Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

abinci nan ku diba ku ci to”.

“Wallahi Mami watarana sena sumar da matar can idan ta sake shiga harkata” ya fada yana sake hura baki. Se na ajiye Mixer hannuna na juya dakyau ina kallonsa nace

“Wace mata zaka sumar kuma Aliyu?”
“Amirah mana” ya bani amsa kai tsaye.
“Kana jina ko Aliyu, karku kuskura kuce zaku saka abinda ya faru tsakanina da mahaifinku a rai har hakan ya shafi alaqarku dashi.

Rabuwar mu qaddarah ce daga ya rigada ya tsara iya lokacin da zamu zauna kunga babu abinda ze chanza hakan, sannan tsakanin ku da matarsa babu rashin kunya dan ba ita ta raba mu ba Allah ne ya kashe auran mu.

Koda wasa karna ji dayan ku yayi mata wani abunda ba daidai ba dan idan ma kunyi a maimakon ku ce kun rama abinda akayi mun qaramun laifi zakuyi aringa cewa ni na saka ku dan haka babu ku babu sabgarta. Duk abinda kuke nema a gidan baku samu ba kuzo nan shikenan”.

“Amma ki gaya mata wallahi Mami duk randa ta qara zagar mun uwa ko tace zata dakeni kafin ta fara ni zan doketa tam” Aliyun ya sake fada kafin ya sauka daga kan freezer ya fice daga Kitchen din gaba daya. A yanda yayi maganar hatta da muryarsa se najita kamar ta Bashir idan yana cikin fushi se kawai na bishi da kallo kafin nace
“Allah ya shirya ka ya rage maka wannan zafin zuciyar” se na juya kan Jafar dake kwasar abinci nace

“Meya hadasu da matar Babanku yake cewa ze daketa?”

GIDAN BASHIR BAYAN FITAR SA
Bayana Bashir ya fita seda Amirah ta tabbatar taji tashin motarsa alamar sun tafi ta sake leqawa taga basa nan kafin ta kulle qofar ta ciki ta yanda dole se an buga zata zo ta bude.

Dakin su Aliyu ta wuce kaitsaye, A zaune ta tatar dashi da Jafar suna magana sama sama tana shiga ta kama qugu daga bakin qofa cikin isa da taqama tace
“Ku tashi ku fito, kai Jafar kaje ka share abincin da qannenku suka zubar kai kuma Aliyu ga kwanukan can a Kitchen seka shiga ka wanke”.

A tsakanin su babu wanda ya tanka mata dan ko inuwarta basu kalla ba suka ci gaba da maganar su, wata Asharvta lailayo ta aika musu da ita kafin cikin Masifa tace

“Wato ga yar iska ina muku magana kunyi mun banza ba kuna zato zan zauna kamar jaka na dafa muku abinci ne a bata guri na gyara duk kuna zaune babu me tayani? Naga da uwar ku tana nan shara wanke wanke duk ku kukeyi mata dan haka yanzu ma lazim kuyi idan kuna so kuci abinci a gidan nan”.

“Seki bari wadanda suka bata suzo su gyara miki ai kuma aike ba uwar mu bace da zamuyi miki aiki, abinci kuma daman bamu ce ki dafa mana ba dan ko kin dafa bazamu ci ba. Kuma daga yau karki sake shigowa dakin nan idan ba haka ba se kin raina kanki Allah” Aliyu ya fada yana tsatstsareta da ido kamar wani Sa’anta aikuwa tayi kansa fuuu da niyyar kwasa masa mari ya goce hannunta ya bugi katakon gado.

Sosai taji zafi dan da qarfin ta ta kai mari ta riqe hannun tana girgizawa da cije baki Jafar ya kwashe mata da dariya kuwa nan da nan ta shiga zaginsu tana cewa

“Shegu yan iska marasa mutunchi wallahi se naci ubanku yau a gidan nan naga me kwatar ku” bata daddara ba ta sake yin kansu, seda taje daf da Jafar zata kai masa Duka ya matsa da sauri kusada Aliyu daya harde hannu a qirji yana ayyana abinda zeyi mata idan ta kuskura ta tabashi, a yanda yake jin haushin ta badan wani abu ba da wallahi rufeta zasuyi su mata shegen duka dan daga shi har Jafar din masu manyan gabbai ne girmansu ya zarta shekarunsu.

Yana cikin wannan tunanin ta kuma kawowa Jafar dake mata dariya duka tana aunawa Uwarsu ashar ai kuwa ya saka mata qafa ta baya ta tafi kamar zata fadi kafin tayi gaba ji kake Qum ta buga goshi a bango da qarfin gaske kafin kace me gurin ya tashi.

Ihu ta kwalla tana shafa gurin dan ta bugu ba qarya ji tayi kamar ma har idonta buguwar, tana kuka tana zaginsu suka tsallaketa suka fice daga gidan ma gaba daya.

Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku

BONONZA; BONONZA;BONONZA;

Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K


MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI
KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
08162859027🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 62

YUSUF

Baze iya misalta irin murna da farincikin daya tsinci kansa a ciki ba jin abinda Ma'u ta fada. A sukawane ya fice daga gidan yana shiga motarsa Driver yaja suka tafi,

Tun kafin su fita daga Get din Estate dinsu Ma'u ya rangadawa Alhaji Qarami waya baya so ya bata lokaci ballantana ta dawo ta chanja magana dan yasan koda Ace abinda tayi niyyar gaya masa kenan to Juma'ar data yanke harda tagomashin bacin ran Bashir ya saka.

Sanda ya gayawa Ahaji Qarami maganar se ya zamana tsakaninsa da Yusuf din har an rasa ma wanene yafi wani murna nan take yace masa ba matsala ya gayawa mutanensa idan sun shirya gobe suje yanzu ze kira Baffan su ya sanar masa.

lafewa yayi a cikin kujerar motar yana sakin murmushi ransa fes jinsa kawai yake kamar wanda akayiwa Bushara da Aljanna tabbas ya yarda mahaqurci mawadaci kuma Allah shine meyi a sanda yaso ba'a saka shi ba kuma a hana shi.

Hajiyar ya dannawa kira dan da ita ya kamata ya fara raba wannan abin Farin cikin ringin biyu ta daga ckin kamilalliyar muryarta ta dattijai ta yi masa sallama.

"Hajiya barka da dare, Albishirinki Hajiya" Ya fada a jere
"Barka dai Babangida wane abin farin ciki ne haka ya faru da har muryarka ta gaza boyewa ko taqaddamar tikitin takarar taku ce ta qare kayi nasara?" Ta fada a sake daga jinta irin mutanen nan ne masu sakewa sosai da yaransu

Wani murmushi ya saki kamar yanagabanta kafin yace
"Wannan ai ba komai bane akan wannan albishir din Hajiya ki canka da kanki wane abu ne kike zaton ze sakani farin ciki haka?"

Shiru tayi se can tace "Asma'u, nasan dai a yanzu idan ba zancen takara ba toh sedai ita din nasan dai wadannan sune manyan burikan ka a rayuwa"

"Kin canka Hajiya yau Ma'u ta amsa da kanta ta bani damar na tura magabata na a daura mana aure wannan Juma'ar me zuwa dan haka Hajiya ki gayawa su Baba Sale idan ze yuwu gobe idan Allah ya kaimu suje, zan tura miki da Lambar Babban Yayansu se ki bashi suyi magana suji ina ne zasuje neman auran".

"Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillah, Babangida kaga abinda nake gayamaka ko? Ita rayuwa kabi ta a sannu. Duk yanda kaso da faruwar abu idan Allah be kawo shi ba haka zaka haqura. Yanzu kaga ribar haquri ko? Allah ya tabbatar da Alkahiri yasa yin na Allah ne, nayi murna nayi murna Babangida Allah yasa za'ayi damu bari na kira Kawun naka yanzu kuwa na sanar masa na tabbatar shima zeyi farin ciki da wannan Al'amari dan ko shekaran jiya dayazo seda yayi mun ciwon baki akan zancen auranka yace wasu da yawa ma basu yarda kana da aure ba ko wannan ze iya kawo maka tangarda a cikin tafiyar siyasarka" Hajiya ta fada cikin tsananin murna.

"Toh ai yanzu ciwon baki ya qare Hajiya in sha Allahu ki dai kirashi yanzun dan Allah kuyi magana a samu goben aje"

"Toh sarkin zumudi gobe ai yayi wuri ina lefinzuwa jibi haka?" Ta fada cikin tsokana, da sauri ya tare ta da cewa

"Haba Hajiya wane irin jibi kuma? Juma'a fa tace a daura aure kuma yau litinin nidai gara suje goben ayi komai. Mansur yana nan duk abinda ake da buqata a karba a hannunsa kafin na shigo"

"Toh Allah ya tabbatar mana da Alkahiri, bari na tura ayi mun magana da kawun naku nasan yanzu yana waje tunda ba'a dade da idar da sallah ba beci ace ya tafi gida ba" da haka sukayi sallama shi murna ita murna.

Ranar qaryar bacci duk iya satar sa hakayaga Yusuf ya qyale dan kwana yayi yana sallahda tasbihi na nuna godiyarsa ga Allah bisa cika masa wannan babban buri na rayuwarsa, gani yake ko Yanzu ya mutu ya samu farin cikin da ya dade yana kwadayi. Ma'u ta amsa soyayarsa ta yarda dashi a matsayin Mijin da zata aura.

Qarfe Sha biyu na washe garin ranar ta kafa tarihin da ko a hasase be taba hasko faruwarsa a rayuwarsa ba. Suna zaune gaban shugaban qasa a lokacin, tattaunawa ce me matuqar muhimmanci sukeyi saboda yana cikin kwamitin tsaro na qasa gaba daya hankalin sa rabi ne akan tattaunawar da sukeyi inda ya kasa rabin a jiran tsammanin sakamakoj neman auran da aka tafi masa.

Kunnensa maqale da Bluetooth yana sauraran duk abinda yake faruwa acan Kumo gidan Baffa Isiya saboda seda ya jaddadawa Qaninsa da aka tafi dashi akan suna zuwa ya kirashi a waya yana so yaji duk abinda akayi karma suje suce a qara lokaci akan abinda ya gaya musu.

Sanda yaji an fara karanto Siga tsakanin Baba Sale Wakilinsa da Baffa Isiya wakilin Ma'u miqewa tsaye yayi cikin tsananin mamaki haka mutanen da suke zaune tare dashi gaba daya suka saka ido suna kallonsa dan dama tuni sun lura da hankalin sa baya kan abinda sukeyi.

Besan lokacin daya sulale yayi sujjada a inda yake ba ta godiya ga Allah lokacin dayaji wani da be shaida muryarsa ba yana jaddada dauruwar aure tsakanin Yusuf Sulaiman Wunti da Asma'u Abdullahi Tukur se gani akayi hawaye suna tsere akan fuskar sa, abin dariya abin takaici fuskarsa shabe shabe yana haqaye kuma yana dariya yake gaya musu abinda ya faru, nan da nan suka hau taya shi murna dan duk wanda yasan Yusuf yasan Asma'u, kai ko mace me sunanta ya hadu da ita se taci wannan  darajar ya karramata.

Dole ya datse mitin ya fice suna ta tsokanarsa, ya ringa neman Layin Asma'u ya gagara samunta se ya mayar da Akalar kiran kan Alhaji Qarami suka hadu suna ta jimamai dan tuni Malam Kabiru ya kira ya zayyana masa dan shine ma Ummul aba'isin da suka sake fanfa Baffa Isiya akan a daura kawai to me za'a jira.

"Wato Yaya nasan halin Asma'u sarai shaqiyyar yarinya ce, wato ainihin dazu da safe ta kirani. Daga muryarta na fahimci ta kira tayi mun shaqiyancin nata ne se na yi kamar ban gane ba, tana ta wani hanya hanya ainihin danaga zata batamun lokaci kawai nace mata muna Kumo ai gashi ma har baqin sun iso ainihin idan sun tafi zan kirata alhalin a lukacin ma ina shan Shayi ne da Kubza ko shiryawa banyi ba" Bayanin da Yaya Kabiru yayi wa Alhaji Qarami kenan.

Duk yanda Yusuf yaso ya daure kasawa yayi dole ya yanki tikitin komawa Lagos na qarfe shidan yamma. baze iya ba yana buqatar ganin Ma'u a yau, ya rungumeta a jikinsa ya kirata da matarsa halalinsa aure ya bashi ita yanzu yana da dukkan wata cikakkiyar dama da iko a kanta wai dadi kashe shi shi Yusuf yau ya zama Angon Asmy.

Yana hanyar zuwa Airport Intee ta fado masa a rai, dafe kansa yayi, tun a daren jiya yaso ya shaida mata maganar auran da zeyi se gashi abubuwan sunzo a yanda babu wanda yayi zaton faruwarsu.

Lambarta ta America ya daddanna ya kira amma akace masa a kashe take, seda ya hadiye wani abu daya taso masa na bacin rai akan wannan dabi'ar ta Intee da sam bata dauke shi da qima ko mutunchi na Miji ba. Ya tabbatar da tafiya tayi wata qasar ba tareda ta nemi izininsa ba ko da yake abinda aka sabane ai, idan har ta gaya masa zataje wani guri to kudi ne bata dashi tana da buqatar ya bata.

Lambar mahaifiyarta ya nemo har ze danna ya tuna da a cikin watan nan da aka shiga akwai bikin qanwarta da suke uba daya da za'ayi a nan Nigeria zata iya yuwuwa sun taho bikin ma shine bashi da qimar da zata sanar masa seya canza akalar kiran zuwa lambarta ta Nigeria cikin Sa'a kuwa ta shiga.

Seda ta qaraci ringin ta katse ya sake kira dana dab da yankewa ta daga cikin muryar bacci tace
"Hello Sweet"
"Intee zaki taho Nigeria amma baki sanar dani ba me yasa kike..."
"Ai kaga halinka sweet qorafi qorafi baka da aikinyi kai se anyi maka laifi toh idan na gaya maka zanzo me zaka mun? Bana son takura ne nasan ina gaya maka zakazo ka fara damun mutum da jarabarka shiyasa ma ban neme kaba" Intee tayi saurin katse shi.

Shiru kawai yayi yana jinta, to meye ma baqo a cikin halinta ne wai shekara bakwai ai sun zama jiki sedai ya mata fatan shiriya idan tana da rabo, tunowa da abinda yasa ya kirata ya saka shi sakin wani murmushi a idonsa yana hango Asmynsa yana ayyana irin Albarkatun da ze diba a jikinta dan ko ba'a fada ba daga kallo kasan Asmy irin matan da Allah ya wadata su da komai ne ma'ana kyau na zahiri dana badini wanda ya same su sedai yai ta sujjada yana godewa Allah.

"Se mutum yayi magana ka fara fushi kuma, to jiya fa nazo ban taho da Asmy bane shi yasa ban kiraka ba kuma kaga hidimar biki zamu fara saura sati daya ina da buqatar na samu hutu saboda kwalliyata tayi kyau" Intee ta fada cikin shagwaba.

"Ba fushi nayi ba ai bakya laifi Yammata ya kamata kam ki huta kiyi kyau sosai kinji, dama ina so na gaya miki ne kin tuna maganar da mukayi kwanaki ko?"

"Wacce magana kasan nifa ban fita riqe abubuwa marasa muhimmanci da basu shafe ni ba"

"Hakane, toh maganar aure na da nayi miki" ya fada bayan daya ja numfashi yana jinjina halin matarsa a ransa

"Oh wai wannan maganar to ai tun lokacin ni na gaya maka bani da matsala da wannan kawai dai ka tabbata idan ka tashi auran ka samu classy mace wadda idan aka nunata aka ce mijin mu daya da ita bazan ji kunya ba kuma zata kulamu  dakai dakayu sosai shine kawai ni damuwata"

"Intee kina sona kuwa?" Ya fada cikin tsananin mamakinta saboda be yarda ba duk sanda take gaya masa gashi yanzu ta sake maimaita wa anya yarinyar nan tasan abinda take yi ma kuwa

"Ina sonka mana Sweet me yasa kake tambaya?" Ta fada ba tareda damuwar komai ba.

"Babu komai, kin tuna Asma'u? Takwarar Asmy wadda kika kaita gurinta a Lagos?"

"Uhm bazan iya tunata ba saboda bata da ajin da zan tsaya na kalleta har na gane kamanninta" ta fada a yatsine. Murmushi yayi me sauti kafin yace

"Koh? Toh ita zan aura ko nace miki ita na aura dan yau akaje tambayar mun auranta se kawai aka daura auran gaba daya"

"Haka iyayenta suka gaji da ita lalai me yasa Nigerians kwata kwata basu da lissafi ne se kace ana neman kai da ita da kyanta da komai daga zuwa tambayar auranta kamar wata tsohuwa za'a bada ita babu jan aji gaskiya an cuceta wallahi" Intee ta fada ranta a sake babu alamar wai Mijinta ne yace mata ya qara aure balle abin ya dadata da qasa.

Dariya Ya fashe da ita jin wai babu jan aji babu komai aka bada ita cikin sigar tsokana yace mata

"Toh ai abin daga ni ne, idan kin manta na tuna miki kema fa kina ganina kika rikice kika cewa Dady idan bani ba se kin fada rijiya haka babu jan ajin babu komai aka bani ke toh itama yanzu kin gani aka bani ita"

"Koma dai mene ne zan koma bacci na, da kasan wannan maganar cema da text kayi mun kawai, Allah ya sanya Alkahiri ka gayawa Amarya ta kulamun dakai sosai, Ina sonka se anjima" tana hama fadar haka ta kashe wayar.

Murmushi ya ringa saki wato ta kowanne bangaren Intee babu abinda ya shafeta ita kanta kawai ta sani, tayi wanka tayi kwalliya yau tana wannN qasa gobe tana waccen shikenan abinda ta saka a gaba babu zancen wasu haqqoqin aure ballantana har ta zauna tana kishinsa to Allah ya kyauta.

Harya shiga jirgi yana ci gaba da gwada Layin Ma'u yanzu ko yana shiga dagawa ne batayi, jikinsa yaji yayi sanyi duk karsashin da ya taho dashi yayi qasa besan wace tarba ze samu a gurinta ba. Da amincewarta aka daura auran nan ko kuwa itama shammatarta akayi irin yanda abun yazo masa?

To koma dai yaya ne aure ya dauru ba saki ba yaji duk abinda zatayi sedai tayi amma ko duniya zata taru bega ubanda ze iya kashe auran nan ba.

Yana sauka a Lagos kai tsaye gidanta ya wuce dan daman Driver sa na Aiport yana jiransa. Tundaga qofar gidan yana iya jiyo hayaniya daga ciki sedai baya gane abinda ake cewa, kwankwasawa ya shigayi amma shiru ba'a bude ba se ya koma mota da sauri ya dakko wayarsa daya bari ya shiga kiran layinta cikin sa'a Yanzu ta daga.

BASHIR
Farkawa yayi ya ganshi akan gadon Asibiti ga ledar qarin ruwa da aka saka masa harta qare Jini ya fara tafiya, da sauri ya zareta dan shi kadai ne a dakin babu kowa, ya jura qafafunsa qasa da niyyar tashi yana yunqurawa Kansa ya sara yayi saurin komawa kan gadon yana dafe kan da hannu biyu.

"Sannu ka tashi kenan?" Wata siririyar nurse data shiga dakin ta fada cikin harshen turanci tana qarasawa kusa dashi, hannun sa ta kama ta duba taga ya cire ruwan seta mayar da hannunta kansa inda ya dafe tana cewa

"Kan yana ciwo ne? Ka kwanta tukunna na dubaka be kamata ka tashi zaune ba daman se jikinka ya qara daidaita".

Seda taje ta yaye labulen window haske ya ratso dakin abinda ya tabbatar masa da cewar safiya tayi kenan kafin ta dawo ta hau auna Bp dinsa dasu pulse duk tana yi tana rubutawa bayan ta gama ta kalle shi tace

"Har yanzu jininka be sauka ba Mr, ka kwanta bari baje na kira likita ina zuwa" ta juya zata fita. Dakyar ya bude bakinsa da yake jin kamar muryarsa ma ta tafi gaba daya yace mata

"Ina so nayi sallah"
"Kayi haquri yanzu likita zezo" taja qofa tayi waje abinta.
Kwanciya yayi kansa yana bala'in sara masa zuciyarsa kanta wani bugu take fat fat kamar zata fasa qirjinsa ta fito kai shi gaba daya ma dubiyar juya masa take, me yasa tunda ya rasa Ma'u ya rasa kwanciyar hankali a rayuwar sa ne shi.

Yana nan kwance har Nurse suka dawo tare da likita, Dattijone ya manyanta nan da nan ya rufe Bashir da fada dan sanda suka shigo ma gaba daya yayi zurfi a tunani Likitan nata yi masa magana sam be ji ba seda ya taba shi kafin yayi firgigit ya farka.

"Da girmanka da komai kake abu kamar wani qaramin yaro, ta yaya kake tunanin zaka samu lafiya bayan ana qoqarin ganin jininka ya sauka kuma kana qara saka kanka a tunani? Koma me yake damunka yanzu ai ajiye shi zakayi ka ji da lafiyar ka amma kana neman ka kashe kanka a banza da tunane tunane haha mutane ku ringa yiwa kanku fada mana".

Shidai Bashir yayi shiru har ya gama dube duben sa yacewa Nurse din ta kama shi ta kaishi qofar bandakin da yace ze shiga. A cukule yace musu ze iya, haka ya daure da bin bango ya shiga dan duk takun da yayi ji yake kamar ana kwada masa guduma a kai.

Seda yayi sallar Asubar da ta kufce masa dan lokacin kusan tara na safe kenan, yana zaune yana lazumi rabi kuma tunanin Ma'u yake da yanda zebi ya gyara kwabarsa. Amirah ce ta fado masa a rai da jaririnta yayi saurin shafa Addu'a ya miqe dakyar dan se yanzu ya tuna da batun suturar jaririn ma.

Da karfin hali da komai ya gama cike duk takaddu aka bashi gawar Babyn a Ambulance suka tafi gida dan ya rigada ya kira Limamin masallacin da suke sallah na cikin Estate dinsu.

Yanzu da a gida yake cikin yan uwansa da komai anyi shi a tsanake amma yanzu bashi me yi masa dole ya daure duk wani ciwo ya tafi yayi.

Se bayan da aka gama Jana'izar Babyn daya sakawa Muhammad Bashir kafin ya shiga gida dukda Asibiti ya kamata ya koma dan shi kadai yasan abinda yakeji a jikinsa bayan ciwon kai yanzu harda zazzabi ne yake neman kama shi.

Addah na zaune zuru a palour ya tura qofar ya shiga, da bala'in sauri ta tare shi tana cewa
"Yanzu Bashir daga fita tun jiya se yanzu zaka dawo ina Amirar? Tun jiya nake kiran wayoyinku a kashe gaba daya hankali na ya tashi har su Nafi na kira na gaya musu da tace Naziru ma ze taho a jiyan amma Babanku ya hana wai ai da babu Lafiya za'a sani
Na ganka kai kadai ina ita Amiran? Qila ma gantalinku kuka tafi kuka barni a gida kwal kamar mayya bayan kasan baqin halin yayanka ba kulani suke ba".

Kujera ya samu ya zauna dan baze iya tsayuwa ba kafin yace mata

"Tana Asibiti"
"Na shiga uku meya sameta? Badai wata matsalar bace kuma?" addah ta fada tana dafe qirji, se yai jim kafin yace mata

"Ki shirya, bari na watsa ruwa muje" ya daddafa ya qarasa dakinsa.

Da sauri Addah ta shige dakin da take ta dauko wayarta da mayafi ta dawo falo ta rafka tagumi jikinta har tsuma yakeyi. Tana nan zaune ta jiyo horn daga waje, har zata leqa sega Bashir ya fito daga dakinsa ita se sannan ma ta fahimci layi yake idan yana tafiya haka tabi bayansa suka fita bayan da yace ta kulle gidan suka hau motar sa da ya saka Samuel ya dauko suka koma Asibitin.

Sun tarar da Amirah na zaune suna yar hira da matar da take dayaj gadon da yake dakin da take. Tana ganin su ta takwarkwashe fuska ta saka kuka Addah tayi kanta da saurin gaske taba tambayar lafiya musamman da bataga cikin Amiran ba se wara ido take gefe da gefe tana neman jinjiri.

Bashir kuwa yana ganin ta fara kukan ya juya ya fice, bashi da buqatar qarin damuwa a yanzu. Dakin da aka kwantar dashi dazu ya koma, yana shiga suka ci karo da Likitan nan ya kuwa rufeshi da fada kamar ze kai masa bugu akan ina ya tafi? Wama ya bashi izinin tashi daga gadon da har ze kama hanya ya tafi wani guri.

Shidai haka ya koma ya kwanta, seda ya karya da Abincin Asibitin da sam babu dandano ko kadan kafin aka masa Allurai harda me saka bacci nan da nan kuwa yayi awon gaba dashi.

Qarfe Biyar na yamma aka basu sallama daga shi har Amiran dan babu abinda yake damunta sedai ta koma gida kuma ta cigaba da jego Allah ya bada rayayye a gaba.

Musa abokinsa daya biya duba shi bayan sun tashi daga aiki ne ya roqa daya kaishi gida saboda gujewa surutuan Addah da suka hau motar sa Samuel ya kaisu gida

tun data samu labarin mutuwar Jaririn fa take kuka da hawaye yanda kasan itace ma Amiran, Gombe kuwa babu lokon da labari be isa ba acewarta dukda an saki Ma'u baqin Asirin da tayiwa Amirah na karta haihu a gidan be karye ba ai kuwa duk inda zata shiga se taje ta nemo makarinsa sedai baqin ciki ya kashe ta amma Amirah seta haifi Yaya a gidan Bashir.

Suna shiga gidan ya wuce dakinsa, wayarsa da

Please Login or Register in order to submit comment