Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

samun aikin nan kusa, abinda yasa muka zo din ma saboda kaga kar aga kamar wasa ne abun” Aminin Baban su Bashir Malam Salisu ya fada.

Se Baffa yayi murmushi yace “Babu komai Malam Salisu in sha Allahu babu abinda ze gagara, kuje kuyi shirinku iya abinda ya zama dole sadakine se ya nemi muhallin da ze ajiyeta duk abinda ya kakare masa yazo ya sameni babu komai” suka yi sallama suna ta godiya, haka suka koma gida suna ta yabon dattako da karamci irin na Baffa, dan lokacin da sukaje gidan daya daga qannen Baban su Bashir din har yana cewa anya za’a barsu su shiga kuwa shi Bashir me ya kaishi dakko abinda yafi qarfinsa.

ASMA’U

Ina kwance ina ta baqin raina tun jiya har yanzu ban ware ba, gaba daya na rasa ya ma zanyi dan bazan iya hasaso rayuwa da wani namiji da ba Bashir ba. Addu’ata kawai Allah ya mantar da Baffa karya kuma tado mun da maganar har zuwa sanda zamu samu mafita.

Ina cikin wannan tunanin Baba Jummai shugabar masu aikin gidan mu ta shigo dakin ta sakar mun guda a tsakiyar kai, da saurin gaske na toshe kunne ina zare ido ita kuwa se sake rangada abarta take ragowar na taya ta.

“Uwar dakina ta zama amarya mun shaida mun tauna goro da alawa Allah ya nuna mana randa zamu sha taushen daurin aure” ta fada kafin ta sake kwasar wata gudar.

Wani mugun bugawa qirjina yayi, waye ya kawo goro na? Na shiga uku kardai fa Baffa ya amsa wa wani daga cikin manemana magana.

Dafe qirji nayi na qara fito ta idanu waje nace “Baba Jummai gorona aka kawo dawa?”

“Wato Uwar dakina kina nan da halin ki na tsokana, baki ma san waya kawo goron ba kenan, to wannan Me gidan da baya dariya ne Engineer kike ce masa kowa” Baba Jummai ta fada.

Se naji kamar an kwararamun ruwan qanqara a tsakiyar kaina, wata wawuyar ajiyar zuciya nayi kafin na koma na kwanta ina yiwa Allah tasbihi. Gaskiya Bashir ya shammaceni.

Waya ta ce ta dauki qara, a jikina na ji cewa Bashir ne, seda na tura baki kamar yana gabana kafin na daga wayar.

“Amaryata” ya fada cikin qaramin sauti, shiru na masa ina ta faman juya baki kamar yana gaba na ina jinsa yayi murmushi yace “Fushi ake yi dani ko Ma’una ayi mun afuwa. Gani a qofar gida nazo bada haquri”.

“Ni bazan fito ba” na fada cikin muryar shagwaba, se ya marairaice shima yace

“Haba mana Amaryata so kike yi na kasa bacci dan Allah ki fito na ganki mana kafin nan da wata shida na dauke ki gaba daya ki zama tawa”.

Rufe fuska ta nayi ina murmushi nace “Dagake bazan fito ba, nima ai jiya banyi baccin ba kaga mun yi 1-1 kenan ka tafi se bayan sati uku zaka sake ganina”.

“Kice kawai sena zare sannan, ki taimaka mun nidai ki fito na ganki ko minti daya ne ki koma na yarda”.

Seda naja masa rai kafin na zura dogon hijabina har qasa na fita, a palour na tarar da Goggo da su Nasir suna kallo naja hannun Mimi yar dakin Hajia Umma ce muka fita.

Bashir na tsaye daga bakin Get gurin masu gadi, har wurin naje nace masa”A nan ka tsaya maimakon ka zauna, muqarasa toh”.

“Aa Gimbiya daman zuwa nayi naga kyakykyawar fuskar ki sannan na kawo miki wannan(ya miqo mun wata farar leda da kwali dan kwali qarami a ciki) ina so na kwanta da wuri gobe zanje wata Interview kiyi mun Addu’a Allah yasa a dace”.

Karba nayi ina cewa “In sha Allah za’a dace, Alah ya bada nasara”.
“Amin” ya amsa mukayi sallama ya tafi ina juyowa mukayi kicibus da Fahad sun taho shida Anwar yayan Alawiyya da take bi.

Fahad qanin Hajia Anjin ne shine auta a gidansu, Fari kyakykyawan saurayi me qirar larabawa ga iya soyayya dan da ace da Fahad na fara haduwa kafin Bashir inaga da yayi nasara akaina saboda iya tsara zancensa.

Hararar sa nayi ta gefe ganin irin kallon da yake mun yana murmushi kafin nace “Uncle Fahad ina wuni”

“Karma ki wani ce mun Uncle, yau dai naganshi daman akan wannan Kika qi ni Asma’u gaskiya kin fado da yawa, har naji sauqin radadin da nake ji tunda nafi wanda ya kasanin sau dari wallahi kuma har yanzu ban cire rai akanki indai ba gani nayi an daura miki aure ba bazan cire ran zaki zama mallakina ba” Fahad ya fada yana kafeni da idanunsa masu kama dana mage, sena fizgi hannun Mimi nayi gaba ina cewa

“Se kayi ta saka ran ai kar Allah yasa ka cire, wai ace ba’a san mutum amma su kamar mayu sun nace kuma ahakan dai shi yayi mun baku ba”

“Indai akanki ne ki kirani sarkin Mayu ma qarewa kenan Asma’u dan sena cinye ki hankalina ze kwanta”.

“Daga murya nayi yanda ze jini nace “sedai ka ci kanka dan kurwa ta daci ne da ita” na murguda masa baki harda fari da ido kafin na shige inajinsu da Yah Anwar suna mun dariya.

Haka kawai duk wanda yaga Bashir seya kushe mun abuna, su kyau da kudi yake a gabansu ni ba matsala ta bace ba.

Sannu sannu watanni naya shidewa harya rage saura wata daya bikin mu kuma a daidai lokacin muka gama jarabawar semistar farko a ND1 zamu shiga hutu.

Sosia hankalina ya kwanta tunda zancen auren mu da Bashir ya kankama nayi fresh abina na qara kyau da haske musamman ga gyaran jiki da tuni Hajia Umma ta fara tsuma nan da nan jikina ya sake mudewa ko ina ya cika bazaka taba iya mun kallo daya ka dauke ido ba se ka qara.

Bashir kansa wani lokacin idan ya kalleni yakan ce “anya Ma’u banyi zari ba kuwa ki kalli kanki ki kalleni ai se ace dan aiken ki ne ni” in ya fadi haka se nayi dariya nace
“Kai dai ka godewa Allah kadai dan shi yake yiwa bawa kyauta irin wadda beyi zato ba.

Ana biki saura sati uku aka kawo Lefen Junaidiyya daga Birnin Tarayya Akwati na dukan Akwai saiti hudu masu shida shida. Kaya kam sedai ace masha Allah dan komai yaji harda danqareriyar sarqar gwal dinta yar dubai ga kudin da suka doro akai dubu dari haka dangi a ka dauka ana ta murna yarinya tayi Goshi sati daya zagayo aka kawo na Yah Fati da Yah Bilki rana daya suma bangaren kowanne sunyi Bajinta akwatinan su Dozen Dozen da dubu hamsin hamsin akai.

Na Alawaiyya ne qarshe ana saura Sati daya suma suka dunguma masu algaita nayi maroqa nayi aka kawo sha tara ta arziqi kai komai dai se sambarka mutane anata yabawa kowa fadi yake saura Na Ma’u kowa naso yaga Lefeen ama’u yasan ba qaramin Miji na fallo ba nidai a raina nace kwaji dashi idan ma gulma ce ta qare muku dan ni banji komai ba da ganin Lefen su na taya su murna kuma ban damu ba dan tuni Baffa ya gaya mun yacewa Bashir ba se yayi lefe ba ya nemi gidan da ze sakani kawai, dan haka ma ya bayar da kudi masu yawan gaske yace aje Kano a hado mun duk abinda Amarya zata buqata sannan duk wata hidima zanyi ta biki Alhaji Qarami yace na gaya masa ze bani kudin to me ze dame ni kuwa.

Har satin biki Bashir nata fafutukar neman gida, duk yan gidaje masu kyau idan ya tambaya se yaji kudin ya shallake Aljihunsa gashi kuma a qalla dai yana so ya samarwa Ma’u muhalli me kyau kodan halaccin da akayi masa a zamanin nan adauki Mace kamarta daga irin gidansu a bashi babu lefe ai wallahi an gama masa komai.

Dakyar ya samu wani gida anan unguwar su babu nisa sosai, gidan dukda tsoho ne amma fasalinsa nada kyau 2 bedroom flat ne se babban palour harda Gurin Dining ga Kitchen da dan qaramin store sannan daga waje akwai wani dan palour haka qarami ga bandakin baqi a tsakar gidan se dan fili da ze ci mota daya.

Da yake ginin tsohone sunyi dakunan manya a wadace duk girman gado zasu iya dauka kuma da akwai bandaki a kowanne daki matsalar da babu tiles sumuntine a dakunan palour kadai suka sakawa tiles din.

Tareda Aliyu suka sha buga bugar neman gidan, bayan sun samu bayan ya biya Aliyun yace masa ya kamata ya gayawa Ma’u tunda tun wancan satin take masa maganar gidan dan tuni anje anga na sauran har ma jiya an tafi kafin Abuja da Bauchi na su na cikin Gomben ne yayi saura, da za’a siyo kaya ma da farko Anty Saratu Babbar Yayarsu Mace itace akan yin order kayan daman tafi kowa jin takaicin auran Bashir da za’ayi cewa tayi baza’a siya musu iri daya da Asma’u ba dan tasan Bashir bashida gidan da za’a zuba su, seda Hajia Babba tayi mata kaca kaca tace kuam karta kuskura ko cokali abanbanta in yaso idan an rasa inda za’a zuba a bawa Ma’un kayanta ko siyarwa ne tayi tasan dai an mata yanda akayiwa yan uwanta.

Ita dai Goggo nata Ido, ko Suhaima data kira tayi qorafi cewa tayi babu ruwanta matar mutum kabarinsa kuma ita bata ga aibun Bashir ba da za’a ce baza’a aure shi ba.

Washe gari sukaje da ita da Bashir din da Aliyu se Alawiyya yar uwa ta rai da rai. Ita kam gidan ma ya mata a haka, bandaki ne matsalar dan duk ya dafe nan take a cikin kudaden data karba ta ware ta bawa Bashir din dakyar ya karba tace a canza kayan bandaki har tiles din qasa dana bangon a cire, ya hada da abinda yake hannunsa ayi sauran gyare gyare da fenti idan yaso dakunan se a saka carpet kawai a ciki,

Haka kuwa akayi a cikin kwana biyu se ga gida ya dawo sabo dan gyara aka masa gangariya kai bakace tsohon gidan nan bane, ana i gobe kamu kuwa aka je aka jera mata kayan ta sega gida ya fito shar yaji kaya yan order. Gadajenta biyu Yan Turkey masu kyau da tsada ga kujeru na alfarma da kayan kallo kai duk wani abu da ake siyawa yar gata an sakawa Asma’u haka kayan Kitchen sosai Goggo ta gwangwaje su da kuloli tunda duk Baffa ne yake siyan Electronics iyaye mata su saka abinda babu ai kuwa tayi qoqari kai baka ce auran Yaya uku take ba.

Tsaf aka shirya gida har yan jere na cewa wai daman qaramin guri yafi kyan kwalliya se suka ga kamar jerenta na neman yafi na masu manyan gidajen kyau.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 34

Ranar Juma'a aka daura aure na da Bashir, Juma'ar data shiga cikin jerin rana kun tarihin rayuwata na farin ciki da bazan taba mantawa da su ba. A qa'ida ranar da aka daura aure a gidan mu ake kai Amare amma mu ba'ayi haka ba saboda Dinner da manyan Yayyenmu suka shirya zasuyi a daren ranar sauran Yayyen mu mata se tsiya sukeyi wai an fi son mu su kuwa kamar ana jira da an daura ake kwashe su.

Da yake tun ana sati daya da biki muka san da shirin Dinner, nasan dole sauran Angwaye zasu gwangwaje suyi shiga ta alfarma tunda suna dashi dukda Bashir ma nasan ze yi iya qoqarinsa amma baze iya kamo su ba saboda tattalin arziqinsu ba daya bane su duk masu dashi ne.

Haka na samu Baffan mu na tasa shi da naci seda ya bani shadda yadi goma cikin irin wadanda yake dinkawa ni kaina bansan kudinta ba kawai dai nasan suna da kyau kuma ko cikin Mutane ina dadewa banga wanda ya saka irinta ba sefa manyan irinsa.

A gurin Yah Mustapha  na samu hula harda takalmi daya siya dan daurin aure saboda duk gidan mu ya fisu gayu, dakyar ya bani wai order su yayiwo takanas seda mukayi ma zan biya kudin rabi nidai dana samu suka zo hannuna nace a gudunmawar sa, yana ji yana gani na masa fin qarfinsu se na bawa Yah Abubakar shaddar nace ya kaiwa Bashir dinki tunda abokinsa ne yasan Size dinsa na roqeshi dan Allah karya gaya masa ina so na bashi mamaki ne.

"Ma'u kenan, yanda kike son Bashir kike tattalin sa Allah yasa kar wata rana yayi miki halin mu na maza" abinda Yah Abubakar ya gaya mun kenan a lokacin da se naji jikina yayi sanyi.

Gaba daya daman na lura dashi kamar hadi na da Bashir beyi masa ba na rasa dalili dan har tambayarsa na tabayi yace mun babu komai, da yake daman shi ba mutum ne me yawan magana ba se na bar maganar kawai nasan idan da Bashir nada wani mugun abu baze barni na aure shi ba.

Tsaf na hade kayan nan bayan an dawo daga daurin aure angwaye sun shigo aka dauki hotuna, masha Allah gaba dayan mu munyi kyau kuma ko wacce ta dace da zabin ta se fatan Alkahiri dangi da abokan arziqi suke yi mana. Suna shirin ta fiya nayiwa Sadiya qawata rada dan daman ita na bawa ajiyar Kayan tayi maza taje ta dakko su, seda suka fita tabi bayan Bashir din ta bashi.

Muna zaune a bangaren da qawayen mu anan ta hira irin wadda ko wanne qawayen Amarya sukeyi idan ana biki, hayani ya na tashi wayata dake hannuna tayi qara, Bashir ne daman zaman jiran kiransa nakeyi sena miqe da sauri na shige bandaki na kullo qofar ko naji maganar sa dakyau.

"Ma'una kayan menene wadannan, ina kika samo shadda me bala'in tsada haka?" ya tambayeni bayan dana gaishe shi.

"Kamanta an jima akwai Dinner da za'ayi, kalar kayan da zan saka ne zamuyi Anko".

"Ina sane har ma nayi dinki nima, mantawa nayi sam ban ma gaya miki kalar nawa kayan ba ai" ya fada daga daya bangaren, sena marairaice nace

"Se ka ajiye su gobe ka saka idan za'ayi budar kai nidai yau wannan nake so na gani a jikinka".

"Shikenan an gama Amaryata, na tabbatar yau ke kadai ce zaki fini yin kyau a gurin nan"

"Haka nake so Angona yafi na kowa, se anjiman idan kunzo, kar dai ku bata lokaci qarfe takwas zuwa Goma Baffa yace za'a tashi" daga haka mukayi sallama na kashe wayar.

A filin tsakar gidan mu aka shirya za'ayi dinner, tun la'asar masu decorashan din da aka dakko suka katange iya inda suke buqata suka fara aikin su, kafin magriba sun gyara guri tsaf se ka rantse wani babban dakin taro ne.

Seda mukayi sallar magriba sannan aka fara shirya amare, munyi kyau har mun gaji cikin dinkin riga da skirt na wani hadadden material da akayi mana kowa da kalar nata da ze dace da shigar Angonta, munsha daurin goggoron mu me kyau dan fa fashion designer guda aka dakko ta shirya mu dukda a sannan ba'a fara kwalliya me fente fenten nan ba amma ta tsatso mana kyau da iya abinda ake amfani dasu a sannan.

Har mun saka kayan sarqoqin mu Hajia Umma tace mu cire, saitin sarqa, awarwaro da zubuna ta kawo mana na gwal qirar dubai wanda sallama ce Baffa yake bawa Iyayen mu mata kudi su siya mana idan za'a kaiki dakin ki saka shi ta bawa kowacce nata ta saka nan da nan kwalliyar mu ta qara qawatuwa se walwali mukeyi ta ko ina.

Seda mukayi sallar Isha'i sannan muka fita babban palour inda kafatanin yan gidan mu mu a lokacin mu talatin da tara ne muka hallara ga Baffa da Matansa Hudu aka shiga daukar hotunan family.

Lokaci daya hawaye suka balle mun kamar sauran na jira kuwa muka dauki kuka wiwi wanda nasan na zallar murna ne Baffa kansa seda ya kauda kai gefe ya goge kwalla ganin irin wannan arziqi da ubangiji yayi masa.

A ko da yaushe kalmar godiya ga Allah bata taba barin bakinsa, ya bashi lafiya, ya bashi arziqin mata, dukiya da Tarin Yaya ya kuma shirya masa su, sannan be jarabce shi da wani babban Alkaba'i daya dame shi a rayuwa ba banda qananun abubuwan da kowanne mumuni ba'a gaza jarabtar su dashi to shi kuwa me zeyi idan be godewa Allah ba da kuma Addu'ar neman cikawa da Imani dan abinda ya rage masa kenan a yanzu.

Bayan mun gama hoto da yan gida Angwaye ma suka shigo, kowa yayi kyau amma wallahi Bashir dina ya fisu dan se ya zama tamkar wani wata a cikin taurari kamar yanda na zama Zara cikin yan uwa na, haka muka sha hotuna musamman da iyaye da manyan yayye suka fita aka bamu guri nan muka baje kojin mu aka dauki hotuna kala kala kafin muka dunguma zuwa gurin dinner.

Taro ne akayi shi a tsare harda Baffa duk fulatancinsa seda Yayyen mu suka tilasta shi ya dan zauna a teburin da aka shirya masa da Aminan sa da be ma san an gayyato su ba, ganin su ya sa ya saki jiki haka iyayen mu mata Goggo ce dai seda aka kai ruwa rana dan seda muka yi mata hawaye nida Yah Bilki sannan ta fito se wani jan mayafi take tana rufe fuska yanda kasan ita kadai ce bafulatana a gurin.

Cikin Awa biyun nan akayi komai aka tashi, anci an sha abinci na alfarma qarshen dai yan gayun Yan Abujan ma sun yaba gashi komai a tsare babu kida balle ayi rawa irin slow music din nan aka saka kawai aka ci abinci aka dauki hotunan tarihi seda aka fara watse wa nema qannen mu suka dage se an saka musu kida ai kuwa waqa biyu aka saka Baffa na hango yanda aka hade mata da Maza ana rawa yace a kashe kowa ya tafi haka muka kwana ana ta hirar taron nan dan babu qarya munji dadin sa.

Washe gari da wuri aka miqa mu. Munsha kukan rabuwa, Junaidiyya aka fara tafiya da ita dan jirgi sukabi qarfe goman safe suna tafiya yan Bauchi ma suka dauki Amaryar su, kafin qarfe biyu an tafi kai Yah Bilki da Yah Fati ni kadai nayi saura tunda kusa da gida ne.

Seda aka dawo daga kai su aka baro wadanda zasu tsaya musu budar kai kamar yabda kowa yasan Al'adar mu ta Gombawa, anayin sallar La'asar nima aka kwashe ni se gidan su BShir inda za'ayi budar kai na.

Seda aka damqani a hannunsu, ga kayan garar da kashi biyu akayiwa ko waccen mu, ta gidan su miji daban tamu daman tun da akai jere kowa an kai mata gidan ta sannan ga turame da kwanuka harda Saitin Gado da akeyiwa Uwar miji seda akayiwa kowacce babban Gado dan Dubai haka aka kai musu.

Bayan sun biya kudin budar kai da Turmin zani da tabarma nan qanne da abokan wasan Bashir suka fara zuwa kowa ta ajiye kudinta se ta fadi sunan da ta sakamun, wannan yar farar yarinyar da muka gani randa muka zo gurin Bashir ta taho da gudunta da naira goma a hannunta.

A inda taga ana ajiye kudin ta ajiye kafin ta kama mayafina cike da rashin ji har tana neman ture mun daurin dankwali ta bude fuskata tana cewa "Na saka mata ANTY" mata suka dauki guda kowa ya yaba da ganin kyakykyawar Amaryar Bashir, hannunta na kama na zaunar da ita nace "Yaya sunanki?"

"AMIRAH" ta fada tana yar dariyar yarinta, nan da nan naji ta shiga raina saboda ina da son yara daman gata yar fara kyakykyawa da ita.

Anyi Budar kai lafiya seda aka kira sallah aka tashi, yan uwana sun mun kara dan ba qaramin kudi suka zuba mun ba haka dangin Bashir ma ba laifi sun mun liqi sosai bayan an gama qawayena suka tattare mana kudin mu muka koma dakin Bashir inda nan aka gyara aka sauke mu.

Anan muka kwana se washe gari muka tafi gidan mu daga ni se Bashir dan daman ba'a raka amarya mu iya kacin su gidan su miji se ku qarasa keda shi kawai.

Soyayya me tsafta suka shimfida a cikin gidan auran mu, ban qara tabbatar da Bashir yana qaunata ba se a yanzu dan a aikace yake nuna mun duk abinda bakinsa baya iya furtawa.

Cikin sati daya da mukayi wata irin shaquwa me qarfi ta sake shiga tsakanin mu dan kullum muna manne da juna babu inda yake zuwa se masallaci da yayi sallah kuma ze dawo gida kuma har zuwa sannan babu wanda yazo mana kullum gidan mu a kulle muna ciki muna kashe juna da soyayya.

Matsalata daya da Bashir dan irin taya aikin nan da naji ana cewa Angwaye na taya Amaren su shi bayayi, yana zaune zanyi komai na sedai na kawo masa idan muka ci abinci yana zaune zan tattare kwanuka naje na wanke qarqari ya zo Kitchen din ya tsaya ina aiki muna dan hira idan yan maganar na kansa kenan dan Bashir be fiya magana ba, miskiline seta raya masa sannan ni kuma gani da dan banzan surutu dole da qarfi da yaji tasa yake biye mun wani lokacin kuma na qaraci maganata idan na ishe shi ya jani ya kashe bakin maganar da Zazzafan Kiss shikenan.

Seda muka kwana goma sannan muka fita, da yamma Aliyu yazo da yar motarsa one door daya siya dan shima ya samu aiki tuni kuma da yake bashida wani nauyi akansa shiyasa har ya iya siyan mota.

Muna tafe yana tsokanata wai me nake bawa Bashir a dan lokaci haka yayi kumatu ya yi haske shima ze zo a ringa samma sa miyar Amarya ko ze dan farfado nidai murmushi kawai nakeyi irin najin kunyar nan har muka je gidan su Bashir.

Cikin farin ciki Dada ta karbe mu harda Anty Amina Babbar yayarsu da bata koma Bauchi ba tunda tazo biki. Haka sukayi ta jana dan saki jiki nidai ina ta sunkuyar da kai, da Dada taga haka se ta tashi ta barmu ai kuwa na dan sake dasu dan basu da duhun kai nan da nan muka saba mukayita hira. Dab da Magriba Alhajin su ya dawo, seda sukayi sallah kafin Anty Amina ta rakani muka gaisa se saka mun Albarka yakeyi.

A gidan mukaci abincin dare sannan Aliyu ya dawo muka tafi bayan na ajiye musu tsarabar da na kawo na manta ta a motar Aliyun ina jin Dada na Tambayar Bashir mun shiga gidan su Addah kuwa yace Aa, tace yayi qoqari ya kaini mugaisa.

Da muka fita a zatona zamu shiga gidan mu dan tun tuni a qagare nake, saura qiris ma na dauki Fainusa dazu muje amma dai na danne .
Ganin da nayi Mun dau hanya har mun wuce gidan yasa na tabo Bashir nace

"Baza muje mu gaida su Baffa bane naga mun wuce gidan?"

Be tareda ya waiwayo ya kalleni ba yace "Ai ni munje dasu Aliyu ranar nan mun gaishe su, ke kuma ba yanzu ba. Se kinyi wata sannan zamuje" ya maida kai suka ci gaba da maganar su da Aliyu. Tsabar takaici bansan sanda kuka yazo mun ba. Muzo har unguwar ina kallon kofar gidan na mu yace wani bazan shiga ba se nayi wata amma ai shi munje nasu gidan idan Adalci ne me yasa be bari duk maje lokaci daya ba.

Sakin kuka na nayi ya fito fili, Yah Aliyu ya shiga bani haquri yana cewa Bashir "muje mana ko a tsaitsayene ta gansu" amma mutumin nan mirsisi yaqi magana har muka isa gida Aliyu ya ajiye mu na shige na barsu a waje yana wa Bashir din mitar be kyauta ba.

Ranar haka na share shi, bayan mun kwanta ina jinsa yana wani shafani nai masa banza qarshe yaja tsaki ya juya ya kwanta nima na gyara kwanciyata a raina nace "kaima kaji yanda naji idan da dadi ai".

Haka na tashi washe gari babu walwala, nayi duk abinda na saba na koma daki na kwanta, ina kallonsa se zarya yakeyi yana kallona amma dan baqin hali ya gagara bude baki yayi mun magana haka muka wani har dare dadai yaga abin nawa bana qare bane se jinsa nayi a cunkushe yana cewa

"Dan bamu shiga gida jiya bane wai kike ta wannan Fushin to shikenan wani

Please Login or Register in order to submit comment