baqin rai ya hana shi Allah yai mana magani dai”.

Guri ta nema ta zauna dan ba abunda zatayi a dakin dama ta tashi ne kawai dan ta bashi damar kallon kwalliyar tata da kyau. Ahmad daya fito daga toilet alamar wanka a ka masa ta shiga shafawa mai kafin Muhammmad ma ya fito, tsaf ta shirya su, kafin su gama an kira Sallar Magriba dan haka tace suje suyi Alwala ita ma ta fita dan zuwa tayi a bakin qofa suka kusa cin karo da Bashir wanda da alama shima wankan yayi ya chanza kayansa zuwa Jallabiyya Baqa da tayi bala’in masa kyau duk da kasancewarsa ba fari qal ba, Bashir nada kyau irin na Maza me sanyi daya hadu da kwarjinin da Allah ya bashi.

“Kayi kyau Baban Ali” ta fada da zuciya daya dan ita bata iya munafunci irin nasa ba kuma rashin yabon kwalliyarta be taba sare mata guiwa akan ta denayi ba.

Kallon ta yayi yana dan Murmushi kafin yace “Koh?”
Seta amasa masa da sarar sa tace “Uhm” tana qoqarin kauce masa a ranta tana mita. A zaman shekara Goma sha shidda baza ta tuna ranar da a karan kan Bashir ya budi baki ya yabi kwalliyar ta ba tun tana qorafi idan tayi se ta tambayeshi tayi kyau sannan ze yaba har ta gaji ma ta dena, yanzu da yaranta suka girma kuwa indai tayi kwalliyarta se sunce Mami kinyi kyau shiyasa ma ta dena damuwa da yabawar Bashir dukda abun da zafi amma ya zakayi (Mazan hausawan Mu Allah ya shirye ku dai 🥺🥺).

Wuce shi tayi ta shiga dakinta itama ta daura Alwala shi kuma ya hada kan yaran suka fita. Data idar da sallah zama tayi ta qara gyara fuskarta dakyau sannan ta fito, sun zauna a Dining da gani ita suke jira dan haka ta qarasa gurin.

Seda tayi serving kowa sannan ta zauna suka fara cin abinci kowa na santi karma Bashir yaji labari dan kunnensa har motsi yake. Besan yawan abincin daya nada ba seda ya qara saka serving spoon ze debo abincin a karo na uku bayan wanda ta zuba masa yaji wayam aiko suka kwashe da dariya suna kallonsa. Seya bata fuska kamar yaro yace

“To ai yunwa nake ji for almost a week fa bamu ci abincin Mami ba, please Mami karki kuma tafiya ki barmu, we are so sorry mun ji jiki wallahi, we missed you alot”.

“Zobon da Asma’u ta kurba ne ya sarqe ta ba shiri ta watso shi tsabar yanda mamakin kalaman Bashir suka nemi kasheta a zaune.

“Bashir dai data sani ne yake wannan maganar?” Kai ita kam badan ciwo ba dadi ba da tace ta ringayi duk wata ko Allah ze saito mata Bashir zuwa abinda ta dade tana fata.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 8

To Aka ce mata da Miji se Allah dan kuwa Ma’u da Basharin ta suna qulewa a daki sukai muqus aka shiga sharafin soyayya dan dama an dade ba’a hadu ba qarshe har makara tashi bacci sukayi. Safiyar ranar duk su biyun da ka kallesu zaka san suna cikin walwala.

Ta cancada kwalliyarta da skirt and blouse na Atamfa komai ya fito se juyi take tana saka kwakwalwar Bashir jijjiga. haka ta hada musu breakfast me rai da lafiya suka ci suka wuce makaranta dukda sam be so yau ta zama ranar aiki ba ya so ace suna gida yau yaci duniyar sa da tsinke ya more amma ba komai ai Gobe Friday zasu hadu.

Suna fita Qarasa yan abubuwan da suka rage mata tayi kafin ta shiga dakin ta ta kwanta dan huce gajiyar da Bashir ya tara mata, “Bashir is too good” ta ayyana aranta. Wato yasan ta yanda duk ze wanke laifinsa ta wannan fanni gwanin malami neda ta tabbatar samun irinsa se an tona.

Tana tsaka da tunanin shauqin daren jiyan ta jiyo qarar door bell da kuma ringing din wayarta. Wayar ta fara jawowa ta duba, Anty ce matar ogan Bashir dake Flat din da yake kallon nasu, seta miqe tareda daukan Qaramin mayafi dan dankwalin kanta ya zame.

A palour suka zube tare da Anty da ta farayiwa Asma’un tsiya tun daga qofa”

“Kai Ma’u kinga wani kyallin goshi da kike daga fitowa daga Asibiti har za’a maida wani kenan”. Daria Asma’u tayi tana cewa

“Haba dai ai na gama nikam wadan nan ma sun isa Allah ya raya mana sisi na kwai zan ci gaba dayi”

“Inafa kika gama kedai ki shirya dan qila wasu biyun ne a tafe”

“Ba amin ba Anty” ta tare Antyn.
Gaisawa sukayi kafin Antyn tace mata

“Shekaran jiya na dawo wlh se dare ma nashigo Honey yake cemun Ai kina Asibiti ba lafiya, har zamu zo jiya da magriba kuma yace sun hadu da Baban Aliyu a Masallaci ya ce masa kin dawo gida”

“Eh wallahi jiya da rana aka sallamoni ai gaskiya Anty kinsha gida kusan 3 weeks fa” Asma’u ta fada.

“Ki bari kedai zama nayi na huta nayi gyara sosai dan anan ba wani lokaci kake samu ka baje yanda kake so ba mutum na saka maka ido” cewar Anty tana bawa Asma’u hannu suka kashe

“Kai Anty a ringa tausayin Baba na dai karki qarasa mana tsohon mu”

“Ke barni fa dole na kwaci kaina sarai kin san Uwargida na bata wasa da gyara dole nima na zage kar a raina ni.

Hira suka shigayi Anty ta shiga fito da abubuwan da tayo wa Asma’u tsaraba tana cewa “Gashinan se a ci gaba da gashi ban ce ki raga masa ko na second daya ba atoh” suka tuntsure da dariya Asma’u tana cewa “Anty baki da dama”. Se wurin 12 sannan ta mata sallama ta tafi bayan ta rakata qofa ta dawo tana tattare kayan zuwa dakinta a ranta tana qara jin qaunar Antyn dan yanda ta dauketa take kula da ita kamar qanwarta da suka fito ciki daya.

Anty Suwaiba matar Engineer Abdullahi Gusau ce ogan Bashir.
Itace Matar sa ta biyu uwar gidan ta ma anan Lagos take da zama amma ba unguwarsu daya ba. Mace ce me tsananin kirki dukda ta dan girmi Asma’u amma yanda take mu’amalantarta kaman qawaye ko shaqiqan yaya da qanwa suke dan tunda suka fara haduwa jinin su ya hadu da Asma’un.

Ita kanta Asma’u tana ji da Antyn dan Ita tunda suka hadu rabon da tace ta siyi wani abun gyara da kudinta, a koda yaushe Anty cikin yo musu aike kaya gangariya daga Zamfara garinsu take kuma duk sanda Asma’u ta tambayeta nawane ta biya seta nuna bacin ranta. Ta kance da Asma’un
“Ni a qanwa na dauke ki, banida kowa a Lagos seke yanzu”.

Wasu daga cikin kayan ta fitar ta fara amfani dasu a ranta tana hasaso haduwarsu da Malam Bash dan tasan yau kam se tafi jiya Armashi. Kafin ta gama an kira sallar Azahar dan haka tayi alwala tayi sallar sannan ta kwanta zuwa La’asar kafin tasan abinda zata dafa musu kuma.

Couscous tayi musu da miyar hanta ganin lokaci ya qure, setayi marinating kifin da zata gasa musu su qara dashi zuwa can anjima kafin a kwanta. Yauma batayi wasa ba gurin cin kwalliya ta daukar magana dan har tafi ta Jiya. Wasu riga da skirt ta saka na kanti Oxblood da suka kama jikinta kamar tanayin nishi zasu yage. Bata daura dankwali ba ta faka dogon baqin gashinta daya sha gyara se qanshi yake yi kafin tabi kowanne lungu da saqo na jikinta ta shafe da hadaddun turarukanta da ita kadai tasan wadanda take mixing da duk bala’in kwakwkwafin mutum baze taba cankar wane turare bane.

Abaya ta fitar Baqa tareda mayafinta ta ajiye a gefe saboda yaranta maza ne, dukda qanana ne tana takatsantsan da irin shigar da zata fita gabansu da ita. Qugin motarsa data jiyo ya sakata saurin dora abayar ta yafa qaramin veil dinta akanta tareda zura slippers din ta ta nufi waje dan ta taro su.

Bashir
Fitowarsa daga mota yayi kyakykyawan gani, Ma’un sa ce kamar wata yar budurwar Balarabiya, tundaga nesa ya fara shaqar qamshin da takeyi wanda be taba jin sa a jikin wata mace ba bayan ita. Tamasa kyau yanda tayi rolling mayafin ya zagaye kyakykyawar fuskarta tareda bayyar da gaban gashinta daya ke nan luf a kwance ya qara qawata kwalliyar tata.

kallonta yake har besan sanda wayar hannunsa ta subuceba. Yana jin yanda yaran suke zuzuta kyan da tayi amma nasa bakin kamar wanda aka sakawa qaton kwado a ka kulle ya kasa koda budeshi se idanu daya zuba mata kawai.

Qarasawa gaban sa tayi ta durqusa tareda dakko masa wayar da ya yar bata miqa masa ba se jinta yayi gaba daya ta rungumoshi, saitin kunnensa ta furta “Welcome home SH (sweet heart)”. Kamar wanda ta tsoma a ruwan qanqara haka ya daskare a gurin yana jin kamar ya shide saboda muryarta da kuma numfashinta daya sauka a cikin kunnensa. Hannunsa ta kama ta zura masa wayar kafin ta juya tabarshi da shaqar qamshinta, batayi ko taku biyar ba taji an janyota ta baya yai mata wata kyakykyawar runguma tareda sauke mata kiss a gefen wuyanta da mayafi be ida rufewa ba.

Zaro ido tayi tana riqe hannunsa, “Baban Ali a waje fa muke” ta fada ganin gogan na neman kauce hanya 😂 se a sannan ya farga dan shifa a lokacin ita kadai yake gani se kuwa yaja hannunta qii suka shige cikin gidan dan tuni yaran suka kama gaban su. Mantawa yayi da batun wata yunwa da gajiya daya kwaso suka shige dakinsa kai tsaye , ai be ida birkicewa ba seda yai arba da ainihin kwalliyar Ma’unsa tuni labari ya chanza 🏃🏽‍♀️🏃🏽‍♀️.

Basu fito ba se qarfe goman dare, Babu kowa a palour alamar yaran harsun kwanta. Ma’u da duk tayi laushi ta nemi kujera ta zauna Bashir kuwa Dining ya wuce dan se yanzu yake jinsa kamar ze fadi saboda yunwa. Ya manta sam rabonsa da abinci tun na safe. A Babban plate ya juyo dukka abincin

Please Login or Register in order to submit comment