Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

gaba da sabgogin mu. Gaba daya dai haka muka cinye weekend din ba dadi tsakanin mu Monday muka koma aiki. Office dinsa yafi kusa da makarantar yara dan haka kullum shi yake fita dasu ni kuma tunda ina rigashi tashi sena biya na debo su amma yau bayan mun fito gaba daya har Ahmad ya kama handle ze bude gaban mota ya dakatar dashu da cewa "kuje Maminku ce zata kaiku"

Sororo nayi ina kallonsa araina nace meye haka toh sukuwa yara suka dauki Murna dan dama mitarsu kullum yawanci Friends dinsu Momys dinsu ke kawo su school dalilin ma daya sa na dawo ina dakkosu ke nan dan da duk shiyake hadawa. Tafiya ta qaru haka nayita sauri gudun makara na samu na ajiyesu amma dukda haka ni seda nayi latti dan school din tana gaba da office dina innaje sena dawo baya while shi kuma yana gaba da school din dole seya wuceta zeje nasa office din.
Wuni nayi ina mamaki wato duk sati da sabon salon da ze bullo dashi? Allah dai ya kyauta.

A daddafe muka cinye satin kullum kuwa sena makara dan kafin na kaisu na juyo traffic ya fara haduwa, abun takaicin wani sa'in zamu hadu a hanya har Horn ze mun in na tsaya ajiyesu ya wuce ni abin na qona mun rai ni kuma nayi alqawarin bazan masa magana ko na tambayi dalilin dayasa yake hakan ba nasan dai duk sare sarin neman fitina ne in tanka su samu nayi dani a dangi to an dena (Dangin fulani dangin magana 😎).


Muna haka Weekend ya zagayo wannan karon ma yaransa ya diba suka fita yawonsu, abunda ya ragemun haushi ranar Saturday wuni nayi rama baccin gajiyar sati daban samu nayi ba danayi sannan Sunday fita mukayi nima da Matan layin mu dama muna haka once in a month zamu hada picnic muje beach a dan warware takaicin Namiji 😂😂 mu shaqi iskar duniya to wannan Lahadin ma can muka wuni dan a gida na fita na barsu ma muka dawo kusan lokaci daya.

Yanda Bashir ya tsume haka nima na tsume na fita a sabgarsa sam tunda haka yake da buqata ina jinsa ze raba dare yana waya da Amaryarsa har inji yana ce mata tayi haquri ta kusa dawowa kusada shi ai, wani lokacin naji haushi wani sa'in nayi mamaki kai Namiji dai a barshi kawai.
A da idan aka cemun Bashir ze sake kallon wata mace da sunan soyayya zance qarya ne amma daga sanda ya koyamun hankali ko ji nayi mace na shan Alwashi akan Namiji zan dakatar da ita dan tabbas Akan Bashir na sake yarda da akace Namiji Badan goyo bane (Inji Asma'u fa 😁).

Ranar Laraba na tashi da ciwon kai da ya saukar mun da zazzabi, ina nade akan gado har Bashir ya fita masallaci, a zaune na iyayin sallah ina idarwa na koma kan gado na nade har ya dawo ya fara shirye shiryen fita office. Dukda ya ganni akwance which is unusual hakan be saka ya tambaye ni dalili ba abinda yai matuqar qona mun rai ace har mun kai matsayin haka kamar wasu maqiya to wai duk me yayi zafi ne?

Seda ya gama shirinsa tsaf sannan ya kalleni
"Yau bazaki je aiki ba kenan? Se ki tashi ki miqasu karsu makara" yasa kai ya fice daga dakin. Wasu hawayen baqin ciki ne suka fara tsere a fuskata, idan Bashir ya gaji da zama dani gara ya fito ya fada mun yafi wannan Kisan mummuqen da yakeyimun ai, shigowar Jafar ta sakani share hawayena, ya matso kusa da ni yana cewa

"Mami mun shirya fa ko Abbi ne ze kaimu yau?" Cikin muryata da kuka ya fara dishewa nace mace
"Kuje maza ku bishi Jafar bani da lafiya"
Nan da nan fuskar yaron ta chanza zuwa tausayi yace "sorry Mami kinsha magani toh?
Bari na hado miki breakfast to Abbi baze kaiki Asibiti ba?"

Dole na qirqiro murmushin dole nace "it is not that serious Jafar Kaina ne yake ciwo nasan stress ne dana qara hutawa ze dena, maza kuje ku tafi and don't tell your brothers ku wuce Makaranta kawai Allah yai muku Albarka ya bada Ilimi me amfani" na qarasa ina dafa kansa se ya amsa da "Amin Mami Allah ya baki lafiya, Bye love you" ya mun peck a goshi ya fita da sauri dan su kansu kwana biyu ba wani gane kan Abbin suke ba.

Yana fita na miqe dakyar na tsaya bakin window ina hangensu,
Shiya gaya musu Abbi ne ze kaisu dan haka suka fita da sauri dan har ya gama Shan Tea ya fita yama kunna mota. Da ido ya bisu ganin sun jere masa a gaba, cike da baqin miskilancinsa yace " yadai kunzo kun mun layi a gaba?"

"Abbi Mami ce tace kai zaka kaimu bata da lafiya" cewar Jafar.
Seda gabansa ya fadi jin bata da lafiya dan ciwon Asma'u ba abune me sauqi ba, irin mutanen nan ce da suke dadewa basuyi ciwo ba amma in ya kwanatar dasu kamar bazasuyi ba. Harya niyyata daya koma yaji me yake damunta se wata zuciyar tace masa qila dan taja attention dinsa ne ya sakata kwanciya tace musu bata da lafiya dan Asma'u can pretend yasanta sarai dan haka ya qara gintse fuska tareda bude qofar sa ya shiga yana cewa "kuje ku ce mata tazo ta kaiku you are getting late"

"Abbi kana jifa yace bata da lafiya base ka kaimu ba tunda hanyar zaka bi" Farida ta fada dan ita yar gaba gaba ce daman, be amsata ba yai wa motarsa key ya qara gaba se suka rakashi da idanu gaba daya kamar yanda nima Mamakin sa ya nemi kashe ni a tsaye BASHIR dai shine haka? BASHIR dana sani me jarabar son yaya da tattalinsu kamar kwai, to kodai shiga tsakanin mu akayi da BASHIR ne?????https://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM

Page 3


A salube suka shigo gidan gaba daya suka zauna A palour banda Abdallah daya zarto dakin da nake, yana ganina ya wullar da school bag dinsa ya taho da gudu jikina se ya sa kuka, nasan kukan me yake Abdallah akwai son karatu indai ba ciwon gaske ba baya Missing school.

Bubbuga bayansa nake da sigar rarrashi ina qoqarin hana nawa hawayen fitowa.
“Mami kinga Abbi ya tafi ya barmu kuma Yah Jafar ya gaya masa bakida lafiya amma ya tafi” ya fada in between tears, se na jashi zuwa gefen gadon dan jin kaina yana dada sarawa ga zazzabin na sake ruruwa.

“Ka dena kuka, sauri yakeyi yana da meeting ne shiyasa”
“Mami bafa yanzu bane se 10 naji yana waya da Uncle Samuel ai”
“Abdallah bana hana ka ba, idan babba ya fada maka magana ka dena jayayya”

“Amma Mami...”
“Shiii ya isa kirawo mun Amna se na kira muku Uber ya kaiku” na katse shi dan bana son aja maganar, fita yayi ba jimawa Amna ta shigo itama fuskarta da damuwa.

“Ki dauko wayata kiyi muku order Uber bazan iya driving ba bana jin dadi” na fada mata ina kaiwa Kwance jin jiri na dibana.
“Mami ko mun tafi ma kafin muje mun makara bazaa bude mana get ba sedai kiyi waya ki fada bazamu zo ba”.
Agogo na kalla tabbas kafin a samu uber su tafi lokaci ya qure dan haka na miqa mata hannu ta bani wayar, Number da suka tanada dan wani uzuri nayi dialing dakyar ina ringing kadan suka amsa, cikin muryata dake nuna halin da nake ciki nayiwa receptionist din bayanin Bazasau samu zuwa ba bani da lafiya Abbinsu kuma yayi tafiya, fatan samun sauqi tayimun tareda cewa idan gobe ma babu me kawo ayi musu Registration na school bus tunda tana zuwa har nan estate din namu, shaf na manta da zancen ma school bus se yanzu dan haka ba bata lokaci nace tayi kawai.

Har na gama Amna na tsaye bayan na aje wayar tace “Mami in kawo miki ko tea kisha se kisha Paracetamol kafin Abbi ya dawo kuje Asibiti?”
Kai na daga mata ta fita ba dadewa se gata da try ta doro tea se toast bread da kuma paracetamol da ruwan roba. Da daddaya suka shigo suka mun sannu har sannan Amna na tsaye seda na shanye ta ballomun maganin nasha nakwanta sannan ta fita.

Koda na farka bayan Azahar na danji dadin jikina dan zazzabin ya sauka sefa ciwon kan da sauran jiri da nake ji, wanka na lallaba nayi na dauro Alwala a raina ina qara mamakin Baban Ali da haryanzu ko waya beyo yaji sun tafi ko basu tafi ba. Agunda nai sallah na zauna naji anyi knocking, izinin shigowa na bada Aliyu ya shigo da Sallama hannunsa dauke da Babban try da suka dora abinci.

“Mami kin tashi tun dazu muke leqowa kina bacci”
“Na tashi Yaya (haka nake kiransa saboda qannensa su saba) ina su Ahmad naji shiru?” Na tambaye shi
“Bacci suka kwanta bayan mun dawo daga masallaci, Maman Ruth ta shigo muka ce mata kina bacci(Maman Ruth maqociyarmu ce)”

“Lallai an samu yanda ake so bacci yanzu, me kuka dafa ne” na fada ina jawo try din gabana.

“Irish porridge Yah Amna ta miki mu kuma Rice and Beans muka ci da fish”.
Kwanon na bude faten se tururi yake da qamshi kai kace Wata babbar chef ce tayi girkin. A plate na zuba wanda zanci muna dan hira da Aliyu har na gama ya kwashe kayan ya fita se nima na fito palour dukda dauriya kawai nakeyi amma kaina yana ciwo sosai, ban idasa zama akan kujera ba wani irin jiri ya kwashe ni daga nan ban sake gane komai ba nidai na farka kawai Na ganni kwance a gadon dana tabbata na Asibiti.

BASHIR
Tunda ya bar gidan hankalinsa ya kasa kwanciya, har ya kai get din estate din ya juyo da niyar daukansu se kuma Shedaniyar zuciyar da take ingizashi ta sake yi masa fanfo. Har ya kai office yana tunanin sun taho ko basu taho ba lokaci lokaci yana duba Mirrow koda ze hango su a bayansa amma shiru harya wuce makarantar tasu. Yana shiga Office be zauna ba ya kira layin makarantar ya tambaya ko sunzo nan matar ta sanar dashi Madam ta kira ta bada excuse ai haka ya aje wayar jiki a sanyaye jin dagaske dai ashe bata da lafiyar ba lambo tayi ba kaman yanda yayi tunani, duk haka ya shiga aiki sukuku babu kuzari har sanda ya shiga Meeting kafin su shigama yana Kallon kiran Amira amma yaqi dagawa dan se yaji yana jin haushin ta ita ce ummul Aba’isin ta komai da yake faruwa ai.

Tun yana sallar Azahar da be samu yi ba se qarfe uku bayan sun fito daga dogon meeting din da suka share awoyi sunayi wayar sa take ta qara dan ya manta be sakata a silent ba, yana sallamewa wani kiran ya sake shigo wa ya zarota a fusace dan ya ayyana Amira ce kadai zata iya masa irin wannan kiran mahaukatan sedai ya cika da mamaki ganin Number Asma’u da yayi saving da MA’UNA akan screen. Be kai ga dagawa ba ta yanke kafin ya yi wani abu aka sake kira se yai saurin dannawa dan tabbas yasan ba lafiya ba.

Muryar Aliyu ce cikin kuka yake ce masa “Abbi kazo Mami ta yanke jiki ta fadi tun dazu bata motsi” ai se yaji tamkar a saka guduma an bugi kwakwalwarsa Asma’u ta fadi meya sameta? Innalillahi.

Ikon Allah ne ya kawo shi gidan kawai yana shiga ya tarar dasu a zagaye da ita suna kuka kamar wadanda aka cewa ta mutu se ya matsa da sauri ya dagota yana jijjigata “Asma’u Asma’u ya shiga kiran sunanta. Danshin da yaji a hannunsa daya tallafo qasan ta ya saka shi duba wurin Jini ya gani wanda duk basu lura ba se yanzu ai kuwa yaran suka sake rudewa da Kuka kamar me shikansa dauriya yayi ya dagata tareda cewa Amna da Aliyu su fito suje Asibitin sauran Yaran kuma yace su Shiga gidan Maman Ruth kafin su dawo dan Anty(Amaryar Ogan sa ta take flat din dake kallon nasu) ta tafi Zamfara garinsu bikin qanwarta.

Bashi da Nutsuwar da ze ja mota dan haka yau Amna da kullum yaga Asma’u ta bata driving se yayi bala’i to gashi yau ta masa rana, ita kanta jikinta rawa yake cikin ikon Allah dai suka qarasa asibitin dan basu da nisa sosai.

Emergency a ka karbe ta, bayan kusan Hour daya Dr Bolaji ya fito daga dakin da suka shiga da Asma’un. Alama yayi wa Bashir daya biyo shi office
Se ya kalli Amna da Aliyu da fuskokinsu suka kode saboda kukan da suka sha,
“Ku jirani a nan ina zuwa” ya fada tareda bin bayan Dr Bolaji.

Bayan ya nutsu a office din Dr Bolaji ya kalle shi tareda turo masa takardar daya gama rubutu.

“Strees da damuwa suka hadar mata har ya jawo jininta ya hau sosai shine kuma yai sanadiyyar fitar cikin jikinta, ga wannan kaje ka kai Pharmacy zasu baka bill na kayan da akayi amfani dasu se ka karbo wadannan magungunan kuma, Allah ya taqaita abun amma ku kiyaye faduwa irin wannan ko a gaba ze iya jawo mata Paralyze bama dai fatan hakan” Dr Bolaji ya fada cikin harsheb turanci yana maida kai ga takaddun dake gabansa, kamar kazar data sha ruwan zafi haka Bashir ya miqe ya nufi Pharmacy din dan karbo magunguna.

Sanda ya dawo ya tarar da Nurse ta fito daga dakin da Bedsheet a hannunta daya baci da jini da kuma kayan jikin Asma’u da suka kawota dasu. Tambayan ta yanda zaayi da maganin yayi tace ya shiga dasu ya ajiye zata dawo yanzu seya tura qofar dakin a hankali ya shiga.

A ciki ya tarar da Aliyu da Amna kowannensu na share hawaye nan da nan yaji shima hawaye da be zata ba sun sakko masa, shikenan ya rasa Babyn da be masan dashi ba. Allah ya dorawa Bashir jarabar son Yara a rayuwarsa, ya kance shi beqi ya haifi yara Ashirin bama in ya fadi haka Asma’u se tayi dariya tace

“Haba se kace Akuya in dai ba kuma mata hudu zakayi ba”. A lokacin ya kan ce mata ke zaki zama Akuyar kuwa kiyi ta zubo su dan kinsan nidai babu gurbin wata mace bayan ke a cikin rayuwata. ko bayan data haifi Yan biyu Asma’un taso tayi planing acewarta yaran sun isa haka amma ya fitittike yace idan tayi koda be sani ba be yafe ba dan shi yana son yaga ya tara zuri’a masu yawa kuma Alhamdulillah yanzu Allah ya hore masa yana da yanda zeyi ya kula dasu, yasan bazatayi ba shi yasa dadewar da tayi bayan Yan biyu be dame shi ba yasan daga Allah ne bayan haka dama ance in shekaru suka fara ja haihuwar na ja baya ita ma kuma Asma’un na kusan shekaru 33 ne yanzu.

A hankali ya ajiye ledar kan drawer dan Nurse tace karsuyi motsi me girma daze farkar da ita ya qarasa gefen gadon yana kallonta tayi wani fresh tana bacci kaman bame ciwo ba se ya rankwafa kanta tareda kissing goshinta, under his breath yace “get well soon my Ma’u, I’m sorry for hurting you”.

Zaman kurame sukayi shida yaran kowa na tunanin abinda ya dame shi basu Ankara ba se jin kiran sallar Magriba sukayi se a sannan ya tuna ai ko La’asar beyi ba. Shida Aliyu suka tafi masallaci har suka dawo kuma bata farka ba dan haka cikin damuwa ya koma gurin likita yana gaya masa.

“Babu damuwa mun mata Alluran bacci ne dan ta samu ta huta sosai jinin ya sauka zata farka amma se zuwa cikin dare, kaje kawai kayi settling bills babu buqatan me jinya Nurses din mu zasu kula da ita”.
Jiki a sabule ya koma dakin, Gurin da Su Aliyu suke ya kalla yace su tashi su tafi gida

“Abbi ni zan kwana a nan” cewar Amna
“Aa baa barin me jinya mu tafi da safe kafin ku tafi school se mu biyo ku dubata”. Dakyar suka tafi har shi kansa ji yake kaman ya sake zama sedai tuna sun bar sauran yaran yasa dole suka tafi bayan ya biya kudin duk abinda ya kamata ace ya biya din.

ASMA’U
Basufi awa uku da tafiya ba na bude ido lokacin qarfe tara na dare harta dan gota, jinina yana da qarfi sosai ba kasafai Allurar bacci take daukata na dade ba. Sakayau na tashi kaman an zare mun qaya dukda bansan ainihin abinda ya same ni ba amma babu ciwon kan babu jiri se kawai kasala da nake ji da kuma bakina da sam ba dadi. Ina qoqarin miqewa Nurse ta shigo tana ganina ido biyu ta fada da fara’a tana cewa “Sannu patient har kin farka lallai kina da qarfin jini muda muke tunanin se kin kai gobe ma”

“Murmushin na mayar mata cikin muryar marasa lafiya nace “gashi har na tashi kam amma naji dadin jikin ma sosai ai”

“Karki tashi Bari na sake duba Bp na gani” ta fada ganin ina qoqarin miqewa daga gadon, zama na koma nayi ita kuma ta dauko Abun auna BP, seda ta gama ta kalleni still tana murmushin tace “kinga kuwa yayi normal bari na hada miki ruwa to ki wanke jikinki dukda naga bakiyi staining bama se kici abinci”

Kallon rashin fahimta na bita dashi fahimtar haka ya sakata Dafani tace “I’m sorry kin samu miscarriage saboda faduwan da kikayi”

“Miscarriage kuma? Cikine dani daman?”
“Eh almost 3 months ma baki sani ba?” Ta jefin tata tambayan, se lokacin na gane a fili nayi magana. Sena qaqalo murmushin dole to ban ma san me zance ba dadi zanji ko rashin dadi ma oho nan ta barni ta shiga toilet din, mintina kadan ta fito bayan ta tara mun ruwan. Ita ta rakani har toilet din kafin ta baroni na fara wankan.

Sosai naji dadin ruwan bayan na gama nayi brush da sabon tooth brush din data ajiye mun na saka pant da pad da duk a nan na gansu sannan na daura sabon towel babba na rufo kaina da qarami na fito ina jina wata sakayau a raina ina yaba tsarin Asibitin komai nasu tsaf kamar A Turai.

Turus na tsaya kofar toilet din ganin Mutum a zaune bakin gadon dana tashi wanda da alama an kuma chanza bedsheet din kai, haka kawai na tsinci kaina da daure fuska abinda yai ma yara da safe yana dawomun se kawai na juya da niyyar komawa cikin toilet din yai zuruf ya miqe tare da biyo ni kafin na samu damar rufe qofar ya turo ta ya shigo ciki bani da zabi kawai na durqushe a qasa na fashe masa da kukan da ban san nima na menene ba.https://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS

🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Page 4

Zama yayi shima a qasan tareda janyoni jikinsa ya rungume yana bubbuga bayana a hankali, cikin qaramar murya yake cewa “I’m sorry Ma’una I’m sorry” ni kuwa kaman yana cemun ki qara volume ne. Kuka nake dagaske kukan takaicin daya dade yana shaqamun, qara tuno wasu abubuwan nake ina qarawa kukan nawa Armashi nasan Bashir baze hanani ba zebarni nayi iya yina ne a cewarsa kuka rahma ne idan yayi yawa ne yake zama matsala.

A duk sanda irin haka ta faru ko yayi mun wani abu da har takaini da zubda hawaye dama shi ba Namiji bane me bada haquri duk kuwa girman laifin da yayi zedai saurare ki da kunne duk irin mita da qorafin da zakiyi se kinci babbar Sa’a ne zece miki “Uhmm” in ta kai maqura daya san shi yake da laifi shine ze rungume ni a jikinsa nayi kukan iya yina yana bubbuga baya na har nayi shiru dan kaina to yau an Auna arziqi har na samu arziqin sorry, Miskili kenan aka ce kafi mahaukaci ban haushi.
Se ya tunamun da lokacin rasuwar mahaifin mu kamar haka ya riqeni nai kuka a jikinsa har seda naji wani kaso na radadin zuciyata ya ragu sannan ya rabu dani ya koma gurin karbar gaisuwa.

Nurse ce ta dawo dakin, sheshshekar kukana da ta jiyo daga toilet ya sakata bude kofar da sauri a zatonta ko wani abun ne ya same ni amma se ta tarar damu

“Haba Alhaji ya zaka barta tana kuka bayan kasan condition dinta please patient taso ki zo ki saka kaya a jikinki kar sanyi ya kamaki”. Fincikewa nayi daga jikinsa na fito ina ci gaba da sheqa kukana, kamar qaramar yarinya haka ina saka kayan baccin data ajiyemun ina kuka har na gama na dauki Mug din tea data hadamun na hausha ina kurba ina kuka kai abun ma abun dariya. Tsayawa tayi kawai tana kallon ikon Allah dan Bashir dai ba sabon abu bane a gurinsa indai Rigimar Ma’u ce, ganin dai dagaske nake ya saka Nurse fita ta kirawo Dr Bolaji.

Tare suka shigo, kallona yayi ya nufi inda Bashir ya tsaya wanda kallo daya zaka masa ka hango tashin hankali da damuwar da fuskar sa ta kasa boyewa, ban san me yace masa ba naga sun fita waje se Nurse din ta juyo wurinata miqa mun magunguna data ballo tana cewa “kiyi shiru kishanye tunda ya tafi se ki kwanta na mayar miki da drip din”

Shirun nayi ina jan majina da ajiyar zuciya hancina kuwa yayi jajir kamar me mura na hadiye kwayoyin tare da gyara kwanciyata raina Fes, a zuciyata nace “Wallahi kadan ka gani yanda zanyi kwanan Asibiti dalilinka kaima bazaka runtsa da dadi ba, ko minti goma ban qara ba bacci ya sure ni ga gajiyar kuka ga allurar baccin data qara a ruwan ko na samu na huta.
Daga ita har Dr Bolaji daya dawo kallona kawai suke Dr yai murmushi ya nufi qofa yana cewa “This Madam na correct trouble maker”
Nurse ta saka dariya kawai tabi bayansa dan dakko abubuwan da zata buqata ita zata kwana dani.

BASHIR
Tuqi kawai yake gaba daya baa nutse ba kansa in banda sarawa babu abinda yakeyi, a duniya babu abinda yake rudashi da hargitsashi irin Asma’u. Matar nan Tasan duk wani lungu da saqo da zata shiga ta tado masa da hankali (kuji fa) in banda fitina irin tata shi yanzu ai ta lafiyarta yake yi amma yaga alama ita neman tada zaune tsayene kawai a gabanta yanzu. Yana tafiya yana jin yadda wayarsa take ta faman vibrating Daidai ya faka motar kira ya sake shigo masa, a mugun fusace ya daga dan yasan Amira ce.

Tun dazun ya gaya mata yana da uzuri idan ya gama ze kirata amma shine take zabga masa kira kamar ta na binsa bashi a qalla ta masa missed calls sunfi 100. Yana daga wayar ta fara magana cikin Son kwaikwayon salon da Asma’u take magana dashi tace

“Yayana ina ta kiranka tun dazun baka answer ba kafasan duk yau banji muryar ka ba ga baby ma yana ta misss.....” tsabar takaici be bari ta qarasa ba ya daka mata tsawar da seda cikinta ya juya sannan ya cigaba

“Ke wacce irin wawuya daqiqiyar yarinya ce, kin kirani nace in na gama abinda nake zan kira ki amma shi ne kika ci gaba da kira kamar kina bina bashi ko? Shiyasa Ma’u ta fiki dan ita bata da shishshigi da wannan mugun takurar, Stupid ki sake kiran wayata wallahi in bani na kiraki ba zakiga hukuncin da zan dauka akanki” qit ya kashe wayar.

Wani huci yake fitarwa kaman kumurci, gaba daya yaji bala’in haushinta yake ji dan itace ummul aba’insin ta komai dayake faruwa. Dukda bata shigo rayuwarsa ba da bata juya masa daddadar rayuwar da suka gino me cike da so, qauna da sadaukarwa ba shida Ma’un sa.

Yafi minti 30 a cikin motar yama rasa tunanin me zeyi se sannan yaran suka fado masa a rai ba shiri ya fito daga motar ya shiga gidan. Gaba daya suna zaune a palour sunyi zuru zuru alamun sun sha kuka sun qoshi har yan biyu basuyi bacci ba, suna ganinsa suka nufe shi gaba daya tareda sake fashe masa da sabon kuka daya sa gaba daya yaji dama shima yayi kukan ko zeji sauqin abinda yake ji a ransa.

Dakyar ya samu sukayi shiru, Amna ya tambaya sunci abinci tace Aa, dare ya rigada yayi dan 12 harta gota

Please Login or Register in order to submit comment