Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

tana sheshshekar kuka, a ranta Addu’a takeyi Allah yasa yace zezo dan wallahi qafarsa qafarta itama se taje an ci uwar da ake ci acan tare da ita.

“Kin gane ki gyara bari na kira Naziru yazo ya kaiki Asibiti yanzu” maganar sa ta katse mata tunani, se ta dan diririce dan bata zaci zece aje Asibitin ba amma kuma idan taqi tasan wata matsalar zata kwantowa kanta in kuma sukaje akaga ba haka ba nan ma ba tsira zatayi ba, daurewa tayi tace masa

“Aa karbar shi dare yayi yanzu kuma bada yawa bane ai da nayi tsarki ma ya dena zuwa, sannan Anty Ramle tana gida (Amaryar babansu Nurse ce) koda wani abu ya taso zata iya taimaka min kafin muje Asibiti”.

Sallama sukayi ya kashe wayar Badan ya gamsu da maganarta ba dai ya qyaleta tunda yasan Anty Ramle tasan aikinta sosai zata kula da ita amma koma menene zuwa safiya dole taje Asibiti dan baze dauki ganganci ba, kai qila gobe ya tafi ma dakansa ya kaita gara in ma wani abune a shawo kan matsalar da wuri.

Tsakin daya sakeyi a karo na ba adadi ya saka Ma’u daga kai ta kalleshi, tunda ya barar da kunun Ayan ta kwashe kwalaben tareda goge Gurin kawai ba tareda ta tankashi ba dan taji duk maganar da sukeyi. A ranta tadan tausayawa Amiran in da gaske takeyi dan dai duk mace tasan wahalar ciki da haihuwa dole in kaga wani dashi ka tausaya masa.

Bata tambaye shi abinda ya faru ba shima kuma be gaya mata ba har sukaje kwanciya, juyi daya biyu ya saki tsaki kai har abin ya fara bawa Asma’u haushi amma ta jure bata tanka masa ba sema danna kanta da tayi cikin pillow ta tilastawa kanta yin bacci. Wai kuma ashe shirun data yi laifine se jinsa tayi yana cewa

“Wai dan wulaqanci kina jina amma bazaki iya tambayata meya faru ba ko?”

“Ikon Allah” ta fada a ranta, a fili kuwa daga kai tayi ta kalleshi sau daya ta juya ta rufe idonta ba tareda tace masa komai ba, ai bashi kadai ya iya miskilancin ba.

Bashir kuwa jin ta masa shiru ya qara tunzurashi, kwafa yayi yana sake zabga tsaki kamar ze katse harshensa, ga damuwar halin da Amiran take ciki ga share shin da Ma’u tayi ta juya masa baya. Wayar sa ya dauka ya shiga duba jirgin Lagos to Gombe a gobe Asabar amma babu dolensa ya haqura, Haka yai ta juye juyensa har shima baccin ya dauke shi.

Asubar fari ya dannawa Amirah kira, tana can tana sharar baccinta har wayar ta qaraci ringing bata ji ba, seda ya kira sau biyu ana uku ta daga cikin magagin bacci.

A tsaitsaye suk gaisa ta tabbatar masa da komai lafiya babu abinda yake damunta yanzu sannan sukayi sallama yana jaddada mata ta shirya anjima Naziru ze zo ya kaita Asibiti ta amsa shi da toh bawai dan zata je din ba to me yake damunta ma.

Suna gama wayar ya maida akalar kiran kan Naziru, gaya masa yayi yaje ya kaita Asibitin duk abinda ake ciki ya sanar dashi sukayi sallama.
Asma’u tana kwance akan gado duk tana jinsa, mamaki take yanda gaba daya ya rikice, ganin yana neman ya hanata baccinta yasa ta miqe ta bar masa dakin ta koma nata ta kwanta.

Har yamma bata san ya aka qare da jikin Amirah ba, ita bata tambayeshi ba shima be mata maganar ba dan wani shareta ma ya shiga yi a dole wai haushin ta yake ji ita abun ma se ya bata dariya. Da yamma ma kudi ya bawa Ahmad yace ya kai mata su fita su siyo abinda suke so shi bazashi ba ta kuwa karbe su ta zuba a jaka suka shige kitchen da yara suka hau yin shawarma suka gasa kaza da zasuci da daren se smoothy na Ayaba daya ji madara.

Ta bayan kitchen dinsu akwai fili da suka gyara ya zama kaman wani garden wurin suka shirya abincinsu, kowa yayi wanka yasha kwalliya kamar masu zuwa wani guri suka haucin abincu ba tareda anyiwa Bashir daya hakince a palour tayi ba. Tunda suka fara gasa kazar qamshin ya fito dashi ya zauna yana jiran a gama a kawo masa amma yaga sun tattare sun tafi baya. Ganin da gaske fa zasu cinye yaja zaune yana jiyo dariyar su cikin nishadi se ya miqe ya tafi gurin ya tsaya a kansu yana muzurai.

Gaba daya suka kwashe da dariya, sunsan dama ba ze iya dauke kai ba Bashir da Nama kamar kura in ya gani se ya ci haka kuwa ya zauna yana zare ido aka ci dashi tas suka dauka pictures kafin kiran magriba ya tayar dasu.

Seda suka zo kwanciya Asma’u take tambayarsa yaya jikin Amiran yace mata da sauqi tayi masa fatan samun lafiya shikenan kuma fushin ya wuce aka shiga sabgogi.

Lafiya lau suka cinye satin, yara sun fara exam ta third term zasu samu hutu me tsaho nan da sati biyu da wannan damar Asma’u take so tayi amfani ta dauki leave ita ma dan ta kwana biyu bata je Gombe ba, sannan tana son zuwa yola ta duba Maman ta da jikinta yake yawan motsawa kwana biyun nan.

Ranar Wednesday daya rage saura kwana biyu kenan yaran suyi hutu, already ta rubuta takardar hutunta har anyi approving tana so ne a ranar friday su wuce Gombe dan babu jirgin Saturday. Da daddare bayan sun gama dinner suna zaune a palour ita da Bashir yaran na dakunan su suna Karatu Muhammmad da Ahmad kuwa sunyi bacci dan su sun gama tasu exam din.

Kallon Bashir dake duba wasu takaddu tayi tace “Baban Ali kayi mana booking flight din kuwa mufa mun gama hada kayan mu”
Ba tareda ya dago ba ya bata amsa da cewa
“Waini saurin me kikeyi ku tafi ku barni ni kadai”

Murmushi tayi kafin tace “ba haka bane, kaga na dade rabona da gida inaso mu dan kwana biyu na zaga dangi ga kuma tafiyar Yola ma gara mu je da wuri ai”
“Hakane” ya fada ya ci gaba da aikin sa.

Gombe
Daga ciwon qarya Amirah ta fara na gaske, haka nan se taji kanta ya sara mata ko in tana tsaye ta fara jin dumm kamar jiri ze kayar da ita idonta ya ringa mata dundumi bata gani da kyau amma Saboda rashin sanin ciwon kai sam bata bawa abin muhimmanci ba ta cigaba da sabgoginta idan ta gayawa Bashir yace taje Asibiti ma bata zuwa Sedai ta karbi kudin a hannun Naziru ta kashe.

A hankali kuma se ta fara kumburi, farko qafarta ce ta fara Se Addah tace mata alamu ne na ciki ya tsufa babu komai ta dai ringa dan tattakawa haka, sau biyu Antu Ramle na mata magana akan kumburin tace ta shirya suje Asibiti amma taqi qarshe ma tace ta dameta ita a rabu da ita ana haka kuwa ta ci gaba da hawa kafin kace me tayi himm ga ciki shima ya qara girma.

Safiyar Friday dakyar dama ta tashi daga kan gado, Addah data shigo dakin take gayawa bata jin dadi tace mata ta daure tayi wanka ta shirya to se suje Asibiti haka ta yunqura ta shiga bayin, wai dan daurewar da jikinta yayi ya warware ta sakarwa kanta ruwa masu zafi gaba daya bayin ya turare kan kace me numfashinta ya fara sama sama yana neman daukewa ba shiri ta yunquro ta fito cikin tsautsayi tana fitowa ta yanke jiki ta fadi cikin tashin hankali suka kwasheta zuwa Asibitin da take Awo.

Lagos
Ranar Friday da zasu tafin yaran basu je makaranta ba dan babu abinda zasuyi takardar hutu kawai za’a basu kuma already an turo musu ta email daman, jirgin qarfe 6pm zasu bi zuwa Gombe amma tun kafin la’asar sun gama komai hatta jakunkunan su sun loda a mota. Se murna sukeyi kamar suyi tsuntsuwa su gansu a Gombe haka suke ji.

Qarfe biyar sukaji tsayuwar motar Bashir dan daman yace ze dawo da wuri ya kaisu Airport sedai daga yanayin daya shigo gidan tasan ba lafiya ba.

“Kuje Mota ina zuwa” ya fada yana shigewa dakinsa, yaran suka fita amma ita se tabi bayan sa. Sanda ta shiga yana waya gaba daya ya birkoto wata shelf daya ke ajiye files dinsa na office da alama wani abu yake nema.

“Ayi duk abinda ya kamata kafin nazo yanzu zamu taho insha Allah” taji ya fada kafin ya kashe wayar ya shiga diban wasu daga cikin filea din daya zubar. Ita ya miqawa yace “Joseph na waje please ki bashi zamu yi waya”

Karba tayi ta fita a ranta tana tunanin meyake faruwa ne toh, haka ta miqawa Joseph files din tana shirin kowa se gashi ya fito bayan ya kulle gidan gurin wutar gidan ya nufa ya kasheta gaba daya, seta kalleshi tana cewa “akwai kaya a freezer fa zasu lalace”

“Please muje kawai” ya fada yana bude motar ya shiga itama seta bude gaban ta shiga kawai ya tayar suka tafi. A Airport din ya ajiye motar suka tashi zuwa Gombe gaba dayan su Asma’u nata mamakin wai me yake faruwa ne dan dai ba dashi suka shirya tafiyar ba yanayin data ganshi kuma bata zaton ze iya mata wani bayani, koma dai yaya ne Allah ya kaisu lafiya zasu gani Allah dai yasa Alkahiri ne.

Gombe
Daga Airport direct Asibitin da suke zuwa Naziru ya wuce da Bashir da Asma’u yaran kuma Sa’ad wanda Nazirun yake bi ne ya kwashe su a tasa motar suka wuce gidan Dada.

“Hasbunallahu wani’imal wakeel” ta furta lokacin da tayi Arba da Amirah dake kwance tayi wani irin kumburi kamar zata fashe, cikin tashin hankali ta kalli Bashir da shima ganinta a hakan yai bala’in tayar masa da hankali.

A yanda akayi masa waya beyi zaton abun yakai haka ba. Yana Office da Safe Isma’il yayanta da suke Uba daya ya kirashi wai Tana tsaye ta yanke jiki ta fadi dama dai tun Kwana biyu take yawan yi masa qorafin ciwon kai da jiri, ya cewa Naziru ya kaita Asibiti ya kuma je amma taqi zuwa Nazirun ya gaya masa. Beyi mata magana ba dan dama bashine karo na farko ba da zata ce bata da lafiyar in yace akai ta Asibiti taqi zuwa sedai ta karbe kudin ta kashe kawai yanzun barinta yayi se yazo sannan ze kora mata warning se kuma ga wannan abun ya faru.

Da aka kawota Asibitin likitan yake gaya musu jininta ne ya hau sosai da sosai ga kuma alamun preeclampsia tare da ita (jijjiga) kuma daman tuntuni ya gaya mata duk sanda taji wani sauyi ko alama tazo a dubata tunda cikinta ya shiga wata na 7 toh awon ma seta ga dama take zuwa gashi yanzu abinda ba’aso ya faru se fatan Allah ya kawo sauqi kawai.

Suna tsaye jungun jungun Bashir ya tafi office din Dr, acan yake gaya masa dole sedai suyi mata aiki in dai ana so a ceto rayuwar ta dan barin ta da cikin ze zamar mata hadari.

“Toh Dr ai kuma cikin be isa haihuwa ba” Bashir ya fada a sanyaye

“Wannan ba matsala bane Engineer idan an cire shi zamu sakashi a kwalba ne mu cigaba da kula dashi har sanda ze isa dauka amma yin aikin yanzu shine kadai maslahar mu, bansan wace irin yarinya bace ita da bata damu da lafiyar jikinta ba ta yaya ma akayi tana zaune har takai wannan stage din batazo Asibiti ba tunda ba abu ne da yake faruwa lokaci daya ba”

Shidai Bashir bashi da ta cewa, takardar da likitn ya bashi yasa hannu, yace su kwantar da hankalin su babu komai insha Allah zasu ci gaba da monitoring nata su samu jinin ya sauka kafin a shiga da ita aiki suyi ta yi mata Addu’a kawai.

A reception daya fito can lungu ya hango Addah ansha kuka an gode Allah se yan idanu kawai take kiftawa se sannan ya samu suka gaggaisa dasu kafin yacewa Asma’u da tuni jikinta ya mutu tabi Naziru ya kaita gida ta hutu jinawa ze taho. Fatan samun sauqi tayiwa Amiran ta bi Nazirun suka wuce gida.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 14


Seda Amirah ta kwana daya a daren rana ta biyu akayi mata aiki cikin ikon Allah aka ciro mata yar qaramar yarta bakwaini me tsananin kama da Farida, sosai Bashir yayi murnar samun mace sanda aka nuna masa babyn kafin aka sakata a kwalba, tun cikin daren kuwa ya ringa buga waya yana gayawa mutane haihuwar.

Ya kira wayar Asma’u lokacin harta fara bacci dan basu dade daga dawowa daga Asibitin ba suna can ma aka shiga da ita aikin, ganin dare ya fara ga yara yasa ta tafi gida.

“Masha Allah, Allah ya raya ita kuma ya bata lafiya, kace Farida tayi yar uwa Abokiyar shawara” ta fada bayan data daga wayar.

“Wlh fa sema kinganta kamar su daya kamar sanda kika haifi Faridan girma kawai ta fita” Bashir ya fada cike da doki kafin sukayi sallama. Baccin ta ta koma dan dama tunda suka dawo ta rufe gida tasan ba dawowa zeyi ba dan jiya ma can ya kwana seda safe yazo yayi wanka ya chanza kaya bare yau da ya samu ya ai ba batun zuwa gida kuma.

Washe gari da wuri ta tashi ta hau shirye shirye dan tana so taje gidan su yau ga zuwa Asibiti. seda tayi girki tayi musu farfesun Kaji ta soya doya sannan ta damawa Amirah kunun gyada dukda bata san ko zata faracin abinci yau din ba sannan ta dafa Tea suka shirya gaba daya ita da yaran suna ta murna data gaya musu sunyi qanwa. Se gurin goma sannan ta hada komai suka tafi.

Dakin danqam da yan dubiya yan gidan su Bashir da kuma Dangin Amiran se hayaniya sukeyi dan ta farfado tun da Asuba. Ba yanda Likita beyi dasu ba subarta ta huta amma sunqi qarshe haushi yaji yai tafiyarsa ya barsu ya kuma gayawa Nurse kar wanda ya nemeshi in wani abu ya faru dan ya gaji da halinsu kuma.

Aliyu da Jafar ne a gaba sunyi kama kaman kwandon da ta zubo Abincin su kuma suna binsu a baya suka shiga dakin da Sallama. Fuskarta dauke da Fara’a suka shiga gaisawa da mutanen dakin tayi musu barka kafin ta juya kam Amirah da tun shigowar Asma’un ta daure fuska tam taqi koda kallon sashin da take.

“Amirah sannu ya jiki?” Ta tambaye ta idan ta amsa ta to ku da kuke karatu kun amsa abin yai bala’in bawa Aisha Babbar Yayar su Amirah da suke uba daya haushi har seda tayiwa Amiran magana tace “Kina ji tana miki magana saboda raini da wulaqanci bazaki amsa ba”

Bata ko motsa ba kuwa sema cuna uban baki gaba da tayi dama fuska duk a kumbure tana qunquni. Asma’u kam ko a jikinta, yo ita bata ga abin da zesa Amirah tace bazata kulata ba idan kishin nema ai ita ya kamata tayi tunda aita aka aurewa miji, Allah ya raya ta sakeyi musu kafin ta juya da niyyar fita dan dama yaran tunda suka gaishe su sukayi waje abinsu, dab da zata fita ta jiyo muryar Addah na tambayar waya kawo abinci ashe tana bandaki seta juyo ta dawo cikin dakin.

Har qasa ta durqusa ta gaisheta, fuskar Addah kuwa a washe ta amsa mata tana tambayarta ina Mazajen nata tace suna waje
“Au shine suka fita ba su bani kudin cefane ba ai kuwa su dawo dan bazan yarda ba” Addah ta fada cikin sigar wasa. Murmushi kawai Asma’u tayi ta miqe tana musu sallama ta fice.

Wato Yanda Addah ta wanke idanunta bata taba nuna wani abu akan auran Amirah da Bashir na bala’in daure mata kai, mutum, ka kalleshi kawai. A reception ta hadu da Bashir daya je gidansu ya dauko Dada dan Naziru yana makaranta yau, cikin mutuntawa ta gaisheta tareda yi musu barka Dada ta wuce ciki Bashir kuma yabi bayan Asma’un.

“Har kun qaraso kenan, yanzu nake so dama na tafi gidan nayi wanka na huta wallahi duk na gaji” ya fada yana jingina da motar da tuni su Jafar suka shige bayan sun gaisa da Dada.

“Ya kamata kam, abincinka na nan ma na ajiye maka nayi zaton kafin mu fito zaka dawo kuma naji shiru, mu zamu wuce Babban gida qila idan zamu dawo da dare mu sake shigowa mu duba su” Asma’u ta fada tana qoqarin bude motar,

“Bazaki je kiga babyn ba?” Ya tambayeta
“Ai bazasu bari ba ka sani ba komai Allah ya bata lafiya idan lokacin fito da ita yayi zamu ganta ai mu da zata dawo gidan mu da zama ma”

“Eh kuma haka ne, bari na shiga na fito to nima na wuce ku gaida mutanen gidan ban samu na shiga ba wallahi Yanzu ma da zamu fito naga Kamar Alhaji Qarami dasu Yaya Mudassir a qofar gidan ashe yana gari”

“Eh yazo daurin auran yarinyar Amininsa ne jiya saurin da nake tayi kenan ma mu tarar dashi ance yau ze koma” da haka sukayi sallama ya shige ciki ita kuma taja mota suka nufi gidansu.

A can dakin kuwa bayan fitar Asma’u dayawan su sukayi wa Amirah caa akan abinda tayi bata kyauta ba, Addah ce ta tambayi meya faru Anty Aisha ta gaya mata.

“Ai ni na rasa kalar wannan yarinyar dan barikin nan ma na mata bata iya shi ba ke se baqin kishi quru quru meye amfanin sa”

“Wallahi fa Addah in nice ita yanda Anty Asma’u ta mayarda komai ba komai ba ake gaisawar mutunchi ai wallahi sake wa zanyi mu ci gaba da yanda muke amma kin zauna kina quntatawa kanki ita kuwa kina ganinta cikin walwala ji jikinta dan Allah wannan shegen Lashin nasan wlh yafi 100k ga zobuna a hannunta ji qanshin turare dan Allah har yanzu be bar gunnan ba” inji Samirah qanwar Bashir da suke Sa’anni da Amirah.

Hirar su suka ci gaba dayi aka shiga da take qonawa Amirah rai dan duk yabon Asma’u sukeyi ga dabgen kaji suna ci abinsu a haka Dada ta shigo ta same su ta kuwa ji dadin Abincin da ta tarar Asma’un ta kawo dukda ita ma ta taho musu da abinci amma tasan ba lallai ya isa ba tunda kusan duk yaran suna nan.

Asma’u kuwa hankali kwance suka isa gidansu wanda layi daya ne ya raba su da gidansu Bashir dan seka bi ta qofar gidan su Bashir din ma zaka shiga layin da gidansu yake da yake close. Cike da murna Seidu dan Baba Buzu daya daga cikin masu gadinsu tun na quruciya daya maye girbin Babansa yanzu ya wangale mata katafaren get din gidan na Alfarma ta shiga.

Tabbas gidan ya amsa sunan sa na Babban gida domin kuwa layi guda ne gidan haka tun daga get da katangar gidan zaka san cewa ba qaramin gidan me Arziqi bane. Tana gama parking a inda aka tanadarwa motoci gasunan birjik da alama yau akwai mutane da yawa a gidan yaran suka fita da gudu saboda hango cousins dinsu yaran Yayye da qannen Asma’u da sukayi se lokacin ta tuna yau Sunday kusan dukka yan gidan da suke a cikin garin Gombe Mata da Maza suna zuwa gida yau da iyalan su su wuni tun zamanin da Mahifinsu yake raye har yau kuwa basu fasa ba.

Seda ta gaisa da Samarin dake zaune a bakin get yawanci duk masu aikin gidan sannan ta shiga cikin gidan, part din Hajia Babba ta nufa dan a irin wannan lokacin tasan acan zata samu kusan kowa ai kuwa tana shiga katafaren palour nata fuskarta ta qara fadada da Murmushin ganin yan uwanta harma da wanda batayi zato ba.

Kai tsaye inda Hajia Babban take ta nufa Farar Bafulatana da a qiyasi ta bawa Sittin Baya amma jin dadin da take ciki ya boye shekarunta “Maraba Maraba da mutanen Lagos” take fada sanda Asma’u ta nufota, seda ta zauna dab da qafafunta tana daukar wani Dan yaro daya ruqo mayafinta da bata san ko dan waye ba sannan ta shiga gaisheta.

Cike da qaunar junan data ginu a tsakaninsu suka shiga gaisawa da sauran yan uwanta da suke a palour se tsiya suke mata wai ta qara kyau tayi wani haskee ta zama wanke ka taba ita dai se dariya kawai take musu. Suna cikin gaisawar Alhaji Qarami ya shigo Aliyu na take masa baya dan dama mutuminsa ne.

Gaishe shi tayi ya amsa mata cike da kulawa yana tambayarta aiki babu dai wata matsala ko tace babu sannan yayi wa Hajia Babba Sallama bayan yayi musu gajeriyar nasiha da tunatarwa daya saba yi musu a duk sanda suka hadu da yawa irin haka akan su riqe zumunchin da Mahaifinsu yasha wahalar gina su akai, seda yabi duk wanda yake zaune da dubu biyar suda yayan su kaf sannan ya musu sallama Driver sa ya ja shi suka wuce Abuja inda yake zaune da iyalansa. Ance daman babban wa makwafin uba to tabbas sudai sunyi dace dan kuwa Alhaji qarami ya maye musu gurbin uban da suka rasa.

A gaba ta saka yaran suka zaga saran part biyu na matan gidan suka gaisa Hajia Ummah da Hajia Anjin kafin suka wuce sabgarsu ita kuma ta koma part din Hajia Babba inda sauran yan committee suke jiranta a tattauna.

“Ke ashe Kishiyar ki ta haihu, dazu naji Abbas yana gaya wa Hajia Babba” Ikilima yayarta ta fada, seda ta cire yafinta ta ajiye a gefe ta zame dankwalin yayi baya sannan tace “wallahi fa ta haihu an mata CS jiya da daddare an ciro mata baby girl”

“Ayya CS ne Allah ya bata lafiya ya raya abinda aka samu” cewar Anty Hauwa matar yayansu Sunusi suka amsa da Amin gaba daya.

“Kinje kenan?”
“Naje mana daga can nake ma yanzu”

“Cab kuma kika kwashi jiki kikaje nifa wallahi Yah Asma’u kina bani mamaki na rantse da Allah in nice kallon banza yarinyar nan bata ishe ni ba bare na arziqi wallahi bazan je dubata ba, bata da mutunchi kwatakwata baki san abinda ta mana ba ranar sunan Rufaida(qanwarsu ce itama tana auran Yayan Amirah da suke uba daya) wai saboda bata da kunya ta kalle mu muna zaune wai bamu gaisheta ba idan Bashir ne ai dole mu gaidashi tunda mijin yar mu ne dan haka matsayi daya take dashi a gunmu ita Kishiyar yayar muce , wallahi Anty Habi ce kadai ta hanamu nada mata dan iskan duka ranar amma da se mun koya mata hankali” cewar Amina daga yanda take maganr zaka gane zallar takaicin Amirah da take ji.

Dariya Asma’u tayi tace “to ai se ku gaisheta meye a ciki zuwa dubiya kuma kema zakije dan ciwo na gaba da komai sannan ranar suna dole kuzo asha shagali daku”

“Tab Allah ya rufa asiri” Aminan ta fada tana tura baki. Dariya suka saka mata dan dama indai aka fara wannan dramar Amina bata da dama a fili take nuna jij zafin Amiran harma dana Bashir din dan ita fa tunda yai auran nan ta dena gaishe shi. Tace yanda beji kunyar ciwa yar uwarta fuska ba itama bazata ji kunyar dauke kai idan ta ganshi ba taqi gaishe shi.
Asma’u ta kance wai
“Amina inda kece a matsayina ban san me zakiyi ba” ita kuma tace
“Ai wallahi yah Asma’u da ko tsirena su Alhaji Qarami zasuyi na gama auran nan dan bazan koma ba”.

Ranar wunin dadi sukayi suka sha hirar su kamar karsu rabu, se bayan isha suka fara watsewa bayan tayi musu Alqawarin zata bi kowacce gidanta su gaisa da kyau tunda zata kwana biyu a garin.

Daga ita se Abdallah suka koma gida sauran yaran kowa ya kama gabansa dan daman idan suka zo indai ba tareda Bashir ba basa zaman gida in yana nan ne yake matsesu baya taba bari suje ko nan da can su kwana yanzun ma abinda yasa ta barsu yana cikin wannan digimi be zama lallai ma ya fuskanci basa gidan ba.

Seda ta biya Asibiti ta sake dubasu, a can din dai ta kuma samun sa kuma suka barshi sukayi gida yace se ya taho har suka kwanta dai be dawo ba seda Asuba sannan taji motsinsa dan a dakinta suka kwanta ita da

Please Login or Register in order to submit comment