Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gida na ba ta gama aure na" Bashir ya fada kamar ze fashe da kuka.

"Kace ka saki Ma'u harta gama Iddah Bashir" Bala ya tambaye shi da son tabbatar da daidai yaji ko kuwa kunnensa ne yajiyo masa abinda ya dade yana fatan faruwarsa.

"Dagaske nake Bala na saki Ma'u saki biyu kuma tayi bari a washe garin ranar dana saketa kaga kenan iddarta ta ciki ka gayamun ya zanyi na shawo kanta ta haqura mu koma auran mu wallahi ina son matata idan na rasata zan iya mutuwa ka sani Bala" Bashir ya sake fada a matuqar raunane.

Bala kuwa seda yayi matuqar qoqari gurin danne farin cikinsa kafin ya aro damuwar qarya ya saka a muryarsa yace
"Ashsha Mutumina ya akayi haka a garin yaya? Amma dai koma yayane aikin gama ya gama yanzu sedai nemi mafita kuma ayi fatan Allah ya kiyaye na gaba.

Kana ji ko ni nasan Ma'u duk fushin da zatayi ba wani me yawa bane kasan irin son da takeyi maka, dan lokaci kawai zaka bata dakanta idan ta sakko zata nemeka ku daidaita kaima kasan duk abinda zata fada buyagine kawai amma Ma'u bazata iya rayuwa babu kaiba kowa ya shaida hakan"haka Bala ya cigaba da dorashi a keken bera har seda ya yarda kafij sukayi sallama.

Suna kashewa kuwa Bala ya daka tsalle yana cewa
"Allah na gode maka, badai kai wawa bane ka raina ni'imar da Allah yayi maka zaka gabe kurenka wallahi muje zuwa yanzu aka fara wasan Ma'u kuwa nasan bazan same ta ba amma tunda kaima ka rasa ko haka aka tashi wasa nayi nasara kuma in sha Allahu bazat taba dawo maka ba".

Allah sarki Bashir shi kuwa Sosai kalaman Balan suka kwantar masa da hankali dukda wani bangare na zuciyarsa yana so yaqi karban hakan dan a yanayin da Ma'u ta nuna tabbas yaga chanje chanje da yawa a gareta yana kuma jin gaskiya ta fada a maganganunta amma yasan so ba qarya ba, ba kuma ya zaton Ma'u zata taba tsanar sa a rayuwa ta bakin Balan zafin abinda ya mata ne ya sakata fadar duk wasu maganganu amma idan ya bata lokaci ta huce yasan zasu daidaita.

Da wannan ya lallashi kansa ya koma kan gado ya qudundune yana so ya manta maganganunta amma ya kasa ga wani irin tsoro da tashin hankali dayake shigarsa a duk sanda ya tuna kalaman ta na dazu har wani zazzabi yaji yana neman kama shi.

Anya ze iya bin shawarar Bala na ya bata lokaci harta huce dan kanta? Ya lura idan mafa fushin tayi ba kadan bane dazu fa har mari yasha, kai ina baze tsaya ya zuba ido yana kallo kwado ya masa qafa ba, a wannan gabar dole ya ajiye girman kai ya kwato Ma'u tun kafin yan iskan mazan Lagos su hure mata kunne.

Haka yaringa hada lissafi yana warwarewa, a ranar dai yanda Bashir yaga rana haka yaga dare sabanin Ma'u da ta shaqi bacci me cike da mafarkai masu dadi.

Washe gari haka ya farka kamar bugagge, ga damuwa ga rashin bacci lokaci daya gaba daya suka nuna a jikinsa seka zata yayi sati yana jinya idan ka ganshi. Amirah ma dai yau ta kama kanta, danfa jiya da daddare jijara yayi mata ta gaske akan taliyar da har daddawa ta saka mata gashi taji kifi amma loma daya Bashir yayi ya ture ya ringa surfa mata cin mutunchi wai bata iya komai ba haka yaran ko dandane basu ci ba suka gudu gidan uwarsu acan suka kwaso abinci tana kallo suka ci suka bata guri kuma haka ta share gudun sake yin wani laifin a gurinsa.

Da safiyar ma harda hawaye seda tayi da tana hada musu abin kari, doya da kwai ta soya sannan ta dafa zallar ruwa ta jefa Lipton ko arziqin kanimfari da citta be samu ba alhalin gasunan tunda ya siyo bata ko kwashe su daga kan inda ta ajiye ba bare ta zuba komai a ma'adanar sa.

Haka ta gama hada abincin nan kafin dukan su su fito, tana tsaye yaran suka fara fitowa tacewa yan biyu suzo suci, harta fara hada musu shayi Aliyu yana fitowa ya kada kansu suka tafi gidan Maminsu suka bar Amirah tsaye tana binsu da kallo tama rasa abin cewa.

Fitowar da Bashir yayi ta sakata waiwaya wa ta kalleshi, a kallo daya ta hango damuwa qarara a fuskarsa amma ina ba wanann ne a gabanta ba, yana zama a Dining din ta dira masa qorafin sunqi cin abinci Aliyu ya jasu sun fita ita dai ya kirasu dan bazata hana kanta bacci tasha wahalar banza ba sannan suqi ci in kuwa ba haka ba zata ajiye musu daga yau har gobe se sun cinye sannan zata sake yin wani girkin.

Bashir daya gaji da jinta, ga damuwar da take kansa ga ta surutun data tsaya masa akai tanayi ya ture plate din data saka masa doyar ya tashi dan daman sam cin yunwa kawai zeyibawai dab ta masa irin yanda Ma'u takeyi ba, jiya beci abincin dare ba, ya fita ya nema ya ga babu motar Ma'u a waje abinda ya kaishi gidan kenan yana tsaye se gata ta dawo yayi wannan mummunan ganin haka ya kwana da yunwarsa gashi yanzu kuma tasa abincin ya fita daga ransa saboda qorafi.

"Yanzu Yaya ina maka magana shine kaima zaka ture ka tashi ni me aka mayar dani a gidan nan ne a tilastani nayi girki sannan aqi ci wallahi bazata sabu ba ba kuma zan iya ba" Amirah ta fada tana shan gabansa.

"Amirah ki rabu dani, ki kuma kama kanki a cikin gidan nan idan ba haka ba zaki ja nayi miki abinda zaki zo kina dana sani tunda duk ke kika jefani a masifar danake ciki, matsa mun daga hanya na wuce" ya fada a hankali amma sautin maganar ya sakata shiga hankalin ta.

Da gani akwai abinda yake damunsa idan kuma ta matsa tasan tabbas zeyi abinda ya furta din dan haka ta matsa masa tana qunquni qasa qasa shidai ya fice ya barta a tsaye.

Yana saka qafarsa a waje idonsa suka sakeyin mummunan gani a karo na biyu, Asma'u ysaye da wani basamuden Beyerabe suna dariya ga jakarta a hannunsa ya riqe mata yana mata alamar da tayi gaba ta shiga motarsa kamar wani saurayi yazo daukar budurwarsa zasu fita ita kuma se washe baki takeyi ta shiga motar yana tsaye mutumin da besan ko waye ba yaja suka wuce Bashir daya dafe motar sa jin jiri yana neman watsar dashi a gurin.

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un, Ma'una ce nake gani a gaban motar wasu mazan daban bayan ni Allah me na tuba ka yafe mun kuskuren da nayi ban butulcewa Ni'imar ka ba wallahi sharrin zuciya da shedan ne suka ingizani" ya fada yana jin ina ma ya samu hawaye ya zubo masa ko ya samu sauqin radadin da zuciyarsa takeyi masa daga jiya zuwa yau, yana tsaye har besan sanda yara suka fito daga gidanta suka shiga mota ba seda Jafar yace masa

"Abbi mu tafi mana karmu makara" sannan ya shiga ya tafa motar, tuqi kawai yake amma ikon Allah ke tafe dasu a haka ya samu ya sauke su ya wuce aikinsa da bashi da tabbacin ze iya tsinana komai yau idan yaje

To Bashir tsautsayi da Asara Allah ya kiyaye 😂😂


Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku

BONONZA; BONONZA;BONONZA;

Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K


MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI
KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
08162859027🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 46

ASMA’U
Bacci nasha sosai abuna se Asuba na farka zuciyata wasai kamar wadda aka daukewa wani nauyi daga kanta. Yanzu babu wani sauran abu a tsakanina da Bashir, aure dai ya qare shima kuma yasan da hakan sedai muyi Addu’ar Allah yasa hakan shi yafi mana Alkahiri gaba daya.

Muna cikin karyawa da yara da tun sassafe suka zo Abokin aikina Prince Yemi ya korani, shaf na manta da yau zamuje gurin wasu mutane ne da muke nema su saka saka hannun jari a kamfanin mu seda ya kirani yake tambayar na shirya tunda wucewa zamuyi base mun biya ta office ba.

Mota ta jiya can na barota dan haka nace masa dan Allah ya biyo ya dauke ni kawai tunda muna ta Area daya ba a wani dade ba kuwa se gashi yazo.

Haka kawai ranar naji ina son yin kwalliya, kodan yanzu na tabbatar da bani da wata igiya akaina ne oho.
Straight gown na saka ta Atamfa blue datayi bala’in bin jikina amma bata kamani ba nayi dauri na a gaban goshi na yafa shantili yellow daya dace da Atamfar na kawo baqin takalmi hill da yar jaka itama baqa na saka, nayi kyau kwarai kamar wata yar late twenties idan ka ganni bazaka ce na ajiye tarin yaran da suke gabana ba.

Tare muka fito da yaran dukka sanda Yemi yazo dan nasan duk inda Bashir yake yanzu ya yi shirin fita shima. Dukda qasan zuciyata se naji kamar be dace yau ma ya sake ganina tareda wani ba amma babu yanda zanyi haka na fito, Yemi yana da faran faran da kuma tsokana, yana ganina nan da nan ya shiga tsokanata wai nayi kama da sarauniya, ya karbi jakar hannuna harda bude mun qofar mota na shiga Yara natayi mana dariyar ganin yanda abinda Yemin yakeyi, to su ina ruwansu basu dauki hakan da wani abu ba ko dan wai ace ina da aure be kamata yayi mun haka ba.

Ina kallon yanda Bashir ya bimu da kallo da yanda ya zaburo mota yabi bayan mu sedai Alah yasa tundaga gate din Estate muka rabu kowa ya kama hanyar sa. Muna tafe muna tattauna abinda zamujeyi lokacin, seda muka sake biyawa ta gidan Olivia muka dauketa tana ganina se wani washe baki takeyi ni kuwa daga gaisuwa ban sake kulata ba muka ci gaba da tattaunawar mu da Yemi.

Mun isa Guest house din mutumin da zamu je yiwa tallan, tun daga Bakin qofa zaka san me gurin ya ci ya tada kai. Harabar gidan kanta cike take da motoci na alfarma kana ganinsu kasan ba hawan su akeyi ba kawai dai an siya an ajiye saboda an rasa abinda za’ayi da kudin haka aka shigar damu wani palour me kama da reception muka zauna muna rarraba Ido dan gaba dayan mu wasu qauyawa muka zama da ganin Aljannar duniya.

Olivia kuwa da Patrick da muka tarar a can Selfie suka shiga dauka abinsu nida Yemi ne wai mukan dan kame kan mu muna kallon gurin seda muka kwashe awa biyu cif muna jira kafin aka yi mana iso gurin mutumin.

Wato wata hadaddiyar daula muka sake tararwa, palour ne qaton gaske na alfarma da fadarsa ma bata bakine kaini fitulun da aka saka ma kadai sun ishe ni kallo wallahi haka muka nemi kujeru muka zazzauna su kansu irin na yan gayun nan ne harda wani guri da ake dannan wa su koma gado ga abin tausa kai masu kudi dai sunji dadi abinsu.

Anan ma seda muka sake jiran kusan minti Ashirin har seda muka fara qosawa sannan mamallakin gidan ya fito, Farine sosai dan tsurut dashi dagani ya hada jini da fulani seka rantse dan aiki ne, badan hotonsa da yake a palour ba da bazan yarda gurinsa muka zo ba.

Cikin girmamawa muka gaishe ni ina ta mamakin wai yanzu duk wannan uwar daular ta wannan dan firit din mutumin ce, yana nan lange lange kamar baya cin abinci se kudi kamar zasu kashe ni.

Nice me bayani, haka na dage na ringa watsa masa bayanai akan muhimmancin saka hannun jarin da zeyi da kuma ribar da ze samu akan hakan, na gama bayani na tsaf yana ji se gyada kai yake kamar qadangare yana kallona, seda na qare tas na zauna Yemi ya dora da nasa se mutumin nan jin mu kawai yakeyi bece komai ba.

Gaba daya se jikin mu yayi sanyi, sosai kamfani yake da buqatarsa mun kuma saka rai da samun nasa amma da alama bayanan namu basu shige shi ba tunda gashi ya mana shiru, haka muka fara tattare takaddun mu kowa fuskarsa ta chanza yanayi, wayarsa ya dauka yayi kira ko minti biyar ba’ayi ba sega wnai mutum ya shigo daganinsa kaga Lawyer.

“Kuje dasu ayi ku kammala deal din a zuba ko nawa suka buqata babu matsala” mutumin ya fada har sannan idonsa akaina, ai kamar zamu taka rawar murna haka muka shiga zuba masa godiya yanda kasan wadanda yayiwa wata gagarumar kyauta ko da yake kyautar ya mana dan Allah kadai yasan kudin da zamu zamu akan qulla yarjejeniyar nan.

Muna shirin tafiya ya tsayar damu, PA dinsa ya kira se gashi shima da jaka ya ajiye a gabansa, da ido ya nunawa PA ya budeta se gani mukayi yana zaro rafofin daloli ya miqawa ko wannenmu daya sannan ya sake dauko complement card aka bani se kawai na karba ina juyashi a hannuna dan basan me zanyi dashi haka dai mukayi sallama muka tafi tareda Lawyer muka wuce kamfani.

Ranar cikin farin ciki na dawo gida jakata cike da daloli, a hanya na tsaya wani shopping mall na siyawa yara kaya kowa set biyu designers masu kyau nima se gani ina lissafi da dollar irin na yan gayu, seda na gama diban kayan idona ya sauka akan wasu singlet da boxers na maza, har na kai hannu na dakata zuciyata na tambayata

“Wa zaki daukarwa?”
“Allah sarki Baban Ali, da yanzu harda kai za’aci kudin nan” na fada a fili ina wucewa bangaren turaruka na dibi wanda nake amfani dasu sannan na quce gurin takalma na daukarwa Amnah wani me shegen kyau da zata hada da gown din prom din su da za’ayi wannan Juma’ar me zuwa.

Sosai na kashe kudi, niqi niqi na wuce gida da kaya ina zuwa na tarar da yaran duka suna nan muka shiga dasu ciki, plates din Abinci dana gani ya sakani cikin sigar wasa nace

“Wai ku baku iya zama a gidan mu sedai kuzo nan ku cinye mana abinci kullum toh gaskiya ya isheku haka kun mayar da Yah Amnah kuku meye amfanin Antyn ku da bazata girka muku ba”.

“Tab ai wallahi Mami bata da amfani kuwa, ni tausayin Abbi ma nakeyi kar ulcer ta kamashi dan rabon danaga yaci abinci a gidan nan tun kina nan fa” Jafar ya fada yana zaro kayan cikin ledar, ban tankashi ba, na bisu da kallo yanda suka rude suna murna kowa yana daga kayan sa se kawai na shige dakina na barsu.

A gefen gado na zauna ina tunanin meyasa Amirah bata girki? Su yara basu da matsala tunda gashi suna ci a nan amma Bashir fa me yake ci shi da sam bashida jumurin yunwa
“Ina ruwanki idan ma ruwa yake sha” zuciyata ta rayamun, sena miqe ina qoqarin cire rigata wayata dake cikin jaka ta hau qara.

Cirota nayi na duba, Number ce wata irin special Number kamar me ita ne ya zabi abarsa dakansa na dubata dakyau batayi mun kama da wadda na sani ba dan haka na mayar da wayar na ajiye dan ban fita daukar wayar da ban sani ba.

Message ne ya shigo bayan data katse an rubuta “ki daga wayar, wanda kukayi yarjejeniyar kasuwanci ne” se nayi saurin nemo Number zan kira dan a zatona Barrister dazu ne a raina ina Allah yasa ba wata matsala bace ta faru kuma dan har an karbi account Number mu a kamfani za’a saka mana kudin aikin mu na kuma gama lissafin kudin sabuwar motata zan cika dasu yanzu idan aka fasa ai mun ga bonu.

Kiran daya sake shigowa ne yasa na dakata, na daga tareda yin sallama.
Seda akaja aji kafin wanda ya kira yayi magana cikin harshen hausa yace
“Meyasa baki kira ba tun bayan da muka baki kati dazu”.

Wayar na cire daga kunnena na sake dubawa, number ce idan kuma banyi qarya ba kamar wannan dan tsamurmurin mutumin da mukaje gurinsa dazu sena mayar da wayar kunnena, cikin dari dari nace

“Bangane wa yake magana ba”.

“Oh babu laifi, sunana Ambassador Mutallab Ali” ya fada

Seda na zauna akan gadona na qara riqe wayar dakyau kafin nace

“Ranka ya dade barka da dare, ina fatan dai ba wata matsala aka samu da takaddun da muka bayar ba?”

“Aa, idan da harkar data shafi aikice ko kudi wasu ne daban suke gudanar mun da ita, wannan kuwa abune daya shafe ni ya shafi rayuwata dan haka ni da kaina zanyi shi. Ba tareda bata lokaci ba tun zuwan da kukayi dazu na ganki kuma kinyi mun a matsayin matar aure, idan kin aminci ina so na cike mata ta hudu dake amma dukka matana ba tare suke ba, kowaccen su qasar da take zama ta banbanta data yar uwarta dan haka kema zaki zbai inda kike so ki zauna ne ni bani da damuwa da hakan”.

“Ikon Allah se kallo” na fada a zuciyata, a fili kuma sena samu kaina da cewa
“Ranka ya dade kayi haquri amma ni matar aurece”.

“Asma’u kenan, baki da aure domin suffarki ta nuna kamala. Babu yanda za’ayi ki fito da irin shigarki ta yau alhalin kina da aure dukda hakan ba wani abu bane ga amma na tabbatar da ko shi mijinki baze taba bari ki saka kayan da zasu bayyanar da kyanki haka ki tafi qulla alaqar kasuwanci da wasu maza ba ko da yake bansan irin mijin da kike aure ba”.

Mamaki ne ya kamani kwarai, ya akayi ya san sunana sannan har ana iya gane macen da bata da aure daman tunda dai ni banyi kala da budurwa ba bare yace sannan daga kira ka fara zayyana mun wani zancen aure harda wasu matansa uku ni Asma’u ce zan fita daga gidan me daya na fada wa uku Allah ya mun tsari.

Kai duk ba wannan ba Allah na tuba ina ni ina wannan mutum haka firit kamar ruwan aski? Ai wallahi ko qaruna ne shi qarewar kudi yanzu dai in rabu da Namiji Kamar Bashir naje na auri wannan busashshen da na kasa tantance tsufane ya figeshi haka ko kuwa abinci ne baya ci kai qilama sickler ne kaga kuwa Bashir se yayi mun dariya dakyau.

“Kinyi shiru Asma’u baki ce komai ba” ya katse mun shirun. Dabara ce ta fado mun ta yanda zamu rabu lafiya tunda dai shi wannan ya wuce mutumin da zance zan wulaqanta ko na kora dan haka nace masa

“Tabbas ranka ya dade mun rabu da mijina amma gaba daya be wuce sati biyu da faruwar hakan bama kaga ban gama iddah ba yanzu baze yuwu na saurari wani namiji ba”.

“Hakane, toh babu damuwa zan jira dan na yaba kuma rabona ce ke, ki turamun da account Number dinki yanzu za’a saka miki saqo”

“Babu komai na gode Rabka ya dade na dazu daka bamu ma ya isa”

“Ni nayi niyya idan kuma baki turo ba zanyi waya har kamfanin naku yanzu su turamun daga can” ya sake fada, gaba daya maganar tasa ta gundureni, dan haka da sauri nace

“Toh shikenan zan tura maka yanzu, Nagode Allah ya qara arziqi” qit na kashe wayar ban ajiyeta ba seda na dannan masa block, na dakko katin daya bani nabi duk numbobin jiki nayi saving dan karma ya kira da wata Number na daga ban san shi bane.

“Haka kawai toni ko auran zanyi ai ba irin ka zan aura ba” na ringa mita ni kadai na shige bayi.

Ina sallar Isha su Abdallah m shigo da gudu yacemun wai nayi baquwa, seda na sallame kafin na fita wajen da hijabin jikina ina mamakin wacece wannan zata zo mana da dare haka.

Turus nayi ganin Amirah dake tsaye farar fuskar nan tayi jajir kamar ma mari tasha. Cikeda fitsara ta waiwayo tana cewa
“Wallahi kijawa Yaranki kunne dan ni ba jakar su bace da zan ringa dafa abinci su tsallake au qi ci kuka ubansu yazo yana mun fada kuma wallahi duk abinda aka mun akan su zan rama ehe”.

“Yanzu qara kika kawo ko jan kunne kika zo kiyi mun? Wai ma bana gaya miki karki sake shigowa gidan nan ba? Ina ruwana da shirgin ku mena hada dake da zaki shigomun gida kina fadamun magana.

Naga alama kin kwana biyu jikin ki be fada miki ba toh kiyi a hankali idan ba haka ba kuwa sena ladabtar dake tunda naga ke baki da hankali ba kuma ki da tunani, abinci kuwa a gidan ubansu suke ko suci ko kar suci dole ki dafa ki ajeye musu idan kuma kinqi kinsan sauran base na gaya miki ba, wuce ki fita tun ban lakada miki na jaki ba anan” na qarasa ina nuna mata qofa, nazata zata sake magana se naga ta juya tana qunquni ta fita a fili na fuskar ta

“Mara kunyar banza, ai da kin tsaya na koya miki hankali. Ku kuka (na juya kan yaran) daga yau ku ringa tsayawa a gidan ku kuna cin abinci idan baqu qoshi ba se kuzo nan ku qara kunji ko”.

“Wallahi Mami bata iya abinci ba, jiya fa data saka wani kifi a spaghetti har yanzu ina jin qayarsa a wuyana qarshe fa a bola ta juye abincin kowa yaqi ci” Jafar ya fada kafin nayi magana Faridah tayi caraf tace

“Waifa doyar da bamu ci da safe ba ta dumamawa Abbi shine ya ringa mata masifa, yanzu ma yana daki a kwance Kamar Bashida lafiya ina ga kuma yunwa yake ji, Mami ki bamu abinci mu kai masa dan Allah”.

Tsayawa nayi ina kallonta, dagaske Bashir bashida lafiya to me ya same shi? Na san dai yunwa tana iya kwantar dashi dan sam bashida jimirinta toh amma ni ina ruwana meye nawa a ciki shida ya dakko yar gwal ai seta dafa ta bashi.

Da zasu tafi Faridah da shegen naci seda ta dibar wa Bashir Friedrice da pepper chicken din da Amna tayi ga hadin kosulo abin dai ba’a magana na qara musu da zobo roba biyu sadaka nace ta kai masa.

BASHIR

Gaba daya haka ya wuni a office ya rasa me yaje masa dadi, ga damuwar rabuwarsa da Ma’u da se yanzu abin ya fara dukansa daya tabbatar da ta kufce masa se yayi da mugun gaske kafin ta sake dawowa hannunsa.

Ya rasa wa ze gayawa damuwarsa, a wannan karon be karbi shawar Bala ba gani yake kamar bazata fiddashi ba, amma wani lokacin idan ya tuna irin son da Ma’u takeyi masa se yaga kamar duk buyagin iska kawai takeyi na dan lokaci zata sakko su koma zaman su.

Wai ma shi me yayi mata ne? A iya saninsa laifi ta masa ta qi bin unarninsa kuskure daya da yayi shine daukar matakin saki a cikin fushi kuma har biyu, daya sani hutu ya bata na lokaci ya fita sabgrta har se ita da kanta ta dawo ta nemi shiri ta kuma yarda da sharadin daya bata kafin su daidaita amma yanzu ya lalata komai, ya bi rudin shedan ya rabu da Ma’unsa.

Ita wadda Shedab din yayi masa kururuwa akanta gashi nan ya dakko ta idan bada gasha shi babu abinda take yi ko iya horon yunwar da take masa aka barsu na shekara daya yasan dakyar idan bazatayi ajalinsa ba wai shi wannan wane irin bala’ine yake tun karar rayuwarsa.

Wayarsa ya dauka ya shiga neman Number Amiru qaninsa da tun ranar da zancen sakin Ma’u yaje Gombe ya kirashi dan yaji menene gaskiyar zancen ya kuma tabbatar masa da anyi daga ranar basu sake magana ba.

Ya kirashi sau ba Adadi amma Amirun baya

Please Login or Register in order to submit comment