Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ya sakko da shi inda take ya ajiye sannan ya koma ya dakko kwanon Fish din da Amna ta gasa.

Yana ci yana bata a baki har suka cinye se wani tarairayarta yakeyi kamar kwai, yanda yake rawar jiki da ita se yake tuna mata da lokutan baya a sanda yana Bashir din Ma’u kafin zaman majalisa da sababbin abokai ya sauya mata shi zuwa wani mutum na daban. Tana tuna irin gata da tarairayar daya ringa nuna mata a shekarar farko ta aurensu. A lokacin ya kan sakata taji tamkar tafi kowacce mace dacen miji duk kuwa da bata samu yanda take so ta bangaren kayan more rayuwa ba amma soyayya da tattalinta da ya ringayi yafi mata komai dan dama ita ai dan soyayya ta aure shi bawai kudi ba.

Suna gama cin abincin dakin suka koma, ta gaji tibis dan haka ta haye gado ta kwanta yana matsa mata jikinta. Wayarsa ce tayi qara, a tare suka duba sunan Amira da ta gani yana yawo yasa ta dauke kanta. Satar kallonta yayi karaf kuwa suka hada ido, haka kawai yaji wani abu kamar nauyin Asma’u ya kamashi cikin son basar wa ya dauke idonsa ba tareda ya amsa wayar ba.

Kiran da ya yanke wani ya sake shigowa ya sakata cewa “ka daga mana ba kiranka akeyi ba” seya dauki wayar, be zauna anan ba ya fita falo. Da kallo ta bishi tana qoqarin hana shedan yin tasiri akanta “Itama matarsa ce matsayinmu daya da ita” ta fadawa kanta sejin hawaye kawai tayi suna bin fuskarta.

Bata san randa zata dena jin zafin yankan bayan da suka mata ba. Da ace wata can Bashir ya aura koda cikin dangin nasa ne damuwarta bazata kai haka ba amma fa Amirah, Amirah data dauka tamkar Amna. Yarinyar da ta gama sanin sirrinta ciki da waje ita ya auro mata a matsayin kishiya se kawai ta rushe da kukan takaicin da duk sanda ta tuna yanda auran Bashir ya kasance seta yi shi.

Babu wanda ze gane zafin da takeji se wadda aka kwatantawa irin abinda akai mata, se yanzu take ganin dalilin da yake saka wasu matan aikata abubuwa da dama akan kishiya ko ma mijin kansa dan wallahi in akayi maka wani abun in ba me qarfin imani da tawallaki ba se kaji kamar bazaka yarda ba se ka dauki mataki. Har bacci ya dauketa Bashir be shigo ba se Asuba ta farka ta ganshi a bayanta.

Ko a fuska bata nuna masa komai tayi sallah a dakin sannan ta fita gurin yara dan jiya basu samu ko yin magana ba. Seda ta hada musu abinci suka shirya tareda zama suka fara breakfast sannan ta koma dakin ganin Baban Ali be fito ba.

A tsaye ta ganshi yana zuge jakar da yake tafiya da ita Gombe, dauke kanta tayi kamar bata gani ba tana cewa”Sun shirya fa gasu can sun fara cin abinci basu jiraka ba” tayi gaba da niyyar shigewa toilet dan bata so yai mata maganar tafiyar sa sedai tun kafin ta shiga ta jiyo shi yana cewa

“Ke zaki dauko su daga school yau zan wuce Gombe ne daga office bazan dawo ta nan ba” ba tareda ta juyo ba tace masa “Allah ya tsare ka gaishe su” tai shigewarta abinta.
Bin kofar yayi da kallo kafin jiki a sanyaye ya dauki Laptop bag dinsa da jakar kayan ya fita, seda ya kaisu mota sannan ya dawo shima ya hau Dining din amma se ya kasa taba komai.

Shiru yayi yana kallon yaran suna cin abincinsu har suka gama Ahmad ya kalleshi yace “Abbi ina Mami zamu tafi”
“Kuje mu tafi wanka take yi” ya fada yana miqewa. Har sun fita ya juyo zuwa cikin gidan, Bayaso su rabu da bacin rai kodan albarkacin farin cikin data bashi a kwana biyun nan. Harya kama Handle din dakin shegiyar zuciyar da take masa famfo ta zugo shi “to me kayi da zaka ke bata haquri ma?” Zuciyar ta raya masa, Seya saki qofar ya juya kawai.

Asma’u da ke zaune tana jiran tsammanin zuwan Bashir ya rarrasheta, ajiyar zuciya ta sauke jin an taba qofa harda qara narke fuska tana ayyana abinda zatayi ta gigitashi se taji shiru, the next thing ko se jin tashin motarsa tayi ta yaye window da sauri har sun wuce se qurar daya tayar, baki bude take kallon motar harya qule mata, “Hmmm” ta sauke numfashi kawai ta shiga shafa mai, bataso ta tuna abun ma bare ranta ya baci ita dai addu’arta idan Bashir nada rabon ganewa to Allah ya maido shi kan hanya.

Gombe gidan Addah
A daren ranar da Bashir ya turo musu da kudi tayi ta kiran Number da Malam Wizy ya basu bata samu ba, bata haqura ba tayita gwada Number har washe gari amma shiru gashi ta kira wayar Hajia Balaraba ma a kashe.

Jikinta dabe gama warwarewa bane ya hanata fita ta bari akan zuwa talata tasan ta warke seta je gidan Hajia Balaraban ta dai ci gaba da kiran wayar tasa ko zata samu cikin Sa’a kuwa ranar Laraba da safe tana kira ta shiga.

Ta gama ringing ba’a dauka ba seda ta sake kira aka daga. Muryar wata tsohuwa taji daga ji taji duniya har ta gaji tana cewa “kai ku duba nan waye ya bugo, Wizy da qaninsa Iliya suna zaune a dakin Kakarsu daidai lokacin sunzo gaishe ta, miqa wa Wizy wayar tsohuwa tayi tana sake cewa ya duba ga gani.

Sallama Adda ta sakeyi, fes Wizy ya gane muryarta se yai saurin datse kiran ya miqe yana cewa Kaka yana zuwa.

Can wani lungu ya buya yayi recharging wayar kaka ya dannanwa Adda kira.

“Salamu alaikum malam ina wuni” ta fada cike da zumudi
“Lafiya lau dawa nake magana” ya tambaya irin be gane ta din nan ba
“Nice Malam wadda Sani ya kawo mu (sunan da Me Napep ya gaya musu kenan)
“To to hajia ya gida naji ki shiru da alama buqata ta fara biya kenan”
“Wallahi malam na danyi rashin lafiya ne kwana biyu kuma na kikkiraka ma wayar a kashe” Addah ta fada

“Eh wallahi kwana biyu kam na kashe waya dan na shiga halwa ne inata ayyukan ku dafatan ana ganin haske ko”

“Sosai kuwa Malam ya fara samuwa”
“To haka ake so yanzu to ya akayi?” Ya sake tambayarta.

“Dama na samu wasu kudin ne nace bari na turo a ci gaba da aikin mu sameshi gaba daya”

“Kin kyauta kuwa ai ina tabbatar miki idan aiki ya kammala hajia nasan indai kin riqe amana har ni dinnan se kin mun kyautar kujerar hajji” Wizy ya fada yana tsallen murna jin wata banzar zata fado.

“Insha Allahu kuwa malam yanzu dai ka bada akawun a tura kudin nan ayi a ci gaba”

“Ba matsala da mun aje waya zan turo miki” sukayi sallama yana qara karanta mata qanzon kurege.

Harya fara typing account details dinsa wani tunani ya kawo kansa, idan ta tashi fa za’a Iya tracing dinsa ta banki, se yai saurin gogewa ya danna mata kira. Tana dagawa yace

“Hajia nace kudinnan ki cire su, akwai yaro da na aika qauye ya siyo ragunan wasu aiki bari naji in be tafi ba se ya biyo ya karba kawai ya wuce” da haka sukayi sallama.

Minti kadan ya sake kiranta yace ze turo yaro, nan ta zayyana masa Address ashe ma basu da nisa ya ma gane gidan daya daga cikin yaran mijinta abokinsa ne. Isma’il me Napep ya dannawa waya suka tafi tareda wani qaninsa me suna Nasiru da yai shigar me zuwa kasuwar qauye. Ko kafin su Iso Adda ta aika Ummi an ciro mata 80k kudin rago biyu yaro na zuwa ya shiga har palour ta ta bashi kudi ya jefa a buhu ya fice.

Gaba suka qara aka tsaya kowa aka bashi rabonsa ya zuba a Aljihu Malam Wizy ya zare sim din Kaka ya ballashi biyu ya zubar yana cewa “mun tatseta ya isa haka” suka sheqe da dariya.

To Addah Allah ya maida Alkahiri ya kiyaye na gaba 🤷🏽‍♀️🤷🏽‍♀️🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM (Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 9

Gombe
Ana kiran magriba Bashir ya shiga gidan sa na Gombe, tun qarfe hudu da rabi suka sauka tazarar tafiyar daga Akko zuwa Gombe ta kaishi Magriba.
A qofar gidansa Me Taxi din daya dauko shata daga Airport ya sauke shi ya fito dakyar yana jan qafa ga yunwa ga gajia tiqis saboda yau yasha aiki a office ga kuma tafiya dukda a jirgine.

Yana qoqarin bude get din a ransa yana ayya Allah yasa ma ta dawo gidan dan yana daga ciki rashin sanin ya kamatan Amirah a duk sanda zezo hankalin ta be taba gaya mata tazo ta gyara gida tayi girki dan tarbarsa ba se in ya tuna mata. Dama can tun tana yarinya yasan qazama ce ta gaske daga baya ne zama da Asma’u ya sa tadan chanza tareda koyar wasu abubuwan amma dukda haka tsaftar biri gareta. Zata yi wanka ta gyara jiki amma fa duk dattin guri haka zatayi zamanta.

Yana jefa qafa busassun ganyayen bishiyar da suka zube ne suka masa Maraba. Compound din ya hada uwar qura dama ga shi an fara Sanyi da Hazo a garin. Takaici ya qume shi danya tabbata bata dawo ba kenan.

Bangaren Asma’u ya nufa dan yasan yace zeje dakinsa na part din Amiran ma ransa ne ze qara baci. Seda ya kunna wutar bangaren sannan ya bude palour ya shiga da Bismillah. Komai na nan a kintse yanda ta barshi, cike da gajiya yake daga qafafunsa ya haye benen da ze kaishi dakinsa. Nan dinma fes dashi ya saka hannu ya yaye ledar da take shimfidawa akan Katifa bayan ta cire bedsheets din saboda qura sannan ya zube kayan daya shigo dasu.

Toilet ya fada ya dan daurayeshi yayi wanka tareda dauro Alwala ya fito. Harya idar da sallah beji alamar waniya shigo gidan ba ransa ya qara baci amma seya danne kawai ya janyo wayarsa ya kira Qaninsa Naziru ya kawo masa motarsa dayake amfani da ita anan. Bayan ya kashe se yayi dialing number Asma’u, deep down yanajin kaman dazu da safe be kyauta mata ba.

Har wayar ta qaraci ringing dinta bata daga ba, ya sake kira nan ma shiru se ya maida akalar kiran zuwa ga Amirah dan yaga alamar hankalinta ragaggene. Ai a qalla yaci ta kira taji yazo ko kuwa tunda tasan da zuwan nasa yau amma still itama bata dauki wayar ba.

Ajiye wayar yayi a kan gado cikinsa na cigaba da qugin yunwa shikadai se sakin qwafa yakeyi da ayyana hukuncin da ze dauka akan Amirah. Kusan minti 20 Naziru ya kirashi ya iso, se ya dauki wallet dinsa da keys ya saka a Aljihu ya fita. Naziru na ganin sa ya fito daga motar da niyyar bude get ya shigar masa da ita Bashir din ya dakatar dashi da cewa

“Muje ka kaini naci abinci yunwa nake ji”.
Suna tafe babu me cewa qala kowa da kalar tunanin da yakeyi a zuciyarsa, Naziru ne ya datse shirun da tambayar Yayan nasa Su Aliyu yace suna lafiya. Wani restaurant ya kaishi be fita daga motar ba ya bawa Naziru ATM yace ya yiwo musu take away ya karba ya tafi a ransa yana mamakin meya faru Amira batayi masa girki ba, tunawa yayi da tana da ciki se yai zaton ko shi ya hanata girkin amma dai ko yaya ne mutum ya taho gari ya gari har Lagos ai ko Indomie ta daure ta girka masa shidai ya siyo abincin ya fito.

Bashir kuwa bayan Fitar Naziru wayarsa ya zaro ya duba ko wata daga cikinsu ta biyo missed call dinsa amma yaga wayam. Na Ma’u be dame shi sosai ba dan yafi gasgata bata kusa da wayar ya santa sarai ko fada suke bata qin daukar wayar sa sedai ta daga tayi shiru amma ita wannan yarinyar fa?

In tana da hankali ai ita ya kamata ta kirashi ko amma gashi haryanzu ana neman 8 na dare bata kira ba. Har qofar gida Naziru ya kaishi ya shiga da Motar kafin ya fito yai masa sallama da niyar wucewa ya tsaidashi yace su shiga ciki.

Har saman ya kaishi yace ya gyara masa dakin dan baze iya kwanciya a ciki haka ba Bashir akwai tsafta koya datti yake a guri baya so abinda yake qara Masa son Ma’u kenan tsabtar ta ciki da waje ya jinjija mata ta wannan fannin sosai.

Har palour seda Naziru ya gyara tsaf ya goge ransa fal mamaki dan ya tabbatar yanzu Amirah bata gida to ko bata san ya zo bane? Shidai ya gama tattara komai ya tsaya jiran yayan nasa daya shiga daki ya fito. Kudi ya bashi yace ya hau mota tareda ce masa idan yaje gida ya cewa Dada seda safe ze shigo ya bishi ya kulle qofar ya dawo.

Yana shiga palour Asma’u ta kirashi se ya qarasa kan kujera ya zauna dakyau yana amsa wayar.

Asma’u.
Lokacin da Bashir ya kirata wayar ta na hannunta tana chatting da Umaima yayarta ce da suke Uba daya amma ita take bi a cikin gidansu. Akwai shaquwa sosai tsakaninsu dan kusan bata da Aminiya ma sama da ita. Hira suke yi tana gaya mata tafiyar Bashir din Gombe da yanda suka rabu.

“Ma’u kenan nidai bazan gaji da ce miki ki qara haquri akan wanda kikeyi ba, zuwa yanzu inda sabo ma ai yaci ki saba da wannan mood swings din nasa, ki watsar lamarin sa idan yayi dariya kiyi in ya daure kema haka. Ki kuma ci gaba da addu’a idan ma wani ne yake shiga tsakaninki dashi Allah ya miki maganin sa” cewar Umaima.

Tana cikin yi mata reply kiransa ya shigo tacewa Umaiman “kinga ma yana kira”
“Ki daga kiji me zece”
“Barshi kawai bazan daga ba se zuwa anjima sun kwanta zan kirashi” cewar Ma’u. Dariya Umaima tayi tana cewa

“Haba ai kuma ba zaki biye mata ku taru ku zama daya ba tunda ke kinsan abinda ya kamata, ki daga kuma karki nuna masa wani bacin rai ko wani abu dukda nasan ki ma Ma’ulle akwai sanin ya kamata ai” tayi maganar cikin sigar tsokana. Da “toh” Asma’u ta amsa ta ta kashe Datan bawai dan zata amsa kiran ba dan ta qudurce a ranta seta koyawa yarinyar nan hankali taji idan abinda take mata da dadi yanda take kiransa duk sanda taga dama kamar ita kadai take dashi.

Yanzu nema ta rage ada bata tashi kiransa wataran se sha biyun dare sun kwanta bacci, farkon wannan cikin nata ma lokacin tana laulayi akwai ranar da suna tsaka da soyayyarsu wurin 2 na dare ta kirashi wai ta kasa bacci se Amai take shine ta kira shima ta tashe shi.

Baqin ciki kamar Asma’u ta fasa ihu har bata san sanda ta fizge wayar ta tuttura mata ashar ba kuma saboda rashin adalci irin na Bashir qarshe ita yaji haushi akan me zata zageta bata ga cewa lalura ce ta sakata kiransa ba ranar kwana tayi tana kukan baqin ciki ai kuwa seda tayi masa yajin kusan wata dakyar ya shawo kanta ta sakko.

Sedata mula dan kanta ta gama komai sannan ta shiga daki ta kirashi, a yanda ta lissafa yanzu dole suna zaune ne suna hutawa dan haka tayi niyyar jan hirar har se illa masha Allahu harda loda kati a wayarta saboda tsaro (Sorry Ma’u wrong timing 😂😂😂😂).

Lafewa ta sakeyi a cikin gado sanda ya amsa wayar ta gaishe shi da tambayar ya hanya ya amsa mata da lafiya lau.

Rai rai ta saki jiki suka ringa hirar da sun manta rabon da suyi irinta, shi mamakin yanda ta sake kamar ba abinda ya faru ita mamakin yanda yake amsata sosai kamar ba Bashir ba yau ba Miskilancin nan babu baqin rai. Yanda take masa shagwaba kamar wata sweet sixteen yana biyeta gaba daya tagama narkar dashi a zaune, Hira tayi dadi tama manta da batun wai dan ta musgunawa kishiya yasa ta kirashi sema kwantowa kansu ruwa da sukayi gaba daya ta rudashi da salon da take masa magana shima ya rudata da masa salon, dakyar suka rabu a wayar lokacin 12 harta gota shima Asma’u ce ta kashe ganin yana neman sakata a uku to ai shi ga matar sa nan itafa sedai ta kama pillow batasan Gogan har ya fita shiga tashin hankali ba.
Haka ta kwanta tana juyi Kafin bacci ya saceta ranta fes koba komai dai Ta qunsawa Amirah.

Bashir
Yana zaune bayan sun gama wayar se zufa yake sharewa duk da sanyin Ac daya karade palour dan gaba daya Asma’u ta warware masa notin kai. Dakyar ya miqe ya nufi fridge din daya kunna tun dazu ya dakko ruwan sanyi ya kwankwada yana sauke ajiyar zuciya Haushin Amirah na sake ninkuwa a Zuciyarsa har ya gama wayar nan beji shigowar kiranta ko message ba gashi yanzu dayan dare ta kusa idan banda bata da hankali ai yaci ta kira taji ko lafiya ya taho ko be taho ba amma ina da dai ya mata alqawarin kudi ne be cika ba da yanzu ta ishe shi da kira kamar yaci bashin ta. Kwafa yayi a ransa yana jin kaman gobe ya juya Lagos kawai tunda zuwan nasa beda muhimmanci tunda bata damu ba.
Haka ya daddafa ya kwanta kafin ya samu bacci ya daukeshi.

Gidan Addah

Wuni Addah tayi tana bankawa Amira jiqe jiqen yan bori da magungunan mata ko tsoron halin da take ciki kar wani abu ya sami babyn basayi, bata haquraba seda Amiran ta fara sheqa Amai tukunna aka koma cushe cushe dana hayaqi. Bayan maganin gurin Wizy ta tura an sake karbo mata wasu duk ta banka mata a cewarta gara a hada hannu da yawa ayi maza buqata ta biya.

Babu lissafin zuwa ta gyara gida bare aje ga batun yi masa girki sukayi zaman su na jira yazo da kansa yace su tafi tunda a kwanakin ta sami kansa suna abin arziqi dan kiran da tayi masa jiya da daddare ma kuka ta saka masa akan ita dai yazo tana missing nasa in ba haka ba zata hawo jirgi ta zo Lagos sedai Anty ta basu daki.

A lokacin yasha mamakinta dan shidai Rashin kunyar Amirah na daure masa kai ko kadan bata jin nauyinsa wanda sam ba haka Asma’u take ba. Ma’u bata masa irin wadannan maganganun gatsal ta dai san signs da signals da take amfani dasu wanda suke bala’in burge shi da qawata zuciyarsa dan kullum cikin qara masa sabon ilimi take amma ita wannan se zance a baki ba abinda ta sani idan an zo wajen.

Se bayan Magriba ta shirya taci uwar kwalliyarta dan tasan zuwa sannan ya sauka Gombe. Ita sam tunanin taje ta gyara gida be zo mata da daman duk sanda zezo shi yake tuna mata to jiya da be magana ba itama tunda tsaftar ba damunta tayi ba se bata je ba a ganinta ai befi sati uku da zuwansa na qarshe ba gidan beyi datti ba ai. Tana zaune Adda na qara karanta mata yanda za’a yi suna jiran zuwan Bashir shiru se ji sukayi ana rufe qofar gidan ta kalli agogo 12 saura.

Seda gabanta ya fadi sanda taga missed call dinsa tun wurin bakwai ya kirata. A yanda ta lissafa sunyi waya sanda ze taso yace mata yanzu zasu taho kenan lokacin da ya sake kira yana Gombe ai ita yaci ta kira taji ya sauka.

To yanzu ya zatayi ta kirashi ne ko Aa haka tayi ta wasi wasi bata ko iya tankawa Addah dake faman sababi naqin zuwan Bashir din ba har tana da safe zata je ta samu uwarsa taji dalili dan baze ja mata asara ba wallahi.

Ita dai Amira daki ta shige ta chanza kaya dan Addah tace karta kuskura tayi wanka ance se ya kwanta da ita tukunna saboda abubuwan da ta sassaka, haka ta kwanta tana zullumin haduwarsu dan dai ta haqura bazata kirashi yau ba gara ta bari da safe se taji duk yanda ake ciki tasan dai ta kwafsa tabbas dama yaya ana lallabawa ne kuma yanzu ta sake ballo musu ruwa.

Tunanin qaryar da zata yanka masa in sun hadu ta shigayi amma duk wadda ta hado seta ga ze dago ta qarshe ta fawwalawa Allah kawai ta kwanta duk yanda goben tayi shikenan.

Washe gari Bashir tun qarfe takwas ya nufi gidansu, tun daga waje yake jiyo tashin muryar Addah data taso Amirah a gaba suka taho gurin Dada dan jin ina Bashir ya maqale dan ita bata magana a hankali. Bacin ransa ne ya nunku wato har sunada kwarin guiwar kawo qarar sa kenan ko? Se kawai ya juya dan bama ya so ya shiga yayi abunda ran kowa seya baci dan haka se kawai ya juya da niyyar fita, ya rigada ya makara dan tuni Addah ta hango shi ai kuwa ta shiga taratsin kiran sunan sa akan ya dawo bashida zabi ya juyo jin Dada ta saka baki fuskar nan a dinke kamar wanda yaga mutuwarsa ya nemi guri ya zauna yana muzurai.

Kallo daya yai wa Amirah data duqar dakai kamar munafuka dan bata so suka hadu a gidan ba yanzu se yace ita ta kawo qarar bayan wallahi Addah ce, seda tace kar suzo amma taqi gashi yanzu ta ja matana jangwam.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 10

Kansa a duqe yana jin yanda Addah take surfa bala’i kamar wadda akayiwa wani abu magana daya biyu seta zagi Asma’u da ya rasa me ta tsare mata a rayuwa. Shifa Addah na bashi mamaki wallahi, idan ya tuna fuskar data zauna da Ma’u ada da kuma bayyananniyar fuskarta ta yanzu. Qiri qiri ta babbake ta hanashi magana bare ya yi nasa qirafin qarshe ma se suka dora masa laifin ai shi ya kamata ya biya ya dakkota tunda yasan halin da take ciki.

Baqin ciki kamar ya fashe lokacin da yaji Dada tana cewa Amirah ta tashi ta bishi su tafi yanzu se ya miqe yai waje fuu yayi waje ba tareda ya shiga ya gaisa da Mahifinsa da kuma Abokiyar zaman Dadan ba. Har suka dauki hanya be ko kalli Amirah data takure saboda tsoron abinda ze mata ba, ita dai bata so akace ta biyo shi ba dan su basusan Bashir bane shiyasa.

Tasan shirun sa ba Alkahiri bane dan haka ta saka ido tana jiran karbar hukunci har suka isa qofar gidan. A waje yai parking ya kashe motar ya fito yana gaba tana binsa a baya. Da key dinsa ya bude palour ta takaicin sa ya nunku ganin tarin datti a palour kamar wanda akayi biki dan robobin lemo ne da take away pack ko ina.

Waiwayowa yayi ya kalli Amirah da jikinta ya fara rawa dan ita se yanzu ta tuno da bridal shower din bikin Qawar ta da sukayi sati biyu daya wuce a nan din, kuma koda suka gama bata gyara ba ta bari akan se ze zo tazo ta share aam kuma ta manta. Nan da nan ta fara inda inda tana tattaro rantsuwa dason yi masa bayani ya katse ta

“Zan fita wallahi ko mutuwa zakiyi kafin na dawo ki tabbatar kin gyara gidan nan har compound ki fita ki share, in kin ga dama karkiyi ko kuma ki kira wani ya taya ki zaki gane wane ne Bashir shashasha da bata san ciwon kanta ba” yai maganar cikin fushin da har a muryar sa take ji kafin yasa kai ya fita.

Ita kam indai iya hukuncin kenan ma ai tazo da sauqi, tasan Yaya Bashir da qazanta ko yaya yanzu za’a ji kanku kuma shi in kayi masa laifi yayi magana abun nada sauqi amma idan muskilancin nan ya motsa se yafi shekara yana azabtar dakai ba duka ba zagi to ita gara yai mata hargagin ya bata horo shikenan tasan ya wuce.

Hijabin ta ayije ta debo kayan shara. 3 Bedroom ne a part dinta kowanne da toilet a ciki biyu nata se nasa daya, Madaidaicin palour,kitchen da store a ciki se Dining area. Nasa dakin ta fara gyarowa ta nutsu sosai dan gudun kuskure, ta share ko ina ta wanke toilet sannan tayi mopping. Bedsheet ta shimfida ta cire tsohon ta boye dan tasan ya gani

Please Login or Register in order to submit comment