Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Baba ya katse ta, se ya dauki Glass dinsa na qara qarfin gani da wayar sa ya fita Anty ta zauna akan kujera tana sake tsinewa Bashir da Amirah nidai in banda aikin kuka babu abinda nakeyi.

Sanda Baba ya fita rashin ganin motar Badhir ya tabbatar masa yafita dan haka ya kirashi a waya itama seda ta kusa katsewa sannan ya daga.

“Bashir kana ina ne nazo gida baka nan” Baba ya fada bayan da Badhir ya daga wayar.

“Na dan fita ne” Bashir ya fada murya a cunkushe kamar wanda aka yiwa duren dusa.

“Idan ka dawo kazo ina son ganinka” Baban ya sake fada kafin ya kashe wayar ya koma cikin gida. A inda ya bar mu nan ya tarar damu ina ci gaba da rusa kuka Anty na faman debewa Bashir Albarka.

“Yanzu Halima a maimakon ki tausheta shine zaki zauna kina fadar maganganu kina sake daga mata hankali ko kin kyauta, ki samo mata ruwa tasha, Asma’u kiyi shiru haka, na kira Bashir din yanzu ze zo”. Baba ya fada bayan daya zauna akan kujera.

Sassauta kukan nayi na shiga jan rai ina ajiyar numfashi kamar zan shide, dakyar na dan zuqi ruwan da Anty ta bani dan jinsu nayi sun min daci a baki, na hade kai da guiwa ina ci gaba da hawayen da na kasa tsaida su, wai ni yau aka saka? Ni Bashir ya saka saboda Amirah.

Kusan mintina 30 aka buga gidan, Anty Baban ya kalla kafin ma yayi magana tace “wallahi yallabai bazan bude masa ba, ni gara ka fita can ka same shi a waje dan idan ya shigo zan iya duddura masa Ashar ma”. Se Baban ya girgiza kai kafin ya miqe yaje ya bude qofar da kansa.

Tare suka shigo da Bashir da kallo daya zaka masa kasan ba’a cikakken hayyacinaa yake ba. Idanunsa sunyi jajir sun koma ciki ga jijiyoyin kansa sun fito rudu rudu. Guri ya samu ya zauna ba tareda ya kalli ko gefen da nake ba, nima sau daya na kalle shi na mayar dakai ina ci gaba da share hawaye na dukkan mu munyi shiru se Baba ya katse shirun da cewa

“Bashir me ya hada ka da Asma’u har ta kai ga yanke irin wannan hukunci mara dadi, koda yake abinda ya faru ya faru dawo dashi bashida amfani dan haka koma menene haquri shine maganinsa dakai da ita duk kuyi haquri ka maida ita dakinta tunda da sauran zama bama se wani ya san Abinda ya faru ba”

Luguden duka qirjina ya shigayi na dago na kalli Bashir ina jiran naji amsar da ze bawa Baban, ina ma ace yace daman wasa yake yimun ba dagaske bane ba. “Daman ana saki da wasa ne” zuciyata ta raya mun, sena sun kuyar da kaina qasa ina jin wani abu me tauri ya taso ya tokaremun maqogaro daidai sanda Bashir yake cewa
“Ayi haquri kawai Baba amma ko zan maida ita ba yanzu ba, taje kawai lokacin data san muhimmanci na idan da rabo se mu koma”.

“Kai dai za’a gayawa haka Bashir kaine zaka san Muhimmancin Asma’u a lokacin da ta rigada tayi maka nisa, se kayi kuka da idon ka kayi nadamar da bazata amfane ka ba wallahi tunda baka godewa Ni’imar ubangiji ba ka shirya godewa Azabar sa” Anty ta fada cikin Masifa kamar zata rufe Bashir da duka kafin ta juyo kaina inda nake durqushe ina kuka tace

“Ke kuma kukan me zakiyi kanki aka fara sakin mace ko yaya idan wani yaqi ka da yini wani da shekara ma ze soka har zaki damu dan wani Bashir da dama can ba ajin auranki bane ya sake ki, in sha Allahu akan idonsa zakiyi auran da se ya gigita shi tashi muje” ta fincikeni muka shige dakin ta.

Bansan me suka tattauna da Baba ba ya shigo ransa a matuqar bace yana cewa “Lallai yaron nan bashida mutunchi Halima, yanzu ka saki mace da yaya shida har kana iqirarin ta bar maka gida a yau zaka kawo wata se yanzu na fuskanci kan abun daman akan ze dawo da kishiyarta nan ya saketa kenan, babu komai duk wanda ya cuci wani a cikinsu Allah ya saka mas.
kuje ki tayata ta hada kayanta zanje Management office yanzu naji yanda za’ayi su bada gidan”.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 32

Tareda Anty muka koma, Bashir na zaune a palour muka wuce dakina. Wayata dana gani ta tunamun da gida, wazan kira na gayawa wannan mummunan labarin??

“Alhaji Qarami” zuciyata ta raya mun, nan da nan na danna masa kira cikin sa’a ringing biyu ya daga yana cewa “wato a kwanakin nan dai Ma’u tana yi dani irin wannan kira akai akai haka”.

Kuka na fashe masa dashi sosai ya shiga tambayata ya akayi, dakyar na iya tsagaitawa na gaya masa cewa Bashir ya sake ni. Seda yayi salati ya sanar da ubangiji kafin yayi shiru na wani lokaci yace

“Ma’u kowa da kalar qaddarar sa a rayuwa kiyi haquri ki dauka jarabawa ce daga ubangiji idan kika jure se ki samu saka mako me kyau. Yanzu kina ina?” Alhaji Qarami ya fada cikin jimami, seda Naja sheshsheqa kafin nace

“Yace ya bani iya yau na kwashe kayana na bar masa gidan sa Yaya yanzu ina gidan kayan nake hadawa”.

“Shike nan, ki hada iya abinda ya samu, bari na kira Abubakar dan yace mun yau ze shigo nan din idan yaso ko hotel ne se ku zauna kafin gobe a duba miki gida zuwa muga yanda hali ze yi, ki dena kuka sannan karki kira kowa a gida ki gaya masa kinji ko”.

“Toh Yaya Nagode Allah ya saka da Alkahiri “ na fada kafin mukayi Sallama naci gaba da taya Anty hada kayan dan tuni ta sauke kayan wardrobe dina tsaf tana ta durasu a akwatuna. Seda muka kwashe komai dan seda muka Hada da manyan Jakunkunan Bakko da muke zubo abubuwa daga Gombe daman in na cire kayan ciki sena ninkesu na ajiye da rabon zasu min rana ashe. Har kayana na dakin Bashir seda ta kwaso komai bayan da tayi masa watsa watsa da nasa a qasa.

Da muka gama da nawa kayan dakin yaran muka koma, lokacin Bashir ya bar gidan suma muka shiga hada musu kaya kowa a akwati kafin wani lokaci mun gama Anty ta fita ta samo samari suka ringa dauka suna kaiwa gidanta.

Mun fito da akwatin qarshe kenan Yaya Abubakar ya tsaya da motarsa a qofar gidan, rabon da yazo tunda Bashir ya auri Amirah suka samu sabani sedai mu hadu dashi a gida idan naje Gombe ko muyi waya.

Kai tsaye na fada jikinsa na fashe da kukan dana samu dakyar ya tsaya mun dazu yana bubbuga baya na yace “kiyi shiru Ma’ulle abinda yake so kenan yaga gazawarki bayan shi yayi asara bake ba”.

Tare dashi muka shiga gidan Antyn muka tarar da Baba ya dawo, cikin mutun taka suka gaisa Baba ya shiga bashi haquri akan abinda ya faru kamar shi yayi laifin sannan ya gaya mana ya samu approval an bani gidan kuma harda 50% discount akan kudin hayar ma suka bayar kuma ya biya yanzu ze kira kamfani masu wankin gida suzo su gyara yanzu se muje mu ga gurin ga Key nan an bashi.

A tare muka fita gaba daya, gidan lafiyar sa qalau dan daman ba’a dade da renovating nasa ba qura kawai yayi se yana saboda babu mutane a ciki, muna tsaye ma sega kamfanin daya kira sunzo da kayan aiki cikin qasa da awa daya suka wanke gidan tas har bangwaye seda suka wanke ko ina ya dauki kyalli.

Bansani ba Ashe tunda muka shiga Yaya Abubakar ya kira Alhaji Qarami ya gaya masa maganar gidan, se ganin motar kayan furnitures nayi sunzo da saitin gado da kujera harda labulaye da carpet kamar wasu kayan Amarya nan da nan suka shiga daurawa.

Muna fito wajen gidan motar makaranta ta sauke su Aliyu, da mamaki suka tsaya suna kallon gidan Farida tace “Mami gida zamu chanza naga ana saka sabon kaya a nan”

Gaba daya kasa kallonsu nayi dan ji nayi wata sabuwar karaya tana zuwar mun, yaya zasu ji idan suka gane mun rabu da mahaifinsu? Fitowar da Yaya Abubakar yayi daga cikin gidan ta ceceni daga tambayoyinsu suka nufeshi da murna nan take na sulale na shige gidan Anty ban san Aliyu yana baya na ba seda naji ya ruqo hannuna yana cewa

“Mami meya faru, kukan me kikeyi?”
Aliyu ya wuce shekarun da zance zanyi masa wayo, kai tsaye ina hawaye nace masa “Aliyu mun rabu da Abbinku, kuje ku duba idan akwai sauran abinda ban dauko muku ba a dakin ku wan can gidan zamu koma”.

Gaba daya se yaron ya kasa magana ya tsaya yana kallona, a sanyaye ya saki hannuna ya juya ya fita daidai sanda Itama Aman ta shigo ina jinsa yace mata suje waje na raka su da ido har suka fice daga gidan.

Rayuwa kenan, dan Adam yana tafe besan abinda ze same shi a mintunan da suke gabansa ba, dazu da safe na tashi da yaqinin gyaruwar Al’amura a tsakanina da Bashir, ga labarin abin farin cikin daya same mu bansan mummunar qaddara na tafe tana shirin shafe duk wani farin ciki da nake shiryawa ba.

Shafa cikina nayi, Allah sarki shi kuma tasa qaddarar kenan baze tashi a tsakanin iyayensa ba.

Da taimakon yaran kafin sallar Magriba mun shirya gidan nan tsaf yayin da muka yiwa gidan Bashir qat dan kaida fata Anty ta kafe sena dauke duk abinda yake nawa ne a cikin gidan nan haka kuwa akayi yara suka ringa jidar kaya qananan se murna suke wai mun chanza gida.

kayan Kitchen dina tsaf Gas da qaramar Freezer da muke zuba nama kadai aka bari dan sune nasa babbar me qofa Biyu Yaya Muslim ne ya bani ita da suka tashi daga gidan su na Lagos ya koma Rivers, haka kayan amfani ko ko cokaci Anty bata bari ba harda su spices seda ta tattare.

Haka palour Kujeru da Da Tv se Dining kadai ya tsira dasu sefa gadon dakinsa dan na dakina ma da kudina na siya, wanda ya saka mun shi na cire na sakawa Farida da Amna a dakinsu dan haka masu daurin Gado na gama hada sabon Anty tasa suka hau kwanto nawa tace ko baze hadu a yau ha su kwance a ajiye gobe su dawo su hada.

Har bayan Isha muna jigilar kaya daga tsohon gida zuwa sabo, mungama tattaro komai wanda ze saku a lokacin muka saka ragowar muka barwa gobe idan Allah ya kaimu se a qarasa.

Na fito raka Yaya Abubakar ze tafi masaukinsa daidai lokacin Bashir ya dawo, tundaga waje ya fahimci aika aikar da akayiwa gidan dan ga winduna nan hanhai babu labule ana hango ciki, a sukwane ya shiga gidan, kai tsaye dakin yaran ya leqa ya kuwa yi sa’a se katakwayen gadajen su ya tarar dan mun kwashe katifun saboda bacci a zuwan gobe suma se a dakko su.

Cikin tsananin Bala’i kamar zeyi aman wuta ya tunkaro inda muke
“Ke kadai nace ki tafi bance ki daukar mun yaro ko daya ba” ya fada yana kallona.

Seda na watsa masa wani banzan kallo kafin nace
“Wannan ne kuma kayi kadan Wallahi Bashir, saki dai na saku kuma kamar yanda kace na barmaka gida kafin gobe gashi nan ka gani Allah be hanani inda zan zauna ba amma maganar yara baka isa in bar maka yarana a hannunka ba”.

Sosai rigima ta barke tsakanin mu shi yana rantsuwar sena bashi yaransa ni ma ina ta bazan bayar ba, Yaya Abubakar ne ya katse mu da cewa “Ya ishe ku haka, wane irin shirme ne zaku zo kuna neman tarawa kanku mutane a titi ga yara duk suna kallon ku akan abinda be wuce ku zauna ku sasanta ba.
Ki shiga Gida Ma’u zamuyi magana”

Sena juya ina cewa “ka gaya masa bazan bayar ba idan ya takura kuma seadi kotu ta raba mu” nayi shige wata gida.

A waje kuwa Asma’u na wuce kafin ma Abubakar ya fara magana Bashir din ya katse shi da cewa “Ka gani cikin lallama ka gaya mata ta bani yarana dan wallahi bazan bar mata su ba ballantana ta koya musu dabi’ar raini da kafiya irin tata”.

Seda Abubakar ya qare masa kallo kafin yaja qwafa, ba qaramin danne zuciyarsa yayi ba yace “Naji, zata baka amma kayi haquri kabarsu yau. Nayi maka Alqawari gobe za’a baka yayan ka”.

Shiru Bashir yayi kamar me tunani se yace “Shikenan, Amma wallahi goben idan ba’a bani ba se anyi tashin hankali”

“Babu da wanda zakayi tashin hankali Bashir dan babu wanda yake da lokacin ka, kuma kayi a hankali idan ba haka ba seka rufta kanka a inda duk ihun ka bazaka iya fitowa ba” yana gama fada masa haka ya shige motarsa ya bar Bashir da cizon yatsa.

BASHIR
Ko kusa beyi nadamar abinda ya aikata ba dan a ganinsa yayi irin abin nan na ya tauna tsakuwa dan Aya taji tsoro. A tunaninsa dole Asma’u zata bishi ta roqe shi ya maida ita dakinta, shi kuma ya qudurce se ya gama wanata son ransa tukunna ta gane muhimmancin sa sannan se ya mayar da ita. A lokacin yasan ta biyu ta yanda ko kara ya ajiye mata bazata tsallake ba.

Be damu da kwashe kayan ma da tayi ba, sema guri daya samu a palour ya dora kafa daya kan daya, a cikin kudin da yayi niyyar biya musu umara shida itan ya yi order sabon gadon da za’a saka a dakin da ta cire nata da kuma labulaye kai kujerun ma chanza su ze kawai idan yaso kayan Kitchen in Amirah tazo se ta siyo da kanta tunda shi be san abinda ake buqata ba.

Koda ya shiga dakinsa ma yaga kaya a watse be wani damu ba yasan duk cikin haushin sakin ne yasa tayi haka, se kawai ya tattare ya watsa su kan gado yayi shigewarsa Toilet yayi wanka kafin yayi shirin bacci ya zauna akan kujera da wayarsa a hannu.

Cikin sa da yayi qara ne ya tuna masa da yau fa be ci komai ba, se ya miqe ya fito palour kai tsaye ya wuce gurin Dining sedai kafin ma ya qarasa ya hango shi wayam daga teburi se kujeru, yar Show gilas din kwanukan da ta qawata gurin ma an dauke bare yasa ran samun wani guntun abinci.

Dolensa ya sake fita ya siyo abincin a waje a ransa yana cewa “Dole yarinyar nan ta dawo a satin nan dan bazan iya sintirin zuwa siyen abinci ba, yana gama ci ya ahige daki yayi kwanciyarsa abinsa.

ASMA’U
Qarfe 11 na dare ina zaune akan abin sallah tun bayan da nayi sallar Isha ban tashi ba, gaba daya hankali na yayi nisa da inda nake na yi nutso a cikin kogin tunanin abubuwan da suka faru dani tun daga haduwata da Bashir har zuwa yau daya yanke alaqar da take tsakanin mu.

Tiryen tiryen komai ya ringa dawo mun lokutan da suka kasan ce masu dadi a cikin rayuwar mu da wadanda suke aka sin haka, haduwar mu ta farko da Bashir wadda har muka qulla soyayya a tsakanin mu nake tunawa.

ASMA’U ABDULLAHI TUKUR shine cikakken sunana. Baffan mu Alhaji Abdullahi haifaffen Kumo ne ta Jahar Gombe.

Yana da matan aure guda hudu Hajia Babba da Hajia Umma rana daya aka saka musu lalle se Hajia Anjim kafin ya auro Goggon mu Maryam daga qarshe.

Ita Goggon mu yar Asalin Numan ce kuma Babanta shine limamin garin a lokacin. A yanda aka gaya mana asali ba Baffan mu Goggon zata aura ba, Baffa Sama’ila Amininsa ne saurayinta wanda har an saka musu rana cikin tsautsayi a ranar da za’a daura auran ya gamu da mummunan hatsari akan hanyar su ta zuwa Numan daga Yola wanda yayi sanadiyyar tabuwar lakar bayansa dalilin da yake kwance kenan har yau yana jinya.

A lokacin su Baffan mu sun riga su isa garin, bayan da aka samu wannan mummunan labari hankalin kowa ya tashi har aka watse daga taron daurin aure seda Baffa Sama’ila ya bar wasiyyar akan Baffan mu ya auri Maryam dan beyi zaton ze tashi ba, haka kuwa akayi se kawai gani sauran matansa sukayi yazo da Maryam da suka je bikin Amininsa a matsayin kishiyarsu babu kuma wata jayayya ko tashin hankali suka karbeta tamkar yar uwa.

Zaman gidan mu zama ne me tsafta tsakanin matan guda hudu wanda suke kishi gurin kyautatawa mijinsu da qoqarin ganin ko wacce ta zama ta gaban go shi bata hanyar cutar da yar uwarta ko tashin hankali ba.

Allah ya azurta Alhaji Abdullahi ta kowanne bangare domin ya masa arziqin Dukiya, mata da kuma Yaya saboda seda ya haifi Yara 42 inda biyu suka mutu tun kafin a haife ni yanzu haka mu 40 cif muna raye Maza 24 mata 16.
Mu 8 ne a dakin mu, maza uku mata biyar.

Zan iya cewa kusan nice mafi soyuwar ya a gurin mahaifina kodan ina da sunan mahaifiyar sane amma dai kowa ya shaida nidin yar gata ce ta gaske, Baffan mu yayi matuqar qoqari gurin bamu tarbiyya tareda hada kanmu dan bamu san wani abu wai shi yan ubanci a gidan mu ba mun tashi tamkar tsintsiya baka taba banbance yan wannan daki dan kowa inda yake so yake warkajamin sa.

Dukda kasancewar Baffa beyi boko ba amma yayansa ya bamu damar yin ilimi iya yanda kaso kuma mata da mazan mu, baya tsawwalawa, dukda anayiwa mata auran wuri a lokacin sam shi babu ruwansa idan yayyen mu mata sun gama secondary school yana basu zabin aure ko makaranta wanda kika dauka shi zakiyi dan tun duniya na kwance Baffa yake fitar da yayansa mata qasashen waje suyi karatu, idan ma kuma kina karatun kika fitar da miji dukka ze miki auranki.

Nice ya ta Ashirin da bakwai a gidan mu, Ma’u kwalisa shine laqabin da akeyi mun a makaranta saboda yanda Allah yayi ni dason gayu abin ya hade mun da irin qirar halittar da nake da ita dan haka nake bawa gayu haqqinsa yanda ya kamata.

Tun muna SS1 na qudurce a raina nifa dana gama secondary aure zanyi duk kuwa da yanda nake da qoqari sosai a makaranta nidai kawai aure nake so abinda ze baku dariya shine ko saurayin bani dashi dan bana kulasu, ni a lokacin ma duk wanda yace yana sona tofa ya zama abokin gaba ta har tsokanata yan gidan mu sukeyi indai kana so muyi rigima dakai to ka nuna wani kace saurayi nane.

Ranar da muka fara haduwa da Bashir wata rana ce mun taso daga islamiyya da yamma, muna hanya wani da Ake kira Ibbah saurayine dan layin mu daya nace shi ala dole sona yake yi mun taho a hanya kawai ya tare mu.

Ibbah girman Ingila ne acan aka haife su dan basufi shekara biyar da dawowa Nigeria ba dan haka gaba daya dabi’unsa na turawa ne abinda yasa nake qara tsanarsa kenan muna tafe muna hirar mu se ganin sa kawai mukayi a gaban mu ya kalleni yana murmushi yace “Hey pretty yau na kamaki bazaki gudu ba, tsaki nayi masa na murguda baki kafin na kauce ina cewa

“Aikin banza mutum kamar maye yayi ta bin mutane, se kayi tayi ai dan wahala” nayi gaba abina se ji nayi caraf ya riqomun hannu banyi wata wata ba kuwa na kwashe shi da mari kafin na hau zazzaga masa tsiwa ina zaginsa.

Tahowar da Yaya Abubakar din gidan mu da Abokanan sa uku yasa na dakata ina hararar Ibbah dayayi mutuwar tsaye yana kallona, Yayan ne ya tambayi meya faru Alawiyya tayi caraf tace masa “Ma’uce ta Mari Ibbah saurayinta” tun kafin ta gama na juya kanta da masifa ina cewa

“Ta ina ya zama saurayina wallahi karki sake hadani dashi niba saurayina bane” kawai na saka kuka kawai se suka samun dariya dan yanda nayi abun seka rantse wani mugun abu aka jinginani dashi.

Daya daga cikin Abokan Yaya Abubakar wanda ban sanshi ba, cikin taushin murya yace mun “waya gaya miki mekyau tana yin kuka rabu dasu ba saurayin ki bane ki share hawayenki”.

Haka kawai naji ya burgeni, na saka hannuna na goge fuskata tsaf kuwa fuu nayi gaba na barsu suna ci gaba da yi mun dariyar ina jin Yaya Abubakar na bawa Ibban haquri kafin ya taso su Alawiyya a gaba suka biyo bayana.

“Ma’u danja Ma’u rigima daga ance mutum saurayinki kawai ki kama kuka ke wai baki san kin girma ba” Bala daya daga cikin Abokan nasu ya shiga taokana tun kafin ma na bude baki Yaya Aliyu da duk yafi sauran abokan su kirki ya tareshi da cewa

“Zaka fara ko Bala, Ma’u kyaleshi yi shigewar ki gida” seda n harari Bala na murguda masa baki kafin na shige dan sam bana son Balan nan saboda yana shan Taba nasha ganinsa yanayi ni ban ma san me yasa su Yaya suke kula shi ba.

Da Daddare muna zaune a palour Baffa muna hira yanda muka saba nake bashi labarin abun da ya faru
“Wani sabon abokin Yaya Abubakar ne yace na dena kuka amma su da duk se dariya ma sukeyi mun” na fada cikin shagwabar da idan ina gaban Baffana jina nakeyi kamar wata yar jaririya zuba tabara nake son raina idan akayi sa’a Goggo na kusa ta make ni.

“Banda dai tsiwa irin ta Mamana ya zaki mari mutum kawai dan yace yana sonki, ki kiyaye kar a sake kuma gobe kuje har gida dasu Alawiyya ki bawa Ibrahim din haquri kinji ko” Baffan ya fada. Sena marairai ce nace “toh Baffa bazan kuma ba.

Washe Gari Alhamis kuwa bayan mun taso boko da yamma babu Islamiyya mukaje har gidan su Ibbah na bashi haquri, da yake yana da sauqin kai yace shi harya manta ma Maman sa se nan nan take dani wai yarinya me kyau da hausarta wata iri ta hado mana kayan dadi muka tafi muna gulmarta wai su a dole turawa.

Muna zuwa qofar gidan mu muka ci karo dasu Yaya Abubakar yau ma su na zaune, gaishe mukayi ina ta satar kallon na jiyan nan daya maida hankali yana danna waya so nake naga ko zeyi mun magana amma har muka shige gida be ko dago ya kalle mu ba.

Baki na tunzura nayi wucewata dakinmu, inajin su Alawa suna cewa nazo mu raba kayan da Maman au Ibbah ta bamu nace bana ci nayi kwanciyata ina jin haushin da ban san koma mene ne ba.

Da daddare Yaya Abu yace na dafa musu Indomie, ina gamawa na juye a flask na bawa Khadija ta kai musu ina zaune a palour Hajia Umma se gata wai naje inji Yayan yana kirana.

Suna zaune a tsakar gida daga gefen inda akayi kujeru na sumunti da tebura, su hudun dai kamar kullum ga kular Indomin a tsakiya an cinye tas Yaya Aliyu ya kalleni yana cewa “wai Bashir ne yace ne yadda ke kikayi girkin nan ba shine muka kiraki ki gaya masa da kanki”

“Wai daman Yaya Bashir kaine” na fada da mamaki ina kallon wanda aka kira da Bashir din. Se yanzu kuma nagane fuskarsa Bashir din gidan Baba me Mota ne, rabon dana ganshi har na manta tunda su ka fara zuwa Jami’a shi aka ce A Zaria ban sake ganinsa ba kusan shekara shida yanzu.

“Daman Fainusa tace Yayansu ya zama dan gayu ashe dagaske take “na fada ina zama a gefen Yaya Abubakar, se Bashir ya dago ya kalle ni yana murmushi yace “dagaske? Har nakai ki gayu?”

Rufe fuska nayi da mayafina irin naji kunyar nan, sosai na ringayi masa tambayoyi meyasa na dena ganinsa yace makaranta ce tasa saboda nisa baya zuwa gida se qarshen shekara, duk sanda yake zuwa mu kuma bama nan munyi tafiya. Haka na shantake seda Goggo ta aiko kirana sannan na tafi.

Tundaga wannan ranar kullum da daddare idan na dafa musu indomi zanje na zauna ina taya su hira kuma duk saboda Bashir dan haka kawai nake jin ina son yin magana

Please Login or Register in order to submit comment