Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

Lagos gashi yanzu an dauke shikenan na kade har ganye na” Hajia Mariya ta sake rushewa da kuka. Ai se akayi tsilli tsilli, masu kukan wayoyinsu da yan kudade sunji wadda akayiwa dungurungun yo satar mota a zamanin nan motar ma ta miji besan ta dakko ba ai abin ayi mata jaje ne.

Nan fa guri ya rikice, ita dai Addah duk wannanba matsalar ta bace jira take ace ga kayanta tunda ta rigada ta kulle Get kuma ta qudiri niyya bazata bude ba se an fito mata da kayanta. Ta kallon wasu suka nufi Get da niyyar su fita suka jishi a qarqame nan aka sakeyo wa cikin gida ana ci gaba da cece kuce Addah kuwa tayi qememe duk yanda Aminan nata suke mata maganar ta bude gidan su fita amma taqi.

Tana tsaye a nan Inna Gaji ta kwaso da gudu daga palour Amirah ta dire a gaban Addah tana haki.
“Yawwa Gaji gara da kika zo ki tayani ganin wannan bala’i wai duk kudin cikin jakar nan da wayata data Amirah an samu wata la’ananniyar ta yashe ni ko na kulle gida babu wanda ya isa ya fita wallahi se sun fito mun da kayana”.

“Yanzu kibar batun wasu kudi Fatu ga bala’in da ya fi wannan can a cikin gida yana jiranki muje” ta shiga jan hannun Addah seta bita kamat raqumi da akala suka shiga dakin.

Qulululu cikinta ya bada sauti tareda murdawa kamar zawo ze kece mata taji lokacin da tayi Arba da yar jaririyar da ke kwance idanunta na qaqqafewa kamar me suma ga qirjinta na sama da qasa da sauri har wani wahalallen tari take saki a shaqe ba’a maji sosai Amirah na gefenta tuni Goggoro yayi ta kansa kwalliya ta jagale tana rusar kuka hannu aka.

Habiba Kishiyar Addah ce tayi qarfin halin cewa a dauki yarinyar a kai Asibiti mana se a sannan ma tunanin su ya kawo nan da nan Ummi ta shiga kiran wayar Naziru tunda shine wakilin Bashir din amma se aka ce mata call waiting, bata haqura ba taci gaba da kiran wayar amma be daga ba.

LAGOS Nigeria
Wato ranar bayan Bashir ya tashi daga aiki se yabi wani abokinsa gidan sa saboda koya dawo gidan baya masa dadi. Suna zaune suna cin abincin da sukayiwo take away a hanya dan shi abokin bashi da Aure suna yan hirarrakinsu. Bayan sun gama Bashir ya dauki remote yana chanza tasha kafin lokacin sallar Magriba yayi su fita shikuma abokin wayarsa ya dauka ya shiga Tiktok dan shi ma’abocin duba Tiktok ne.

Bashir na daga gefe lokaci lokaci ya daga kai ya kalleshi jin yanda yake dariya shikadai, sedai ya girgiza kai kawai yana mamaki besan me mutane suke ji ko gani a wannan Tiktok dinba. Yana yawan ganin Abokanan sa suna shiga suyi kallace kallacensu har Ma’u ma yana ganin tana shiga ta kalli video Girke Girke amma shi a shirme yake daukansa. Dukda sunce akwai abubuwan amfani amma gani yake rashin Amfanin yafi amfanin yawa ai.

“Mata da bidi’a abarsu kawai yanzu suna ma ya zama biki kenan ji wannan ai wallahi bama ko wanne biki ba” Abokin Bashir din Musa ya fada yana nunawa Bashir video bayan yayi joining Live din da wata friend dinsa takeyi. Kallo daya Bashir yayi musu “yace Allah ya sawwaqa” ganin mata nata tiqar rawa abinsu.

“Masha Allah amma mejegon tayi kyau nima fa mutumina Gomben nan zanzo ka bani wata yar fara haka na aura wallahi” Musa ya sake fada. Haka kawai se ya samu kansa da juyawa ya sake kallon wayar karaf idonsa ya sauka kan mejego Amirah tana kwaso shoki.

Murza idonsa ya sakeyi dan ya tabbatar ita dince ko kama ce ya miqa hannu ya karbi wayar daga hannun musan daidai Live Video ya katse.

“Musa bude mun page din yarinyar nan na gani” Bashir din ya fada. Se Musa ya saka dariya yana cewa
“Kai mutumina biyu ne fa dakai tsalatsala ka barmu dai mu zero mu nema amma banda kai” ya qarasa yana miqa masa bayan ya budo masa page din Nabila Dikko qawar Amirah.

Videon farko da tayi uploading kadai ya kalla ransa yai qololuwar baci, videon da aka mata ne bayan an gama mata makeup da Baby Iman a hannunta. Wayar ya miqawa Musan kawai ya zaro tasa Musa kuma ya bishi da ido ganin yanda fuskarsa ta nuna bacin rai qarara.

Number Naziru ya kira ringing biyu ya daga.
“Naziru me yake faruwa a gidan nan?” Ya tambayeshi. Naziru da daman yake shirin kiran Yayan nasa dan dawowarsa daga makaranta kenan Dada take gaya masa ana can ana taron sunan, ze kira Bashir din kuma ta hana dan haka ya karkace ya fara jero masa yanda akayi

“Wallahi yaya taron suna sukeyi gida ya cika da mata harda me kida suka dakko tun daga Kano wai Feli sunansa kowa nadai manta sunacan dai sunayi wallahi ga sanyi ya kankama a Gombe kuma.....”

“Kanaji ko, kaje gidan ka kulle qofar ta waje kayi tafiyarka kawai kabarsu” Bashir din ya katse Naziru jin zancen nasa yaqi qarewa.
“Yes” Nazirun ya fada ransa qal dan dama yasan Indai Bashir ne ya san takan Tsiya aikuwa Kwado ze siyo qundumeme ya garqame su kuma baze bude ba se irin sha biyun daren nan gobe ma su sake zuwa suna.

Be fadawa Dada yanda sukayi ba haka be bi takan Kiran da Ummi takeyi masa ba dan daidai lokacin ne suna waya Bashir. Machine ya hau dan yafi sauri bayan ya siyi garqamemen kwadonsa kamar me kulle kurkuku ya nufi gidan.

A gidan suna kuwa bangaren su Ma’u sun sha hirarsu sosai har Magrib sannan driver Zahra yazo, sallama sukayi kamar karsu rabu Sannan Ma’u da Rahma suka rakota kallon matan da sukayi cirko cirko a tsakar gidan sukayi dan duk budirin nan basu san me yake faruwa ba suna sama abinsu kuma da yake sun rufe windows yasa basa jin qarar kidan sosai koda aka kashe ma abun be dame su ba.

Rabawa sukayi suka nufi Get dan bama wanda hankalin yakai kansu Asma’u ta saka key din hannunta ta budewa Zahra a ranta tana mamakin ganin an garqame qofa harda kwado Zahra na saka qafarta waje Naziru na dira ai harda gudu ya hado har yana tsorata su Zahra tayi Waje Ma’u tai ciki da sauri ganin yana neman datse mata hannu abinda ya ankarar da matan dake tsaye kenan suka yo Get din da gudu amma ina kafin suzo tuni ya danna Kwado ya bame.

Baki bude Rahma da Ma’u suke kallonsu,
“Kiyiwa Allah Hajia ki bude mana mu tafi dare yanayi haka kawai an kullemu kamar wasu barayi” wata mata ta fada. Kiran sunan Naziru Ma’u ta shigayi gaba daya kanta ya kulle se ya amsa mata yana cewa

“Anty kije kawai zan kiraki a waya in miki bayani”. Seta juya ita da Rahma sunajin matan wasu na magiyar a bude wasu na zage zage.

A palourn qasan suka zauna ta dannawa Naziru kira.

“Baba Naziru wai ya akayi ne meya faru aka garqame mana gida” ta tambayeshi bayan ya daga wayar. Seda yai dariya san ransa dannan yace

“Wallahi Anty ina zaune Yaya ya kirani yace na siyi kwado nazo na kulle gidan nan da duk jama’ar ciki inyi tafiyata ze kirani sanda ya kamata nazo na bude”.

“Ikon Allah, me akayi toh” ta tambayeshi.
“Oho inaga dai daman besan da zasuyi taron nan ba shine dalili qilan” cewar Nazirun.

“Toh Allah ya rufa asiri nidai yayana suna waje daman yanzu nake shirin naje na dakko su tunda gaka taimaka ai kasan gidan Su Qawar Amna Amina ka debo munsu”

“Ba case Anty Bari naje” sukayi sallama ta ajiye wayar.

“Kinji me gidan ne yace a kulle masa gidansa” Ma’u ta gayawa Rahma.

“Amma naji dadi dan fa sanda Abban Ilham ya kawoni yaga taron nan tambayata yakeyi meya faru nace nima ban sani ba nadai yi hasashen suna ake, yace aikuwa dakyar idan yaya bashir ya sani toh Allah dai yasa atashi lafiya nace Amin
Yanzu kuwa naga alamar kamar ba lafiya ba dan banga iyayen bikin ba a gurin”.

“Koma meye susuka sani dai, muje muyi Isha naji an fara kira” Asma’u ta fada suka miqe suka shiga dakinta na qasa dan yin sallar.


Dakin Mejego kuwa kiran duniya Naziru be dauki waya ba haka suka tasa ya a gaba suna kuka ita se qaqqafewa take Su kuma suna aukij kuka Amirah kamar itama zata shide babu wanda fasahar kaita wani Asibitin tazo masa a cikinsu.

“Ina Fatun, wallahi tun da sauran mutunta juna tsakaninmu kizo ki bude mu mu fita idan ba haka ba wallahi bazaki so abinda zan aikata a gidan nan ba” Hajia Mariya datafi kowa shiga tashin hankali dan kamar Mijin na jira ta gane an sace mota se gashi ya kirata akan yana Airport za’azo a karbi key din motar a dakko shi, seda wanda ya tura yaje aka ce masa bata nan ya kirashi gashi yanzu se kiranta yake yana Zazzage mata kwandon rashin mutunchi yace ta kuma tattaro dik inda take karya rigata zuwa gida in ma ita bata dawo ba to motarsa ta rigashi isa.

Qaqawara qaqa 🤔🤔🤔🤔🤔🤔


Ayi qara haquri dai yanayin se a hankali 🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 19

Tunda Bashir ya qulla tsiya ya kuma tabbatar Naziru ya kulle gidan dan sun sake yin waya ya gaya masa ya je dakko su Amna a gidan qawarsu a sannan ce masa yayi ya wuce ya kaisu gidan Bilkisu yayar Asma’u kawai dan idan yace gidan Dada zata zargi wani abu kuma baya so labarin ya isar mata da wuri.

kashe wayarsa yayi dan karma wani dayake ganin mutunchi ya kirashi ya roqeshi. Beko qara minti goma a gidan Musa ba ya tafi yana tuqi a ransa yana wassafa irin hukuncin da ze dauka akan Amirah tunda har ta take dokarsa ta nuna bata jin maganarsa tabbas ze nuna mata shima ba kanwar lasa bane.

Daya isa gida shikadai ya ringa safa da marwa a cikin palour yana kwafa tabbas se ya hukunta yarinyar nan hukunci me tsanani, tunanin halinda Baby Iman take ciki yake yana fatan Allah yasa yarinyar tana lafiya wani abu be sameta ba hakan ze dan rangwanta wa Amirah hukuncin da zeyi mata amma ya rantse tabbas wani abu ya sami yarinyar nan se kansa besan me ze mata ba. Yana so ya kira Ma’u amma bayaso ya kunna wayar wani kiran ya shiga qarshe haka ya haqura ya zauna jiran lokacin daya diba kafin ya sake kiran Naziru.

Gidan suna kuwa gagarumin ruguntsumi ne ya sake tashi. Ana tsaka da dambaruwar yanda za’ayi a bude qofa, dangi da qawayen Addah sun taru suna mata tijara sun cika palour Amirah taf kaman an sakko daga Idi daidai da iska me kyau babu ta shaqa se kaya kaya akeyi.

Amirah na durqushe se rasgar kuka take har sannan akan yarinyar da harta gaji da komawa da numfashinta ta kwanta laqwas kamar mara rai ita duk wannan hayaniyar ba ganewa take ba, buqatarta a samu me kai mata ya Asibiti dan ta dade da saddaqarwa yau kashi ta ya gama bushewa.

Addah data gaji da tijara da cin mutunchin da Jama’a suke mata ta zaro Key ta cillawa Hajia Mariya datafi kowa hasala a cikin matan dan ita aka dira daka, so take kawai ta fita ta san nayi dan ko karan hauka ya cijeta bazata doshi gidan mijinta yanzu ba se da wannan mota da bata san uban da ya sace ba dan haka ta yanke shawarar daga nan office din Yan sanda zata ta bada report daga can kuma tayi gidansu dan tasan waye mijinta sarai haka kawai ma yayi bala’i bare yau da aka taboshi da lasisi.

Cafkar key din tayi tana watsawa Addah kallon wulaqanci tace “da karki bayar wallahi da sena tubeki na dauki muqullin nan yau” ta fara kutsawa da niyyar zuwa bude qofa Hajia Hassana ta katseta tana cewa
“Mariya wannan muqulli fa aikin banza ne dan ta waje wani hatsabibin yaro ya kullo mu wallahi. Kuna tsaka da hayaniya dazun nan Uwargidanta ta raka baquwa ta bude kofar tana fita yaron nan ya danno daga waje ya rufe jeki duba ma ki gani babu kwadon nan ta ciki”.

Kafin ma ta qarasa dayawa sun dauki sabon kukan tashin hankalin rashin sanin wane kalar bala’in ne kuma yake tunkaro su, To bala’i mana in ba haka ba ta yaya za’a ce an kullo su ta waje ma bata ciki ba yanzu suyi yaya su fita dan dai wannan katangar gidan basu isa su tsallakata ba.

Ummi ce da tuni itama ido sukayi mici mici saboda kuka ta sunkuci Iman tana ceda Amirah “nidai matsa ki gani wannan hayaniyar da hucin numfashin kadai sun isa su qarasata muje ko a Napep ne mu tare mu kaita Asibiti” ta nadeta a cikin shawl din ta kyau ta juya da niyyar fita kamar ana jiran ta kuwa dif wutar palour ta dauke duhu ya mamaye ko ina bame ganin wani a ciki.

Gaba daya guri ya sake rikicewa da ihu dan kina tsaye sedai kiji an wafce miki jaka nan aka shiga turereniyar fita ana faduwa duk wadda kuwa ta fadi sunanta sorry dan taketa za’ayi ana neman hanyar tsira a garin haka aka dungure mata Tv ta fado qas tim Centre table kuwa daman tuni ya karbi rabonsa se fatan kar wani ya taka kwalba a garin gudu.

Wata qara me kama da rugugin tsawa a ka fasa kafin sukaji faduwar abu tim a qasa, sabon gudu ne ya falle ga duhu ba wanda yasan takamaiman ina yake dosa aka ringa gwabza karo ana faduwa kuwa kafin kace me anyi wada wada da kayan palour Amirah,
Seda aka kwashi a qallah minti goma se ga haske ya dawo ai kan kace kwabo wayam sun fice daga palour an dawo tsakar gida kowa tayi cirko cirko fuskokin mata jagejage da hawaye wannan Suna ko jaraba?

Addah data ja qafa da niyyar gudu itama caraf aka riqeta cikin abinda befi sakan uku ba ta saki fitsarin tsoro ganin sunyi ido hudu da Hajia Mariya dake yashe a qasa da ko ba’a gaya mata ba tasan riqaqqun iskokanta ne suka tashi. Tun da tace an sace motar nan abinda take taraddadi kenan dan indai ranta ya baci se sunzo kuma Al’amarin bazeyiwa kowa kyau ba dan Aljanunta basu da mutunchi yanzu basuqi suyiwa kowa na gidan sunan nan bulala dari dari ba.

Sake yunqurawa tayi da niyyar gudu Mariya ta miqe cikin muryar yara tace mata “Addah fatu muje washan goyo ja’ayi yau kowa seya goya ni in ba haka ba nayi masha buyayay goma ke zaki faya kuma”

“Quuuu” cikin Addah ya bada qara, yo ai badanba gara bulalar akan tace a goyata. Ita kadai ma Hajia Mariya ba kadan bace qaruwar mace ce ta gaske bare idan wannan yar Aljanar tata tazo me son goyo seta Allah in kuma bakayi ba kaci na jaki. Addah naji tana gani ta tasata a gaba suka fito inda Jama’a sukayi cirko cirko ta dane bayanta kuwa.

Zanso kuga idon Addah haka ta goya hajia Mariya tana nishi kamar zata mutu ta kaita ta dawo da ita amma taqi sauka tace se an sake haka ta kuma sahu daya da ita sukaje suka dawo sannan ta sauka. Zaba ta ringayi wanda ze goyata in ka tsaya gardama sedai kaji dundu kamar an buga maka guduma kuma in ta hau marasa qarfi suka fadi nan ma ta hau tamola da mutum aifa gida ya sakw zama kamar gidan Allura se kuka ake wannan jaraba har ina.

Aliyu dake cikin dan dakin da Change over da Solar su ta gidan yake ya kwashe da dariya har yana kaiwa qasa. A kan idonsa komai yake gudana dama jira yake gari ya qara duhu ya kashe haske ya qara musu tension akan wanda suke ciki gashi kuwa yayi ga kuma sabon show an samu kai amma fa abu yayi kyau kuma yaji dadi, fitowa yayi ya wuce part dinsu, knocking biyu Jafar ya bude masa ya shiga yana Dariya.

Asma’u dake zaune akan kujerar Dining suna waya da Yaya Bilkisu ta gayavmata su Farida suna can Naziru ya kaisu ta dago ta kalleshi, tun ma kafin tayi magana yace “Mami kinga yan suna kuwa ga wata can tana Aljanu tace se sun goyata kowa takalminta a hannu lipstick duk ya goge”.

Duk yanda taso dakewa tayi masa fada kasawa tayi ta fashe da dariya dan tana hango harabar gidan dan tarwai yake da hasken fitulun da aka zagaye shi dasu, saboda ma taga komai dakyau yasa ta dage labulaye suka rage hasken fitulun palour duk drama da akeyi akan idonta ne tana ganin haske ya dauke kuwa jikinta ya bata Aliyu ne dan ta san aikinsa ne kashe wutakuma dazu ta ganshi a zaune a qofar power room din magana ce kawai bata masa ba ta wuce.

“Allah ya shiryeka, kar naga ka sake fita in ba haka ba ranka ze baci” ta fada tana miqewa.
“Sunan wani film waishi daga murna” ta fada tana shiga kitchen dariya fal ranta, Yogurt ta dauka da cups biyu ta koma dakinta inda ta bar Rahma tana sallar Isha tunda yaranta sun samu mafaka ai shikenan ita kam.

Abuubuwa sun sake rikicewa Addah ido ya raina fata, data san haka ce zata faru kuma da bata kulle qofar ba gara tabar kowa ta tafi gidan ta idan yaso tayi Allah ya isa amma gashi yanzu an bata goma daya bata gyaru ba. Dakyar ta samu ta zillewa yar zulai Aljanar Hajia Mariya tayi bayan gidan gashi ta Rasa wanda ze kira mata Dada dan ita kadaice kuma madafarta a yanzu idan ma ba’a san wandaya kullo su ba ita zata iya nemo wanda ze zo ya buge kwadon amma wannan garqamewa da akayi musu idan wuta ta tashi fa Allah ya kiyaye subi ina su fita?

To kuma kiran Dadar ma ba hali dan an sace waya kuma tasan babu me bata aron tasa idan ma an bata ita ba haddace Number ta tayi ba, dabara ce ta fado mata arai, bari taje gurin Ma’u ta kira mata Bashir ai shine me gida dukma tsiyar da za’ayi sudai a bude su tukunna jama’ar data tara su tafi wannan bala’in ya ragu dan dai kam taga suna yau ganin idonta bakuma ta fata Allah ya sake maimaita mata irin wannan taron. Sadadawa tayi ta faki ido ta zagaya ta kofar kitchen din Ma’u.

Kamar zata balla qofa haka ta ringa doka musu bugu tanayi tana wai waye gudun kar wani ya ganita Har Jafar ze bude Aliyu ya riqo shi yana cewa “kai baka da hankali ko to jeka bude musu baka san me yake faruwa a gidan nan bane” se Jafar din ya fasa amma be zauna ba ya tafi ya gayawa Ma’u.

Ta yar hudar jikin qofar ta hango Addah fuska tayi qozai qozai abunka da fara daurin da aka dandasa mata dazu yayi ta kansa ga kunnenta daya da dan kunne daya babu ta tabbatar bata ma lura da hakan ba. Bude mata qofar tayi tana shigowa kuwa takai qasa tana rushewa da kuka kamar qaramar yarinya.

Kiyiwa Allah Asama’u ki kira Bashir azo a budewa mutanen nan qofa su fita kafin su kashe ni nidai nayi dana sanin wannan qaddararren taron suna ashe rabon wahala ne yasa muka nace se munyi” ta sake rushewa da kuka harda sheshsheqa.

Ba qaramin dauriya Ma’u tayi ta riqe dariyarta ba amma dukda haka da Addah a hayyacinta take seta gane dariya take mata tace “toh Addah meya faru kuma ni da naji shiru an dena kida ma na zata kun tashi ne.
Wayar Baban Aliyu kuwa a kashe take fa dan na kirashi tun dasu naji amma bari na same kira ko yanzu ya kunnata” ta fada tana danna wayar ta lalubi Number sa ta danna kira, kai kodan ta sake kunno musu shi idan be sani ba ai yasa ta kirashi sedai kamar dazu data kira ce mata akayi a kashe take.

“Wallahi Addah a kashe take” ta fada tana janye wayar a kunnenta
“Kiramun Nafi dan Allah ita ta samo mana wanda ze bude mu” Addah ta katseta seta maida akalar kiranta kan Dada itama seda ta mata kira biyu sannan ta daga ba tareda ta yi magana ba ta miqawa da Addah wayar ta karba tana rushewa da Dadan da kuka.

“Nafi na shiga uku na hada taron masifa da Bala’i yau ki taimake ni yar uwata ki kawomun dauki” Addah ta fada cikin matsanancin kuka. Dada da harta kwanta dan cikin ikon babu wand aya kirata ya gaya mata wannan Al’amari dan yayanta da sukaje suna bayanda Asma’u da Amirah suka gwanya musu rashin M fushi sukayi suka bar gidan, ragowan dangin da suke can kuwa tunanin su kirata be zo musu ba koda yake rabi da kwatan yan suna an kwamushe musu waya wadanda suka tsira kuwa sunyiwa tasu boyo me kyau kafin a sane ta.

“Addah lafiya, meya faru? A ina kuma? Dada ta tambayeta cikin damuwa da jin kukan nata tasan ba lafiya ba amma Number Asma’u data gani yasa hankali be tashi da yawa ba tasan koma mene ne da sauqi.

Addah kukan ta taci gaba dayi, ganin da Asma’u tayi bata da niyyar ansawa Dada ya sakata karbar wayar ta danyi mata bayanin iya abinda ta fuskanta da lamarin.

“Ashsha abu beyi kyau ba, yanzu waye ya kulle gidan? Shi Bashir din ya sani?” Dada ta tambaya se Asma’u tace mata
“Muma bamu sani ba Ai, Baban Ali kuma ban sani ba gaskiya ko yasan maganar dan wayarsa a kashe take tundazu dana kira”.

“Shikenan bari nayiwa Amiru magana gashi can yana cin abinci daman nan gidan naku ze taho ya dauki Rahma in yaso se suzo da Naziru yanzu Allah ya kiyaye gaba” Dadan ta fada zuciyarta sam babu dadi, yanzu wannan wane irin abune ai yanzu Allah kadai yasan inda maganar sunan nan zata tsaya sun jawo musu abun fada a gari. Fitowa tayi daga dakin ta ta tarar da Amirun a tsaye yana niyyar fita dan sunyi sallama ta shiga ciki.

“Amiru ka nemi Naziru ku tafi tare gidan Yayan naku ba lafiya ba”.

Da”Allah ya kyauta” ya amsa mata ya fita yana dannan kiran wayar Naziru dan shi duk a zatonsa be wuce a ce rigima ce tsakanin Ma’u da Amirah ba, a hanya ya dauki Naziru daya maze kamar besan me yake faruwa ba, gama wayarsu da Bashir kenan ya kirashi da wani layi yace masa duk me za’ayi karya kuskura ya bude gidan nan qasa da qarfe goma na dare yanzu kuwa har tara ta gota dan haka ya qara musu awa daya se sha biyu ze bude su kuwa.

Kamar wata boarding school ranar hutu haka suka tarar da qofar gidan cike da motoci, yawanci mazajen wadanda Allah ya taimakesu suka tambaya kafin suka fito ne an kuma san inda suka tafi da sukaji shiru suka biyi sahunsu se wadanda yan uwansu suka kira su dauke su.

“Kai lafiya kuwa gidan meyake faruwa haka” Amiru ya fada se Naziru ya marairaice kamar na Allah yace
“Yanda ka gansu yaya nima haka na gani, mu qarasa mugani Allah yasa dai lafiya. Bakin get suka qarasa inda wasu suke qoqarin yanke kwado amma kamar na tsafi yaqi yankuwa wasu daga gefe kuma suna musu magana akan su bari, ta yaya zasu budewa mutum gida bada izininsa ba duk abinda yake ya dawo su tabbata yana kansu.

“Wai meyake faruwa haka ne” Amiru ya tambayi masu yanke kwado dan shi tunaninsa ya tafi kodai gobara ko wani babban Al’amari ne kuma yake faruwa amma kuma hmga kwado ta waje ga kuma kururuwar mata suna jiyowa daga ciki suna ihun a taimaka musu.

“Kagane Alhaji nima bansan me yake faruwa ba gaskiya Beb dita ce ta kirani tace nazo na dauketa a gidan nan tazo suna daman ni na kawota dazu se kuma tace na taho da me yankan kwado idan zan zo kaji iya abinda na sani nidai” shugaban masu kiciniya da kwado ya fada.
Se Amiru ya kalle shi cikin masifa ce“wannan wane irin rashin hankali ne, meye a cikin gidan da har zaku zo ku

Please Login or Register in order to submit comment