Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

kullum kuwa se ya bini.

Bansan ya suka qare da Amirah ba nasan dai ta tafi, dukda abinda ya aikata ai ba laifi bane ko babu komai ai matarsa ce daman ai yana da ikon kaita ko ina amma yanda ya biyo da abun ne babu tsari a ciki. Dan haka fushin kwana biyu na qara kafin na ware muka koma daidai kamar bamu samu wani saba ni ba.

Amirah
Da baqin ciki da takaicin Ma’u da Bashir ta koma Gombe, har kuka tayi sanda take labartawa Addah abinda ya faru.

“Se kinga yanda ya rikice Addah harda durqusawa yana bata haquri a gaba na ita kuma se yankwana shi takeyi saboda ta nunamun ta isa dashi. Saboda wulaqnaci fa gidan Ghali ya turani na qarasa kwana sannan da zan taho ma Taxi yasa ta kaini Airport se a waya mukayi sallama”.

“Tab lallai Asma’u ta gawurta yanzu Bashir din ne ya duqa mata, lallai dole mu sake tashi tsaye. Ni ina ganin komai yayi lafiya yanda kwana biyun nan aketa abin arziqi ashe da sauran rina a kaba” Addah ta fada tana kama baki.

“Ai wallahi bata ci bulus ba, yanda ta rusa mun tsarina nima sena rama” Amirah ta fada, daga nan suka shiga qulle qullen yanda zasuyi su rama abinda Ma’u tayi mata.

Lagos
Ranar Juma’a data kama litinin a koma makaranta Amna da Farida suka dawo, ban gayawa Bashir ba na saka Naziru ya siya musu Tickets dan daga Yola Gombe aka kaisu se ganinsu kawai yayi ai kuwa ya ringa masifa akan me zan doro masa yara a jirgi su kadai me yasa ba’a gaya masa yau zasu dawo ba yaje ya taho dasu ko shi Nazirun ya rako su nidai nayi banza dashi tunda sun dawo ai magana ta qare.

Monday qalau muka rabu kowa ya tafi aikinsa ranar na dan jima a office saboda shirin Tafiya Abuja da mukeyi wani conferees se bayan Magriba na shigo gida. Seda mukaje kwanciya sannan nake gayawa Bashir dan saura sati daya tafiyar.

“Lallai Big woman anya nima bazan zo a dan sama mun guri ba naga fa kuna kwasa da yawa a office din nan naku” ya fada da dan murmushi yana danne danne a wayarsa, sena gyara zama ina cewa

“Kaidai bari wallahi yanzu ma fa package din tafiyar nan naji Accountant yana cewa kusan 700 huns za’a bamu each kudin TP da accommodation ni daman gidan Alhaji Qarami zan sauka kaga sena soke kudina, Goggo nake so ma na biyawa Umarar Azumin su tafi tareda Maman Ayman”.

“Hakan yayi kyau, nima idan na samu yanda nake so se mu tafi da ke ita kuma Amirah se taje Hajji”.

“Allah ya yarda toh” na fada sannan muka ci gaba da hira har bacci ya dauke mu.

Weekend din daya kama satin da za’a shiga zanyi tafiyar ranar Asabar da daddare na sake gaya masa zancen tafiyar base ranar Monday ya ganni da jaka ba.

Yana zaune na kawo masa coffees da yace yana so nake masa zancen ina cewa “Allah ma ya taimake ni Amna na gida yanzu da bansan yanda zanyi tafiya harta sati guda ba”.

Shiru ya mun yaci gaba da shan coffee dinsa nima se na mayar da hankali na kan Tv seda ya mula dan kansa se cewa yayi “wai dole ne se kinyi tafiyar nan?”

Ban waiwayo ba na bashi amsa “Kaji Baban Ali da wata magana, tun fa last week na gaya maka, me ze kaini toh idan ba dole ba”.

Tsakin daya ja ne ya saka ni waiwayawa na kalle shi, fuskar nan a mugun hade seda gaba na ya fadi dan rabon da nagan shi a irin haka an kwana biyu.

“Lafiya” na fada ina gyara zama na fuskan ce shi da kyau, se ya miqe kawai ya shige dakinsa nima na rufa masa baya.

“Kibar tafiyar nan kawai dan bazan iya zama har sati guda ni kadai ba” ya fada yana cire rigar jikinsa da alama wanka ze shiga. Sena marairaice cikin lumana ina cewa

“Haba Engineer satin fa kamar yaune qilan ma baza mu kai haka ba, kayi haquri ka daure In Sha Allah gaba idan haka ta taso zan nemi a chanza wani dani amma yanzu lokaci ya qure kaga jibi ne fa tafiyar”

A maimakon ya sakko se nagama kamat fetur na qarawa wutar dan hargagi ya shiga yi mun yana cewa “nidai na gaya miki kawai, ke ni aikin nan ma gaba daya bana sonsa daman idan mace taga tana samun kudi gani takeyi kanku daya tunda babu abinda zata nema a gurinka, kai ta yaya ma za’ayi mutum yana da mata amma ta tafi wani guri tayi har sati daya meye marabar sa da gwauro” bam ya shige Bandaki ya bugo qofar sena rakashi da ido kawai ina karanta Hasbunallahu wani’imal wakeel a zuciyata.

Abin ya motsa kenan, haka naja jiki a sabule na fice na koma dakina. Rasa wanda zan kira na gayawa wannan abu nayi ina zaune sega kiran Babbar yayar mu a dakin mu Anty Suhaima da take America ta kirani.

Bayan mun gaisa mukayi shiru dan babu sabo sosai tsakanin mu saboda ita da wuri tayi aure ta auri dan Abokin Baffan mu yan Kano ne a lokacin Baban sa shine Ambassador na Nigeria a America dan haka tunda tayi aure can aka kaita kusan shekara Ashirin da biyar yanzu.

Jin shirun naw yayi yawa ya sakata cewa “Ma’u lafiya kuwa kamar akwai abinda yake damun ki” haka kawai naji kuka ya taho mun ba kuwa ta hanani ba ta barni na yi abuna seda nayi shiru dan kaina kafin na gaya mata yanda mukayi da Bashir.

“Daman baya son aikin naki tun farko ne ko yaya” ta tambaye ni,
“Wallahi Anty be taba nuna baya so ba, tun ma ba yanzu ba kinsani kafin wannan nayi wau qananun ayyukan kuma be taba hanawa ba a koda yaushe yana bani goyon baya, yanzun mafa ya yarda yau ne kawai dana sake gaya masa zancen tafiyar shine kuma ya bullo da wannan maganar”.

“Shikenan, ki rabu dashi ki ci gaba da Addu’a zuwa goben ku sake maganar idan be yarda ba ki haqura karki tafi ba tareda izinin sa ba idan yaso ki gayawa Alhaji qarami se aji me yake nufi da aikin naki daman ai zaman aure dole akwai qalubale Ma’u Allah dai ya sa mu dace kawai” nasiha taci gaba da yi mun kafin mu ka gaisa da yaranta dukka su hudu sannan mukayi sallama bayan na tura musu da Number Aliyu da Amna da suka ce.

Ban koma dakin Bashir ba a zato na kuma ze biyo sahu amma har dare ya tsala naji shiru.

Da safe na sake tun kararsa da maganar se kuwa cewa yayi “In dai izinina kike nema toh ban yarda ba” ya sa kai ya fice daga gidan.

Yana fita na dannawa Dadan su kira dan kuwa bazata sabu ba, tas na gaya mata yanda mukayi tace na kwantar da hankali na zata masa magana, ilai kuwa da daddare ina zaune se gashi fuskarsa nan kamar Hadari yace

“Wato qarata kika kai Gurin Dada ko? Shikenan kije amma ki tabbata sena dauki hukunci akan hakan”.

“Tunda dai ka barni ai zance ya qare” na fada bayan daya fice daga dakin, washe gari na cale zuwa Abuja bayan na barwa yara komai da zasu buqata karma ya huce haushi na akansu.

Amirah
Sosai ta kunnowa Bashir wuta tunda ta fuskanci shi mutum ne me son a girmama shi ba kuma yason raini se tayi amfani da wannan damar gurin nuna masa ai Asma’u ta raina shi kuma abinda take nuna wa mutane kenan cewa tafi qarfinsa.

Da Samirah qanwar sa suka shirya komai dukda ita Samiran bata san amfani da ita Amirah tayi ba. Tana zaune ta kirata take bata labarin abinda ya faru ai Bashir ya durqusaw Ma’u, Smairah kuma irin masu dan banzan surutun nan ne idan taji abu kamar dukka dangi kowa yaji ne dan haka kafin kace me wannan Labari ya karade kowa kamar wutar Daji cikin haka maganar ta koma kunnen Bashir.

Amma saboda rashin Adalci irin nasa a maimakon ya ji haushin Amirah data fada tunda a gabanta akayi se laifin ya koma kan Ma’u a cewarsa da batayi masa boren da tayi ba ai da be durqusa matan ba har Amiran ta samu abin yayatawa ba wannan fushin ya qudure a ransa.

Kwana biyu tsakani har ya huce tayi masa zancen biyawa Goggonsu Umarah se akayi dace washe gari Bala ya kirashi, suna cikin waya yake ce masa

“Mutumina ashe Ma’u ta siyi gida nan kusa damu, jiya mun zagaya ta gurin naga gidan hadadde nake tambayar na waye akace na matar ka ne kamar ma guda biyu ne fa ko Su Aliyu ta siyawa ne”.

“Anya kuwa Ma’u ta siyi gida ba tare da na sani ba me zatayi dashi, ina ga dai ba nata bane sedai wata daga cikin yan gidan su ko” Bashir ya fada.

“Lallai Bashir baka san mata ba, ka manta lokacin baya kenan yanda yan uwanta suka tinga zugata akan karta doraka akan dukiyarta. Yanda take karbar kudin Hayar gidajenta ga Albashi me tsoka ai dole ta ringa siyan kadarori tana boyewa baka sani ba,

nifa wallahi nama ga baikenka kana zaune na tabbatar yanzu ta ninkaka sau uku a arziqi wallahi in bakayi wasa ba kwanan nan zaka zama mijin Hajia se yanda tayi dakai tunda tafi qarfin komai babu abinda zata nema a gurinka.

Da zaka ji ta tawa ma kasa ta ajiye aikin nan wallahi dan tana dab da finka Albashi bashi ne taqamarka ba”.

Wadannan maganganun na Bala dana Amirah su suka yi tasiri a ransa dan yana ganin abinda Balan ya fada gaskiya ne.

Tunani ya shigayi Rabon da ya dauki kudi ya bata ma shi harya manta daidai da kudin sati na man mota da yake bata yafi wata shida be bayar ba kuma bata tambaye shi ba.

Daman cefane baya yankewa a gidan kusan zece buhun huna kadai yasan yana siya amma sauran abubuwa tunda daman ita yake bawa kudin tayi mantawa yake kuma bata tambayarsa haka zega komai a ajiye. Yanzu a satin daya wuce ta ce masa Bilal ya turo mata wasu motoci idan yana so ita ma zata chanza tata ko School Fees din makaranta na wannan term din ita ta biya se daga baya ya mayar mata da kudinta gashi kuma a kullum cikin yin suturu na alfarma take daga ita har Yaranta har shi tana siya masa takalma da Agogo ga turaruka.

Wadannan abubuwan daya hasaso a shirmensa su yake ganin zasu sa tafi qarfinsa har ya kasa juyata gashi kuma sauran mutane ma sun fahimci cewa Asma’u tafi qarfinsa a ganinsa babbar gazawa ce kamar shi ace matar sa tafi qarfinsa dan haka dole ya dauki mata ki akai.


Kunsan December ansha Bukun kuna
Allah ya bawa Amaren mu zaman lafiya ya kawo na yan baya 🙏🙏🙏🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 30

ASMA’U

Cikin kwanaki biyar muka gama abinda ya kaimu, ada naso na yi weekend na huta ne har nadan zaga dangi amma saboda yanayin rabuwar mu da Bashir yasa na fasa daga gidan Alhaji qarami ko gidan Yayata Junaidiyya da mijinta yayi Accident, naso naje na dubashi amma gudun kar sauran suce banje musu ba yasa kawai na haqura.
A ranar Juma’ar da muka gama na bi jirgin dare zuwa Lagos.

Kadaran kadahan Bashir ya karbe ni, ban damu ba na shiga sabgogina ina dai ta qoqarin ganin komai ya daidaita a tsakanin mu amma yaqi bada hadin kai sam.

Ranar Talata da daddare bayan mun gama cin abinci Bashir da Aliyu suka fita siyo Biredi sauran yaran kuma duk suka koma cikin palour ni kuma na zauna a Gurin Dining din ina danna waya, kiran Muslim Yaya nane ya shigo wayata, mun dan jima muna magana kafin mukayi sallama yana kashewa Khadija qanwata ta kirani.

Abdallah ne ya taso ya kawo mun littafinsa na quantitative reasoning ya kakare a wani guri daman ina jinsu da yayyan yanata su koya masa kowa yaqi dan haka na saka wayar a speaker muna hirar ina nuna masa.

Hirar wata faccalarta takeyi mun, babansu yana da kudi kamar su kashe shi amma irin matsolon nan ne ba’a cin kudin sa se akayi dace data tashi aure ta auri me kwadayi dan shi dalilin auranta ma saboda kudin baban nata ne.

Tofa tunda akayi aure yaga babu lashi se rashin mutunchin yau daban na gobe daban qarshe ya yiwo mata kishiya ma shine yanzu ba’a dade ba baban nasu ya rasu anyi musu rabon Gado ta samu kudi sosai se kuma ya dawo kamar yaron ta se yanda take so yakeyi har Kishiyar ma yanzu ya mayar mata da ita kamar me aiki kome take so shi za’ayi a gidan nan.

“Wallahi Anty se kin ganshi jiya da mukaje sabon gidan da tayi yana tsaye yanda kika san dan aiki daga tayi motsi ze zaburo yace Hajia me kike so Hajia me za’ayi, ni ban taba ganin meson zuciya irin Rabi’u ba wallahi” Khadija ta fada.

Dariya nayi ina cewa “kudi ake gaya miki huce takaici kenan, ai idan mace ta gawurta zakiga har mijin ma wani shakkar ta yakeyi balle kuma kishiya. Shiyasa kika ga mun dage muna neman su maganin wulaqanci” na fada dai dai sanda Bashir da Aliyu suka shigo, wani kallo dana kasa fassara ma’anarsa ya yimun kafin yasa kai ya shige dakin sa.

Hirar mu muka ci gaba sannan mukayi sallama lokacin na gamawa Abdallah Homework din se na tashi daga gurin nima na shiga dakin Bashir.
Qarar ruwa da naji yasa na gane yana Toilet, sena zauna a gefen gado ina jiransa ya fito.

Kudi nake so na ara a gurinsa ina so na qarasa mana siyayyar kayan sallah dan haka nakeyi kafin lokacin yazo na siyi komai idan ya bani kudin se nayi wasu hidimar dasu yanzu kudaden hannuna duk na tattara na bada kudin Umarar Goggo daman Kudin Hayar da zan karba na saka rai dasu to su kuma tun kafin suzo ma na bada Aron su.

Seda na barshi ya gama shiryawa ya zauna sannan nace “Baban Ali Aron kudi nake so dan Allah”.

Shiru yamun ban damu ba na cigaba da cewa
“Kasan na gaya maka zancen tafiyar Goggo to na bada kudin, wadanda kuma nake saka rai na hayar gidajen nan wallahi Yaya Abubakar ya rance wai ya cikawa su Bilal sun tada ginin gidajen su bayan Babbar Sallah nan muke saka ran bikinsu”.

A maimakon ya amsa ze bani ko baze bayar ba se ji nayi yace “Lallai Ma’u karanki ya isa tsaiko.
Wato ban isa ki tambayeni kudi ba sedai kice na ara miki ko? To bari kiji ni ba sakaran namiji bane da har kike tunanin dan kina riqe wasu yan kudade zaki fi qarfina, inaji har fada kikeyi kudi maganin wulaqanci idan mace ta gawurta miji zeyi shakkarta to bari kiji ko kin fi Dangwote kudi ina nan a matsayin mijin ki kuma baki isa na biki ba.

Daman tunda kika fara aikin nan naga halayenki da yawa sun chanza, saboda zan fita nema kema ki fita kina ganin kanmu daya ba? to ya zama dole zan dauki mataki, ki fara shirin ajiye aikin nan”.

Kamar sokuwa haka na ringa binsa da kallo har ya gama magana. Dan Allah meye laifina anan? Daga neman rancen kudi shine ze tado wadannan maganganun haka.

Sena sake matsawa kusa dashi ina cewa

“Yanzu saboda Allah Baban Ali rashin tambayar ka kudi da nakeyi ashe nan ma laifi nake ada da nake tambayar ka kuma cewa kayi ai na ishe ka da bani bani kai bakaga amfanin Kasuwancin da nake yi ba wai dan Allah me yasa ba’a maka gwaninta ne??

Kuma ni a yaushe kaji nace nafi qarfin ka ko ina so ka bini idan dai ba neman tada zaune tsaye ba daga ji mutum yana waya se kace dakai ake baka san hawa ba baka san sauka ba.

Maganar aiki ko kuma wani kudin daban da nake samu kasan idan da tarawa nakeyi da yanzu na kai inda nakai wallahi amma ko na samu jikinka suke komawa tunda kafin na amfani kaina da biyar na amfana wa yaranka da dari. Yaushe rabon da ka dauki sisinka ka bani da sunan wata hidima tawa kota yaran nan?

Siyowar da kakeyi da kanka ma tunda kaga idan ya qare inayi ka sakar mun se sanda ta raya maka sannan zaka siyo ko ka bada kudi a siyayyar.

Idan ba sallah ba na manta rabonda yau Baban Ali ka kawo dankunne kace gashi wannan naki ne kuma kullum kana ganina da sabon abu amma baka taba tambayata a ina na samu ba duk ba sauqin ka bane, idan da bani da abinyi ai duk nauyin a kanka suke”.

“Oh gori zakiyi mun kenan daman ni nace ki ringayi ko ke kika dorawa kanki?
To ki dena, daga yau karki sake saka silenki a hidimar gidana kota yayana ki gani idan bazan iya ba” Ya fada a fusace.

Haka kawai naji zuciyata ta karye wani kuka yana neman taho mun, wai me zanyi na burge Bashir a rayuwa ne? Duk abinda nayi aje a dawo wata rana se ya zama abin fitina, seda na dauke hawayen daya zubo mun akan fuskata kafin nace

“Ko baka fada ba nima bazan sakeyi ba idan yaso seka gani in abin kirki nake maka ko akasin haka” daga haka naja bakina nayi shiru ina goge hawayen da suke zuba daga ido na dan na kasa hana su fitowa.

Meyasa maza ba’a iya musu a rayuwa ne? Idan kika zauna baki nemi na kanki ba a goranta miki idan kin tashi kin nema shima baki tsira ba to ya ake so kayi?

Wayar sa ce ta katse mana shirun da mukayi se ya daga yace “zan kiraki” kafin ya kashe.
Ina lura da yanda yake satar kallona yana zuba tsaki se na dena goge hawayen na barsu kawai suna shata se ya miqe gaba daya ya bar mun dakin yana fita kuwa na fashe da kuka me sauti harda sheshsheqa.

Bashir
Gaba daya jikinsa yai sanyi da ganin hawayen nata, shi da kansa yasan be kyauta sam Asma’u bata cancanci wani abu a gurinsa ba bayan kulawa da tattali amma dole tasa kashi yin koma menene dan a nasa ganin an fara dakko sare sarin da zata fi qarfin nasa saboda sam ada ai ba haka take ba.

Idan ya gaya mata magana tana ji amma yanzu abinda tasa a gaban ta kawai shi takeyi. Bata yij shawara dashi sedai kawai ta gaya masa zatayi abu kaza in aka ci gaba da haka ai wataran ma se tayi sannan ze sani dan haka ya quduri niyyar kawai ta aje aikin nan tunda shi yake sake bude mata ido tana hulda da manyab mutabe tana ganin rayuwa kala kala.

Kwana biyu a tsakanin gaba daya na dauke masa wuta na fita a sabgarsa na kuma qudurce a raina yar biyar dita Bashir baze sake ci ba. Dakansa ya sakko ya ringa neman shiri dayaga yanda na watsar dashi seda na gara shi kuwa sannan na haqura amma fa ba wai na chanza ra’ayi ba jira kawai nake wata yayi na fara tatike Aljihun Bashir.

Sati biyu tsakani wata ya qare kuma a satin nasan zeje Gombe, ina sane na zauna na rubuta uban list kai harda abinda muke dasu seda na rubuta na hada total dina kusan dubu dari da Ashirin, ana gobe ze tafi ina jinsa yana mitar an qara kudin jirgi seda ya gama na miqa masa takardar ina cewa

“Ga wannan karna manta ka tafi, na manta Gas din mu ya qare shima qaramar cylinder da tayi saura ita aka saka jiya sannan lemon yan makaranta da Biscuits suma babu na manta ban rubuta”.

Takardar ya karba ya duba se ya dago ya kalleni yace “Wannan kudin duk na menene haka kusan dubu dari da Ashirin?”

“Shi yasa fa na rubuta maka komai dalla dalla da kudinsa karma kace qari nayi maka ko wani abu” na fada ba tareda na kalle shi ba, seda yaja wata qwafa kafin naji yace

“Yanzu kudin zan baki kenan?”
“Ka siyo da kanka ma duk daya ne ai” nayi saurin katse shi. Beyi magana ba mintina kadan naji wayata tayi qara alamar shigowar message na jawo na duba Alert ne na dubu dari da Hamsin daga Bashir nayi murmushi nace
“Sun shigo harda qari ma muka samu toh mungode Allah ya qara budi”.
Washe gari ya tafi Gombe.

Weekend din a daddafe nayi shi dan gaba daya bana jin dadi, zazzabin dare ne yake damuna safiya nayi kuma naji garau na bari akan Monday idan be dena ba zanje Asibiti.

GOMBE

Wato wata Irin ladabi da biyyaya Amirah ta ara ta yafawa kanta wanda duk hudubar Sa’ada ce. Jikinta na bari Daman yanzu da yace zezo zataje ta qalqale gida a gyara ko ina dukda dai da taimakon Ummi harda Sa’adan ma suke zuwa wani lokacin sannan idan yazo tana iya qoqari tayi tsafta harya tafi a bangaren girki ne dai har yanzu da saura yana ci yana qorafi dan baya masa kamar na Ma’u.

Wannan zuwan da yayi sosai yaji dadinsa ga tarairaya yana samu da kula kamar wani jariri babu aikin office babu hayaniyar yara.

Butulci irin na dan Adam a yanzu se yake ganin Yafi samun yanda yake so a gurin Amirah musamman da yanzu ta dena masa qorafin da tambaye tambayen kudin da takeyi gashi a karan kanta ta canza sosai komai tana yi yanda yake so.

Suna zauna ana gobe ze tafi tana bare masa Ayaba yana ci ya kalleta yace “kina son zuwa Lagos?”

Sam Amirah bata kawo da ita yake ba dan a bazata maganar tazo mata har seda ya sake maimaitawa kafin tace “Meze hana mana Yaya ai kowacce mace zata so ta zauna kusada mijinta daman, wani gidan zaka samar min kenan”ta fada tana danne zumudin ta, lallai ta yarda kissa tafi Asiri tunda gashi yanzu hankali kwance tana samun abubuwan da suka wahala suka kashe kudinsu a banza akansu.

“Aa ina ganin zaku ringa karba karba ne dan baze yuwu na ajiye ku gaba daya acan ba”.

“Toh Anty fa ya zatayi da aikinta” ta fada tana gyara zama a ranta tana Addu’ar Allah yasa matsala suka samu daman ta lura tunda yazo bata ga sunyi waya ba.

Seda Bashir yasha ruwa kafin yace “Ina ganin zata ajiye aikin ne kawai idan yaso ta cigaba da kasuwancinta kema ya kamata ki samu wani abinyi zaman haka ya isa”.

Tamkar Amirah ta taka rawa haka taji amma ta dake, cikin kisisina tace “Toh yaran kuma fa su acan za’a barsu ko suma nan zasu dawo?”

“No su zasu zauna can saboda School”

“Amma Yaya indai makaranta ce anan ma fa akwai ko wacce iri kake so, ni ba wannan ba ma abinda yafi damuna Tarbiyyar su kasan fa yaran da suka tashi a Kudun nan duk zaka gansu se a hankali ko a gida ana musu tarbiyya tunda kullum suna fita su cakudu da yara kala kala se kaga anayi tana warwarewa. Ni da zakaji shawarata ka dawo dasu nan ga makarantu nan na kudi masu kyau a saka su”.

Shiru Bashir yayi yana tunani, baza’a hadama karantun boko nacan da na nan ba amma maganar tarbiyya tabbas tayi gaskiya abinda yasa ya hana Amna yin Jamb wannan shekarar kenan yace ta bari se next year saboda kafin nan ta dan qara girma da wayo yana tsoron turata Jami’a cikin Yayan Arnan nan.

Su kansu su Aliyun yasan badan Ma’un ma Jajirtacciya bace irin yaran da suke cakude dasu a makaranta da sun debi dabi’un da ba nasu ba.

“Haka ne kuma, shikenan zanyi magana da Ma’un se muga yanda za’ayi”.


Litinin ya koma Lagos da wannan qudurin a ransa. A daren ranar suna cin abinci bayan ya gama ya kalli Asma’u da tunda suka zauna ta kasa cin komai yace “Inason magana dake idan kun gama” ya wuce dakin sa.

ASMA’U

Yana tashi nima nabi bayansa gaba daya jikina baya mun dadi dan haka ina shiga na

Please Login or Register in order to submit comment