Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

dan haka yace ta hada musu cornflake kawai su sha. A qaton bowl ta hado shi suka hadu kowa da spoon suna sha yana kallonsu dan bayajin ko ruwa ze iya bita maqoshinsa. “Kai anya ze iya rayuwa babu Asma’u kuwa?” Ya tambayi kansa
“Idan ta mutu fa” wata zuciyar ta qara tambayarsa
“Kai ina insha Allahu ma sena rigata mutuwa” ya fada a fili ba tareda yasan a fili yake maganar ba da Alama Ma’u na dab da zarar dashi 😂😂

Bayan sun gama yace suje su kwanta amma qememe Suka qi yana tashi suka bishi Amna Farida da Aliyu ne kawai suka zauna a palour, ba yadda ya iya haka ya jera su akan gadon ya shiga toilet ya dauro alwala ya fara sallah dan yasan bama ze iya bacci ba yau, haka yai ta jera salloli in ya gaji ya huta har bacci barawo yai nasarar sace shi.

HAJIA AMIRAH
Sororo tabi wayar da kallo hawaye na kwace mata ta kalli Mamanta Adda Fatu da har tafi Amirah kidima dan a hands free ta saka wayar, ita dama bata so ta sake kiransa ba tunda yace ze kirata amma Adda Fatu ta sata a gaba dan a yau take so ya aikowa da Amirah kudaden da sukayi qaryar zatayi siyayya saboda tafiyarta Lagos amma wani uzurin daban take so tayi dasu.

“Adda kin gani ko bamu samu biyan buqata ba yanzu mun ballo matsala Allah kadai yasan yanzu hukuncin da zeyi mun” ta fada tana share hawaye.

“Ke dalla can ba abinda zeyi miki qarshe ma kiga ya kira ki yanzu ya baki haquri ta yuwu wani ya bata masa rai kika taka sahun barawo” bata qarasa rufe baki ba sukaji alamar shigowar message wayarta, baki washe Adda tace “kingani ko duba muga ko kudin ya sako”

Ita dai Amirah jikinta be bata ba dan tasan waye Bashir a tsorace ta bude message din ashe MTN ne suke gaya mata zata iya aron kati dan nata ya kusa qarewa. Wata muguwar dariya Ummi qanwar ta ta sheqe da ita tana tashi zaune daga kwanciyar da tayi tace

“Wai ke kin yarda Yaya Bashir ne ze kiraki ya baki haquri to sannu uwarsa, ai wallahi ki shirya ma Allah kadai yasan abunda ze biyo baya dan kinsan sarai fadansa kamar na kurma yake baya mutuwa”

“To se kijie ki saka shi ya dauki matakin ai dan uwarki shegiya me baqar fuska” Amirah ta fada tana hayayyaqo mata

“Gata nan a zaune ai uwar tawa baqar fuska kuma na gode keme farar ai gaki nan kin zama Bora a gurin miji, Allah dai ya rabamu da auran cin Amana” Ummin ta mayar mata dan itama ba baya bace gurin fitsara. Nanda nan fada ya kaure a tsakaninsu seda Adda Fatu ta zuzzunduma musu Ashar sannan suka yi shiru kowa tana harar yar uwarta.

“Shegu kuda baku gudun abun magana a daren nan kunsan an kasa kunne a jiyo zancen mu a yada shine zaku min tijara kishiyoyi naji ni kubarni nayi tunanin mafita ma kun hanani” ta fada tana hararar su duka. Yunqurawa Amira tayi dan cikinta yayi girma sosai ta shiga daki har tana takewa Ummi qafa da gangan

“Salon na taba ki wani abu ya same ki ko to bazan kula kiba aniyarki ta biki” Ummi ta fada.

“Tashi ki shige kafin na rade ki yar kwal uba” Adda Fatu ta fada tana neman madoki, setayi saurin barin wurin dan tasan tsaf zata sha dukan kuwa.

Tunani ta shiga yi ta yanda zata samu kudi kafin wayewar gari, bashi ne tun na lokacin Auran Amirah har yau bata gama biyaba kusan shekara biyu dan a zatonta zasu samu a hannun Bashir din ganin yanda Ma’u take wadaqa sedai tunda akayi auran ita dai bata ga kyautar dunkulalliyar dubu dari yayiwa Amiran ba, ze dai aje mata komai na buqata amma baze bata kudi ba.

Ganin ba mafita kuma ta tabbatar kaman yanda matar tace da safe zata biyo kadin kudinta ko kudi ko kayan kudi tofa rashin mutunchi zata mata dole ta nemi mafita qarshe ta yanke shaqarar zuwa gidan su Bashir din gurin Nafi ai ita Uwarsa ce idan ta kira shi baze qi dagawa ba, da wannan shawara ta kwanta akan asubanci zatayi kafin matar tazo insha Allahu ta dawo.

LAGOS
Malam Bashir kuwa dakyar ya iya farkawa da Asuba kansa kaman an dora masa Dala tsabar ciwon da yake masa, basu iya fita masallaci ba a gida sukayi sallah suka hau shirin makaranta dan zasu fara biyawa Asibiti su duba Mami.
Tea suka dafa suka soya kwai suka karya, basu daukar mata komai ba se kaya kala daya wanda zata saka idan An sallameta tunda Asibitin nada uniform na marasa lafiya baa buqatar kaya haka abinci ma a can ake basu..

A hankali ya tura qofar hadi da sallama, a nutse ta dago ta kalleshi tareda amsa sallmar, fuskarta dauke da wani kyakykyawan murmushi. Magana take yi da yaranta kowa na gaya mata yanda yayi missing nata.

Qara shigowa yayi idanunsa akanta yana qarewa kyakykyawar fuskarta me cike da kalama kallo ganin yanda Omo blue din Uniform din Asibitin ya amshi fatar ta matuqa kamar wasu kayan kwalliya. Aliyu ne ya bashi kujerar da yake zaune akai still idanunsa akan ta yaja ya zauna dukda daqi sake dagowa ballantana ma su hada idanu da ita.

Shigowar Nurse da taje kawo mata breakfast yasa ta daga kanta Yaran suka shiga gaida Nurse din tana amsa musu da kulawa, Dan gyaran murya yayi tareda kallon yaran yace “kuje mota ku jirani kar mu makara idan mun taso se mu sake biyowa aga Mami ko? Basu musa ba da daddaya suka fice bayan sun mata Addu’ar samun sauqi itama Nurse aje kayan tayi ta gaishe shi kafin tayi waje abunta.

Cikin sanyi jiki ya miqe zuwa gefenta da tun kafin ya qaraso ta dauke fuskarta zuwa dayan side din, be haqura ba ya bita, can qasan maqoshinya furta “How are you feeling now? Ina ne yake miki ciwo?”

“Oh really ka damu ne daman da lafiyata toh Alhamdulillah Yanda kaso be samu ba jinina ya sauka ya dawo dadai”. Be kula maganar taba ya sake matsarta yana cewa “Why? Me yasa baki gayamun that you are pregnant ba??”

Ita se a yanzu ma ta gane dalilin wannan fake concern din wato saboda cikin da ya zube, murmushi tayi me kama da yaqe tana tashi zaune sosai tace
“Baban Ai kenan, to ina ruwanka da ina da ciki ko bani da shi naga yanzu ai baka damu dani da yaya nane bako? Ko da yake dama ai bazaka damu ba tunda qaddarace tasaka kuka hada Zuri’a dani
Yanzu ai gashi za’a haifar maka jininka yayan dangi na meye zaka damu akan wanda Allah ya taqaita samuwarsa bare yazo shima a barshi a titi a bula masa qura ko yaje makaranta ko kar yaje duk ba matsalar ka bace.

Wallahi Baban Ali kayi nasarar doramun Hawan jini amma ina tabbatar maka bazan bari ka nakastamun rayuwa ba idan kuwa haka ta faru sedai muyi mutuwar Kasko”.

Kaman wanda aka dasa haka ya bude ido da baki yana Kallon ta, kai wannan Mata wai ita bata yafiya ne a ko yaushe burinta ta ringa hukuntaka da kuskuren da ka aikata? To in ba haka ba meye na dawo da wadannan maganganun marasa dadi? Yana shirin maida mata da martani wayarsa ta dauki qara, hadiye bisashshan yawu yayi kafij ya zaro wayar yana tattara kalaman da ze bata amsa dasuba zuciyarsa.

Sunan “DADA da ya gani ya saka shi saurin daga wayar ya kai kunnensa. Cikin harshen fulatanci ya shiga gaisheta ta Amsa tana tambayarsa Asma’u da yara.

“Bashir Meya sami wayarka Amirah tace tun jiya tana kira baka dagawa” ta fada bayan sun gama gaisuwar.

“Qarata ta kai kenan, ai kuwa seta gane bata da wayo” ya ayyana a ransa a fili kuwa se yace
“Dada Ma’una ce bata da lafiya tayi Bari muna Asibiti tun jiyan”
“Subhanallahi a garin yaya” ta tambaya muryarta na nuna Alhini se ya sake narkewa abin tausayi yace

“Nima ban sani ba ina office aka kirani wai ta yanke jiki ta fadi ina zuwa muka hato Asibiti” ya yanko maganar da shi besan gaskiya ya fada ba ko qarya. Asma’u dai kallonsa kawai takeyi tana qara mamakin Bashir a ranta, miqo mata wayar yayi seta tsaya kamar bazata karba ba kome ta tuna kuma ta karba.

Sama sama ta gaida Dadan tareda amsa ya jikin da take mata dan itakam ai sun shata ta warke abinda mutanen nan suka mata ta yaya zata manta dashi?

Kallonta Bashir yake a ransa baya jin dadin yanda alaqar Dada da Ma’u ta lalace be kuma san ta yanda ze gyarata ba, yasan sun mata laifi amma Ma’u ma akwai ruqo da kafiya ai.
Miqo masa wayar tayi ya karba sukayi sallama da Dadan sannan ya kashe. Hannu yaki ze riqe nata tayi saurin janyewa se ya girgiza kai kawai yace “Ki kwanta ki huta bari naje mun makara ma idan mun taso zan ga Dr ance be shigo ba yanzu naji yaushe zeyi discharging naki”

Bata amsa ba shima be saka rai ba dan haka yaja qafafunsa ya fice yana sake kallon Wayarsa dan ganin da gaskw sun makara din.
Asma’u kuwa da harara ta raka shi kafin ta zumburi baki tana qunquni tace “wato in dawo kaci gaba da Gallazamin ko toh ba inda zani se na tatike Aljihun ka qat na huta wallahi”
Ita kadai tayi ta sababi har bacci ya dauketa sannan tayi shiru.

Bashir kuwa sauri sauri ya kai yaran har an rufe get dakyar suka karbe su suna ta masa qorafin in suka sake makara bazasu karbe su ba shida ya ajiye su ya wuce nasa aikin da baya zaton ze amfani komai yau. Gaba daya shima ji yake kamar bashi da lafiya ga wani mugun bacci dayake jin idon sa yayi fici fici har wani yaji suke masa,haka ya lallaba ya qara sa office din.

GOMBE
Bayan da Dada ta ajiye wayar se ta maida hankalinta kan yayartata Adda fatu datayi kamar bata gane me Dada da Bashir din suka tattauna ba.
“Ashe Ma’u ce bata da lafiya tayi bari suna Asibiti” Dadan ta fada.
“Allah sarki Allah ya bada na aike” Adda Fatu ta amsata a ranta kuwa murna tayi gara ma da cikin ya zube ita duk wadannan yayan data zuba bazata haqura ta barwa Amirah itama ta samu rabonta ba ita dai fatan ta Allah yasa ba ita Amiran ta gado ba dan ta fara ganin sare sarin hakan, seta gyara zamanta tana cewa

“Kinga daman maganar shirye shiryen tafiyarta lagos din nan ce lokaci nata tafiya yace ze turo mata kudi tayi siyya anan kafin ta tafi yanda kinga in lokacin haihuwa yayi ta howa kawai zatayi komai na jiranta a nan to kuma naga yana nema ya shiriran tar da maganar ga yarinya kuma ko baccin kirki wallahi bata iya yi to Allah ya hada ta da jarababben ciki gara dai yazo ya tattarata su tafi dan nikam na fara gajia gaskiya”.

Kallonta kawai Dada tayi ita kam Adda Na bata mamaki da kunya wallahi in ba haka ba ina ita ina irin wannan magana ai tsakaninsu ne can ko amma ita babu ruwanta tana manta cewa Matsayin Suruka take a gurin Amira ba kowacce magana ya kamata ta ringa yi da ita b, dakyar ta bude baki tace

“To Adda nake ga siyayya ai bawata matsala tunda in kayane ai can Lagos sun fimu in taje din se su siya acan su turo kuma ni da zaki ji ta tawa ma da tayi haquri ta yi zamanta a nan tunda yana zuwa sati biyu dan gaskiya abinda ake shirin yi ba Adalci bane. Yarinyar nan Asma’u mun mata abubuwa da yawa ni wallahi har kunyarta nake ji to yanzu kuma akace wannan gaskiya ya zama da daukar Alhaki kuma.https://chat.whatsapp.com/GBC9U1ddKHO94q4CSL2jZ8


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM (Marubuciyar Rubutacciyar Qaddarah)

Page 5

“Ban gane ba Nafi me kike nufi da ta haqura da binsa ko baki gane halin da yarinyar nan take ciki bane, yarinya na buqatar mijinta a kusa idan kuma ba halaka ake so ta fada ba se naji, nifa dama na gane take takenki kina so ki fifita bare akan yar uwarki ko Nafi. Kuma da kike zancen za’a shiga haqqin Asma’u ita Amirar daba uwace ta haifeta ba ai ba’a shiga nata haqqin bako” Adda Fatu ta fada cike da jin haushin Dada, se Dadar ta gyara zama tareda cewa

“Ni ba haka nake nufi ba amma gani nayi ai tun farko tare suke a can, yanzu ko cewa akayi suringa yi idan wannan ta je ta kwana biyu se wannan taje kinga bame yiwuwa bane tunda Asma’u tana aiki a garin bakuma ze yuwu muce tabar aikin ta ba tunda idan Amira ce a matsayinta muma bazamu bari a mata ba ko?

Ni dai a nawa ganin Adda ayi haqurin shi yafi a zauna lafiya tunda har komai ya daidaita tsakaninsu bana son wata rigima ta sake tasowa kindai san sharadin da Malam ya kafa mun dan Allah bana so ya sake ganin laifina akan lamarin gidan Bashir”.

Se Adda Fatu ta miqe nan da nan ta fara sababi da fadan maganganu ta inda take shiga bata nan take fita ba, ga baqin cikin rashin samun biyan buqata a gurin Bashir gashi da Alamu wannan Karon Nafi na nema ta bata matsala amma ina bazata sabu ba wallahi dole tasan abinyi. Miqewa tayi still tana masifar ta nifi qofa,

“Wato Nafi kina ganin yanzu kinkai matsayin da zaki qalubalance ni ko? Kin manta duk halaccin da nayi miki a rayuwa saboda qasa ta dade da cinye Naman Baffa da Inna dole ki watsar da maganar su tunda kina ganin yanzu kema Kin kawo qarfi. Na gode zan kuma tafi amma daga yau kisa a ranki baki da sauran wata yar uwa data rage miki a duniya tunda kin zabi Matar danki akaina da Yata shikenan Nafi na yafewa Duniya ke” ta qarasa tana rushewa Kukan munafunci wanda dashi take cin galaba akan Nafin.

Ta kuwa samu yanda take so dan nan da nan hankalin Dada ya tashi ta shiga son nuna mata ita fa ba abinda take nufi ba kenan,
“Idan har da gaske kike kuma kina so na haqura nida kawai kiyi yanda zakiyi Bashir ya dauki Amira ta koma kusa dashi, kuma baze yuwu yace Ze kwashe su su dukka ya kai can ba se dai ki saka shi ya dawo da daya ya dauki daya idan kikayi haka shine kadai Ze sa na haqura in ba haka ba wallahi ki saka a ranki baki da wata Yar uwa Fatu a raye”

Ita dai Dada son su rabu lafiya ya saka ta amince mata, dole ta hado yan kudaden hannunta dubu 30 ta bata tace gashi nan ta kaiwa Amirar ta riqe kafin Bashir din yazo se a san yanda zaayi haka ta rakata har get Addan na sake jadda da mata fa akan tana nan tana jiran saka mako da haka suka rabu.

Numfashi ta sauke bayan ta dawo cikin palour ta tazauna, gaba daya ta tasa ina zata kama akan wannan al’amarin. Har ga Allah bata so ta sake yin wani kuskuren akan na baya amma ya zatayi da Adda Fatu yar uwarta tilo a kaf fadin duniyar nan bata da kamarta. Addan tayi mata komai a rayuwa ya kamata ace ita ma ta saka mata da abinda ta mata. A zatonta Auran Bashir da Amira ya isa ga tukuicin kyautatawar amma se yanzu take dana sanin ma aikata hakan domin kamar ta bude wata qofa ce da Addan ta mayar da ita tamkar birin wasanta.

Ko da yaushe cikin daga mata hankali take tunda akayi wannan auran da ita dai bata ga amfaninsa ba in banda bacin rayuka da ya janyo da yawa, shigowar Nazir Autan ta ya sakata dagowa ta kalle shi
“Yanzu na hadu da fitinanniyar yayar ki a hanya seda tayi mun fashin 10k wallahi, gaskiya Dada ki ringa yiwa Adda fada abubuwan da takeyi basa dacewa. A yanzun fa ga kudi a hannunta amma ta tsaya suna fada da Dan Napep dan yace a 200 ze kaita gida”

“Hmm Allah ya rufa asiri kawai Naziru amma ni lamarin Adda ya fara bani tsoro, yanzu ma fa kaji abinda ya kawo ta” tiryan tiryan ta labarta masa yanda sukayi.

“Wallahi Dada ki kiyayi matar nan, ni dai ina ga Asiri take yi miki ma kike wasu abubuwan idan ba haka ba dan ta riqe ki ai ba baiwarta bace ke da kuma zata ringa juya ki yanda taso. Tun farko abinda muka guda a hadin wannan auran kenan amma kika rufe ido kika ce se anyi zumunchin ku ya qara qarfi ko ai gashi tun ba’aje ko ina ba kinzo kina dana sani. Shima Yayan banga qaddarar daya gani a jikin wannan mara mutunchin yarinyar ba daya yarda ya aure ta”

“To Naziru yaya zanyi Adda yar uwata ce da bani da kamar ta ka sani kuma farincikin Yayanta shine nata idan banyi mata ba a rayuwa ta wa zan yiwa?”

“Ai kuwa gashi nan, kafin da ki sake yanke wani hukuncin se ki tuna cewa Auranki kema yanzu lilo yake yi a garin faranta mata kuma baza muso ace Uwar mu ta shiga zawarci a wadan nan shekarun ba” ya fada ya miqewa dan ya fita dan dagaske Bala’in haushin Adda yake ji har ma da Dadan da yake ganin tana biye mata ne.

“Allah ma baze sa ba Naziru zan lallabata insha Allahu babu abinda ze faru ma” Dada ta fada itama tana miqewa dan neman abinda zata ci, ko karyawa batayi ba Adda ta doko mata sammako.

ADDA FATU
Bayan barinta gidan Dada gaba ta qara dan kuwa bazata koma gida yanzu ba dan tuni Amira ta gaya mata matar tazo karbar kudinta gata nan a tsakar gida tana ta zuba Rashin mutunchi akan Adda ta fito ta bata kudin ta sunce mata bata nan amma taqi yarda, gara ta qara gaba ko Allah ze sa ta dace ta samo wani abun koda taimakon da zesa Bashir ya turo musu kudin ne. Gidan Aminiyarta Haj Balaraba ta wuce, ta sami Balaraban a qofar gida an kira mata me Napep zata fita unguwa.

“Fatu daga ina da safiyar nan haka” ta fada tana qoqarin rufe gida.
“Ke zan tambaya Balaraba keda nasan se ki kai 12 ma baki tashi ba”

“Hmmm ta ina Kishiya na neman sabautani ina naga ta bacci, kinga yanzu ya akayi dan ni a tafe nake neman taimako zan tafi” Balaraba ta fada tana jefa muqulli a cikin jaka.

“Ai kawai muje dan nima matsalar ce ta kawo ni ma tattauna a hanya” nan suka fada Napep Balaraba ta fada masa inda ze kaisu. Suna tafiya Adda Fatu na jerowa Hajia Balaraba matsalinta.

“Ni na rasa wane irin shegen yaro ne Bashir wallahi naje gun malaman naje gun Yan Bori amma an kasa cin galaba akansa, ke har fa nafi ganin aikin kissa idan tayi masa akan na asirin nan wallahi dama Da Nafi nake samun yanda nake so a gurinsa to itama naga alamar tana so tayimun Bore. Ga shegiyar me kayan can da kika hadani da ita bashi kamar na masifa na kasa biyanta”.

“Tab ai seda na gaya miki daman ita fa Indo in kaci bashin ta wallahi toshe maka hanyoyin samu yake kika ce bakomai shiyasa kika ni kudi hannu muke sabga da ita gata bata san sabo ba akan dubu daya seta keta miki rigar mutunchi”

“Ai na gani kuwa yanzu haka fa tana can gidan tana ta tijara nidai na ce su Ummi su kulle qofa kar su bari ta shiga bare ta daukar kun wani abun, kudinta Dubu dari biyu yai saura da Mun samu kan Bashir zan tattara na biyata mun rabu kenan”.

“To ai shi wannan yaron fa se kin dage masa gaskiya amma bari muje nan gurin, Maman lurwanu ta kwatantamun tace aikinsa sha yanzu ne dan shi yai mata aiki akan Isah ya saki Kishiyoyinta dukka biyun rana daya yanzu bakiga yanda take shanawa a cikin gidan nan ba ita kadai” cewar Balaraba

“Kice Allah, ashe gara da nayo nan Allah yasa qarshen wahalata kenan (ko kuma farkon wahalar ki ba) in samu ina kafa Amira da kyau sannan in waiwayo kan nawa qananan kwarin ko da yake ni da zaman su da babu duk daya ai kin sani” haka suka ci gaba da tattauna wa har suka isa unguwar da aka mata kwatancen sedai ta kasa ganewa, sunyi tambaya kowa yace be san mutumin da suke nema ba kuma ta kira Number Maman Lurwanu a kashe.

Kamar Adda zatayi kuka ta kalleta tace “yanzu Balaraba ya zamuyi dan Allah wallahi na gama saka ran waraka ta zo” kafin ta bata amsa Me Napep da tunda ya dakko su bece komai ba, tsaf ya gama nade hirar su ta hanyar voice note daya kunna tareda fahimtar matsalar ko waccen su se ya kashe mashin din yace musu bari ya kama ruwa kafin su gama yanke shawara.

Can Nesa dasu yaje ya zaro wayarsa ya shiga kiran abokinsa aransa yana ayyana Banza ta fadi daga can bangaren aka daga wayar ana cewa “ungulu baka jewar banza da alama ta samu”

Dariya yayi kafin yace “yi maza ka shirya area, ka duba whatsapp na tura maka saqo nan da minti Ashirin zan qaraso idan ta saitu”

Dayan ya bushe da dariya yace”an gama kwaro kamar kasan wallahi dama ina ta lissafin ta inda zam samu kudin yiwa Latifa Anko gashi ta matsamin kwana biyu babu kasuwa, Allah dai yasa ta waru, se kun qara so toh” sukayi sallama.

Gurinsu ya dawo harda karbar pure water a wani shago ya fasa ya zubda rabi ya taho yana wanke hannunsa,
“To hajia ina muka nufa yanzu” ya tambaye su bayan ya kunna Mashin.
“Maidamu inda ka dakko mu kawai” Balaraba da abun duniya ya ishe ta ta fada, se ya cilla suka dau hanya yana jin yanda suke ta jimami. Daidai wani gidan mai ya tsaya ya sha, seda ya dan bata lokaci sannan suka ci gaba ya gama shirya abinda ze gaya musu se yayi gyaran murya.

“Am nace Hajia kuyi haquri fa dukda ban gane kan damuwar taku ba amma idan kuna so akwai wani guri da wancan satin nakai wasu passengers, can na jirasu suka gama gaskiya daga yanda naji sun fito nasan sun samu biyan buqatar data kai su, kun gama saqon daya daga cikin su daga Kano tazo ashe suka karbi Number dazu naje na karbo zan saka mata ta tasha akai mata” ya fada yana bude dan gurin da suke zuba kudi ya zaro baqar leda, basu san mene ne a ciki ba gadai shi harda suna da Number waya an rubuta ta wanda zaa turawa saqon. To wanda kwakwalwar sa ta toshe ai se a hankali ba tareda tunanin komai ba suka ce ya kai su, a ransa ya ayyana “Madallah” ya cilla kan mashin suka dau hanya dan yasan zuwa yanzu an kimtsa komai dukda haka seda ya sake yi masa text ya tabbatar masa komai is ready su taho.

Tafiyar yan mintina takai su layin gidan har qofar gidan me dauke da shago se kuma soro na shiga cikin gidan. Wasu yan samari biyu ya gani daga gefe kan dakali yai musu sallama tareda tambayar su ko Malam yana nan

“Ai kuwa ya fita amma nasan ba dadewa zeyi ba qilan ma yana hanya.. au ka ganshi ma muna maganar” daya daga ciki ya bashi amsa. Se ya nufi gurin Wizy abokinsa daya sha uwar babbar riga harda wani rawanin iskanci shi a dole ga malami ya miqa masa hannu suka kashe amma se ka zata musa baha sukayi. Cikin daga murya Yanda su Adda zasu jiyo su Wizy yace “Mal Kamar kaine ka karbi saqon hajia Larai dazu ko lafiya dai ko mantuwa kayi”
“Eh wallahi Malam nine ba mantuwa nayi ba wasu iyayen daki na na rako ne”

“Ah to to bismillah ku shigo ka barsu anan kuma kai Iliya me yasa baku bude musu shago sun shiga ba ko ka kaisu cikin gida gurin Maimuna kan nazo” ya fada yana hararar samarin da suke zaune. Seda Iliya yayi dagaske gurin riqe dariyar sa kafin yace

Please Login or Register in order to submit comment