Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register



Da Asuba da muka hadu kamar kububuwa ya wuceni ya shiga kitchen, ya gama diri dirinsa ya fito daman nasan ba abinda ze iya tsinanawa mutumin da inaga ruwan zafi kadai yasan yanda ake dafawa. Amna ya kwalawa kira ta fito daga dakinsu yace maza ta soya masa kwai.

Ina kallonsa ya shiga dakin ya fito yana doka uban tsaki ya kalli inda nake ya sake komawa seda ya shiga sau biyu ana ukun ne yace “Dan Allah Ma’u kizo ki hadamun kaya su Musa har sun kusa qarasowa”

“Au wai baka hada kayan ba me kake jira toh” na fada ina tashi zaune akan kujera.

“Kin sani ban iya ba ke kike hadamun, please Ma’u”.
“Badan halinka ba muje” na fada ina miqewa. Kusan rabin wardrobe din ya watso su qasa, cikeda takaici na shiga hada masa kayan a qaramar akwati na gama ina zugewa ya shigo da kofin shayi a hannunsa ya ajiye akan mudubi yana cewa “har kin gama”

Ban amsa ba na shiga kwashe na qasan ina mayarwa, horn da muka jiyo daga waje yasa na dakata na daukar masa Laptop bag dinsa shi kuma yaja akwatin muka fito, Jafar na tsaye a kofar dakin su ya gaishe shi yace “Abbi a kawo fa”

“Za’a kawo Sheik ina sauran yan uwanka”

“Sun koma bacci Abbi”
“Ok idan sun tashi ka gaya musu na tafi Delta zamuyi waya idan na sauka” ya fada yana tafiya.

“Allah ya tsare Abbi” Amna da Jafar suka fada. Daga bakin qofa na tsaya ya miqawa Driver Akwatin ya karbi jakar hannuna bayan na masa Adawo lafiya naja kofar na koma ciki. Seda na kwashe kayan da ya zubar tsaf ina mita “Abinda ko Su Muhammmad baza suyi mun ba shi yake yi, da yake buqatar kansa ce ai ya iya roqa a masa mtsw” naja tsaki.
A dakin na kwanta na qarasa baccina.

GOMBE

Acan Gombe kuwa ranar talatar da safe Bashir sukayi waya da Naziru ya gaya masa yaje Asibiti ya karbi Iman daga nan ya wuce da ita gurin Dada kafin ya gama yanke abinda za’ayi.

“Ni se nake ganin yaya da kayi haquri, be kamata ace ka raba Uwa da yarta ba idan kayi haka kamar ai bakayiwa Amirah da ita kanta Babyn Adalci ba. A yanayinta tana buqatar dumin uwa da kuma Nono ko dan ingancin lafiyarta” Naziru ya fada bayan da ya gama jin umarnin yayan nasa.

Shiru Bashir yayi, Tabbas gaskiya Nazirun ya fada amma toh amma meye amfani mayar mata da ita ma yanzu bayan ta riga ta yaye ta kusan sati bata sha Nonon ba se madara ai dakyar ma idan zata karba yasan, kuma fa shi ya gama yanke hukuncin sa ta hakane kadai ze hukunta Amirah taji a jikinta yanda gobe bazata sake gwada yin abinda tayi ba.

“Kaje kawai ayi yanda nace, na rigada munyi magana da Dadan, zuwa Next week idan na samu dama zanzo nan Lagos zan dawo da gurin Ma’u”

“Anty kuma? Ita tace zata riqeta?” Naziru ya tambaya cikin mamaki. Se Bashir din yace

“No, bata rigada ta amsa ba amma ai gida nane ina da ikon sawa da hanawa ko”

“Hakane” Naziru ya fada sukayi sallama, a ransa yana mamakin wannan zallar rashin Adalci irin na dan uwan nasa. Tayaya zaka taba jaririya da uwarta ka dauka ka kaiwa wata wadda ita kanta tana da buqatar me taimaka mata. Ÿaÿa Bakwai nefa a gaban ta take kula dasu ga shi sannan kullum seta fita aiki ai wallahi ko ita kanta yanzu kamata yayi yace ta dakata da haihuwa ta ji da abinda yake a gabanta balle har ya dauki raino ana zaune lafiya ya kai mata.

Daman lokacin daga wanka ya fito dan haka ya zura rigarsa ya cewa Dada bari yaje Asibitin ya karbo yarinyar “Amma fa Dada kiyi masa magana idan ba haka ba wallahi ze janyo abinda za’a zo ana samun sabani daga qarshe kuma ace za’a ga laifin Anty Ma’u” ya fada yana tsaye daga bakin qofa.

“Ka rabu dashi Naziru, gurin uwarta za’a maida ta, shi a ina ma ya taba ganin anyi haka? Idan so yake ya kaita cikin yan uwanta se ya bari idan Allah ya rayata ta isa sakawa a makaranta a sannan yana da hujjar da ze iya dauketa ya maida ita can ko dan ta samu ilimi irin na sauran amma ba yanzu ba. Ni wallahi na rasa me yake damun Bashir, mutum tamkar wanda yake da wani motsi a kansa”.

“Ba wani motsi wallahi Dada tsabar samun gurine tunda yaga duk sharar daya debo kina goya masa baya shiyasa”.

“Yanzu dai jeka, idan ka dawo se muje tare can gidan nasa, dukda ya kamata na kirashi ma yabar yarinyar nan ta koma gida tayi jego ko ta dawo nan dole se an taimaka mata kafin ta saba ai” Dada ta fada, Naziru yayi mata sallama ya tafi Asibiti.

Yana zuwa ya tarar da wannan tashin hankalin, bashida karfin guiwar kiran Bashir dan haka likitan ne ya kirashi shi kuma ya kirawo Dada ya gaya mata.

Bayan an gama cike ciken takardu ya saka hannu aka bashi gawar, be iya tafiya ba seda Ya kira Sa’ad Yayansa da yake bi yazo suka tafi tare suna kaita gida Dada tace suje su dakko Amiran sannan ta kira Ummi a waya tace suzo ita da Addah yanzu.

Fadar tashin hankalin da Amirah ta shiga bata baki ne dan sumanta uku ta ringa kururuwa tana ihu kamar wadda ta hau bori, se da Goggo Ladi qanwar Alhajin su Bashir tayi mata tatas sannan aka samu ta lafa da ihun amma fa bata dena kukan ba.

Addah kanta tasha kuka fadi take daman yan baqin ciki basu so aka haifeta ba gashi yanzu anyi manaqisar da seda aka rabata da duniya su dai Allah ya isan su bazasu yafe ba.

Babu wanda ya ko bi ta kanta, da dare yayi zata tafi da Amirah Alhajin su Bashir ya hana yace ta barta acan dan yasan idan sun tafi ma a maimakon ta taishe ta Allah kadai yasan abinda zata je ta kitsa mata kuma.

A wayar Ummi Bashir sukayi magana da Amirah, yanda ta ringa ya bala’in daga masa hankali gaba daya tausayinta ya rufe shi. Allah ya sani yana son yara kuma wannan yarinyar haka kawai yaji duk cikin Ÿaÿan sa tafi shiga ransa kamar sanda aka haifi Farida sedai har nata ya zarce Faridan.

Badan Assignment din da yake gabansa ba da a ranar yaso yaje amma ya mata Alqawari daya gama zezo Gombe, ya ringa rarrashinta yana gaya mata kalamai masu kwantar da hankali tareda Alqawarin kwanan nan zasu samu wata qilan ma yan biyu, da haka ya samu tayi shiru har tayi bacci sannan ya kashe wayar.

Kunsan December watan hidima ne 😁😁 weddings everywhere

To all the December brides Allah bada zaman lafiya 🙌🏼🙌🏼🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 26

Har Bashir ya gama kwanakin sa a Delta ba wani magana mukeyi ba, a ranar da ya tafi dai bayan sun sauka ya kirani haka washe gari da safe kafin su fita field munyi waya bayan nan kuwa har suka kwana hudu be sake kirana ba nima kuma ban kirashi ba.

A tunani na ko aiki ne yayi masa yawa, dan daman yawan ci idan yana field bamu cika yin waya ba shine dai idan ya samu lokaci ze kira to wannan karon ma na dauka a hakan ne.

Ranar Lahadin da suka kwana hudu da daddare muna zaune wayar Aliyu dake kusa da ni tayi qara,
"Aliyu wato har ka rarrabawa Jama'a Number ka ni bani da ita koh, waye yake kiranka da daren nan?" Na daga wayar ina dubawa.

"Super hero" naga an saka, na gane Number Bashir ce sena miqa masa ina cewa "uhm uhm su Bat Man ne ko Spider man naga an sa super hero".

Gaba daya suka saka dariya, Aliyu ya daga wayar suka gaisa, ban san meya gaya masa ba nadai ji yace "toh ga Mamin ma ko na bata ka gaya mata?"
"Tam Abbi bye" ya sake fada kafin ya kashe wayar yana kallona.

"Mami, Abbi yace Mr Kunle ze zo yanzu ya kawo saqo, akwai kudi a bedside drawer dinsa ki bashi 20k".

Kamar wata sokuwa haka nake kallon Aliyun harya gama. Abubuwan mamakin da yawa, ashe Bashir yana da lokacin kiran waya nice baze kira ba.

Sannan yaushe muka fara haka da ze fadi abu ni baze kirani da kansa ya gaya mun ba sedai ya kira Aliyu?

Wayata dake kan centre table na janyo na danna power button dan na tabbatar ko a kashe take be sameni ba ya kira Aliyun naga a kunne take. Ga network dina full to meye dalili?

"Hmmmm" na fada a fili kawai na ci gaba da kallon da muke, ba'a jima ba kuwa aka danna Door Bell Jafar yaje ya bude se gashi da Babban Package da alama PS din da aka ishe ni da naci kamar nina ce zan siya aka kawo.

"Mami yana jiran saqon wai" ya fada bayan ya zauna ya fara budewa Abdallah na taya shi.
Se na waiwaya na kalli Aliyu nace

"Kaje ka dakko masa baya gaya maka inda suke ba?"

Seda yai dan jim kafin ya miqe ya shiga dakin nasa, be jima ba ya fito da kudin a hannunsa ya miqo mun yana cewa "Gashi na dakko".

A hasale nace masa "zaka tashin mun akai ne ko yaya, ina kai ya gayawa saqon kuma kazo kana nunamun me zanyi dasu".

Zugui zugui ya fice ya kaiwa Kunle kudin ya dawo. Ina kallon yanda yake satar kallona ganin na dora qafa daya kan daya ina girgizawa duk sanda suka ga ina haka to sun san zuciyata a kusa take, ina iya make su idan suka matsamun.

Hayaniyar da Jafar da Aliyu suka fara suna qoqarin jona PS din da Tv tasa na daka mutsu tsawa ina cewa "ku bace mun a nan, ba gobe Monday ba shine a wannan lokacin kuke shirin dasa wata Game, ku tattara ko yanzu na fasata wallahi".

Kama kansu sukayi sum sum gaba daya suka watse, ina zaune ina sakin tsaki, son na tabbatar da zargina sena janyo wayata na dokawa Bashir kira na kuwa taki sa'a akace call waiting.

A da, indai na kira Bashir ko da wa yake waya se ya dakata ya amsa kirana, ba qaramar waya me muhimmanci bace zan kirashi ya kasa katseta amma yau har ta gama ringing ta yanke be daga ba.
Na sake kira nan ma be daga ba, seda na jera masa kira hudu amma bawan Allahn nan ko a jikinsa kuma har sannan call waiting.

Agogo na kalla, tara harda rabi tayi, nasan babu wani official call da ze ce yana yi yanzu, kuma na tabbata bada Dada yake waya ba dan sanin da na mata da Tayi Isha take kwanciya to da uwar wa yake waya da baze amsa tawa ba?

"Amirah" zuciya ta ta raya mun, se ta yuwu kuwa din. A jiye wayar nayi ina jiran ya biyo baya amma har goma da rabi shiru ba kiran Bashir babu labarinsa, sena miqe jiki a sanyaye na shiga dakina.

Tunani na shigayi ko na masa wani abu a wayar da mukayi qarshe, iya hasashena ban gano komai ba dan lafiya mukayi hira kamar ma be tafi muna fushi da juna ba. Haka na ringa juyi a gado ina tunane tunane to wane sabon shafin ne kuma ze bude mun, koma dai menene Allah ya bamu wuce wa lafiya da haka bacci yayi awon gaba dani.

Daga mamaki mani abun na Bashir tsoro ya koma bani, dan fa washe gari be biyo kirana ba, da yake na koma aiki nima ranar na shiga busy ban wani nutsu ba se da daddare na duba wayar na tabbatar da be kira ba kuma qarin abun mamaki da magriba ma seda ya kira Aliyu ya bawa dukka yaran sukayi waya harda tambayar me ze taho musu dashi.

Nidai ido na kawo na zubawa sarautar Allah, duk tsiya dai ze dawo gidan se inji me ya faru kuma.

Na zata ranar Larabar ze dawo tunda itace cikar sati da tafiyar su daman kwana biyar yace ko sati to gashi har yau Talata dan haka na saddaqar se gobe ze dawo.

Bayan na tashi aiki  na biya na dakko yara, dukda magriba ta kawo kai haka na biya wata yar kasuwa da ake siyar da Dangin su Kaji masu rai, Bashir yana son Danderun Zabi dan haka na siyi manya guda biyu aka yanka su aka fige kamun muka kamo hanyar gida Ba mu muka isa ba se ana shirin shiga sallar Isha saboda holdup.

Jakata kawai na ajiye muka shiga Kitchen tareda Amna, seda na wanke Zabon tsaf yanda nake so kafin na saka a kwando su tsane na bar Amna ta hada kayan hadi dan tana fashin sallah ni kuma na tafi nayi magriba da Isha .

Sanda na dawo ta hada komai na marinate dan tasan yanda nake so, seda na saka wuqa na huda jikinsu sosai yanda kayan hadin zasu shiga na shafe lungu da saqo na ko ina ya juqu sannan na nade a Foil paper ya nadu da kyau, Already ta kunna oven yayi zafi dan haka na dora su akan Baking try da aka zuba ruwa na kunna wuta sama da qasa na rufe.

Ban san sanda ze dawo ba da safe ne koda daddare dan haka A daren nan seda na hada masa zobo irin wanda yake so na saka a fridge, na gyara zogale na yanka Albasar da zanyi masa Dambun shinkafa nice harda dakan gyada kamar aljana na turara tsakin shinkar  na saka komai a fridge yanda gobe kawai sedai na hada.

Na gaji tiqis, haka na koma palour na kwanta ina yi ina duba naman dana saka ina qara ruwan dan karya qone nice har qarfe biyu, jin bacci na neman fin qarfina na kashe kawai tunda nasan zuwa yanzu yafi rabin dahuwa in Allah ya kaimu gobe na ci gaba.

Dakyar na iya tashi sallar asuba dan ji nayi kamar ma ina kwanciya aka tashe ni. Haka ina yin sallah na koma kan aikin, ga shirin yan makaranta da ni kaina. Qarfe bakwai muna breakfast Bashir ya kirani.

Rai a sake na amsa wayar duk da qasan zuciyata akwai haushin qin kirana da yayi amma na daure dan babu qarya nayi kewarsa sosai, rabon da mu kebe tun muna Gombe.

A dake ya amsa gaisuwar da nayi masa, mukayi shiru gaba daya kafin ya nisa yace
"Yau zamu dawo In sha Allah zuwa dare zan shigo gida".

"Masha Allah, Allah ya dawo daku lafiya nayi kewarka da yawa". Na fada cikin shauqin da na kasa dakatar da kaina.

Wani miskilin murmushi yayi kafin yace "Na sani ai"
"Oh ka ma sani kenan" na fada adan shagwabe.
"Zan kiraki anjima" ya fada, ko kafin na bashi amsa ya katsewa wayar, sena ajiye na ci gaba da kurbar Tea na rai fes.

Seda nayi yar murya sannan aka bar yaran suka shiga makaranta saboda mun makara, School Bus nace su biyo idan an tashi kawai dan inaga idan Bashir ya dawo kawai zan masa magana su ringa bin school bus din kamar zefi sauqi.

A office ma ban wani maida hankali ba, qarfe biyu na dauki excuse na tafi gida. Seda na gyare gidan qal na chanza Bedsheet din dakin Bashir na saka turaren wuta.

Kayan harkar dana hada na shanye kafin na dakko wani hadin dilka da Anty ta bani na na mutstsike jikina tsaf na turara sannan na dauraye jikina na koma Kitchen.

Na riga naci qarfin aikin tun jiya, Danderun na duba yayi luguf dan tun shigowata na ci gaba da bashi wuta gaba daya gidan ya dume da qamshinsa ga na turaren da nayi se suka hadu suka bada wani kalar qamshin yan gayu, nan da nan na hada Dambuna sannan na dora tuwon semo da miyar Danyar kubewa taji naman rago dan Bashir yana sonsa.

Kafin Magriba munyi wanka nida yaran munyi kwalliya yanda kasan ranar sallah. Wata Atamfa na saka Batik Maroon da akayiwa dinkin A line me dogon hannu babu ado a jiki se aikin stones da aka mata se walwali takeyi na kashe daurina na baza qamshi duk inda na juya yara se sun ce "kai Mami kinyi kyau wallahi" ni kuwa se jin dadi nakeyi.

Ina tahiyar qarshe a sallah naji waya ta tana qara kafin nayi sallama ta katse. Bayan na idar na janyota dan nasan Bashir ne, ilai kuwa wani kiran nasa ya sake shigowa.

"Ranka ya dade Mijin Ma'u, ka iso nazo na bude maka qofa ne" na fada da yar dariya.
Dariyar shima yayi cikin jin dadin sunan dana kira shi yace

"Mun dawo amma ban qara so gida ba"
"Masha Allah, sannunku da dawowa, muna jiranka nida yara mun shirya maka babbar tarba".

"Dagaske, me kika tanadar mun?" Ya tambaye ni, seda na gyara zama kafin nace
"Duk abinda kake so" na bashi Amsa.

"Ke kadai nake So Ma'una" yayi maganar cikin wani salo da yayi mun dirar mikiya dan har seda naji kamar numfashina ya tsaya na dan lokaci, jikina ya karbi saqon sa dagaske, se na yi qasa da murya kamar me gudun wani yaji abinda zan fada nace

"Na tana dar maka kaina, kai kadai nake jira Farin cikin Ma'u". Na fada sannan muka kashe waya. Cike da zumudi na tashi na mayar da dankali na na sake gyara fuskata sosai na qara turare. Palour na dawo muka zauna motsi kadan mu kalli qofa kowa ya qagara Abbi ya dawo har dai aka kira Isha Malam Bashir shiru.

Tafi tafi fa har qarfe tara babu Bashir gashi yara har sun fara qorafin yunwa suke ji, se na tashi a sanyaye na dibar musu abincin bayan sun shimfida Table mat a qasa dan kar a bata gurin suka zauna suka ci.

Muna zaune goma ta buga zuwa sannan hankalina ya fara tashi anya lafiya kuwa gashi na kira wayar sa har sau biyu bata shiga daga qarshe ma aka ce a kashe take.

Muna tsaye tsuru nida Amna da Aliyu dan ragowar sun kwanta, Aliyu ya kalle ni yace "Mami ko naje na tambayi Baba Audu naga yana gida".

Se a sannan ma tunanin yazo mun da mu gayawa Baban, na dago kai da niyyar bashi amsa wayata dake hannuna tayi qara alamar shigowar message. Number Bashir ce, sena bude da sauri na fara karantawa

"I'm sorry Ma'una, na wuce Gombe" Abinda ya rubuta kenan.

Wani duhu ne ya gifta idona na saki wayar a qasa nayi baya kamar zan fadi Amna da Aliyu suka riqe ni,

"Mami meya faru? Wani abu ya samu Abbin?" Aliyu ya shiga tambayata a rikice, dakyar na iya cewa

"Dauko mun Inhaler" se ya sake ni ya tafi da gudu dakina. Wayata Amna ta dauka ta bude, ina kallon ta bayan ta karanta message din ta goge daidai sanda Aliyu ya dawo yana bani Inhaler ya karbe wayar aga hannunta yana cewa

"Na gani me aka turo" se ya bude ya kalle ta yace "Ni banga komai ba, Mami wai menene?".

Seda naji numfashi na ya daidaita, Ina da Asthma kuma yawan ci baqin cikin Bashir ne yake motsamun ita dan ni da na shiga damuwa ko tashin hankali zanji numfashi shina yana sama sama.

"Ku tashi kuje ku kwanta babu komai, ashe ma basu taho ba" na fada ina qoqarin miqewa. Se Aliyu ya zuba mun ido kamar be yadda da abinda na fada ba, seda na sake maimaitawa sannan suka miqe.

Hannuna ya kama yace "Mami muje ki kwanta toh"

"Aa Aliyu sena kwashe abincin nan karsu lalace" na fada cike da qarfin hali dan na matsu subar gurin ko zan samu damar fashewa da kukan daya tokare mun maqoshi.

Qarfin hali kawai nayi muka kwashe kayan, ina shiga dakina na jingina da qofar na fashe da wani irin kuka na zallar baqin ciki da takaici, wannan wane irin wulaqanci ne, meyasa kwata kwata Bashir baya darajani?

Meyasa ze yaudareni yace yana hanya sannan ya zagaye ya tafi gurin Kishiyata? Idan ya ce mun Gombe ze wuce ai bazan hana shi ba tunda itama matarsa ce amma wannan ai zalunci ne yasa na bata lokaci na na shirya tarar sa sannan ya zagaye ya tafi gurin wata.

Haka na kwana ina kukan baqin ciki idona sunyi luhu luhu ga wani azababben ciwon kai daya kamani, sauqi daya dana samu Amna ba zataje makaranta ba saboda wani satin zasu fara WAEC ita ta shirya yaran ta basu abinci sannan tayi musu order Uber suka tafi.

Ina zaune a gaban mudubi ina shafa mai bayan na samu nayi wanka dakyar ta shigo da Try ta dora Mug din shayi da plate din dankalinda kwai. Akan Coffee table ta ajiye kafin ta zauna akan daya daga cikin kujerun.

"Mami" ta kira suna na, sena waiwayo nayi mata kallo daya na mayar da kaina.

"Mami kiyi haquri dan Allah, wallahi ba laifin Abbi bane kin san su Anty Amirah har gidan bokaye suna zuwa qilan Asiri sukayi masa" ta fada muryarta na rawa alamar kuka zatayi.

Sena juyo na kalleta ina murmushi nace

"Kinsan menene Amna?" Seta girgiza kai alamar Aa, numfashi naja kafin naci gaba da cewa

"Abbin ku be kyauta mun ba, inda ya fadamun ba yau ze dawo ba kinga da ban sha wahalar hada masa abinci ba. Kina kallo fa jiya ko baccin kirki banyi ba ina gasa masa zabo amma duk wannan wahalar ta tashi a banza kuma fa da magriba ma fa seda mukayi waya yace sun dawo yanzu ze taho gida".
Na qarasa ina share hawayen daya zubo ta gefen ido na, gaya matan da nayi se yasa naji wani sanyi sanyi a zuciyata.

"Haka ne Mami, nidai kiyi haquri ki dena damuwa daman abinda suke so kenan"

"Na haqura Amna, kije ki kwanta ki huta toh nima idan na karya bacci zanyi" na fada ina miqewa na bude wardrobe na dakko Doguwar rigar Yadi me laushi na saka. Tura abincin kawai na ringayi dan bakina sam babu dadi. Bayan na gama na sha Paracetamol na kwanta.

Dakyar ya yakice tunanin abinda Bashir yayi mun na samu bacci me nauyi ya dauke ni, gana jiya da banyi ba ga bashin na shekaran jiya.

BASHIR

Tun washe garin da ya sauka a Delta da daddare suna waya da Amirah tana ci gaba da yi masa kukan data ara ta dorawa kanta.

Cikin kukan take cewa "Kowa ya kira ni yayi mun gaisuwa dangi na kusa da na nesa amma banda Anty, ai ko ba komai tsakanina da ita ya kamata ace tayi mun gaisuwa ko su Aliyu ma ai duk ya kamata su kirani ko banza qanwarsu ce" .

"Ma'u bata kira ki ba?" Ya tambayeta da mamaki,

"Bata kirani ba mana inda ta kira ai Zan gaya maka  indai kuma ba murna take da mutuwar Iman ba". Amiran ta bashi amsa. Wannan fushin cewa bata kira Amirah ta mata gaisuwa ba shi ya hana shi kiranta har tsahon kwanakin da yayin.

Ko ranar data kirashi da Amiran suke waya, sanda kiran ya shiga harga Allah yaso ya daga dan yayi missing dinta amma daya gayawa Amirah nan da nan ta rikice ta fara masa kuka, basu kuma gama wayar ba se gurin sha biyu dan haka suna gamawa bacci ya kwashe shi.

Gaba daya yanzu shi tausayin Amirah yake ji. Koshi me Ÿaÿa Shida rasuwar yarinyar nan ta tabashi sosai bare ita me guda daya sannan ga irin wahalar da tasha shiyasa yake biye mata ko zata samu sassaucin abinda take ji.

Rabar laraban kuma da zumudin son ganin Asma'u ya taho, yasan be kyauta mata ba ya kuma bari ne se ya dawo sannan ya goge laifinsa, sanda ya kirata dagaske yana Lagos saukar su kenan amma suna ajiye waya Amirah ta kirashi tana kuka tamkar ranta ze fita.
Akan gashi har anyi sati da rasuwar Iman amma beje ya ganta ba.

"Ni daman nasan baka sona Yaya, baka qaunata farin cikin Anty da Ÿaÿan ta ne kawai matsalar ka baka damu da ni na rayu ko na mutu ba. Karinga tunawa nima matarka ce kamar ita, kuma ina da haqqi akan ka. kuma idan har ban yafe ba kasan Allah babu ruwan sa

Please Login or Register in order to submit comment