Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

har mun fita Samurah ta kwaso da gudu tana tambayata wai
“Anty zan samu chanjin sabon kudi?”

“Sabon kudi ai yana banki Samirah, ki nemi Sa’ad mana sune ma’aikatan banki” na bata amsa muka qara gaba.

Oh ikon Allah, ada fa idan zanje gidan irin haka sena shaqe uwayen kuloli da Abinci kala kala, Dubu Goma nan sena aje mata ta goron sallah banda wadda zan rabawa kaf jikokin gidan idan sunzo sannan su kansu qannen nasa wasu su fake da chanjin sabon kudi wasu kuma kai tsaye ma zasu ne na basu barka da sallah idan kuma zamu tafi nawa Yayan ko yar biyar babu me basu idan ba Amiru ba shi daman har gida yake zuwa ranar idi tareda Sa’ad da Naziru suci tuwon sallah ya raba musu kudi amma matan babu me karar ko dan kunne ta kawowa Farida seni jaka na hidimta musu nayiwa Yayansu kai kar Allah ya kawo abinda baze wuce bama.

A daren ranar Alhaji Qarami yaki rani bangarensa yana tuntubata wai ya muke ciki da Yusuf?
“Mutumin nan na qaunar ko Ma’u, dukda baka shaidar Dan Adam amma ina kyautata masa zato akanki wallahi ga danginsa suna sonki”

“Uhm toh Yaya nidai ina ta Addu’a Allah ya zabamun mafi Alkahiri dai, kuma fa shi Yusuf din nan ma ni ban gama gane masa ba. Wai ita matarsa wane irin aure nema suke tana wata duniya yana wata nifa sau daya naji yace yaje can inda take” na fada ina gyara zama.

“Wayaga Ballan sori, ke har lissafin wannan kikeyi ma ai in kinji ana da ita da babu duk daya to wannan mata ta Yusuf kenan. Ita fa tsabar Gayunta ne ta girmi zaman Najeria, daman yar uban gidansa ce Ambassador Musa Manzo ya aureta uwarta Baturiya ce.

Shikansa Baban nata irin wannan gantalallen auran sukeyi da uwar tana can America shi da sauran Matansa suna Nigeria se sanda yai ra’ayi yaje ko ita tazo to itama Inteesar din da akwai yayarta itama me aure ce duk haka dai suke wannan gantali da Yusuf din.

Dan haka ma ki saka ranki a inuwa kamar ma ke kadaice bakida wata kishiya dan yanda kika San ba Mata ba wallahi. Su yawon shaqatawa da zaga duniya da kwalliya suka saka a gaba. yo tikita ta yanka masa fa yaje ya nemi duk wadda yake so akan dai tazo Nigeria tayi zaman aure wai kuma a haka sonsa take kamar me badan ma Allah yasaka nutsatstse neba aida yayi tambari yanzu a neman matan banza tunda auren fa kusan shekara biyar kenan ana wannan gantalin kawai ki amsa mana musha biki se mu daura Addu’a qanwar mu ta zama Firs Lady ai mukam ras damu” Anty Ladi da muke cewa Momi uwargidan Alhaji qarami ta koromun wannan jawabin.

Tagumi na rafka ina jinta, ikon Allah kunji wata sabuwa kuma su haka suke kenan daga uwar har yayan?

“Toh kinji ai se kuma me kike buqatar sani ki tambayeta” Yaya ya fada yana yar dariya.

“Kai ni fa Yallabai randa mukaje ganin ginin nan nasa kwana nayi da takaicin da yanzu mu zamuje muyita iyayi muna zuba kaya gidan qanwar mu, na ringa raya da ina da Yar data isa aure ko qanwa to fa duk ma yanda za’ayi se an hada auran su da dai a dakko bare taci arziqin dan nasan aure ze qara.

Harfa na fara tunanin na qyasawa Suwaiba se kuma nace kar kayiwa kishiya hanyar arziqi se abu ya samu a manta dakai kwatsam se gashi wannan abu ya wakana kai nifa harda sujudushshukur nayi kana fita randa ka gaya mun maganar nan, yo ko zuwa nayi na dauki hoto a gidan ai an biyani wallahi”

Sosai muka ringa dariya nida Yaya musamman wai kar ta gayawa Anty Suwaiba kishiyarya ae arziqi ya samu su manta da ita.

“Ku zauna kuna dariya shi ai yasan me muka gani wallahi keni ko bakyason sa dan Allah ki aure shi kowa ya san gaba kika ci ba baya ba”

“Aa dai gara tana son nasa dai, ni na zata ma sun gama komai ai yanda yake addabata da waya duk lissafina kawai mu hada danasu Bilal a daura daga baya se suyi tariya ko” Alhaji Qarami ya fada

“Ai da ka gama mun komai wallahi yallabi kawai ayi haka, kai infa aka biye ta Ma’u ba wanda zata so wannan mijin nata me fuskar shanu ya rigada ya rubuce sunanta a Allon qarfe se ta Allah kawai gara in ma dole za’a mata ayi a wuce Gurin”

Dariya sosia Momy ta ringa bani daman ita haka take akwai abin dariya, tana da matuqar kirki ta kuma kama girmanta a matsayinta na matar babban wan mu babu raini haka babu wulaqanci kowa natane sefa wanda yazo mata da abin da be mata ba bazata dauka ba.

A gaba da sakani da hudubobi dan Alhaji tashi yayi ya barmu bayan daya jaddadamun na san matsaya dan Goggo fa dagaske tace tana dawowa dole na fitar da miji nayi aure kona tattaro na dawo Gombe na bar aikinsa yayi sanadin gurgudewar aurena.

Ranar raba dare nayi ina saqa da warwara, daga qarshe na tashi na raya daren addu’ata dai a kullum zabin Alkahiri daga Allah (To Hajia Ma’u kwankwasa qofa za’ayi ace fito ga zabin da Allah ya miki ko yaya? Ke zaki saki ranki ki bude zuciyar ki sannan ne zaki fahimci abinda Allah ya zabar mikin).

BASHIR
Haka ya sallace cikin quncin zuciya da takaici da dana sanin me yasa ma be tafi Gombe ba shima. Sallah guda haka ya zauna a gida yana zare ido dama dama ran idi yaci abinci dan Fried rice Amirah ta daure tayi musu ranar harda Salad ga Zobo me sanyi da dabgen kaji.

Haka yaci ta a babu yanda ya iya to yaushe rabon ma daya samu kamarta din? Babu tuwon sallar nan dasu Sinasir da waina kai gaba daya Eatate din qiyau miyau kodan qamshin abincin sallar nan da zakaji gari ya dauka babu toh duk musulman sun wuce garuruwanau sallah shima tsautsayi ya zaunar dashi dan be tabayi ba se wannan karon.

Yana daki yana aikin kallon status din Jama’a na sallah kowa da Yayansa sunje Ido seya tuna yanda Ma’u take tasa shi su kashe hotuna ran sallah da duk wnada ya kalla seya yaba wannan karon ko Babbar rigar ma ajuye ya sakata seda yaje masallaci aka gaya masa ya gyara dan sanda ya shirya ya tafi Matar gidan bata ma fito daga daki ba bare ta taya shi shiri, daya dawo dai ya tarar ta cancada kwalliya da kayan daya mata ta kuwa yi kyau sosai masha Allah haka gidan an gyara abinda ya sauqaqa bacin rabsa kenan sannan ko ba komai ya dan samun abin kaiwa bakin salati.

A status din Amnah yaga hotunan su na Idi, shaddar gurin Yusuf me babar riga yaran suka saka sunyi kyau kamar ka sace su ka gudu haka ya ringa zooming yana murmushi da jin kansa na fasuwa wai fa yayansa ne da Ma’u, yo ko dan su ai dole ma ta haqura ta dawo su zauna.

Hoton da sukayi ita da yaran ta cakare kamar wasu qannenta sun sakata a tsakiya ya tsaya yana kallo nan da nan ya kwafa ya dora a status dinsa kuwa. Haka ya wuni kallon hotuna Daya gaji da zaman gida ya fita zaga gari, su Addah dai ana palour ana warkajami da Kajin da sukayi Dabgensu.

Ranar kwana uku da salllah da yamma sakakiya Dada ta kirashi tana gaya masa abin tashin hankali zancen wai Asma’u ta samu miji sun daidaita lokaci kadan ya rage ta daura aure.

Yana zaune a gurin da yake zuwa cin abinci lokacin ta kirashin, tsabar rikicewa besan sanda ya watsar da lemon hannunsa ba ya miqe jiki na rawa ya shiga neman layin Ma’u sam ya manta ma da cewar ta toshe shi seda yaqi shiga sannan ya koma kiran Amnah, akayi rashin Sa’a bata gida sun tafi yawon sallah gidan qawayenta.

Seda ya je mota aka bishi da bill dan be biya ba da ze tafi, Yarinyar nan ce ta kwanaki.
“Me yasa a koda yaushe kake cikin yanayin damuwa da tashin hankali ne Bawan Allah?” Ta fada bayan daya bata kudin ya shiga mota.

Harara ya zabga mata yace
“Gafara daga nan kona take miki qafafu” ya figi mota yayi gaba, seta kama baki tace
“Toh daga magana? a sauka lafiya to nima maganina kenan ta juya ciki abinta.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 59

An daura auran su Bilal munsha shagali sosai dan mun dade rabon mu da biki a gidan mu.
Washe garin ranar daurin auran ba tareda na sanar da Bashir ba muka kwashe kayana na sedai yaji a gari mukayiwa gidan qaf tsinke bamu bari ba dan wannan dibar kayan harya fi na Lagos tunda da yan gidan mu mukaje daidai da gadon dakinsa daya siya da kudinsa seda suka cire wai Yaya sun bani kayansa kuwa haka suka zube masa akan Katifar dayaci arziqi aka bar masa.

Seda suka ga gida ya zama kango kafin suka haqura, na kwashi abubuwan da nake so akayi packaging ragowar kuwa Wani shago da suke siyan kayan hannu muka kaisu, sun siya da daraja sosai dan kayan masu qarko ne da kyau kuma basuyi komai ba tun kafin mu bar gurin aka fara wawason su suka cake mun uwayen kudadena a akawun muka tafi zan juya su zuwa sanda Allah ze yanke mun na sake siyan wasu. Kwana uku muka qara muka tafi  dukda naso na bar su qarasa hutunsu se kuma dai muka koma gaba daya.

Tare muka gyara gidan  dukda ba wani datti yayi ba dan mun kulle ko ina sanda zamu tafi. Seda muka gama komai nace wa Aliyu yayi wanka ya rakani mu siyo abinci saboda saukar Yamma mukayi base munyi girki ba.

Muna tafe a hanya Yusuf da bamu samu mun hadu a Gombe ba ya kirani mukayi magana.

"Mami dan Allah ina so muyi magana" Aliyun ya fada bayan dana gama amsa wayar, sena waiwaya na kalleshi. Tuntuni na lura da rashin walwalarsa ko biyonin da yayi nasan da dalili gaba daya ya canza dukda daman bashi da sakin fuska sosai amma yanzu abin ya qaru ko yaushe yana cikin qunci da damuwa.

"Ina jin ka nima daman inaso nayi magana dakai me yake damunka duk kabi ka takura rayuwarka Aliyu?" Na fada ina kallonsa.

Ajiyar zuciya ya sauke bayan daya faka motar dan shi yake janmu saboda gurin da mukaje babu nisa daga gida.
"Mami bana jin dadin yanda kukeyi keda Abbi, nasan yayi miki laifi amma Mami tunda ya baki haquri to ki haqura mana ki yafe masa"

"Aliyu ni laifin me Abbin yayi mun? Kuma koma menene ba kana kallo ba ai shiyake zuwa kullum har inda nake yana takala ta da fada dan haka shi ya kamata kaje ka yiwa magana ya dena abinda yakeyi tunda har kayi hankalin gane badaidai bane" na fada fuska a daure dan karma ya kawo mun wani shirme,

"Toh amma Mami.."
"Kaga ni yunwa nake ji zaka shiga ko a mota zaka zauna" na katse shi ina balle murfin qofar. Seya gyada kai kawai ya kashe motar muka fita yanda muka jera seka zata irin qanina ne haka muka shiga gurin na samu guri na zauna tareda gaya masa abinda zeyi mana order.

"Assalamu Alaikum ranki ya dade" naji an fada daga gefe na na dago da sauri jin kamar nasan muryar, Ambassador Mutallab Ali ne shida wani a teburin da yake gefen namu se wannan PA din nasa yana tsaye yana zare ido.

"Ranka ya dade barka da rana" na fada ina sunkuyar da kai da tuno yanda na dannawa lambar sa block tun a kiran farko qila yayi ta kira harya haqura tunda bata shiga.

"Daga kiran waya malama Asma'u se kikayi blocking dina kuma laifin me nayi?" Ya fada kamar ya shiga zuciyata. Kaina na qas ina dan murmushin yaqe ya sake cewa

"Tunda na kira naji line busy nace to gimbiyar bata son damuwa bari a barta ta huta, kwanabiyu abubuwa sun sha kaina shiyasa ma ban sake gwadawa naji ko an bude ni ba se gashi yanzu Allah ya hadamu dan haka a gabana zaki bude na gani".

Wato yanda ya dage yana magana ni gaba daya ma kunya ya bani ko ganin girman kansa beyi ba yake wani lankwashe harshe gashi kuma Abokin nasa se wata dariya yake kamar wanda akewa cakulkuli ni duk ya bani Haushi nama rasa me zance musu.

"Kinyi shiru Asma'u, koda yake fara dakko wayar kiyi unblocking dina mayi magana daga baya dan yanzu sauri nakeyi, Alhaji Sani ka ganta nan ita ce yarinyar danake baka labari"

"Ah ai na ganta tayi sosai kuwa bazamu bari wannan ta wuce mu ba" wanda ya kira da Alhaji Sani ya fada cikin hausarsa da bata fita sosai daga ji ba cikakken Bahaishe bane se na fara laluben wayata akan Tebur din da nake, Ajiyar zuciya na sauke dana tuna na manta ta a mota da zamu fito na juya na kalle shi da dan murmushi nace

"Ai kuwa na manta ta a gida ina sauri zamu fito" daidai sannan Aliyu ya qaraso da Waiter na binsa da ledojin abinci. Tsabar wulaqanci kallo daya ya musu ya dauke kai kamar wanda yaga kashi ya zauna a kujera yana muzurai.

"Wannan Qaninki ne?" Ambassador ya fada yana kallon Aliyun, sena qaqalo murmushi nace

"Aa, first born dina ne, Aliyu baka ga mutane bane?"
"Nagansu mana" ya fada kansa tsaye kamar be gane yaran ya gaishe su nake masa ba. Tsabar takaici na bude baki kawai ina kallon yanda ya hade fuska yaja Ice cream din daya taho dashi a hannunsa ya hau sha, zanyi magana Alhaji Sani ya tare ni da cewa

"Aa barshi yaro ya gida? Ina qannenka kana taya Babanku kishi ko banga laifin ka ba".
Murmushi Ambassador yayi kafin ya miqawa PA hannu se yayi saurin bashi wata briefcase dake hannunsa, budeta yayi ya ciro rafar Dala dari dari guda biyu ya ajiye mun daya yace
"Gashi idan kun gama seki biyu kudin muna sauri ne bari mu wuce, Yaro ka saka katin waya ko" ya ajiye ragowar dayar a gaban Aliyu.

"Haba Ranka ya dade ai da ka barshi mun rigada mun biya ai" na fada ina tura masa kudin, gaba yayi abinsa yana cewa
"Zan sake gwada wayar naji idan kin koma gida" ya wuce suka take masa baya bayan da Alhaji Sani ma ya sake ajiyewa Aliyun wata Dalar harda dafa kansa yace yana yar dariya yace

"Yaron kirki me taya Babansa kishi" suka fice gaba daya.

"Wallahi sekaci ubanka Aliyu ni ka kunyata a idon mutane ka nuna musu baka da  tarbiyya ko?" Na fada kamar zan kwada masa mari Saboda haushin abinda yayi din. Ice cream din ya ture kamar zeyi kuka yace

"Toh ni Mami ina ruwana da su dazan gaishe ni ai ban san tare kuke ba tunda bada su muka zo ba"

"Zaka rufe mun baki ko sena kwade ka anan, idan ba tare muke ba daman haka kukeyi idan kunga na gaba da ku? Ko darajar shekarunsu beci ka gaishe su ba tunda ai ba kai ba ko ubanka sun girme shi" na fada cikin masifa.

Seya miqe tsaye ya kwashe kudin gabansa yana cewa
"Nidai kiyi haquri"
"Ajiye su dan ubanka, ka wulaqanta su saboda baka da kunya ka dauki kudin da suka baka" na fada ina fizege kudin, saboda wulaqanci se ya saka dariya ma yana cewa

"Toh Mami ai ba roqar su nayi ba, ki bani kinga se na kaiwa Abbi ya auro wadda zata ringa dafa masa abincin da kika ce".

Tsabar mamaki kawai bude baki nayi ina kallonsa, lallai Aliyu ko da yake ba laifinsa bane wannan yafi kama da Tunanin Bashir qila shi yake karanta masa duk abinda zeyi to kuwa duk zasu ci ubansu shida Bashir din.

Haka muka wuce gida dani dashi babu wanda ya sake cewa komai. Tare muka ci abincingaba aya aka gama aka tattare gurin, Seda akayi Isha ina daki Aliyu ya leqo yana cemun ze tafi seda safe

"Ba anan zaka kwana ba?" Na tambaye shi,
"Eh zanje can gidan da safe na dawo" ya fada yana sosa kai.

"Allah ya kaimu, kuja mana qofar idan kun fita" na fada ina ci gaba da lazumi na.

Washe gari da wuri na shirya fita aiki saboda babu makaranta duk yaran ma suna bacci abinsu. Naci gayuna, Shayi kawai nasha na dauki jakata ina cikin kulle qofa Bashir ya qaraso qofar gidan shima cikin shirin fita aiki.

"Barka da Safiya Ma'u" ya fada yana kallona.

"Ina kwana Baban Ali?" Na mayar masa da amsa ina ciro muqullin mota daga jakata.
"Ashe kun dawo, se ganin Aliyu nayi yace jiya da yamma kuka dawo"

"Uhm wallahi saboda aiki kasani, da se satin sama idan hutu ya qare zamu dawo" na bashi amsa cikin sauri sauri ina danna mabudin motata.

"Nace in ba damuwa inaso zamuyi magana ne dan Allah ko zuwa anjima idan na dawo se nazo gida" ya fada yana shafa kai kamar wani yaro,

"Toh magana kuma dani? Allah ya kaimu" na bashi amsa ina shigewa motata, shiya rufo mun murfin yana mun adawo lafiya wai sabon salo kiran sallah da usur, seda na kai qofar gidansa na hangi Amirah tsaye cikin shiri kamar a tsikara mata tsinke ta fashe tsabar kumburi da alama fita zasuyi ya tsayar da ita.

Da yamma kuwa gurin qarfe shida sega Bashir, na fito wanka kenan dan nima ban dade da dawowa ba sannan Farida ta shiga take gayamun ga Abbi.

"Ma'u wata magana naji da hankali na ya kasa nutsuwa da ita wai aure zakiyi" ya fada bayan da muka gaisa. Sena kalle shi yanda gaba daya yabi ya rikita kansa duk ya sukurkuce gayun nan da yakeyi da yanzu babu da alama ko hutawa ma beyi ba yana dawowa ya taho nan dan rigar saman kayan sa kadai ya cire.

"Toh ashe labari ya iso maka a ina kaji?" Na tambaye shi da dan murmushi a fuskata seya zaburo kamar ze sauko daga kujerar da yake yace

"Bangane ba kina so kice mun da gaske ne Ma'u aure zakiyi? Wane irin Aure? ki zauna da wani namiji bani ba ko hada soyayyata da ta wani a zuciyarki?"

Seda na gyara zama dakyau na dora qafa daya kan daya ina girgiza su kafin nace

"Aure kala nawa ne Bashir? Shi din dai wanda ka sani na mata da miji da zasu zauna a qarqashin inuwa daya.
Batun na zauna wani namiji kuma da Mace yar uwata kake so na aura ko yaya? Ita kuma soyayya ai yanzu tashi ce kadai a cikin zuciyata tuni anyi waje road da taka tsohon labari kenan".

Miqe wa tsaye yayi har yana tunkude kayan Lemon da aka kawo masa suka zube a qasa ya nunani da hannu yana cewa

"Qarya kike Asma'u bazaki taba son wani Namiji a duniya ba bayan ni idan ma zakiyi aure da gaske sedai kiyi kawai amma badan so ko jin dadi ba ina kuma tabbatar miki da cewa duk ma inda kike tunanin zakije sekij dawo dan zuciyarki bazata taba aminta da wani bayan ni ba wannan alqawari nayi miki"

Ko a jikina na miqe tsaye nima ina kallonsa cikin ido nace
"A lokacin dana nuna maka kaine rayuwata Bashir ka dauka shirme nake ban san kaina ba a sannan, a yanzu kuwa ka bude mun ido ka kuma bani damar da nayi karatun sanin matsayina da abinda ya cancanta dani.

Oh wai fata kake mun nayi aure na sake dawo maka? Toh ai tunda na iya zama da kai da halinka Bashir ni kuwa wane kalar miji ne zan gagara yin haquri dashi zance ma kawai kake yi wannan" ina gama fada nayi gaba zan bar gurin yayi saurin shan gabana tareda riqo hannuna, kallon dana jefa masa na kayi hauka ne yasa shi saurin sakina yaja baya yana cewa

"Kiyi haquri naji koma menene ki gaya mun duk abinda bakya so zan dena wallahi nidai kiyi haquri ki dawo dakinki muci gaba da zama kinji wallahi bazan iya rayuwa babu ke ba".

Ni kuwa kaga yanzu ma na daura danbar rayuwa ba tareda kai ba, kai ni ai yanzu bama zan iya maimaita zaman da nayi a baya dakai ba Bashir kaje kawai ka zauna da matar da Allah ya zaba maka ka barni nima na gwada wata rayuwar haba karka zama me son kanka mana"

"Ma'u dan Allah..."
"Dan girman Allah Bashir ka fita, da nasan wannan maganar ce zata kawo ka ma da tun da safen munyita wallahi base kazo ka tasani gaba da magiya ba ko da dole ne nace bana so bazan koma ba ka qyale ni mana idan kuma kana da qarfi seka dauke ni aka ka maida ni gidanna ka haba" na fada a hasale dan ya ishe ni kuma.

"Shikenan seki shirya ganin gawata dan duk ranar da kika auri wani bani ba nasan daga lokacin rayuwa ta zata zo qarshe".

"Allah ya jiqanka, karka damu su Aliyu bazasuyi maraici ba" na fada ina wuce shi. Ina ji a jikina yanda ya bini da kallo harna shige daki.

BASHIR

Jiki a sanyaye ya kama hanyar gidansa yana tunanin wai shi mezeyi Ma'u ta dawo masa?
Ya gwada duk yanda akace masa yayi nasa dabarun amma duk a banza kullum ma sake botsarewa takeyi a maimakon ta sakko. Yanzu mutum biyu suka rage masa da yake ganin zasu iya shawo kanta daga Babansu se Alhaji Qarami.

Kai shi yana kunyar Alhaji Qarami wallahi abinda ya masa a rayuwa ko darajar wannan yaci ace ya dagawa Ma'u qafa koda ita ta takaleshi yaci ya dauke kai. Baban dai ze kira tunda dai ai duk tsiya ubansa ne bakuma ze zabi Ma'u akansa ba kuma ai shima yana son zamansa da ita dan haka ze saka baki ta dawo masa.

Wayar Baban ya kira amma Dada ta daga take gaya masa yana bacci saboda jikinsa ya matsa kwana biyu. Shi se sannan ya tuna da zancen kudin maganin da ze tura musu gashi account dinsa yayi qasa sosai saboda hidimar sallah da yayi kuma wata ya raba balle ya saka rai da zuwan Albashi.

"Kai komai ma ya rikicewa mutum kudin kansu sun dena Albarka kamar wanda ake kwashe su" ya fada a fili bayan da yayi wa Sa'ad transfer abinda ya samu na siyan maganin, dan abinda ya masa saura baya zaton ze rufa masa watan gashi za'a koma makaranta biyan school fees kadai ya ishe shi yana ganin dole seya karfi wani abu a kudin super market saboda biyan kudin makarantar dan da wuya ya taba kudin idan an hada lissafi ribar sake mayar da ita ake se idan ta qure masa ne yake taba wani abun a ciki.

Yana shiga gida ya tarar da Amirah na murqususun ciwon ciki kuma, kai Jama'a haka suka kwasa se Asibiti likita ya ringa fada akan wai wani abun tasha irin magungunan Hausa, daya matsata qarshe take gaya masa wai magani Addah tasa aka aiko mata daga Gombe a qaryar su na zaqi ne tunda cikinta ya shiga kusan wata Bakwai yanzun shine ta karbo mata zancen gaskiya kuwa sabon malami ta samu ta hannun Anty Talatu ita tayo musu aiken saboda sun gaya mata sun rasa kan Bashir din zaman dai se a hankali.

Ya kuwa ringa bala'i kuwa yana cewa Idan wani abu ya samu cikin ita ta sani babu ruwansa tunda ita bata tausayin kanta haka suka dawo bayan da aka bata magunguna su kansu seda ya kashe kusan dubu Hamsin a daren.

Kwana biyu a tsakani aka kirasu a waya cewar Ummi ta haihu ta samu ya Mace amma ta koma murna Addah ta ringayi tana hamdala da  akace yar ta mutu sedai murna ta koma ciki jin wai an daurawa Ummin aure da dai shi mijin da bata so ta aura din dan daman seda sukayi yarjejeniya da iyayensa akan tana haihuwa za'a daura aure suka yarda dan haka ana kiran Alhaji Murtala daga can Katsina inda ya kaita gurin wani Amininsa cewar ta haihu ya tashi ya tafi gidan su saurayin ya gaya musu. Ana sallar Azahar kuwa a masallaci aka daura musu aure se saka ranar da zata dawo ta tare.

Kusan

Please Login or Register in order to submit comment