Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dashi, haka ko a cikin gida banida labari se na Bashir yayi Bashir yace kaza ana haka muka fara shirin qualifying exam daga ita zamu shiga SS3.

Bashir ne yake tayani karatu yana ganar dani inda ya shige mun duhu, wannan kusancin da muka qara samu ya saka Shaquwa sosai ta shiga tsakaninmu dan idan na wuni ban ganshi ha har ji nakeyi kamar bani da lafiya gashi lokacin sun fara Service dan ma anan Gombe yakeyin nasa.

Banfarga cewa nayi nisa a soyayyar Bashir ba saboda ban ma san menene so ba, abu daya dana yarda Ya zama wani bangare na jikina haka ina bala’in jin haushin na ganshi yana magana da wata mace ranar haka zan wuni ina qunci.

Yaya Bilkisu ce ta fara haska mun cewa son Bashir nakeyi, nayi futu futu nace qaryane ni ba wani so kawai dai Allah ne ya hada jinin mu amma a qasan raina ina jin dama hakan ta kasance yace yana sona dana ji dadina kuwa.

Mun shiga SS3 kamar anyiwa Samari bushara da zuwa gurina sukayi mun caaa saboda yanda kyau da surata suka sake bayyana sosai, ban kuma canza hali ba ina nan ina tatawa duk wanda yace yana sona rashin mutunchi a qasan raina kuma ina cike da damuwa da takaicin me yasa shi Yaya Bashir baze ce yana sona ba se wannan banzan Balan ne ranar ya wani ce wai yana so na se kace nayi masa kalar budurwar yan shaye shaye.

Muna second term aka fara Registration na Jamb, duk su Alawiyya sunyi ni kuwa ranar da za’a kaisu siyi qin zuwa nayi nace banida lafiya, washe gari da yamma Su Yaya sun shigo gida ake hirar, Ina ji Bashir na tambayar kowa course din daya cike nayi banza dasu sanda yazo kaina har seda Junaidiyya ta tabo ni sena tura baki nace
“Ni ba zanyi ba”.

Kafe ni yayi da idanunsa masu sakani a wani irin yanayi da bansan na menene ba yace
“Me yasa bazakiyi ba?”
“Haka kawai” na fada ba tareda na kalleshi ba, se ya miqe yace na biyo shi muka fita can tsakar gida inda muke zama muna hira.

Idonsa akaina na sunkuyar da kai ina wasa da yatsun hannuna yace mun “me yasa bazakiyi Jamb ba”
“Ni babu komai kawai bana so nayi” na fada ba tareda na kalle shi ba.
“Toh aure kike so kenan?”

Sena dago da sauri na kalleshi, ganin ni yake kallo se na sauke idona ina tura baki nace
“Ni ban ce haka ba”.

“Toh idan ba aure kike so ba me yasa bazaki ci gaba da karatu ba bayan ma ko saurayin baki dashi wa zaki aura ma”.

Harara qasan ido nayi masa kafin nace “Allah ze kawo ne Idan lokacin yayi”

“Idan kuma yanzu ya kawo fa” ya fada cikin qasa da murya, se na daga kai na kalleshi.
“Allah kasa yace yana sona” na fada a raina tamkar kuwa Bashir yaji ni se ji nayi yace

“Idan kuma ni ne mijin naki fa Ma’una zaki aure ni?”

Abunku da ba kwaila tsabar murna se kawai na tashi nabar gurin da gudu ina dariya ina jinsa shima yana mun dariya abinda ba kasafai ya fiya yi ba.

Kan gado na na hau na ringa tsalle ina ihun murna, Yaya Fati Dake kwance akan Nata gadon ban sani ba ta tashi ta rufeni da fadan wane irin shirme ne zanzo ina wa mutane tsalle a gado kamar wata yarinya. Sena fada kanta ina cewa
“Tsallen murna ne Yah Fati ki barni nayi”.

“Murnar me kikeyi” ta tambayeni bayan data daga ni daga jikinta.

“Bazaki gane ba Yah Fati kawai kedai se lokaci yayi” tashi nayi na shige Toilet nayo alwala, inajinta tana cewa Allah ya shirye ni nidai na tayar na ringa jero sallolin godiya ga Allah daya sa Bashir yace yana sona.

Washe gari dakansa ya tasani a gaba mukaje nayi register Jamb, Law na ciki muka gama komai muka koma gida.

A hankali soyayyar mu ta bayyan kusan kowa yasan abinda yake tsakanina da Bashir. Da yawa gani sukeyi kawai shirme nane haka shima a bangaren Bashir lokacin daya gayawa Aliyu halin da muke ciki se yace masa

“Anya Bashir kana ganin abin nan me yuwuwane?”

“Me yasa kace haka Aliyu” Bashir din ya tambaye shi, se ya ci gaba da cewa

“Kawai gani nayi kamar akwai tazara me yawa tsakanin mu dasu, ka ture abotar mu da Abubakar wannan ba wani abu bane amma ka fahimceni da wuya kaga mace ta fito daga gidan Attajiri ta auri na qasa da ita sedai shi namiji me kudi ya auri diyar talaka, sannan idan ka dubi irin mazajen da yaran gidan su suke auri babu qaramin mutum a ciki ita kanta Ma’u a kalar da Allah yayi mata Bashir ko a gidan talauci ta fito ba matar qaramin mutum me fafutukar neman abinda ze rufawa kansa asiri irin mu bace ba”.

Shiru Bashir yayi dan tabbas Aliyun yayi gaskiya. Shidin ba dan kowa bane Babansa me rufin asiri ne kawai Ma’aikacin gwamnati me da yake dab dayin ritaya kuma ba wani babbaba kusan yanzu shi ake saka ran ya zama jigo a cikin gidan su tunda shine Namiji Babba yayar sa daya da qanne biyar,

a yanzu ne ma ya gama makaranta yake bautar qasa kafin ya fara fafutukar neman aikin yi kuma.

Amma tabbas yana son Asma’u kuma itama ya yarda tana sonsa ba kuma ya fatan ace ya rasa ta.

“Haka ne Aliyu, ka taya ni da Addu’a Allah ya zaba mana abinda yafi Alkahiri toh”

“In sha Allahu, Allah ya sadamu da akhairan mu” Aliyun ya fada.

Wannan maganar da sukayi da Aliyu seta sa ya dan fara ja baya da Ma’u musamman yanda a yanzu kullum yaje gidan ze tarar da zaratan samari yayan masu qunbar susa a manyan motoci sunzo gurin Ma’un duk da bata fitowa amma hakan se yake ganin kamar wata rana zata iya chanza ra’ayi ta zabi wani daya fishi dan haka se yayi baya da zuwa gidan.

Da yake itama suna shirin fara SSCE se bata damu ba dukda indai sun hadu se tayi masa qorafin me yasa yanzu baya zuwa gidan sosai se yace mata aiki ne ya masa yawa dan yanzu ya samu temporary aiki a wani company yana zuwa.

Cikin dan lokaci su Ma’u suka gama Jarabawar su, kamar kuma yanda Alhaji ya saba a shekarar ya kaisu gaba daya suka sauke Farali tafiyar da sukayi kusan rabi da kwatan tsarabar da tayiwo ta Bashir ce harda yan gidansu. Randa suka dawo bata jira yazo ba ta hada akwati guda ta kai masa har gida tayi sa’a ta same su gaba daya yan gidan suna nan harda Alhajinsu dan haka bata zauna ba suna gaisawa ta tafi.

Bayan tafiyarta Su Fainusa suka bude akwatin suna zaro kayan ciki, sosai mamaki ya kama su ganin uban tsarabar se Dada ta kasa haquri tana kallonsa tace “Bashir ni meke tsakanin ka da yarinyar nan haka irin wannan uwar tsaraba data kawo mana?”

Fainusa ce tayi caraf tace “Dada soyayya sukeyi, ina jin a Islamiyya ma Ma’un Bashir ake ce mata”. Se Bashir ya harareta yace “ke waya tambaye ki? Tashi a nan kona mammake ki”.

“Ikon Allah, Anya bata fi qarfinka ba Bashir kaida zaka dauko daidai”

“Daman mace tana fin qarfin namiji ne Nafi?” Alhaji Amadu ya katseta, seta girgiza kai tace

“Gani nayi Alhaji idan ka kallemu ka duba gidan data fito kar ace son zuciya ne yasa ya nemi auranta”.

“To ai Annabi ma yace ana auran mace dan Asali da kuma dukiyarta kinga in hakan yayi ma ba laifi bane ballantana nasan ma ba hakan bane, idan matarsa cea se kiga Allah ya qulla abun, kiyi masa fatan Alkahiri kawai” cewar Alhaji Amadu.

“Hakane Allah ya tabbatar da Alkahiri toh ai Asma’u yarinyar kirki ce”. Daga haka suka ci gana da hirarrakin su.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 33

ASMA’U
Mun rubuta jarabawar Jamb cikin Nasara kuma ko wannen mu ya samu isashshen makin da ze samar masa gurbin karatu a fannin daya zaba yanzu se jiran sakamakon SSCE mukeyi.

A dan tsakanin Baffa ya taramu, daman munsan maganar bazata wuce ta aure ba dan haka tun kafin ranar kowa ta fitar da zabin ranta dan dukkan mu wannan karon yan Aure ne maci gaba da karatun a can.

Da Daddare muna zaune a palour Baffa ni, Alawiyya, Yaya Fati, Yaya Bilkisu se Junaidiyya mune yan candyn Bana, cikin sakin fuskar da Baffa yake da ita a cikin iyalansa muka dan taba hira kafin ya gabatar mana da maqasudin kiran namu.

“Na kiraku ne dan naji ra’ayinku dukda dukkan ku nasan kunyi jarabawar shiga Jami’a me kuka zaba aure ko kuma Bokon za’a ci gaba?”

Seda muka kalli juna muka qara sunkuyar da kawuna kafin muka hada baki gurin cewa “dukka gaba daya muka zaba Baffa”.

Alhaji Qarami da yake gurin ne ya shiga tsokanar mu da cewa “wato gaku cinye du ko zaku ce wani dukka kuka zaba to baze yuwu ba sedai ku dauki daya” se Baffa ya katse shi yace

“Aa bana so karka takuramun yara, shiyasa bana saka iyayenku mata a cikin magana ta dan karma wata ta tilasta su fadar abinda ba ra’ayinsu ba shine kai yanzu zaka zo kana tsokanarsu ko, gasunan se su gaya maka su waye surukan naka idan yaso se ka ci gaba da bincike muga abinda hali zeyi”.

Da daddaya kowa ta fadi sunan rabin ranta, nice ta qarshe harda gyara zamana na bude baki zanyi magana Alhaji Qarami ya tare ni da cewa
“Ai ke nasani Amaryar ta Excellency ko?” (Yusuf kusan abokin Alhaji Qarami ne dukda a shekaru Alhaji Qaramin ya girme masa sosai, yaro ne a cikin manya da Allah yayi masa nasibi sosai a rayuwa, Asalinsa dan Bauchi ne kuma guri daya suke aiki da Alhaji qarami a Abuja tunda yaga Ma’u yace a duniya nan shi yaga mata haka kuwa take garashi kamar kwallo amma be sare ba kullum yana kan binta.
Yanzu haka ya shiga siyasa ne ya tsaya takarar Dan Majalissar Taraiya dan yace se ya kai har shugaban qasa in Allah ya yarda shiyasa suke kiransa da Excellency).

Lokaci daya na hade fuskata kamar ban taba murmushi ba ina kallonsa nace “Ni Bashi bane Alhaji Qarami ai na gaya masa ni ina da wanda nake so”.

“Haba Ma’u yanzu kice bakyason Yusuf duk yanda yake bala’in sonki kullum cikin hidimar ki yake yana hanyar zuwa gidan nan” Alhajin ya fada, sena tunzura baki gaba kaina a qasa nace

“To ni nace yayi mun ne ai tun ranar da ya fara zuwa na gaya masa nacin sa ne yasa kashi ci gaba da zuwan ai”.

Ze sake magana Baffa ya tare shi da cewa “ya isa Muhammadu barta ta fadi zabinta babu dole a al’amarin aure”.

Karkacewa nayi ina murmushi nace “Ni Baffa Yaya Bashir nake so”.

Se Baffa ya kalli Alhaji Qaramin da son qarin bayani, cikin takaicin qin zabar Abokinsa da banyi ba yace “Wai wannan yaron Bashir Abokin Abubakar dan gidan Alhaji Ahmad na qasan layin nan take nufi”.

“Toh toh na gane dan waje Amadu me Mota kenan toh ai babu laifi se aje a cigaba da addu’a Allah ya tabbatar mana da Alkahiri gaba daya”(Inkiyar Baban su Bashir ce saboda ya tabayin Direban Babbar mota yana saurayi tun sannan ake kiransa haka)”.

Godiya mukayi wa Baffa kafin muka fice kowa ranta qal.
“Amma Ma’u baki kyauta ba tayaya Babban Yaya ze miki magana ki musa masa” Bilkisu ta fada bayan da muka yi gaba nida ita, sena kalleta nace “kiji ki Yah Bilki da wata magana, so kike nayi shiru haka kawai a cuceni yanda yake so na auri abokin nan nasa tsaf ze iya zuga Baffa, yanzu kuwa dana fada a gabansa kinga ai nayi maganin abun”.

“Dukda haka da kin sani bari kikayi ki same shi ke dashi ki gaya masa, kuma ni wallahi nafi miki sha’awar Yusuf din ma gashi Kyakykyawa dan gaye ga Kudi”.

“Ai se kije ke ki aure shi nidai bana so” na fada ina harararta, Alawiyya data qaraso gurin mu
Tayi caraf tace “ga ma Uncle Fahad banza duk samarinta na arziqi ta rasa wa zata zaba se wannan me girman kan tsiyar da ita kadai yake yiwa murmushi a gidan nan”.

Hayayyaqo mata nayi ina cewa “Eh shidin na zaba ba’a son Fahad din saboda dan uwanku ne baza’a aureshin ba sedai haushi ya kashe ku, Nida Yaya Bashir kuwa nan gani nan Bari yan baqin ciki sedai su mutu”

“Allah ya baki haquri ni ba da wata manufa na fada ba ta Bashir” Alawiyya ta fada dan ita baiwar Allah ba ruwanta bata iya wa fitinata. Banza na musu nayi shigewata daki ban qara kula kowa ba inajinsu suna ta maimaita zancen kowa aka gayawa se yayi mita na rasa me yasa basa son Bashir.

Idan ma lissafin su bekai sauran manemana Arziqi ba ni wannan baya gaba na dan Arziqi da rashinsa duk nufine na Allah, zaka iya auran mutum yana dashi ya tsiyace ko kuma ka aure shi bashi da komai daga baya ya samu wadatar nidai kwanciyar hankali nake nema kuma a gurin wanda kake so yake son ka kadai zaka same shi.

Dan haka inason Bashir ko a bukkar kara ze ajiye ni na yarda zan rayu dashi har qarshen rayuwa indai akwai so da qauna ba matsala.

Cikin dan lokaci maganar auran mu ta taso kuma a daidai lokacin makarantu suka fara sakin Admission, Alawiyyah da daman ATBU ta saka saboda daman saurayinta dan Sarkin Bauchi ne lokacin har ina tsokanarta nace Allah yasa se ta samu Admission acan kuma yaqi auranta toh Allah ya taimaketa ta samu ga batun aure ma har an kawo kayan nagani inaso na alfarma abinka da gidan sarauta.

Ni, da Yah Fati da Yah Bilkisu harda Junaidiyya duk GSU muka cike su ukun dukka sunansu ya fito a first Batch kowa ta samu course din da take so amma ni har aka saki second batch babu sunana bayan kuma gaba daya ma makina ya fi nasu a Jamb din.

Har aka fara Registration Admission dina be fito ba qarshe har makarantar seda akaje amma wai babu sunana sukace wai sedai a sakani a yan Alfarma a bani wani course din daban nace bana so abarni kawai inda rabo badi sena sake Jamb haka kuwa akayi se Alhaji Qarami yace bazan zauna ba ko Diploma ce naje nayi kafin wata shekarar nan da nan kuwa aka samomun diploma a Computer Science na fara.

An kawo goron Yah, Fati da Yah Bilki suma anan cikin Gombe ne suka samu nasu mazajen duk yayan Babban gida nida Junaidiyya ne ba’a rigada an kawo ba ita dai anzo tambaya Dan Abuja ta samo yaron wani Minister abinda ya dakatar da kawo kudin ma wai Babansa ne yayi tafiya se qarshen watan da muke ciki zasu zo.

Ganin duk anyi maganar su amma nida Bashir shiru yasa hankali na ya fara tashi. Sau biyu ina sake masa magana bayan da aka bashi damar ya turo amma se yace na qara masa lokaci akwai abinda yake jira gashi kuma a kwanakin gaba daya ma ya janye da zuwa gidan mu musamman da Yaya Abubakar baya nan, daman shi a Kano yayi service se Allah ya taimake shi gurin suka riqeshi.

Seda muka ci sati kusan biyu Bashir yana mun wala wala har takai Baffa ya sakeyi mun akan yaji shiru saboda yana so a hada gaba daya a aikawa da gidajen mazan sa rana shiyasa yake so yasan shirin Bashir din.

Ranar dana gaji da zilliyar tasa takanas na kama hanya muka tafi gidansu tareda Alawiyya wadda da dakyar ta yarda zata rakani, muna tafiya tana zagina wai in banda asara ga Maza da suka amsa sunansu suna bina amma na nace se wani Bashir gashinan yana wulaqantani kuma tsabar rashin zuciya na dauki jiki zan je gidansu. Nidai ban kulata ba har muka shiga gidan.

Kai tsaye Dakin Dada muka shiga, da yake daman na saba zuwa gaishetan se hakan be zama wani abun mamaki na daban ba. Mun sameta tareda Yayarta wadda naji suna cewa Addah da yaranta guda biyu babbar bazata wuce shekara shida zuwa bakwai ba se qaramar itama zatayi hudu haka.

Matar nada matuqar kirki ga faran faran da Jama’a nan da nan ta shiga hidima damu musamman da taji ance budurwar Bashir ce bakinta har kunne take tambayar wacce daga ciki aka nuna mata ni.

“Wai wai zuqi masha Allah, ashe yanda Bashir yake sunkuyar dakai har ya iya zabo mace haka kai Allah ya nuna mana lokaci musha biki, sannunku sannunku” haka tayi tayi dauke wannan ajiye wannan nidai kaina yana qasa ina ta Addu’ar Allah yasa ya shigo amma har mukayi kusan minti talatin shiru bayan kuma sanda muka shigo na ga qofar dakinsa a bude alamar yana gidan.

Naziru qaramin qaninsu ne ya shigo, ya qaraso inda nake da dan gudunsa ya zauna yana gaishe ni da yake muna shiri dashi sosai, seya miqe da gudun sa yace “bari naje na gayawa Yaya ga Anty Ma’u tazo” be dade ba se gashi sun dawo tareda Bashir din muna hada ido na tabo Alawiyya nace mu tafi daman jiran da nake kenan nasan dole ai ze bimu.

Mukayi musu sallama bayan mun ajiyewa Dada ledar dana zubo turarukan fesawa dana wuta da sababbin kudi yan hamsin hamsin na dubu biyu Addah ta dauke ledar tana zuba mana godiya kamar ita aka bawa mudai muka tafi.

Seda muka danyi nisa da gidan sannan Bashir ya biyo mu, sama sama suka gaisa da Alawiyya tayi gaba ta barmu, se ya kalleni yana cewa “Jiya munyi waya amma baki gayamun zaki zo ba”

“Me yasa zan gaya maka tunda baka son mu hadu yanzu, daman zuwa nayi in gaya maka dan karka ji a gari, tunda dai ka gagara turowa zan bawa wadanda suka shirya dama. Na kuma gode da batamun lokaci da kayi da duk alqawarirrikan qaryar da kayi mun akan zamu rayu tare” ina gama fadar haka nayi gaba na barshi a tsaye ina jinsa yana kwala mun kira nayi banza dashi.

A zatona ze biyo mu amma har muka je gida babu ko sahunsa, abinda ya qara qona mun rai ya tabbatar mun dagaske kenan daman Bashir yaudarata kawai yayi ba aurena zeyi ba yasa na gama fadawa a soyayyarsa sannan yanzu ze gudu ya barni. Ranar haka na kwana ina kuka, gashi ko a waya be kirani ba, babu wanda yabi ta kaina a gidan,

Hajia Anjij cema da safe da ta ga yanda idona ya kumbura ta jani tanayi mun nasiha da nayi haquri, lokaci da yawa abinda muke so be zama lallai shine Alkahiri a gare mu ba dan haka na fawwalawa Allah, idan Bashir mijina ne se munyi aure idan kuma Allah be yi ba duk nacin mu sedai mu haqura.

BASHIR

Tun lokacin da Asma’u ta gaya masa zancen an ce ya turo gida se maganar ta rabe masa biyu, bangare daya na farin cikin ya kusa mallakar Ma’unsa se kuma daya bangaren tashin hankalin da me ze aureta?

Har yanzu bashida komai be kuma bawa wani ajiya ba, dan aikin da yakeyi dubu goma ce ake biyansa a wata wadda dawainiyat karan kansa ma ba isar sa takeyi ba ga qannensa suma da qananun buqatunsu tunda Babansu yayi ritaya, kudin garatutinsa suya har hada yake dan juyawa ana samun abinda za’ayi cefane a gidan yanzu gaba daya duk burinsu akansa suke na ya samu aiki toh ta ina kuma ze fara daddago maganar aure.

Kullum da wannan zulumin yake kwana yake tashi ya kuma rasa dawa zeyi shawara baze iya tunkarar Abubakar ba, Aliyu kuwa tun tuni daman ya gaya masa ya rabu da Asma’u dan tafi qarfinsa toh se a yanzu ya ga gaskiyar abinda yake fada din amma kuma baya jin ze iya rabuwa da ita saboda sonta ya riga yayi masa irin shigar da fitar rai ce kadai zata iya raba shi da shi wannan dalilin ya sa yake zille mata dan ganinta ma kullum qara rura wutar sonta yake a zuciyarsa sannan ya rasa ta yanda ze fahimtar da ita halin da ake ciki.

Maganar data gaya masa dazun ba qaramin tayar masa da hankali tayi ba, gaskiya bazata sabu ba. Dole ya nemi mafita dan yana ji yana gani baze iya zuba ido wani ya raba shi da Ma’u ba ya rusa duk wani tsari da mafarkin sa akanta.

Jiki a sabule ya koma cikin gidan, palour Dada ya shiga ya tarar dasu ta zazzage turarukan tana ta santinsu gaba daya ta kwashe se kwalli daya ta barwa Dadan wai ai kullum ana kawo mata na yau rabonta ne kudin ma seda ta raba biyu ta dauka, ganin yanda Bashir ya shigo kamar kazar da tasha ruwa yasa suka dakata suna kallonsa.

“Lafiya Bashir ka shigo kamar wanda aka zarewa qashi” Addan ta fada tana kallonsa, se ya ja guntuntsaki yana kallon Dada yace “Dada maganar da mukayi dake akan sunce mu tura ne, kinsan tare ake so a hada dana sauran toh shine yanzu tayi fushi har tana cewa kawai zata bawa wasu dama tunda ban shirya ba”.

“Me zanji haka magana babu dadin ji, kai yanzu Allah ya kashe ya baka shine ka tsaya salubanci da sunce ka tura din amma ba’a je ba to uwar me kake jira?” Addah ta fada tana gyara zama.

Shiru Bashir ya mata, dan shi kwata kwata baya so tana shiga sabgarsa ma, Dada ce tace
“Toh Addah kin manta har yanzu be samu aiki bane, aure ai baze yuwu ba babu abinyi dame ze riqe matar?”

“Sannu Nafi, kai Allah Nagode maka da Halin Nafi. Wane irin aiki kuma kuke magana mutumin da Allah ya kawo masa hanyar arziqi, yanzu in banda rashin tunanin irin naki har kwa tsaya kuna zancen wani aiki ga babban aiki ya samu.

Ka samu yarinya irin wannan daga babban gida tana sonka kuma iyayenta sun yarda zasu baka qarewar aiki harda gida da mota se an hada maka nasan kai dai kawai ka tura ayi magana asan dagaske kake seka gaya musu baka da aikin yin Aradu zasu samo maka tunda yarsu tana sonka.

Kai ashe Nafi kina dab da ja mana Asara kai Jama’a Allah kayi magani”.

Kallon ta kawai suke har ta gama hayagagarta, se Bashir ya miqe ya fice a ransa ya na qudurce kawai ze gayawa Alhajin su aje, idan yaso su abar maganar nasu bikin zuwa sanda Allah ze sa ya samu madafa tunda ya rarraba CV dinsa a gurare yanzu jiran tsammani kawai yake yi. Kasa zama yayi a gidan ya fice, yana so ya kira Ma’u kuma yana tsoron abinda zata sake gaya masa Allah Allah kawai Yake Alhaji ya dawo ayi wacce za’ayi kawai.

Addah kuwa ci gaba tayi da surutan ta har tana cewa Dadan idan ma maganar kudi ce se a nemo Bashi ayi komai da an gama biki abinda ya samu a tattara a biya.

“Kiji ki Addah wane irin bashi ana zaune qalau dan Allah, babu komai idan Allah ya nufa matarsa ce to se kiga Allah ya kawo hanyar da za’ayi komai cikin rufin asiri. Haka suka rabu dai Addah na sake jaddada aje ayi maganar nan kar su bari damar nan ta wuce su.

Bashir kuwa Alhajin su na dawowa da yamma ya shaida masa, ba tareda wani ja inja ba kuwa ya amince shima abinda yace Allahn daya taso da maganar ze hore yanda za’ayi komai cikin rufin asiri, tun a daren ranar ya tashi qaninsa ya aikashi gurin Baffan su Asma’u akan a basu dama zasu kawo goron gaisuwa, a take kuwa yace duk sanda suka shirya suzo, washe gari kuwa suka hadu da Qannensa guda biyu da Amininsa daya sukaje aka kai gaisuwa.

Tarba me kyau suka samu daga gurin Baffan da yayyen Ma’u biyu manya, nan da nan aka qulla magana sedai sun nemi alfarmar a qara musu lokaci akan wata shida da Baffa yace ya yanke ranar auren.

“Kasan haryanzu Alhaji be samu wani aiki na gaske ba, yar buga buga ce kawai akeyi ana dai saka ran

Please Login or Register in order to submit comment