Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

ta tafi ta kai Ummi a cire mata ciki tsoro nake ji karta mutu ban san ina zan saka kaina”

“Zaki matsamun daga nan ko se nayi ball dake mahaukaciyar banza kawai, ta mutu mana ina ruwan wani ko ni na aike? Wallahi kika bari na miqe sena karya miki qafa idan yaso naga da yanda zaki sake fitowa nan gurin” ya fada yana qoqarin miqewa amma ciwon kan daya samu dakyar ya barshi ya sake dawo masa yanzu sanadiyyar bacin ran da zuciyar sa ta shiga.

Waiwayawa yayi inda su Aliyu suke zaune yaga babu kowa seya sauke ajiyar zuciya a hankali ya kalli Amirah data juya dakinta tana rusa ihu hannaye biyu akai. Ture abincin gabansa yayi wanda shima Aliyu ne ya hada musu dan ita gwanar se yanzu ma yaga idonta tun jiya da yamma.

Gaba daya kansa ya masa zafi, ya fahimce wannan yarinyar kwata kwata batasan me takeyi ba. Idan ma yace ze cigaba da zama a gidan qara masa ciwo zatayi se kawai ya dauki muqullin motarsa ya fice daga gidan.

Yana fitowa yayi mugun gani, Asma’u ce tsaye da wannan mutumin daya tsana sama da kowa a duniya yanzu suna magana se dariya sukeyi kamar wasu masoya.

A fusace ya nufi inda suke sedai kuma meya tuna yaci burki ya koma da baya zuciyarsa na masa zafi kamar wanda ake watsawa tafasashshen ruwa.

Motar sa ya bude ya shiga ya kifa kansa akan sitiyarin yana sauke numfashi a jere a jere, ya tabbatar idan har yaci gaba da ganin Ma’u da wani namiji zuciyarsa tana iya bugawa ya mutu lokacin sa beyi ba.

A zatonsa tunda har ya bata haquri yace su komawa auransu zata saurareshi ko dan darajar so da kuma yaran da suke tsakanin su amma se yake gani kamar ma ta goge shine ma daga babin rayuwarta.

Al’amuranta kawai take yi kamar babu wani abu me suna so daya taba shiga tsakaninsa da ita, to wai yanzu wa ze kaiwa kukansa ya samr masa mafita ne??

Bala ne ya fado masa arai, se ya janyo wayarsa ya kira lambar Balan a ransa yana lissafa tsahon lokaci rabonda suyi waya tun ranar daya gaya masa ya saki Ma’u.

Seda ya kirashi sau biyu amma ta qaraci qararta ba’a daga ba be haqura ba ya sake kira dan dai yau Sunday yasan Balan yana gida ko baya da haka yana da buqatar wanda ze tattauna dashi ko zeji sanyi a ransa.

Sake kira yayi yana ringin daya aka kashe, ya kalli wayar dan ya sake tabbatar da rejecting kiran akayi seya sake dannanwa tana shiga kuwa aka sake kashewa abin yayi bala’in bashi mamaki dan tunda yake da Bala be taba qin daga masa waya ba kai ko lokacin aiki ne balle har ya kira ya katse se yau amma dai ya kyautata masa zato qila yana wani uzuri ne a lokacin.

Motar ya kunna kawai ya hau titi yayi ta tafiya idan ya gaji da tuqin ya samu guri ya tsaya gaba daya zuciyarsa ta hargitse da tunanin Ma’u, ya kasa hasasowa kansa rayuwa babu ita.

Sati biyun nan kadai yaji jiki dauriya yakeyi dan karya nuna gazawarsa amma yaga alamar a wannan karon Ma’u ta daura aniyar kaishi qasa so takeyi se taga raunin sa.

ASMA’U
Da safe Yusuf ya kirani akan ze zo anjima ya dauki Ma’u, dakaina na tashi na hada mata kayanta da yan abubuwan da ba’a rasa ba a nake dasu duk na hada mata kafin na koma daki na kwanta amma sena kasa komawa bacci.

Tunanin makomata na shigayi a yanzu. Har yanzu na kasa yarda da cewa dagaske Bashir ya cire ni daga rayuwarsa ba kuma ya buqatar sake zaman aure dani tunda tun waccen ranar be sake tarata akan makomar auran mu ba kai ni bamu sake haduwa ba ma se jiya a gurin taron su Amnah.

Wasu hawaye ne suka zubomun na saka hannu na share, tabbas dole na yarda da gaskiya komai dacinta cewar Bashir baya sona, alfarma yayi mun ya aureni ya zauna dani saboda tarin soyayyar dana nuna masa.

Haka nan se kuma banji haushin sa ba, so ba qarya bane dan ni zan bada shaidar hakan kuma ba’a tilastawa zuciya taso abu na yarda duk hasasheb da nakeyi akansa a baya kawai dan ni ina cikin mayen sonsa ne shiyasa ban taba ganin laifinsa ba amma yanzu na gane Bashir baya sona idan ma ya soni to be kai ko kwatan irin son da nayi masa ba, qaddara da rabon haihuwa ta tsawaita zaman mu yanzu kuma da Allah ya kawo qarshen gashi ya raba mu.

Dole na haqura da Bashir na koyawa zuciyata yanda zata rayu ba tareda shi ba duk da nasan ba abu bane me sauqi dan da soyayyarsa na raini zuciyata idan har nace zan cire shi gaba daya daga raina na tabbatar daidai yake da zare duk wata walwala da jin dadi da sukayi saura a rayuwata ko da yake meya tage mun nema?

Tunda Bashir ya sake ni nayi ban kwana da farin ciki, duk wata walwala da nake nunawa a iyakan fuskata take amma qasan zuciyata Allah kadai yasan irin wutar da take ruruwa a ciki amma dole na na koyi rayuwa ba tare da shi ba.

Dole na daraja kaina na haqura dashi tunda har ya fito ya nuna mun alfarma yayi mun daya zauna dani tsahon lokaci yanzu daya samu zabin ransa ya gwammace rabuwa da ni uwar yayansa saboda farin cikinta.

A yanzu babu lissafin aure a gabana dan na rufe, bana tunanin akwai sauran gurin da zan iya saka soyayyar wani kuma bayan Bashir a cikin zuciyata.

Zan riqe kaina na tsaya da kafata na nemi na kaina na zamarwa mata irina da muka dauki soyayya da zafi madubi na kuma haska musu cewar rabuwa da Mijin da kike so ba shine qarshen rayuwa ba, sannan duk son da kake yi wa mutum idan har ya nuna baya buqatarka a rayuwarsa ka barshi koda kuwa hakan yana nufin rasa komai naka in dai zaka tsira da mutunchinka.

Ina cikin wannan tunanin bansan lokaci yaja ba seda naji wayata tana qara ina dubawa naga Yusuf ne ashe har qarfe goma da rabi na safe tayi.

Bandaki na shiga na wanko fuskata kafin na dora dogon Hijabi har qasa akan riga da wandon baccin da suke jiki na, ina shirin Fita Farida ta shigo tana cemun ga Dadyn Little yazo muka fito tare har qofar gida inda yake tsaye jikin wata shegiyar mota ya saka qananan kaya a raina na ringa mamakin yanda sam Yusuf baya tsufa, duk sanda na ganshi gani nakeyi kamar qara zama yaro yakeyi.

“A kwana a hantse se kyakykyawa, Allah yasa dai ban tashe ki daga bacci ba” ya fada fuskarsa dauke da murmushi yana kama hannun Farida, nima murmushin na mayar masa ina cewa

“Aa, ai tun sanda mukayi magana dazu ban ma koma ba ina zaune, ban ma zata da wuri zaka zo ba ai”.

“Ta matsa na mayar mata da yarta inaga gobe zasu wuce” ya fada yana bina da wani kallo da gaba daya ya saka ni diriri cewa. Sakin hannun Farida yayi yace mata taje ta hadawa Ma’u kaya tana wucewa ya matso inda nake tsaye yana cewa

“Kinga yanda kike wani kyalli kuwa daman ashe kin fi kyau babu kwalliya ban taba sani ba”

Saurin ja da baya nayi nace “Yusuff..” be bari nayi magana ba yayi saurin tareni da cewa

“Yi haquri, ni kaina idan ina tare dake kasa riqe bakina nakeyi amma dagaske kin yi kyau Ma’u, ina so naga Mace da Hijab ga wannan qamshin naki ya ilahi Allah kadai yasan yanayin da yake jefani”

Juyawa nayi, seda na kai bakij qofa nace masa
“Bari ta fito, na gode kwarai Allah ya qara zumunchi”

Se kawai ya tuntsure da dariya harda sunkuyawa yana kallona yace
“Matsoraciya, naga ma rowar gidan naki kike yi mun ko bayan nasan miskilin mijinki baya ciki. Wai ma ya akayi kika bari ya ajiye ku maqotaka da kishiyarki? Kinga idan nine ko qasa bazan hada muku ba bare unguwa daya saboda bazan yaba bari wani abu ya sosa miki rai ba indai ina da ikon hanawa”.

Cikin gida nayi shigewata ina jin yanda zuciyata take bugawa da qarfi kamar wadda tayi tsere, na rasa dalilin da yasa indai Yusuf yayi mun magana nake shiga irin wannan yanayin, yanzu da ace ina da aure muka hadu dashi haka zamu ringa dibar wannan dakon zunubin??

Seda nasha ruwa me sanyi dukda banci komai ba kafin na wuce dakin Amnah na tarar suna drama da Ma’u ta riqe akwatinta qam baza’a fita dashi ba.

Duk yanda naso na lallabata na nuna mata Dadynta ne yazo amma fafur tace itafa bazata tafi ba taga gurin zama, haka ta ringa birgima tana buge buge a qasa mamaki yasa kawai na tsaya ina kallonta ni ba abin na mammaketa ba ubanta na waje dan da ace yan biyu ke yi mun tabarar da tuni naci ubansu dan ni ba’a haka dani wannan yarinyar kuwa naga alamar an gama sangartata se a hankali kawai.

Dole na fita na gaya masa, badan naso ba ya shigo gidan, yayi lallashin duniya taqi ji qarshe a wuya ya dauketa tana kwala ihu kamar wadda aka sace ya sakata a mota yaja suka tafi muna daga mata hannu, haka muka wuni yara sukuku abu kadan ace Little kaza ni kaina nayi kewarta dan tana da shiga rai barta da yar banzar barna kamar beran turawa.

GOMBE
ADDAH
Tiryan tiryan me Napep ya kaita har qofar Asibitin data kwatanta masa saboda saurin da take ko musu batayi ba ta dakko kudin daya ambata mata ta bashi ta shiga jan Ummi da dauk ta galabaita suka shiga ciki.

Kai tsaye gurij Nurse din dake bada kati taje ta ce mata likita suka zo gani aka yanka mata kati dari biyar ta zaro ta bayar, babu mutane da yawa a gurin, mace biyu suka tarar su na uku ganin yanda Ummi take kuka ma Nurse din ta dauka ko ciwo ne dan haka ta roqar musu alfarma Gurin wadan da suka tarar ta ciki na fitowa suka shiga.

Likitan na zaune kai idan ka ganshi me hankali dai baze yarda ya dubashi ba saboda yanda yake a hargitse sam be mayi kala da likitoci ba, ba bata lokaci Addah ta zayya na masa abinda yake tafe dasu da kuma buqatarta.

Shiru likita yayi yana kallonta, Addah da taga yayi shiru ta har ziqo tana cewa
“Ko bazaka iya bane ka fada ka zuba mana ido kamar maye yaga nama, ni karka bata mun lokaci idan baka yi mu qara gaba ai likitocin kuna da yawa”.

Seda yaja numfashi kafin yace “cikin wata nawane Hajiya?”

“Wai wata hudu tace, kana ji ko karka damu da wani watannin sa ka markade mun dan banza ko nawa ne zan biyaka”

“Yawwa daman maganar ta kudi ce Hajiya tunda kinga cikin ya girma dole cireshi zeyi wahala dan haka se kun biya kudi da yawa amma tunda kince babu matsala to za’ayi aiki zaki biya dubu dari biyu da hamsin ne kudin aiki se kuma dubu hamsin na magunguna da jini da zamu siya saboda tsaro gaba daya kinga dari uku kenan” Likita ya fada yana wani murmushi da gani banza ta fadi

Dafe qirji Addah tayi ta zaro idanu waje tace “Likita dari uku fa kace cire cikin? Ina laifin in baka dubu hamsin shima saboda naji kace da wahala amma da ni dubu talatin ce kaga na ruqo ta” ta qarasa tana bude yar jakar ta ta zaro kudi, seda likita ya ha tareta kafin yace

“Bata mun lokaci daman kawai zakiyi Hajiya ba aiki kuka zo ayi muku ba. Kinsan hatsarin da yake cikin abinda kika zo yi kuwa idan fa aka samu matsala aka kamani daurin shekaru zansha a banza ki gudu abinki kinga ku tashi tunda naga wasa nema ya kawo ku na samu na duba sauran da suka zo da gaske”

Ganin da Addah tayi ga samu ga rashi yasa ta marairaice tana cewa
“Dan nan ba wasa bake ba kudin ne daka fada sunyi yawa amma yanzu shikenan, kayi mana ragi naji abinda zan bayar In sha Allahu baze gagara ba”

“Ki bada dubu dari biyu shine qarshen magana idan beyi miki ba ga hanya nan” ya fada yana hade rai, Addah tayi shiru, a jakarta gaba daya dubu hamsin ne ribar kasuwarsu da Alhaji ya bata jiya, tama tabasu basufi Arba’in ba yanzu ina zata kwakwulo dubu dari da sittin ta hada dan bazata taba bari wannan damar ta wuce ta ba.

Ajiyar zuciya tayi ta kalli likita tace
“Shikenan na yarda, yanzu ga dubu Arba’in zan baka idan yaso ta zauna zanje gida na karbo ragowar sena kawo maka”

“Aa ai ba anan za’ayi aikin ba Hajiya, inada guri daban da nakeyi kuma se da daddare zaku zo zan baki lambar waya da Adireshin gurin se ku same ni acan” Likita ya fada nan da nan Ummi ta qara wa kukan da takeyi qasa qasa qara, mayar da hankalin sa kanta yayi yana cewa

“Ki rarrasheta Hajiya ta dena kukan nan dan idan jininta ya hau za’a iya samun matsala a gurin aikin. Yanzu zan rubuta muku magani ku siya a waje daya zata shanye shi yanzu dayan kuma idan kunje gida kamar saura awa hudu ku taho yin aikin ta saka kwaya daya a qasan harshen ta zasu nuna muku ko wanne da yanda zaku yi dashi din”.

Godiya sosai Addah ta ringa zuba masa kamar wanda ya bata kyauta, ta kawo dubu talatin da biyar ta bashi biyar din zata siyi maganin sannan suyi kudin mota.

Tana fita kuwa a dan gurin siyar da maganin Asibitin nasa suka tsaya ta siya a take ta saka Ummi seda tasha na shan suka kama hanyar gida tana ta lissafin inda zata samo kudi.

Amirah ce ta fado mata a rai, daman shegiyar yarinyar tunda ta tafi bata tuna da ita ba balle ko biyar bata aiko mata da ita nan da nan ta kunna wayarta ta shiga kiran Amiran.

AMIRAH
Tana zaune a daki tana kuka, san baqaqen maganganun da Bashir ya gaya mata basu dameta ba ita yanzu ta yanda zata samu Addah ta hanata abinda tayi niyya take, tana tsakanda aikin kukan kiran ya shiga.

Da sauri ta faga wayar tana cewa
“Addah kina ina ne tun safe nake neman wayar ku bana samu ke da Ummi?”

“To uwata, an baki ajiyata ne da kike tambayar ina naje ko yaya ina ruwanki? Ni yanzu kirani nayi ki tura mun kudi zan samu POS na tsaya yanzu na basu lambarki ki sako kudin na cire”

“Addah me zakiyi da kudi? Ina Ummi? Kun koma gida ne Baba ya kirani dazu yana cewa...”
“Wai dan uwar ubanki Amirah zakiyi abinda nace ne ko tambayoyi zaki tsaya yimun kamar alqaliya?

Baba ya kira yace miki ubanki ina ruwanada wani Baba babo mata ni wutar gaba na ta isheni yanzu, na samu wanda ze cirewa yar uwarki abin kunyar data kwaso mana kudin nake hadawa yanzu anjima zamu koma ayi aiki” Addah ta katse Amirah.

Se Amirah ta zaro ido kamar tana gabanta tace
“Addah mutuwa akeyi wallahi kin manta Harira lokacin tayita zubar da jini har seda ta mutu dan Allah Addah karki sa na rasa Ummi kinga ita kadai ce yar uwata.

Ki qyaleta ta haihu wallahi ko ni zan dauki abinda zata haifa na riqe nasan Yaya baze hana ba”

“Idan kika sake cewa wani abu se kinci ubanki Amirah, bazaku kasheni ba yanzun nan zan turo miki da akawun na fasa zuwa POS din ma zan shiga gidan Talatu kawai mu zauna a can zuwa lokacin da zamu koma idan yaso se na turo miki da ko na Dan ta ne ki saka kudin nasan in muka koma gida wannan Uban naku ba lallai ya sake barina na fita ba” tana gama fadar haka ta kashe wayarta tana aunawa Amirah Ashar shidai me Napep se leqenta yake ta mudubi Allah Allah yake ya sauke su ya samu wanda ze bawa labari.

Amirah kuwa tana jin Addah ta kashe waya ta shiga neman layin Babansu, yana dagawa kai tsaye ta gaya masa Addah na gidan Anty Talatu ta kashe wayar tana Addu’ar Allah yasa Babansu yaje kafin su Addah su koma inda tace.

Addah kuwa a gidan Anty Talatu suka yada zango, yar uwarta ce yayan mata suke yar bala’i ce ta gaske itama dan har tafi Addah rigima.

A tsakar gida suka tarar da ita tana wa wata jikarta masifa, ko sallamar Addah bata amsa ba seda taji yarinyar na gaida Addan sannan ta waiwaya inda suke tana huci.

“Aa Fattu kune a tafe? Ku shigo mana ita kuma wannan me aka mata ta dora hannu aka tana kuka? Nifa bana son fitina shiyasa kikaga bana qaunar baqar yar nan taki saboda mugun halinta gara Amirah tafi mun ita sau dubu”

Cikin dakinta suka shiga tana gaba suna binta a baya. Seda ta kawo musu ruwa me sanyi da Fura, ta futa ta bawa jikar tata kudi tace taje qaro taliya leda daya dan gama miyar ta kenan sun maida ruwan taliyar yarinyar ta juye tayi wanka dalilin masifar tata kenan.

“Daga ina haka Fattu da uwar ranar nan fatse fatse keda bakya gajiya da yawo” Talatu ta fada bayan data zauna.

Se Addah ta janye tagumin data buga tace “ki bari kawai Talatu wannan yarinyar ce ta kwaso mun tashin hankali” nan ta zayya na mata abinda yake faruwa.

Anty Takatu ta hau salallami tana tafa hannu tace “yanzu Ummin? Ke da nakeyiwa kallon ta kirki kai yaran yanzu se abarku abinda se dai muji daga nesa shine kika kawo mana a cikin zuri’ar mu Allah ya wadaranki dai Ummi”

Nan suka hadu suna ta nanata zancen, seda ta dafa musu taliyar suka ci kafin Anty Talatu ta kalli Addah tace

“Ni Fattu maganar zubar da cikin nan ki barta kina gani dai ance mutuwa akeyi wallahi, yanzu abinda duk ya kamata ayi shine tunda tasan uban ciki a nemo shi a taru a rufawa juna asiri ko yaya ne ayi musu aure shikenan”

Hayayyaqo mata Addah tayi tana cewa
“Ban gane abar ciki ba in barta ta haihu kenan a ringa nunani a gari ace nayi jika shege to bazata sabu ba wallahi, kuma zancen aure da kije badai da wannan matsiyacin ba sedai idan mutuwa nayi”

“Ai kuwa idan baki mutu na zakiyi ta goya shegu tunda ke zuciyarki irin ta kafiran farko ce. Yanzu tashi zakiyi mu zagaya nan baya gidan me sittin tara a kwantar da cikin daga nan a nemo yaro idan sukayi aure wata kadan se a tayar dashi dukma uban da za’a fada dai daga baya ne tunda sun rigada sun yi aure”.

Shiru Addah tayi qasan zuciyarta ta yarda da shawarar Anty Talatu, miqewa sukayi Anty Talatu tace Ummi ta shiga ciki ta hau gado ta huta kafin su dawo suna zuwa qofar gida sukaci karo da yan sanda a tsatstsaye.

“Lallai Asabe, ba nace ta bani sati daya zan biyata kudin ta ba shine zata hadani da hukuma ai kuwa wallahi tayi ta kudinta muje duk uwar da za’ayi ayi amma bazan biyata ba kuwa” Anty Talatu ta fada dan a zatonta wata mata da rigimar Adashi ta hada su tace zata dakko mata yan sanda ce ta turo su.

Fitowar a Alhaji Murtala daga mota ce ta dakar dasu Addah ta shiga zare ido tana komawa bayan Anty Talatu.

“Gata nan yallabai” ya fada yana nuna musu Addah nan da nan yan sanda mata biyu sukayi kanta se ta sake riqe Talatu tana cewa

“Me kuma nayi Alhaji? Wane munafunchin aka qullamun da zaka dakko mun yan sanda saboda ka tozarta ni”

“Ai kin rigada kij gama tozarta kanki Fattu, ina Yata take? Se na tabbatar da lafiyar ta idan wani abu ya sameta daga nan kotu zamu wuce dan se nayi shari’a dake Fattu” ya fada cikin tsananin dacin rai.

Anty Talatu ce ta tare yan sandan da suke neman jan Addah tana cewa
“Ummi tana ciki Alhaji lafiyarta qalau, bari na kirawo maka ita ka ganta wannan kuma ai abu ne na cikin gida be kamata ace ka saka hukuma a ciki ba”

Daga bakin soron gidan ta tinga kwalawa Ummin kira, Ummi da har bacci yadan fara fizgarta ta fito jin muryar Talatun tana fita tayi arba da Baban su seta fada jikinsa ta fashe da kuka tana cewa

“Dan Allah Baba kar ka bari ta kaini a cire mun mutuwa ake yi ni kuma bana son na mutu”.

Riqeta yayi sosai a jikinsa zuciyarsa na tafa sa, tausayinta ya cika shi ya tabbatar duk abinda ya sameta qaddara ce da kuma halin Fattu ya janyo.

Cikin bacin rai ya kallo yan sandan yace “ku rabu da ita tunda naga Yata kuje kawai zan zo station din anjima na gode”

Sukayi masa sallama suna harar Addah sukaja mota dan sun so sun samu damar moreta.

A motar sa ya saka Ummi ya zagaya ze shiga Addah ta biyo shi ba ko dar tana cewa
“Bari nazo mu tafi Alhaji, Talatu se munyi waya ko zan kiraki idan naje gida”.

“Idan kinje wane gidan? Da alama baki ji saqona ba kenan” Alhaji Murtala ya fada yana dakatawa daga shiga motar da zeyi, Addah ko qoqarin bude mota take tana cewa

“Saqon me kuma wa ka bawa ya bani? Ni ba’a ce mun komai ba”.

“To bari na gaya miki yanzu da kaina, na yanke igiyoyin aurena biyu da suke kanki, ma’ana na sake ki Fattu saki biyu”

“Alhaji ka sake ni fa kace kuma har saki biyu? Uku fa kenan ko ka manta akwai daya daman?” Addah ta fada cikin ihu tana ja da baya hannunta aka, seda ya shiga motar ya danna lock kafin yace mata

“Ina sane Fattu na gaji da halinki na dade ina Addu’ar Allah ya yakice mun ke se yanzu ya karbi Addu’ata, zan ma aiko miki dashi a rubu ce saboda shaida” yana gama fada yaja motar sa Addah kuwa kamar sabon kamu ta bishi da gudu tana ihun ta shiga uku ta lalace.


*SODA COMMUNICATION📱💻📱
*CHEAPEST & RELIABLE DATA SERVICES*💃🏽💃🏽 with the validity of 30days at affordable price we are available 24/7 08137145294

*MTN DATA*
1GB@280✅
2GB@550✅
3GB@850✅
4GB@1150✅
5GB@ *1400* ✅
10GB@2800✅

*AIRTEL DATA*
1gb@320✅
2gb@640✅
3gb@950✅
5gb@1600✅

*Pay through👇🏽👇🏽*UNION BANK*
*0139814463
Khadija shehu soda*🥰🥰🥰we are always there at ur service. WhatsApp/Call📞08137145294🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 51

Seda motar Alhaji Murtala ta bacewa Addah kafin ta tsaya tana haki ta dora hannaye biyu akai tana rusa ihun ta shiga uku ta lalace

“Ni Murtala ze saka? Shekara Hamsin da aure ace zanyi zawarci gidan ubanwa yake so naje yanzu wallahi be isa ba, ban saku ba dole na koma” Addah ta ringa sambatu tana rusa kuka.

Anty Talatu ce ta ruqota suka shige gida tana cewa
“Se kace kanki aka fara saki ji yanda kika bishi da gudu kamar wata karya. To Fattu ai ya miki da kyau ma daya tsaya a iya sakin dan ni na dade ina hasaso miki haka a irin tashin hankalin da kika dade kina kwasowa bawan Allahn nan. Ni da ban kaini Jaye jaye bama aka sake ni bare ke? Kawai muje ki share guri ga daki nan na kusa da nawa ki shiga ki zauna Allah ya kiyaye na gaba”.

Kuka sosai Addah ta ringa sharba se kace qaramar yarinya. Anty Talatu tun tana bata haquri har abin ya bata haushi ta tashi qarshe ma ta fice gaba daya ta bar mata gidan ta tafi karbo zubin Adashen mutane dan ita uwar Adashe ce.

Se bayan Magriba ta dawo gidan, lokacin Addah tayi kukan ta dangana, dukda ba haqura tayi ba ta bari ne zuwa gobe da safe zata koma gidan ta idan Alhaji yaqi kuma zata bi Aminansa da yan uwa a saka baki dan bazata iya barin gidan nan ba.

Toh ta kama ina dan zaman ta da Talatu tasan ma ba me yuwuwa bane kawai dai zata zauna na dan lokaci kafin komai ya daidaita.

Tana kan sallaya bayan ta idar da sallar Isha Talatu ta shigo tana ta masifa akan matan sunqi bada zubi. A qofar daki ta zaune kan taburma, Addah ta leqo kamar wata me takaba murya duk ta dashe saboda kuka tace

“Talatu se yanzu? Tun dazu nake zuba ido na jiki shiru

Please Login or Register in order to submit comment