Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana shiga ta kama qugu daga bakin qofa cikin isa da taqama tace
“Ku tashi ku fito, kai Jafar kaje ka share abincin da qannenku suka zubar kai kuma Aliyu ga kwanukan can a Kitchen seka shiga ka wanke”.

A tsakanin su babu wanda ya tanka mata dan ko inuwarta basu kalla ba suka ci gaba da maganar su, wata Asharvta lailayo ta aika musu da ita kafin cikin Masifa tace

“Wato ga yar iska ina muku magana kunyi mun banza ba kuna zato zan zauna kamar jaka na dafa muku abinci ne a bata guri na gyara duk kuna zaune babu me tayani? Naga da uwar ku tana nan shara wanke wanke duk ku kukeyi mata dan haka yanzu ma lazim kuyi idan kuna so kuci abinci a gidan nan”.

“Seki bari wadanda suka bata suzo su gyara miki ai kuma aike ba uwar mu bace da zamuyi miki aiki, abinci kuma daman bamu ce ki dafa mana ba dan ko kin dafa bazamu ci ba. Kuma daga yau karki sake shigowa dakin nan idan ba haka ba se kin raina kanki Allah” Aliyu ya fada yana tsatstsareta da ido kamar wani Sa’anta aikuwa tayi kansa fuuu da niyyar kwasa masa mari ya goce hannunta ya bugi katakon gado.

Sosai taji zafi dan da qarfin ta ta kai mari ta riqe hannun tana girgizawa da cije baki Jafar ya kwashe mata da dariya kuwa nan da nan ta shiga zaginsu tana cewa

“Shegu yan iska marasa mutunchi wallahi se naci ubanku yau a gidan nan naga me kwatar ku” bata daddara ba ta sake yin kansu, seda taje daf da Jafar zata kai masa Duka ya matsa da sauri kusada Aliyu daya harde hannu a qirji yana ayyana abinda zeyi mata idan ta kuskura ta tabashi, a yanda yake jin haushin ta badan wani abu ba da wallahi rufeta zasuyi su mata shegen duka dan daga shi har Jafar din masu manyan gabbai ne girmansu ya zarta shekarunsu.

Yana cikin wannan tunanin ta kuma kawowa Jafar dake mata dariya duka tana aunawa Uwarsu ashar ai kuwa ya saka mata qafa ta baya ta tafi kamar zata fadi kafin tayi gaba ji kake Qum ta buga goshi a bango da qarfin gaske kafin kace me gurin ya tashi.

Ihu ta kwalla tana shafa gurin dan ta bugu ba qarya ji tayi kamar ma har idonta buguwar, tana kuka tana zaginsu suka tsallaketa suka fice daga gidan ma gaba daya.

Assalamualaikum Barkanmu da wannan lokacin AUNTY ZEE TAKU CE ,Ina uwar gida Amarya da yanmata albishir gareku

BONONZA; BONONZA;BONONZA;

Nazo maku da SAHIHIN MAGANIN CIRE TUMBI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI,KINCI GAYU ANA TAMBAYARKI YAUSHE ZAKI HAIHU TUMBI YA HANAKI ADO DA KWALLIYA SHA KURUMINKI NAZO MAKI DA MAGANI CIKIN SATI DAYA ZAKI BAN LABARI ZAN DANDANA MAKU SHI AKAN RABIN KUDINSHI DAGA NAN ZUWA SATI DAYA 7K DUK ROBA DAYA KI BIYA 3500 KI MALLAKI NAKI NAN DA SATI DAYA ZAI KOMA 7K


MAGANIN BREAST WANDA ZAICIKO MAKI DA TUWON NONO DAN ALLAH KIJARABA ZAKIZO KINA GODIYA DAN DUK WADDA TA GWADA SAITA DAWO MANYAN MATA SUKE GYARA KAMAR YANDA KUKASANI 8K YAKE ZANKARA TALLATA MAKU SHI KI BIYA 4K KI MALLAKI NAKI
KI BIYA TA WANNAN ACCOUNT DIN KITURA MAN SHAIDAR BIYA
3968303018
ZAINAB SHU AIBU
FCMB
08162859027🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 44

Har Magriba Amirah na sharbar kuka kamar qaramar yarinya ga takaicin qulun da goshi ta yayi gashi har yanzu Bashir basu dawo ba ta kira shi kuma bema tsaya ya saurareta ba yace mata se ya dawo ya kashe wayarsa.

Seda akayi sallah suka shigo gidan da ledoji niqi niqi na kayan maqulashen da suka siyo.

“Kai Anty kalla wani bump a goshinki” Abdallah ya fada yana kwashewa da dariya qannensa na taya shi tayashi.

“Bari muga, faduwa kikayi a toilet? yah Aliyu ma ya taba yin haka kun tuna?” Farida ta qara tana qoqarin kai hannunta kan goshin Amirah a mugun fusace kuwa ta doketa har seda ta fadi qasa dai dai lokacin da Bashir ya shigo gidan.

“Baki da hankali me tayi miki da zaki bugeta haka idan taji ciwo fa” Bashir ya fada yana dago Farida daga qasan, se kuwa ta kwararrabe fuska tana matsa hannunta tace

“Abbi hannuna akansa na fadi” se hawaye sharr kai kace wadda ta karye ko wani abu.
A rude Bashir ya shiga duba hannun, ya jefawa Amirah mugun kallo yace

“Wallahi idan wani abu ya samu hannunta se kin gane kurenki saboda baki san zafin ta ba shine zaki tureta ta fadi uban me tayi miki”.

Itadai Amirah gaba daya ma seta kasa magana, daga shigowarsa baze tambayi ba’asi ba se ya hauta da Fada harda yi mata gorin haihuwa, tana shirin buda baki ya tare ta da cewa

“Dallah tashi ki dubo mun man zafi na saka mata, kuma wallahi koda wasa karki sake yin abinda ze taba mun lafiyar yara dan bana hada komai dasu kin sani”

Baiwar Allah haka ta tashi zugui zugui ta dakko masa se hadiyar zuciyata takeyi tana rarrashin kanta dan kartayi kuka a gaban yaran su mata dariya, haka ya shafawa Faridah man zafin ita kuwa saboda sharri se sake langwabewa takeyi ya gama ya dorata akan kujera se sannu yake yi mata, yana juya bayansa tayiwa Amirah dake tsaye tana kallon ikon Allah gwalo kafin ta koma ta noqe a cikin kujera sauran yaran suka wuce dakin su suna yi mata dariya.

Bashir kuwa dakinsa ya shige, da walwalarsa ya shigo gida amma daga dawowa har ta bata masa rai. Yana cikin cire riga ta shigo dakin, se a sannan ya kalli fuskarta yaga kumburin goshinta, ba tareda wata damuwa ba ya kalleta yace

“Meye wannan a fuskarki kuma bugewa kika yi?”

Kamar tana jira se hawaye shaaaa harda sheshsheqa tace masa
“Ba su Aliyu bane suka tadeni na fadi shine na buge goshi ita kuma Faridah suna shigowa tazo zata taba naji zafi na tureta shine ka dauka da gangan nayi”.

“Su Aliyu suka tadeki kika fadi kamar yaya? Meya hadaki dasu da har zasu tadeki?” Ya fada yana tsatstsareta da ido, kanta a qasa tana tunanin qaryar da zata shirga musu yanda idan suka dawo ze rama mata, can ta dago tace

“Kawai fa dan na sake shiga nace su fito suci abinci shikenan suka hau zagina shida Jafar, ban kulasu ba na juyo zan fito kawai Aliyu ya sakamun qafa na fadi kuma suka fice sunayi mun dariya. Yanzu dan Allah kamar ni ko babu aure tsakanina dakai ai akwai yan uwantaka ya kamata su girmamani amma ba haka ba se ma kaji irin zagin da sukayi mun ta uwa ta uba” ta qarasa tana goge majina da hannun rigarta.

Bashir kuwa sakare yayi yana ji da ganin ikon Allah, wai suka tade ta ta fadi to ai koda Aliyu da Jafa nada girman jiki ya tabbatar Amirah bazata tsaya su kada ita ba tunda itama ba kadan bace idan ma sun kayar da itan dole akwai abinda ya hado su dan haka kawai bazasu kamata da komawa ba.

“Kina ji ko? indai kina so ki zauna lafiya da yaran nan to ki kama girmanki a cikin gidan nan. Babu ruwanki da shiga shirgin Aliyu ko Jafar. Su ai ba kamar twins bane da se kin ajiye su kin zuba musu abinci ko su ci abinci ko karsu ci ba damuwarki bane abunda yake naki ki dafa musu ki ajiye idan sunji yunwa da kansu zasu fito su nema.

Bana so na sake jin wani abu makamancin haka ya faru wai kin shiga dakinsu har ta kai ku gayin rigima wani yaji ciwo, ki kiyaye”.

“Oh abinda ma zaka fada kenan, laifina ka gani yanzu bana su bama kenan? Toh wallahi bazan yarda ba, daman na bari ne ban dauki mataki ba ina jiran seka zo amma tunda bayansu kabi wallahi se jikin yara ya gaya musu a gidan nan dan babu shegen dan da ze taka ni in saka ido ina kallonsa” Amirah ta fada tana miqewa tsaye zata wuce, a fusace Bashir ya tsayar da ita yana cewa

“Na rantse da Allah kika sake kiran yarana da shegu sena chanzawa bakin ki halitta tunda ke baki da hankali ba kuma kisan abinda zaki fada ba, sannan karki fasa dukan su ni kuma babu yaron da zan tsawatarwa a gidan nan idan ya miki rashin kunya tunda abinda kika zaba kenan” fuu ya wuce daki ya barta a tsaye tana qunquni.

Tana tsaye a gurin su Aliyun suka shigo, ta waiwaya ta kalle su, badan ba wallahi seta tsinka musu maruka koma ta rufe su da duka dan gani takeyi zata iya, amma tsoron abinda Bashir ze iyayi ya sakata watsa musu harara kamar idonta ze fado suma kuwa basu bata lokaci ba suka maida mata har Aliyun yana cewa

“Da magana ne?”
Seta ja tsaki kawai ta wuce dakinta, tabbas da sake dole ta dauki matakin gaggawa tun kafin abubuwa su rin cabe mata yanda bata tsammata ba daga uban har yaran seta dauki mataki akan su ta yanda babu wanda ya isa ya sake nuna mata yatsa a cikin su.

Haka ta kwana saboda tsabar takaici ko dakin Bashir bata je ba, sanda Faridah ta shiga zata kwanta ma da masifa ta hauta yarinyar na kuka ta tafi dakin uban lokacin yana zaune yana aiki a laptop dinsa. Gobe Monday, gashi yana da ayyuka a gabansa da yake so ya qarasa dalilij da ya saka be fita ya kulata ba kenan se kawai ya cewa Faridan ta hau Gadonsa ta kwanta ya ci gaba da aikinsa yana ayyana hukuncin da ze dauka akan Amirah.

Washe gari da Asubar fari ya buga mata qofa sanda zasu wuce masallaci akan ta fito ta samar musu abin karyawa da wuri.
Har suka dawo kuwa yar gaske bata leqo ba dan daman daya tasheta yana fita ta koma baccinta dan tace ba shegen da zata yiwa girki da Asubar nan su tafasa ruwan shayi akwai komai har Buredi su sha ita bata saba wannan wahalar ba.

Sanda suka suka shigo a zatonsa ta tashi tayi sallar harta shiga Kitchen dan haka dakinsa kawai ya wuce ya tashi Faridah yace taje dakin Amirahn tayi wanka ta shirya shima ya shiga wanka.

Da dari dari Faridah ta shiga dakin se ta tarar da Amirah ta shanya baki tana bacci abinta dan haka sadaf sadaf ta shige bandakin ta rufe a hankali dan karta tasheta, har kuwa ta gama wankanta ta shirya ko motsi Amirah batayi ba, saboda neman tsokana ta kwashi turaren Amirah ta feffesa da sauri ta kwashe kayan data cire ta fella gidan Ma’u da gudu dan ita daman Uniform kadai ta dauka a kayanta komai yana dakinsu na gidan a can ta barsu.

Sanda ta je ta tarar da Amna na hada Breakfast Ma’u na wanka dan sun makara tashi da safen, tana ajiye kayanta ta wuce Kitchen takwashi dankalin da Amna take soyawa tana cewa

“Yah Amnah ki qara wani nasan yanzu yunwa zata koro su Yah Aliyu zasu zo har Abbi, bafa ta tashi daga bacci ba haryanzu Anty Amirah bare ta bamu breakfast” se ta miqe da sauri kuma ta shiga hada tea tana cewa “bari na zuba a Water bottle na sha a mota dan nasan yanzu Abbi ze fara a fito a fito bata rufe bakinta ba sega sallamar su Aliyun yan biyu suka tuga Kitchen da gudu jin qanshin abinci babu bata lokaci kuwa suka dirar wa Dankalin dan ma kamar Amna tasan za’ayi haka ta soya da yawa daman niyyar ta ta zuba musu su qara ko a mota kafin suje makaranta.

Tas suka cinye kowa ya dauki container cake dinsa da inibi da yar cakulatin da ake saka musu Suna haka ma’u ta shigo Kitchen din ta shirya tsaf cikin wata doguwar rigar Jallabiyya baqa da bata da Adon komai ta saka hula a kanta kafin tayi rolling mayafin rigar hannunta riqe da qaramar handa bag Fara se qamshi me sanyi takeyi.

ASMA’U

Da mamaki na kalli yaran ina cewa “ku kuma daga ina haka da sassafe se dambe kukeyi da abinci kamar wadanda sukayi kwanan yunwa”.

“Mami ai tashin yunwar mukayi shiyasa ba’a bamu abin karyawa ba” Jafar ya fada yana dariya,

“Allah ya rufa asiri, se kuyi saurin kunsan yana jiranku” na fada ina rufe baki kuwa sega horn din Bashir kamar wanda ze tashi gari.

Tareda su muka fito tunda sun cinye abincin na haqura idab naje office na nemi wani abun, kallon second daya nayi wa Bashir daya bude mota ya fito a fusace inaga da binsu cikin zeyi, har zan wuce se na sake waiwaya wa nace

“Baban Ali ina kwana” be amsa ni ba nima kima daman ban saka raiba, na kunna mota ta na ajiye jakar na sake komawa ciki dan na manta da wayata. Sanda na fito sun yafi nima naja na wuce nawa uzurin a raina ina ta mamakin ya akayi Amirah bata basu abin kari ba?

“Qila tana ta baccin nan nata na asara” na ayyana a zuciyata kafin na tabe baki na ci gaba da tuqina.

BASHIR

Qarfe bakwai saura ya fito daga dakinsa tsaf cikin shirin tafiya aiki, gaba daya wani daban ya ringa jinsa, kayan kansu ji yai kamar ba daidai ya saka ba seda ya ringa kallon kansa a mudubi ya tabbatar dai daidai yake kafin ya fita palour.

Ya rigada ya saba daga litinin zuw Juma’a Ma’u ta ware masa Suit din da ze saka hatta da takalmi da agogo komai seta ajiye masa sannan idan ze shirya tana tsaye tana taya shi ya gama ta fesa masa turare sannan su fito suci abinci cikin nishadi kafin kowa ya tafi aikinsa.

A shirye ya tarar da yaran, Aliyu ne yayiwa yan biyu wanka ya shirya su tsaf kowa ya fito goye da jakar makarantar sa suka zauna a palour shiru dagani shi suke jiran fitowar sa. Yan biyu ne suka gaishe shi ya amsa dan sun rigada sun gaisa da ragowar tunda Asuba, seya kalli kan Dining yaga wayam dan haka ya nufi Kitchen a zatonsa tana ciki amma yana zuwa nan ma babu kowa babu ma alamar an girka wani abu a cikin sa.

Dakin Amirah ya tafi yana shiga tana miqewa zaune da alama tashinta kenan ta gantsare tana miqa, cikin muryar wanda ya tashi daga bacci tace
“Kai qarfe nawa ne naga harka shirya yaya ko daman da Asuba kake fita?”

Be amsa tambayarta ba, ya ce mata “kinyi sallah?”

Shiru ta masa alamar bata yin ba kenan abinda ya qara bata masa rai a mugun fusace yace mata

“Da zan fita sallah ban tasheki ba sannan na gaya miki kiyi mana abin kari da wuri shine saboda rainin wayo kika ci gaba da baccinki ko?”

Seda ta zauna sosai kafin ta kalle shi tana tura baki tace “ni banji sanda ma ka tasheni ba, kuma abin kari baga kayan shayi nan ba harda buredi kawai ruwa za’a saka a kettle fa kawai shine sena tashi nayi muku” ta qarasa tana juyar da fuska gefe, Bashir kuwa kallonta kawai ya ringa yi, badan ba seya kwada mata mari wallahi amma dukan Mace ba dabi’arsa bace, dan haka ya juya kawai yana cewa

“Wallahi Kinji na rantse idan na dawo na tarar da wani abu ba yanda ya kamata ba a gidan nan se kin gane kurenki tunda naga alamar ke ba’a gaya miki magana kiji da kunnenki to masan maganin ki” bamm ya buga mata qofa ya fice.

Amirah kuwa ko a jikinta ta miqe tana cewa “oho dai, girki ne bazanyi ba haka kawai ni ban haifa ba a ringa sakani tashin Asuba. Dama kai kadai ne na daure nayi amma wallahi bazan girkawa wasu qattin yara har shida abinci da Asuba ba suci su zageni ko to sedai suje uwarsu ta basu badai ni ko in ka gaji ka ringa dafa musu” tayi shigewarta bandaki, ba ita ta gama rashin hankalinta tayi sallar Asuba ba se kusan takwas na safe.

Bashir kuwa yana fitowa yaga basa palour, yasan bazasu wuce gidan Ma’u ba a ransa yaji wani sanyi ko banza zaman ta a kusa dasu Alkahiri ne.

Yaransa basu taba tafiya makaranta basu karya ba ko shi kansa se dai idan baqin halinsa ya motsa yaqi ci amma babu ranar banza da bazata dafa masa abinci ba amma yanzu daga zuwan wannan yarinyar ta fara yi musu horon yunwa dole ya taka mata burki.

Yana sane ya ringa fafara musu horn ga haushin yasan yanzu suna can suna cin dadi shi kuwa sedai yaje yaci a Cafeteria kawai yayi manaji gashi har an fara saka masa ido kwanakin nan da yake ci acan har suna tambayarsa ko dai Madam tayi tafiya ne yace musu Eh yanzu hakan dai zeje yau ma amma daga gobe dole ta shiga hankalinta, idan batayi wasa ba harna rana seta girka ta aika masa dashi kuwa.

Ganin da yayi wa Ma’u y sake hasalashi, tayi qara fari tayi kyau abinta a yanda ta fitan nan babu me mata kallo matar aure ma bare har a hasaso mata yaya shida dole itama yaja mata kunne gaskiya tunda dai haryanzu ai da auransa akanta. Haka ya wuni ranar a gurin aiki cikin quncin dashi kamsa be san na menene ba, sanda ya tashi ya tsaya ya siyi fruits da kaza kafin ya wuce gida.

ASMA’U
Hankali kwance na ringa tuqina harna isa ma’aikatar mu, muka gaisa da abokanan aikina cikin mutun taka suna yimun sannun rashin lafiyar danayi qaryarta har na zauna ranar aka bani tukuicin saki nidai se yaqe nake ina amsa musu dan a yanzu bana son wani abu da ze ringa tunamun da wancan Al’amari.

Se da muka fita break din rana Olivia wata abokiyar aikina ta same ni ina cin abincin da se a sannan na samu na siya.

Cikin harshen turanci take cewa
“Asma’u Juliet tana gaya mun wata magana ranar amma ban yarda ba wai dagaske ne kun rabu da me gidanki baku tare yanzu?”

Sak nayi ina kalllon Olivia, daman Olivia irin mutanen nan ce maso shegen gulmar bala’i duk wani abu na ma’aikatar nan kaji shi a bakinta ka rasa ta inda ma take samun labarai akan mutane kuma idan taji daman ka qaddara kamar anyi yekuwa ne dan kowaanne ma’aikaci se labarin nan ya isar masa.

Dagaske yanzu dai mutane sun dena kiwon akuya sun koma mutum tabbas, Juliet din da take magana qawarta ce ni kuma a estate dinmu take budurwar wani abokin aikin su Bashir ce a gidan sa take da zama bama fa layin mu daya ba suna can qasan mune amma ace har labari ya kai musu ashe dai ba a arewa kadai mata suka iya gulma da sa ido ba harda suma a nan kudu.

Bude baki nayi da niyyar bata amsa Maman Islaha qawata ta gurin aiki ta qaraso wurin, cikin fada fada tace da Olivia din

“Wannan wane irin rainin wayo ne zaki ajiyeta kina mata wannan tambayar ina ruwanki da auranta da kike tambaya akai ita wadda ta baki labarin meya hana ki tsayawa kiji inganjinsa a gurinta? Dallah malama bar gurin nan tunda baki da aiki se soka baki a rayuwar mutane da shegiyar gulma kawai” sosai ta balbaleta da fada dan Maman Islaha irin yarabawan nan ne da basa daga qafa.

Olivia kuwa simi simi ta bar gurin tana waiwayena, mayar da kai nayi ina juya abincin dan gaba daya ya fita a raina Maman Islaha ta dafa ni tana cewa

“Ki manta da ita kici abincinki ni wallahi mamaki kika bani ma da baki dauke ta da mari ba ace kina zaune tazo tana miki irin wannan maganar se kace ubanta ne ya kashe miki auran, idan kuma mijinki take so tun wuri se ki san me ake ciki...” seta dakata ganin ina hawayen da ni kaina bansan sanda suka fara zuba ba.

“Maman Faridah lafiya meya faru?” Ta fada a rude tana ruqoni, sena saki kukan gaba daya ina cewa

“Yanzu dan aurena ya mutu shikenan har na zama abin gulma ana yayatani a duniya kenan?”

“Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un auranki ya mutu Maman Faridah dagaske? yaushe? Kardai yarinyar nan son mijinki takeyi din da gaske kiyi mun magana” ta jero mun tambayar daga ganinta kasan hankalin ta ya tashi da jin maganata.

Seda na tsagaita kukan dan har hankalin masu cin abinci ya fara dawowa kanmu kafin nayi mata bayanin komai cikin sanyi tun kafin na kai qarshe ta qundumo wata ashar me maiqo da yarbaci ta aunawa Bashir ta qara lailayo wata ta watsa mun kafin cikin fushi tace mun

“Amma kin bani mamaki Maman Faridah yo se me shi ya tafka asara fa ba ke ba dan wallahi harya mutu baze taba maida kamar ki ba shine har zaki tsaya kina kuka wani ana yayata ki a duniya an dade ba’a fada ba tunda ba kanki faru ba sakin aure har a sakeki akan kishiya kintaya kina wani zubda hawaye mtsw,

Kansa ya cuta in sha Allahu se kin samu me sonki wanda yasan darajar ki kuma akan idonsa zega yanda za’a ringa tarairayarki sedai ya hadiyi zuciya ya mutu, Allah ya kaimu ki gana iddah ni kaina ina da Candidates se wanda kika zaba kika darje”.

Haka Maman Islaha taci gaba da gaya mun maganganu da suka sake bani kwarin guiwar yakice Bashir daga rayuwata, har tana ce mun se na chanza shiga tunda yanzu bani da aure na dena zumbula wadannan Dogayen rigunan da suke boye dirina se nayi dariya nace mata

“Maman Islaha ko da aure ko babu dole in rufe jikina in kare mutunchin kaina, bafa yarinya ce ni ba sannan ga yara ina dasu nan da kika ganni ma babu lissafin sake aure a gabana zan ci gaba kawai da neman kudina na kula da yarana shikenan”.

A ranar bamu tashi da wuri ba saboda mitin din gaggawa da mukayi, abin takaici ina zuwa na kunna motata taqi tashi bayan nasan lafiya qalau take ba’a ko yi sati uku ba da a ka kaita a dubata a sannan dinma ba abinda ya sameta shine yanzu zata mun halin qarfen nasara.

Ina tsaye ina ta faman zabga tsaki, David daya daga cikin yaran da suke kula da gurin pakin ya qaraso yana tambayata lafiya nagaya masa abinda ya faru shine ya bude gaban motar yana duddubawa duk ya gama yan dabarunsa amma taqi tashi, haka na kwashe kayana daga ciki na kulleta, ga Magriba tayi gashi duk yan arear mu sun wuce haka dai na kira uber dukda bana son hawa da daddare.

Ina tsaye a daga can gaban get ina jiran me uber wata dalleliyar mota Marsandi qirar shekarar da muke ciki baqa wuluk se qyalli ta wuceni, da ido na bita a raina ina yaba motar aga quginta kadai zaka san ba qaramar mota bace a raina nace

“Allah kayi mana arziqi muci me kyau mu saka me kyau mu hau mota me kyau” ina cikin haka se ganin motar nayi tana dawowa da baya. Matsawa nayi daga inda nake ina waiwaya wa bayana dan naga tazarar gurij da cikin ma’aikatar mu idan ta kama da abin gudu in fece kar inje masu satar mutane ne se gani nayi motar ta sake biyo ni ai kuwa na daga qafa na fara sauri, sunana danaji na ciki ya ambata ya saka na juya da sauri na kalle shi.

“Asma’u” ya sake ambata yana kallona, nima kallonsa nakeyi ina so na tuna ko na sanshi amma banga alamar hakan ba.

Baqi ne amma ba irin wukuk din nan ba fatarsa a goge take alamar hutu da jin dadi sun ratsata a kallo daya zaka tabbatar da kyakykyawa ne irin kyau na maza me cike da kamala. A zaunen da yake na tabbatar da dogone irinsu Bashir sannan yana da cikar halitta bashida qiba amma jikinsa a murde yake alamar yana daga qarfe daga damtsen hannunsa da yake a bude ma zaka tabbatar da hakan.

Gaba daya a abinda be wuce second talatin ba na qare masa kallon, nayi guntun tsaki dan ban gano wata alama da take nuna na taba sanin ko me kama dashi ba a rayuwa qila irin samarin nan ne ya canki suna akayi sa’a ya fada daidai se kawai na juya na

Please Login or Register in order to submit comment