Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

magana ai tunda har kika furta kina sona da bakin ki yanzu zan kira Alhaji Qarami na gaya masa. Daman yace na nemi soyayyarki shi kuma ze tsaya mun da izinin Allah a wannan karon sena sameki Asmyta" Yusuf ya katse ni ciki tsananin murnar da muryarsa ta kasa boyewa.

Be barni nayi magana ba ya kashe wayar, mamaki da dariya suka kamani duka lokaci daya. Wai da girmana da komai Yusuf yayi mun wayo dukda ni bada wata manufa na fadi Ina son sa ba kawai dai na fada hakan ne jin yanda yayi magana bawai dan har cikin zuciyata abin da yake raina kenan ba.

Tuqina naci gaba dayi hankali kwance harna isa gida. A bakin qofa na tarar da Bashir a tsaye ya harde hannaye da alama ni yake jira, na gama daidaita fakin kafin na fito fuskata a sake na shiga gaishe shi ina qare masa kallo yanda naga gaba daya ya zabge yayi baqi kamar wnada yayi jinyar shekara daya.

"Bari na shiga sena turo maka yaran seda fa na gaya musu su ringa zama a gidan ubansu amma saboda rashin ji irin nasu shine suka taho Yi haquri yanzu dana shiga zan tattaro maka su kuwa" na fada ina qoqarin wuce shi na shiga gida seya dakatar dani da cewa

"Ba gurinsu nazo ba Ma'u gurinki nazo ina so muyi magana".

"Toh gurina kuma?" Na fada ina kallonsa da mamaki, be amsani ba na ci gaba da magana ina cewa

"Kaga yanzu na dawo ko sallar magriba banyi ba ga gajiya na kwaso, idan ba abin sauri bane ka bari ko zuwa gobe Juma'a da wuri zan taso ko kuma Weekend ma kawai kaga ina gida se muyi maganar"

"Maganar sauri ce Ma'u, na kiraki a waya ma bata shiga na tura miki da saqo duk babu amsa" ya fada yana tsatstsareni da ido. Ko a jikina, gaba na sakeyi ina cewa

"Koh? Qilan saboda idan banyi saving lambar ba kira baya shigowa ne, to tunda kace abin sauri ne bari idan na dan huta zan aiko yara se su gaya maka" na fada ina tura qofa na barshi a tsaye.

Har qarfe tara na gama cin abinci kenan sega Abdallah wai Abbi yace yana jirana. Da mamaki na kalle shi nace ina Abbin yake dan nifa shaf na manta da mun hadu da wani Bashir ma har munyi magana ban qarasa cika da mamaki ba seda Abdallan yace mun wai ai yana qofar gida tun dazu ya saka kujera ya zauna.


Haka na saka dogon hijabi ba na fita saboda dai wulaqanci babu kyau. Yana nan zaune kamar wani sabon Almajiri na zauna a Empty kujera dana tarar ina cewa

"Kasan shaf na manta ma da munyi magana, koda yake ban zata zama kayi ba tunda nace idan na gama zan aiko yara su kiraka ai".

Zamowa qasa naga Bashir yayi kamar wanda yaje neman gafara a gaban Dada ya kama qafata na janye ya riqe qasan hijabina yana cewa

"Ma'u haquri nazo baki akan abinda ya faru tsakanin mu. Wallahi nayi nadama, sharrin shaidan ne ya angizani kuma na gane kurena na yarda idan babu ke a tare dani rayuwa ta bazata taba cika ba. Dan Allah ki yafe mun ki Yi haquri mu koma wa auran mu nayi miki alqawari baza kiyi nadamar komawa zama dani da dan nasan kina sona nima ina sonki zamu ci gaba da zaman mu cikin aminci kamar yanda muka faro shi".

Ido kawai na saka masa ina kallon wannan wasan kwaikwayo har ya kai qarshe kafin na miqe ina cewa

"Ka tashi dan Allah ko da yake kai naga baka tsoron kaga hotonka a Ticktock yanzu idan ba haka ba meye na durqusa mun. Asma'u ce fa Bashir daka danqara mun har saki biyu saboda matar so ka kuma bani rana daya tak dana tattara inawa inawa na bar maka gida har ka manta wannan shine zaka zo kana durqusa mun wai nayi haquri na komawa auranka?

To bari kaji, shi son da kake iqirarin a koma Saboda darajar sa daga sanda ka tsinke igiyoyin auran nan suka tattaro Son gaba daya sukayi awon gaba dashi, dama ai saboda auran ne ko tunda babu shi kaga babu sauran wani so tsakani na dakai, ko da kaga ina gaisuwar mutunci dakai darajar zuri'ar da take tsakanina dakai ne amma badan haka ba kai Bashir baka isheni ni Asma'u kallo ba ka sani.

Ada tabbas na So ka amma a lokacin da bansan menene So ba ba ayanzu da na hadu da limamin So ya fayyace mun shi na gane ma'anarsa ba. Dan haka idan kana mafarkin ni zan komawa auranka to ka tashi dan kuwa tamkar a baka tsinke a ce ka zunguro sama ne kaga kuwa wannan abu ne da baze taba yuwu ba kayi sake Bashir nayi maka nisan da har abada bazaka tarar dani ba"

ina gama fadar haka nayi shigewata gida na barshi a tsaye zuciyata kuwa yanda take bugawa ina tsammanin wanda yake tsaye kusa da ni ma ze iyajin bugunta.

A karanta da haquri, wani qundumemen uzuri ne ya taso mun beyond my control 🙏🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 55

BASHIR

Kamar wani dolo haka ya rakata da idanu harta bacewa ganinsa kafin ya sauke ajiyar zuciya me qarfi ya miqe daga durqushen da yayi yana jin kamar an sare masa qafafu tsabar yanda jikinsa yayi sanyi.

Tabbas Wannan ba Asma'u daya sani bace data jiqu cikin so da qaunar sa, ba Asma'un da take shiga damuwa saboda damuwarsa ba bace wadda take hana kanta bacci a duk sanda yake cikin damuwa ko bacin rai wannan wata Asma'u ce ta daban a gabansa.

"Idan ma kana mafarkin zan koma gidan ka to ka farka dan nayi maka nisa na har abada Bashir kayi sake" kalamanta suka ringa dawo masa a sanda yake jefa qafafunsa inda shikansa be sani ba dan burinsa a sannan ya ganshi a cikin gida kawai ya samu makwanci.

Shirim ya fada kan kujera ya dafe kansa da hannaye biyu yana juya shi. Wai menene SO?Yaya SO yake? Menene tattali da kulawar da mace take da buqata wanda Asma'u ta rasa a gurinsa da har take iqirarin ta samu wanda ya fayyace mata su?

Allah shine shaidar sa yana son Asma'u son da duk duniya be taba yiwa wata mace irinsa ba. Yana sonta tana kuma da wani matsayi na daban a zuciyarsa ta yanda tayiwa sauran mata zarra amma kowa ya gaza fahimtarsa mutane suna yi masa gukunci da zahirinsa ne kawai ba tareda sanin ainihin abinda yake cikin zuciyarsa ba wai me yasa kowa ya gaza fahimtarsa?

Dole ya san abinyi ba ze zuba ido yana gani ya rasa Asma'u ba faruwar haka daidai yake da yankewar duk wani farin ciki da walwala daga cikin rayuwarsa ya shaida hakan dan kuwa gashi a iya lokacin da suka rabu tun sannan be sake kwanan farin ciki ba. A kullum sabuwar damuwa da tashin hankali ne suke dirar masa.

Gidansa ya rushe, nutsuwar sa ta gushe lafiyarsa kanta ta tabu a cikin qasa da watanni shida besan yaya ze tsinci rayuwarsa ba ace ze qareta ba tareda Asma'u a cikin ta ba.

Wai ma wane ibtila'i ne ya haushi da har ya kaishi ga sakin Ma'u?
"Qaddarah" zuciyarsa ta raya masa se ya dafe kansa da hannu biyu yana fadin

"Hasbunallahu wani'imal wakeel" a fili yana jin yanda qirjinsa yake masa quna wanda ya zame masa jiki yanzu a duk sanda ya zauna yana tunanin makomarsa da Ma'u to se yaji wannan ciwon kamar numfashinsa ze dauke wani lokacin.

Wayar sa ya janyo daqyar idanunsa sunyi jajir sun kawo ruwa, lambobinsa yake bi yana karantawa ya rasa waze kira a yanzu. Duk wadanda ya kamata ya fadawa damuwarsa a yanzu ya dade da datse alaqa me kyau a tsakaninsu saboda a da yana ganin kamar suna masa katsalandan a rayuwarsa da qoqarin nuna masa yanda zeyi gashi yau ranar su tazo amma bashi da kwarin guiwar kiransu.

Lambar Bala ya kalla, wani tuquqin baqin ciki ya taso masa nan take ya danna mata block tareda goge ta gaba daya. Ba tun yanzu ya kamata ya ankare da ingiza me kantu da Bashir yake masa ba amma se yanzu da komai ya lalace sannan ya fito masa da ainihin kalar sa gaskiya.

"Allah sarki Aliyu, Amini na kwarai Rahmar Allah ta kai maka" ya fada yana dauke kwallar data ziraro masa ta gefen ido, yana kewar Aliyu da gasken gaske Aboki ne irin wanda ya zamar masa dan uwa wanda samun irinsa se an tona.

Aliyu ne kadai yake iyawa da halinsa, koda ace ya nuna masa gaskiya yaqi binta baya haqura ze yi ta naci da nusar dashi har se dan karan kansa ya fahimci hakan ya kuma ya aikata abin hirar su ta qarshe ta sake fado masa snada yake jaddada masa daya kula da Asma'u domin matar rufin asiri ce Allah sarki ashe shi ya hango masa abinda shi be gani ba gashi yanzu a daidai sanda Asirinsa ke neman ya bankade Aliyu baya nan ballan tana ya tayashi maido da mayafin ya lullube rayuwarsa.

Abubakar ne ya fado masa a rai, shi kuwa be yi wannan riqar da ze iya tunkarar Abubakar a yanzu ba bayan duk abubuwan dasuka faru tundaga auransa da Amirah zuwa yanzu daya sakar masa qanwa ya tabbatar ma baze saurare shi ba idan kuwa ya saurare shi to tabbas maganganu ze yayyaba masa da se yayi dana sanin kiransa.

Haka ya ringa saqa da warwara, shi da kansa ya tsinewa hali irin nasa yafi sau dubu ganin cikin lambobin sama da dari biyar da suke cikin wayarsa ya rasa shaqiqi daya da ze kira ya gaya masa damuwarsa ya bashi shawara akai.

Duk wadanda zasu bashi shawarar arziqi yayi fada dasu a lokuta mabanbanta lokuta amfabin zama da mutane lafiya kenan a rayuwa yanzu gashi yana cikin damuwa amma ko cikin yan uwansa da suke ciki daya ya rasa wanda ze tunkara dan ba saurarar sa zasuyi ba.

Wayar sa ce tayi qara, da sauri ya daga ganin Naziru ne me kiran a ransa yana Addu'ar Allah yasa ya sakko ne ya neme shi suyi magana dan yana da yaqinin ko iya Naziru idan ya shiga maganar ze iya shawo masa kan Ma'u saboda dab dakinta ne akwai kyakykyawar alaqa sosai a tsakaninsu.

A cunkushe kamar an wa Naziru dole ya gaida Bashir, ya amsa masa kafin yayi shiru yana jiran yaji abinyze fada

"Jirgin qarfe bakwai da rabi zata biyo idan sun sauka zata kirawoka" Naziru ya fada a taqaice.

Be damu da sanin wacece me zuwan ba yace masa
"Zan tura maka da Lambar samuel yanzu idan sun sauka kawai ta neme shi ze kawota gida, yawwa Naziru dan Allah...." qarar da wayar tayi alamar an kashe ce ta katse masa magana Wato Naziru ya gama jin abinda yake da buqata ya kashe masa waya.

Tagumi ya buga a gurin, ga damuwa, ga Yunwa ga ga kai abubuwan ma sun masa yawa. Tunawa yayi da ko sallar Isha beyi ba yasa ya miqe dakyar ya wuce dakinsa.

Gaba daya ko ina a hargitse yake komai yana nan zaune da kafafunsa daidai da takalman sa duk inda ya cire ya ajiye anan suke basu matsa ba yo daman waye ze gyara masa?

Badan ya tsawatar bama da har dakin nasa zata ringa sauke kwandon hauka da rashin hankalinta a ciki ai.
Haka ya dauro Alwala ya fara jera salloli yana ta kaiwa Allah kukansa har seda gabbansa suka gaji kafin ya zauna yana jin yanda cikinsa yake karta.

Dole ya tafi Kitchen ya hada shayi ya sha da burodi dan babu komai idan basu din ba sannan ya sake dawowa ya zauna a palour se sannan ma ya tuna da beji motsin yaran ba se ya miqe ya leqa dakinsu Aliyu.

Gaba dayansu suna ciki sun kwanta bacci, dakin Amirah ya koma bega Farida A ciki ba seya sake komawa kai tsaye ya kunna filita ya qarasa kusada kan Aliyu ya tsaya yana kiran sunansa.

"Ina Faridah?"
"Tana gidan Mami" Aliyun ya fada a cuskule kamar ma daman ba bacci yake yi ba se ya juya yana ce masa

"Kayi muku Addua seda safe" ya kashe fitilar yaja musu qofa.

Ranar dai kwanan zaune yayi idan yayi sallah ya gaji se ya zauan ya hau jan charbi har aka kira Sallar Asuba suka fita masallaci suna dawowa ya kwanta saboda wani bacci daya ji yana neman fin qarfin sa.

Can kamar a mafarki ya ringa jiyo karadi da hauragiya kamar ta Addah, qofar dakinsa dayaji ana duka tasa yayi juyi yana jan tsaki saboda katse masa daddadan mafarkin da yakeyi ya bude ido dakyar yana tambayar waye

"Nice nan Bashir gamu mun iso" ta fada daga waje. Dakyar ya iya tashi ya bude qofar a ransa yana mamakin wanene ya turo masa wannan matar? Kaf dangi a rasa wa za'a turo musu se Addah ai ba taimaka musu zatayi ba sedai ta qara masa yawan damuwar dayake ciki.

"Fisabilillah saboda wulaqanci irin naka Bashir seka turamun wani qedari da ko zo na kashe ka be sani ba duk ka gama kadamun hanta kasan da yanda na iya gano inda ma yake a cikin iyafot din ina zuwa kuma naganshi wani basamusen Arne. Nidai badan sunyi turanci da Naziru ba kuma Nazirun ya gaya mun na bishi babu komai Alqur'an da sedai nayi ta yawo a iyafot din idan suka gaji da ganina na nuna musu hotonka ai nasan dai baza'a rasa wanda yasan inda kake ba" Addah ta shiga jera masa bayani tana riqe da wata qatuwar Akwati kamar wadda tayo hijira.

"Ya akayi suka barki kika taho da wannan jakar" ya fada yana kallon Akwatin tata.

Seta gyara tsayuwa tace
"Kaidai bari ai Allah ya tsinewa mutanen nan seda sukawa jakata tsirara kamar wadanda na sako uwarsu a ciki, dakyar fa seda Yaron nan Naziru ya biya wani kudi wai nayi lodi da yawa kafin suka barni na wuto da ita dukda haka seda suka kwashe mun wasu abubuwan wallahi nidai nayi Allah ya isa".

Juyawa yayi ze koma ciki dan kansa harya fara masa ciwo da wannan surun nata se kuwa ta tareshi tana cewa

"Ina kuma zaka? Ita Amirar tana ina ko bata ji shogowata bane? Sannan ina zan ajiye kayan nan ga Yunwa ni ina jin ai se a bani abin kari".

"Ina zuwa" ya fada yana shigewa ciki tareda murzawa qofar key. Wayar Dada ya shiga kira yana shafa goshinta ko tsayawa gaisuwa beyi ba yace mata

"Dada me yasa zaki turo mana Addah kin manta matsala ce matar nan nida nake neman sauqi ya zaki qara mun damuwa?"

"Toh Bashir idan ba ita ba wa kake so tazo karka manta fa ita ta haifi Amirah kuma ko ba haka ba yar uwata ce kaga tana iya zuwa gidan ka ta zauna ai. Nidai Koma mene ne dai se kayi haquri ka dauke kai kwana nawane da Amirah ta warware ai zata dawo ne ta barku ko" Dadan ta fada.

Sallama sukayi dan bashida abinda ze kuma fada toh mema zece bayan aikin gama ya gama ai tun kamin ta taho ya kamata a gaya masa da se ya dauki mataki yanzu kuwa ya zeyi ma da ita.

Wanka ya shiga yana jiyo yanda take ta mita tana buga masa qofa harya shirya tsaf kafin ya bude qofar ya fito.

"Wannan wane kalar wulaqanci ne haka, ka barni a gantale ko masauki baka bani ba idan Nafi ce tazo haka zaka barta a tsaye ka shige daki ka rufo qofa koda yake mantawa nayi ai ba mutunchi ne dakai ba daman to ina ita Amirah tunda uwarta ce ni ai bazata wulaqantani ba".

"Nifa bance a turo ki bama kawai ki jira yanzu za'a zo a mayar dake Airpoki wuce gida" Bashir ya fada cikin hade rai.

"Ai wallahi ko ubanka Amadu be isa ba dan naga guri nan zama me nawuda ta samu katifa duk baqin cikinka se naci arziqin da kuka tare a nan bakwa tunawa da mu se abinda kuka ga dama kuka yafa mana ina ita daya shegiyar nace maka tunda ita na haifa ai bazata koreni ba" Ta fada tana riqe qugu kamar wata qaramar yarinya.

"Tana Asibiti se gobe za'a sallamota" ya fada a cuskule yana qoqarin wuceta.

"Yau naga abinda ya ishe ni, to ka kaini Asibitin mana kana jan qafafu kamar na zalbe zaka wuceni zamane daram ba inda zani sedai baqar zuciyarka ta kashe ka shege me baqin halin tsiya@ ta fada tana gyara mayafinta. Ba tareda ya kalleta ba kuwa yace mata

"Ba'a zaman jinya ki jira da Yamma wanda ya kawo ki ze zo seya kaiki ki dubata ku dawo" yana gama fada yayi ficewarsa dan gara yayita yawo a gari yana qona mai daya zauna a gidan nan wannan birkitacciyar tsohuwar ta chaza masa kai.

Rasa abinyi Addah tayi, ta shiga Kitchen ta duba gadai kayan abinci amma bata san ya zata yi amfani da kayan wutar ba dan Gas cooker dinsu ma soft touch ne. Palourta dawo ta tsaya tayi sa'a sega Aliyu ya fito daga daki da Kofin shayi da farantin daya soya dankali da kwai ga ragowar nan be cinye ba seta nufeshi tana washe baki tace

"Yawwa Dan Albarka taimaka nima ko shayi da kwan ne ka bani wallahi Yunwa nake ji ban karya ba na fito, bani wannan na fara dashi kafin ka hadomun wani" ta fada tana qoqarin riqe farantin hannunsa.

Kallon daga ina ya mata kafin yayi kwana ya fasa shiga Kitchen din da yayi niyya, akan idon Addah ba tareda ya kalata ba ya fita qofar gida ya zazzage abincin a inda suke zubawa karnukan da suke gadi abinci ya sake dawowa ya wuceta ba tareda ya kulata ba.

Haka ta ringa masifa kamar zata ari baki amma dan gaske yayi banza da ita qarshema Tv ya kunna ya hada Game dinsa ya fara bugawa daidai Nan Jafar ya shigo, shine me farat farat nan da nan ya gaishe ta. Shi ya rakata har qofar gidan Ma'u be shiga ba dan yasan qila tayi masa fada se ya koma gidansu yana shiga kuwa Aliyu yayi kansa da fada kamar ze dakeshi shi dai yayi shiru be amsa masa ba.



ASMA'U
Cikin filo na cusa kaina dana dafe da hannaye bibbiyu, na kasa yarda Bashir ne ya durqusa a gabana yana bani haquri sannan waini Asma'u na iya gaya masa maganganu haka ba tareda wani dar ba.

"Kar fa ace na dena son Bashir da gaske" na fada a fili ina tashi zaune. Tagumi na rafka hannu biyu gaba daya na rasa me ma yake damuna. Ina jin wayata dake gefen gado tana ta qara amma naqi dubawa dan nasan dayan uku ne ko dai Bashir ko Yusuf ko kuma dayan Mayen Hayatuddeen.

Gaba daya daren haka na qarar dashi ina juyi da tunane tunanen da ni kaina bansan me nake tunawa ba. Saboda rashin samun wadatacce bacci da ciwon kai na tashi idona yayi ja kamar wadda tayi kuka.

Da yake Asabar cema abin yazo mun da sauqi nayi wanka na saka riga mara nauyi kafin na fito palour na tarar da Amnah da Farida suna cin abinci.

Bayan mun gaisa Amnah ta tafi kawo mun abin kari se Farida ta dawo kusada ni tana cewa
"Mami kin san me?"

"Meya faru sarkin labari?"

"Mami, Addah ce fa tazo yau, gasu can se fada suke da Abbi yace seta tafi shi bece a turota ba ita kuma tace ba inda zataje. Nidai Mami na dawo nan gidan da kwana dan Kinsan halin Addah fada ne da ita har da dadddare nasan hana mu bacci zata ringayi".

"Ikon Allah" na fada ina karbar Kofin shayin da Amnah ta hadamun, hankali kwance na shiga cin abincina har na gama ba tareda na bawa Farida amsa ba can qasan raina ina mamakin dalilin zuwan Addah.

Ina shirin tashi daga gurin naji an doko sallama bana buqatar qarin bayani nasan wacece lokaci daya na hade fuskata tsaf yanda kasan ban taba dariya ba a duniya ina kallon qofa daidai sanda ta shigo cikin palour fuskar ta dauke da wannan dariyar tata dana kira data qeta tana cewa

"Ga baqin Asuba ko da yake rana ta daga ai. Se kuka ganmu babu sanarwa ko?"

Ban amsa ba sema harde hannu da nayi a qirji ina qare mata kallo har ta zauna akan kujera. Idan ba ido na ba se naga ta zabge babu wannan qibar kuma tayi baqiqqirin kana ganinta kasan tajin qari matuqa.

"Asma'u ina kwana?" Maganar ta ta katse ni, daga tsayen na amsa mata da
"Lafiya" na qara daure fuska. Ina kallon yanda ta bini da ido alamar mamaki qarara akan fuskarta kafin kuma ta waske tana cewa

"Uhm daga dayan gidan naku nake, kinsan qanwar taki bata da lafiya an kwantar da ita a Asibiti ciki ne da ita shine fa nazo zaman jinya ashe u Asibitin naku ba'a kai musu me jinya.

Jirgin Asubanci muka biyo ko karyawa banyi ba, ga Bashir da baqin hali wallahi ko ruwa be bani ba in gaya miki ya ma fice ya barni a gida ni kwal kamar mayya ni ba iya amfani da kicin din ku na zamani nayi ba shi kuma wancan me kama da uban nasa ko kallon arziqi be mun ba shima daya.

Shine fa na fito waje sena ci karo da dan kirki Jafaru yace na shigo nan na samu na sakawa abakin salati".

Tsam nayi ta gama rattabo jawabin ta kafin na juya dakina ina cewa

"Ayya gashi kinyi rashin sa'a fita zamuyi muma. Koma ba haka ba baki sanar mana da zuwanki ba dan haka ba'a dafa dake ba".

Sena waiwaya na kalli yaran da sukayi tsuru suna kallon mu nace
"Ku tashi ku shirya fita zamuyi"
"Mami ina?" Abdallah ya tambayeni, sena harare shi nace

"Inda ka aikeni ubana".
Ina shiga dakin na kwalawa Amnah kira ta biyo ni da sauri.

"Ko ruwan fanfo ku ka bata senaci uban mutum wallahi ku wuce ki shirya Yan biyu ku jirani a waje" na fada cikin sigar umarni.

Harna fara qoqarin chanza kaya wata zuciyar tace mun to akan me zan fita ma ta koma inda tazo meye hadina da ita toh? Se kawai na kwanta akan gado na sake kwalawa Amnah kira nace mata

"Kije ki ce mata ta fita zaku rufe gida ne" jim naga tayi alamar bazata iya ba, na ja tsaki ina miqewa nace "matsa mun daga nan"
Na bi bayanta muka fito har sannan Addah na zaune ta rafka tagumi kamar wadda akawa mutuwa.

Fuska a daure ba tareda na kalleta ba nace
"Ki koma can gidan ina so mu rufe qofa saboda baqi masu shigo maka ba tareda iso ba".

Allah sarki se kuwa ta miqe tsam da natacviyar qatuwar pos dinta dana rasa uwar datake durawa a ciki tana kallona tace

"Toh bari naje, amma dan Allah ko gayan biredi idan kuna dashi ki bani sena hada shayi koda ruwan sanyi ne nasha tunda naga madara a can din".

"Kije za'a kawo miki" tayi mana sallama kuwa ta fice.

Kwai na saka Amnah ta soya mata guda shida nace su hada mata da biredi sinqi daya me yanka yanka ta bawa Jafar idan yaje ya jona mata ruwa a kettle seta sha shayin na sake komawa dakina ina shiga wayata dake kan mudubi ta fara qara.

Yusuf ne, na daga da sallama ya amsa yana cewa
"Amaryata barka da safiya" Yusuf ya fada daga daya bangaren

"Wacece Amaryar ka?" Na tambayeshi ina gyara zama se ya bani amsa da cewa

"Wata ce, yau zan shigo Lagos nayi kewar ki da yawa da naso na bari se sati na sama amma naga bazan iya ba ke din kawai nake so na gani dai"

"Wancan satin fa kazo" na fada se yayi saurin katse ni da cewa

"Idan kika ce na zauna sena haqura ya zanyi girmanki ne amma wallahi dagaske nayi kewarki ni kadai nasan yanda nake azabtuwa da rashin ganinki din nan. Ki taimaka mun ki zama mallakina dan Allah ko hankalina ya tattaru a guri daya na dena raba shi".

"Uhm" na fada kawai dan ban san me zance masa ba.

Sosai ya kwantar da murya yana cewa
"Asma'u bana so na sake yin saken da

Please Login or Register in order to submit comment