Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

suyi maganar kasuwar ya ringa gwada wata sana’ar ko babu komai ya zama mutum yana da wata madafar bayan albashi saboda gudun bacin rana akwai sanda har magana ya gaya mun wai ko fata nake masa ya rasa aiki ya ringa fushi yana jin haushi na daga nan nace bazan sake masa magana akan yin wata sana’a ba.

Abinda na lura dashi wannan a halin mazan Bauchi da Gombe yake sunbada amanna da aikin Gomnati, kadan daga ciki ne suka yarda da kasuwa, Nidai dana tashi gidan mu naga ba’a zaman banza zan ci gaba da saida saidena dan bazan dogara da se abinda miji ya dakko ya bani ba.

A wannan yanayin na haifi Jafar, wannan karon a gida na na zauna daman kuma ban saka rai da samun komai a gurin Bashir ba kodan halin da muke ciki ma da yaya ya biya kudin haya haka dai akayi suna na kuma samu Alkahiri sosai daga yan uwana.

Bayan haihuwar Jafar abubuwan da suka faru ba masu dadi bane dan sosai muka shiga matsin rayuwa, tun muna iya siyan kayan abincin wata a ajiye har seda takai mun koma awo a kullum na abinda za’a dafa kuma duk nice qarfin riqon gidan a abinda nake samu zan bashi yayi a haka har seda muka cinye jarin nawa duk ma abinda zan samu a haka yake qarewa tunda komai da shi mukeyi babu wani abu da yake shigowa Bashir daidai da ci gaban karatunsa da tallafi na yake yi seda takai har mota ta na siyar na bashi kudin akan ya kama wata sana’ar sedai wane tudu wani gangare kudin suka narke, Bala ya bawa akan ze saro masa kaya daga Lagos wai yan Fashi suka tare su suka karbe sukayi masa dukan tsiya dan seda yayi kusan wata a kwance yana jinya.

Haka muka ci gaba kullum ina hanyar zuwa gida karbar kudi seda ta kai ni da kaina na fara jin kunyar hakan na dena zuwa, aiki kuwa kullum ina tafe, ina Teaching ga wasu training centers dana ke koyarwa suma duk dan dai mu rufawa kan mu asiri seda ya zama wata rana idan mun samu abinda zamu ci da rana sedai ni dashi mu haqura da na dare yara suci nakan kwana ina kuka wani lokacin idan na tuna yanzu fa akwai wadanda tunda suka somi rayuwa cikin irin wannan qunci da matsin suka tashi ko?

Idan kaga yanda na koma sena baka tausayi yanda kasan nice Mijin ba Bashir ba dan shi yana zaune a gida zan fita aiki na dawo kuma na dafa abinda ya samu muci wannan abun yana bala’in baqanta ran yan uwana kuma yana daga dalilin daya sa duk suka zuba mun ido suga gudun ruwana ni kuwa ko a jikina, Ina son Bashir bana jin duk abinda zanyi masa na fadi kuma ko banyi dan shi ba zanyi dan yayana dan haka ban taba jin haushin kaina akan abinda nake yi ba.

Abin takaici daya lokacin qannen sa da sukayi aure Allah ya taimake su gaba daya sun samu gidan hutu dan haka yanzu gidan su basu da wata matsala ko wacce na iya qoqarin ta se kuma ya zamana sun ware Bashir domin ko gidana yanzu babu wadda take zuwa tunda bani da abinda zan basu.

Ita kanta Dadan yanzu wani gani gani takeyi mun idan munje gidan babu wannan sakin Fuskar irin nada wanda duk cikin zugar Addah ne, a cewarta baqin ciki da kyashi ne ya hana nasa a bawa Bashir kudi a gidan mu na gwammace mu zauna cikin talauchi ni da shi din saboda wai ina baqin cikin yana wahaltawa yan uwansa sama dani, a raina nace ashe sun san da yana da shi din ma su ya ringa wahaltawa bani ba dan kafin ya mun abu daya ya musu goma sannan wane baqin ciki zanyi da har zan zabi zama cikin

Daidai da Addah se in manta rabonda na sakata a ido ko su Aliyu na kai gidan ba’a minti Ashirin se a dawo mun dasu tace fita zatayi, Amirah kanta yanzu ta rage zuwa idan nace mata me yasa se tace Addah ce take hana ta rayuwa kenan se kana dashi mutane suke yi da kai a duniya.

Ana cikin haka wata rana Bashir ya shigo gida cikin tsananin murna yake nuna mun saqon gayyatar da wani wani kamfani suka aiko masa daga Lagos, a cikin ayyukan da Alhaji Qarami ya ke ta fafutukar nema masa se yanzu Allah yasa daya suka gayyace shi, a yanda yake gaya mun mutum biyu za’a dauka kuma su biyar aka gayyata Jarabawar gwajin nan da kwana uku ze tafi.

Tun daga ranar na fara Azumi ina Yiwa Bashir Addu’ar nema sa’a. Gogan kuwa se shiri yake ya binciko tsofaffin littattafan sa yana ta karatu. Ana gobe ze tafi da daddare har wurin daya yaha zaune yana fama da takaddu na kalleshi nace

“Baban Ali da ka ajiye karatun nan haka ka huta Addu’a ya kamata muyi tayi dan a irij wannan abun fa sa’a ake nema ba wai karatu ba”.

“Ma’u kenan, a irin karatun da nayi na tabbatar da duk tambayar da sukayi mun sena amsata sannan duk wata kwarewar aiki da zasu nema ina da ita, kedai kawai ki fara shiri dan har na hango mu a Lagos” ya fada yana ci gaba da bude littafinsa, se na ja numfashi na gyara kwanciyata nace
“Toh Allah ya tabbatar da Alkahiri”.

Washe gari ya hau mota se Lagos, kwanan sa biyu ya juyo bayan sunyi Jarabawar ya dawo da tabbacin kamar ma ya samu aikin dan har yana ce mun “ko mutum daya zasu dauka nasan nine, bakiga yanda su kansu masu Jarabawar suka ringa jinjina qoqari na ba”
Ni kuwa nace masa

“Kadai ce In sha Allahu, kuma muci gaba da Addu’a idan rabo ne za’a samu”.

Sati daya sakamakon ya fito amma babu sunan Bashir wasu mutum biyu daban ne dan daya ma babu shi a wadanda sukayi Jarabawar tare, ina jin abokin da yayi yana gaya masa wai dan wani Minister ne aka aiko da sunan sa dole aka cire mutum daya aka saka shi.

Haka Bashir ya ringa qunci da bacin rai akan rashin samuwar aikin, duk yanda naso na nuna masa komai na rayuwa rabo ne idan Allah be tsaga da naka ba duk wuya haka zaka haqura bazaka samu ba amma yaqi fahimta qarshe ma abin ya zamar mana rigima har yana gaya mun magana akan niyyar samar masa aiki ne kawai ba’a yi ba aka wahalar dashi idan ba haka ba duk hanyar da muke da ita ace an rasa ta inda za’a samar masa aiki me yasa su yan gidan mu mata da maza da sun gama makaranta suke samun aiki ga Abubakar tuni ya samu chanjin aiki daga inda yake a Kano zuwa NNPC.

Ganin fa yana neman ya raina mun hankali yasa nima na horance masa, nayi masa tatas na gaya masa ai ba haqqi na bane na samar masa aiki dan haka idan ze tashi ya nema tun wuri ya nema kuma na cire hannuna daga duk abinda ya shafi sabgarsa, idan har ya aureni ne saboda ya samu kudi toh ya sawwaqe mun kawai.

Wannan abun ya bala’in dagawa Bashir hankali se gashi har yana bina yana bani haquri akan sharrin shaidan ne shi ba abinda yake nufi kenan ba, haka muka ci gaba da jalan ta rayuwa yau fari gobe baqi a haka na kammala karatuna na fara hidimar qasa.

Ranar wata Talata da bazan manta da ita ba, muna zaune da yamma nida Jafar dan a lokacin Aliyu ya fara zuwa Islamiyyar da take cikin layin mu. Shekarun sa uku a sannan tuni bakinsa ya bude sosai dan haka nake hadashi da Amirah suna tafiya kuma sosai yake karatun dan in aka dawo ya ringa tilawa Bacci kadai yake saka shi yayi shiru.

Lokacin zafine kuma babu wuta dan haka na shimfida mana tabarma a tsakar gidan muka zauna Jafar nata wasa da Yar motarsa me Batiri ni kuma ina duba takaddun Test da nayiwa dalibai na a makaranta Aka bugo Get, Hijab na na saka na leqa, Alhaji Buba ne me gidan da muke haya shida wani mutum da wani saurayi me kama dashi daga gani dan sa ne.

Seda gabana ya fadi da ganinsu dan nasan zancen baze wuce na kudin haya ba amma ai da sauran kusan wata biyu nan gaba haka muka gaisa nace musu Bashir din baya nan.

“Eh ba wurinsa muka zo ba munzo ne mu duba gidan daman mun riga mun gama magana dashi” Alhaji Buban ya fada. Sena kalleshi da mamaki dan ban gane su duba gida ba,

“Wani abu aka ce ya samu gidan Alhaji” na fada ina kallonsa, se ya girgiza kai yace “Shi Bashir din Beyi miki bayani ba? Hidima ce ta taso mun yaro na zeyi aure dan haka ina buqatar gidan nan ze zauna a ciki, dalilin zuwan mu kenan yanzu ma dan ya duba ya gani ko akwai wani abu da za’a chanza kafin lokacin bikin” Alhajin ya fada ba tareda damuwar komai ba.

“Amma kuma Alhaji muna da sauran lokaci kafin kudin hayar mu ya qare ko ba wannan ba ma ya kamata ka bamu notice da wuri domin mu nemi inda zamu koma ko?”

“Ta yuwu kece baki da masani domin shi mun dade dayin magana dashi daga lokacin kuma zuwa yanzu ya kamata ace ya nemi wani gurin daban, maganar ragowar kudi kuma ba matsala bane zan mayar muku da abinda yayi saura a kudin hayar ku dan haka se ku fara shiri zuwa nan da sati daya nake da buqatar gurin”.

Seda na hadiye abinda ya tokare mun maqoshi kafin nace “Shikenan, zamu tashi in Allah ya yarda amma yanzu babu yanda za’ayi ki shigar mun daki se ku jira idan mun kwashe kayan mu daga baya ku duba” ina fadar haka na mayar da qofar na rufe.

Bansan hawaye nake ba seda naji Jafar yana goge mun fuska se kawai na saki kuka ganin haka yasa shima yaron ya fashe da kukan.

Kuka ne na zallar baqin ciki da takaicin nake yi, yanzu saboda Allah ace an bamu notice mu tashi daga gida Bashir ba ze gaya mun ba kenan da se ranar da aka bashi ta cika zece na fita ko kuma se masu gidan sun watsar mana da kayan mu tukunna.

Kwata kwata ni banga Lefin Ahaji Buba ba tunda gidansa ne yana da damar da ze buqace shi a duk sanda yaso sannan ya gayawa Bashir din tuni nice beyi niyyar gaya mun ba to yanzu ina zamu dosa wane tanadi yayi mana?

Da dare yana dawowa na tare shi da maganar
“Na sani kuma ina ta qoqarin ganin an samu wani gurin har yanzu dai babu, samun gidajen yayi wahala sannan kuma sun qara kudi” Abinda ya gaya mun kenan yaja bakinsa yayi shiru.

Nayi masifar nayi bala’in amma ko kallo ban ishi Bashir ba qarshe na fashe da kuka haka na kwana ina tunanin mafita a raina, idan nace zan jira naga abinda zeyi bana tunanin samun mafita daga gareshi dan ko an samu gidan nasan bashi da kudin da ze biya dan chanjin da za’a bashi ba isa zeyi ba qarshe dai ni din ni zanyi fafutukar yanda za’ayi.

Kafin safiya na yanke zuwa gurin Baffa na, shi kadai nake dashi da ze share mun hawaye masan kuma baze kasa sama mun mafita ba dan ko kusa ban hasaso rabuwa da Bashir ba akan wannan dalilin, gari na waye wa kuwa na shirya yara muka tafi gidan mu saboda haushi ko Bashir ma ban gayawa inda zani ba shima be tambayeni ba.

Kuka na fashewa Baffa daya zuba mun ido yana kallon yanda na lalace na fita hayyacine kamar wata matar qauye. Seda na gama lissafa masa matsalolina yana ji, murmushi yayi kafin yace

“Ko wanne aure da kalar qalubalensa Ma’u ayi ta haquri zan duba naga yanda za’ayi kafin lokacin da suka dibar mukun, tashi ko shiga cikin gida ku karya kin debo yara ga Sheik Jafar nan da gani bacci be ishe shi ba”.

Haka na wuni a gida ranar ina jin kamar kar na tafi duk yanda Na ringa shan zagi a gurin yan uwana kowa na fadar ni na jawa kaina.

“Ba kalar mutanen arziqin da basu zo kanki ba Ma’u amma kika nace se wannan Bashir din da ba mutunchi ne dashi ba. Ki ajiye maganar bashi da shi a gefe dan mu ba itace matsalar mu ba Aa girman kansa da yake hana shi fita ya nema shi ya jefa ku a duk halin da kuke ciki shi se aikin office zeyi ko ke ce yar wahala yana zaune ki fita ki nemo masa.
Se kije kiyi tayi, ina dai jiye miki ranar da dadi ze zo ya dakko miki yar tayin cin arziqi ta hanaki zaman lafiya idan ma be yar dake a sannan ba tunda kin gama masa aiki” Anty Zubaida Yayar mu ta biyu a Mata dana tarar a gidan ta gayamun.

Haka suka ringa gayamun maganganu kala kala wanda ko dar banji a raina akan Bashir ba, abinda na yarda na kuma amincewa zuciyata Bashir yana so na ba kuma ze taba juya mun baya ba dan haka zan taimakeshi da iya qarfina in har ni ina dashi.

Da zan tafi Goggo ta sake yi mun nasiha akan nayi haquri na zauna lafiya da mijina kar na yarda da abinda yan uwana suke gayamun. Allah sarki ita kadai ce take qaunar Bashir a gidan mu se ko Baffa da bazance ga bangaren da yake ba. Haka na koma gida ba tareda na cewa Bashir komai ba.

Kwana biyu a tsakani Baffa yace naje gida, a gaban Yayyena dukda suke gari da Iyayen mu ya mallaka mun takardun gida wanda aka siya da sunana sannan ya bani kudi naira miliyan biyu a sannan yace naja jari.

“Ku zama shaida nayiwa Asma’u kyautar wannan gidan sannan ga kudi nan taje suja jari ita da mijinta su riqe kansu”.

Haka na tattaro na dawo gida cikin dimbin farin ciki bayan Yah Abubakar ya karbe kudin daga hannuna yace naje nayi tunanin abinda zanyi dasu. Godiya sosai na ringa zuba wa na kuma qudurce a raina in sha Allahu bazan sake komawa gida da niyyar neman wani taimako ba.

Zanyi tunanin abinda zanyi da kudin ba kuma zan gayawa Bashir batun su ba gida dai gashi nan muje mu zauna a ciki.
Da na nuna masa takardun gidan ma kada ran kada han fuskarsa, washe gari mukaje muka ga gidan.

Sabon gida ne me kyau ginin zamani a cikin GRA Flat me dauke da Qaton palour da Dining se dakuna bibbiyu a cikin corridor hagu da dama ko wanne da bandakinsa a ciki ga qaton kitchen da store tsakar gidan kansa a qalla zeci mota uku zuwa hudu sannan ga dakin me gadi.

Ni kadai na ringa tsalle ina murnata Allah sarki Baffana Allah ya biyashi da Aljanna, tun a ranar muka fara kwashe kaya, a kwana na uku muka tare bayan da yan uwana da Abokanan Arziqi suka rakani kowa se yaba guri yakeyi yanda yayi kyau dan har kujeru da labulaye na sake.

Satin mu daya a unguwar na fahimci matsalar masu kantina da take damun gurin duk abinda kake nema seka fita can babban titi ko kaje kasuwa.

Ni da nake neman abinyi se na yanke shawarar bude provision store kawai dana gayawa Yah Abubakar shima yayi na’am da maganar nan da nan yasa aka fashe dakin me gadi aka sake ciyo filin cikin gidan aka yi babban shago a gurin.

Lokacin da nakeyiwa Bashir zancen muna zaune se yake cemun “ai kuwa hakan yayi dan kinga ko ni ma se na ringa zama a gurin kafin na samu wani abinyin”.

A lokacin ba qaramin dadi naji ba, dan daman tunanina kenan amma ina tsoron na gaya masa ya fassara maganar da wata manufa ko yace na rainashi shi yasa na yanke kawai zan sa a nemo min yaro da ze ringa zama tunda ga qofa anyi ta cikin gida na ringa leqawa naga yanda abubuwan suke tafiya.

Cikin dan lokaci aka hada shago sosai aka shaqe shi da kayan masarufi harda su ruwa da Lemo duk muka zuba cikin ikon Allah kuma ya samu karbuwa dan sosai ake ciniki kafin cikar wata biyu seda ya zamana har buhun huna muke siyarwa na kayan abinci da muka ga ana yawan tambaya.

Bashir ne yake zama se wani yaro Shafi’u dayazo yace ze ringa taya shi. A dan qasan mu yake maraya ne ake ruqonsa a gidan qanin Babansa sedai beyi sa’ar mariqiya ba ai kuwa na riqe shi sosai gashi da amana.

Shekarar mu daya a gidan na sake haihuwa yar mace da se naga kamar Bashir yafi yin murna akan ta sama da sauran haihuwar da nayi har na ringa tsokanar sa wai saboda an samu Dada ne yasa yake murna amma yace Aa shi ba sunanta ze saka ba.

A raina har na dauka ko ni zeyiwa kara ya saka Goggona se ji nayi ya mata huduba wai da Aisha Farida.

“Ni na zata Dada ko Goggo zaka saka ai” na fada bayan daya gaya mun sunan, se ya kalleni yace

“Bani da ra’ayin yiwa wani takwara, ko Aliyu da kuke zaton sunan marigayi Aliyu ne kawai ra’ayin kainane”.
Haka naci gaba da rainon Faridata dan tuni an saka Aliyu da Jafar Makarantar Boko da Islamiyya.

Nisan da mukayi dasu Addah be sa Amirah ta dena zuwa ba dan yawanci duk Juma’a se sunzo musamman tunda na haifi Farida wani lokacin ta kwana daya ko biyu wani sa’in ma ni zan kira Addah nace ta turo mun ita tayi mana kwana biyu dan yanzu ta fara zama yammata ta rage fitsara da rashin kunya abu daya yake hadani da ita qazanta da rashin son aiki dan in tazo se nayi da gaske take kama mun ayyuka ga bata guri haka zasu ci abinci su bata ko ina idan bani nace a kwashe ba sedai su zauna a cikin dattin.

Daman batayi mun raino qarqari ta in zanyi wani abun na ajiye mata Faridar ta kula da ita amma fa ko zata kwana tana kuka Amirah bazata goya mun ita ba bare naci arziqin tayi mun wankin yara ko yi musu wanka ba tayi to kanta ma se nayi dagaske take wankan bare tayiwa wani.


Watannin Farida Shida Allah ya karbi rayuwar Baffan mu sanadiyyar ciwon ciki da yayi na kwana daya har seda aka kaishi Asibiti inda acan ya rasu. Fadar irin tashin hankalin da muka shiga ma bata lokaci ne, munyi kukan rashin Baffa babban bango ya fadi se dai mu bishi da fatan Alkahiransa da halinsa na gari su bishi. Rasuwar Baffa da kwana Arba’in aka yi mana rabon gado kamar yanda ya bar wasiyya bayan an gama tattara komai kowa aka bashi kason sa.

Wannan karon ma ba’a bani komai nawa a hannuna ba dan ana gama rabon Yah Muslim ya danqawa Alhaji qarami nawa dana Amna. Bansan dalilin da yasa sukeyi mun haka ba, amma koma menene banyi magana tunda nasan baza su cutar dani ba.

Seda Alhaji qarami ya gama tsara duk yanda yake ganin yayi sannan ya sameni har gida wata rana yake gaya mun, mota biyu ya kawo mun cikin rabona yace gashi nan se na dauki daya na bawa Mijina daya. Na samu gonaki manya har biyu yace za’a ci gaba da noma su kamar yanda akeyi dabbobi na suma ze zuba mun su a gidan gonarsa.

Akwai fili manya guda biyu dana samu se ya bani shawarar tunda mun samu wani gida me flat takwas a Abuja aka raba mana ni biyu, Junaidiyya biyu se nasa guda hudu idan na yarda ayiwa kowanne kudi muyi musanye ya karbi filayen ya bani gida itama idan tana so ayi haka mu ringa karbar kudin hayar duk shekara dan a cikin gari suke nan take na amince na kuma bar masa duk sauran abubuwa a hannunsa yaci gaba da kular mana dasu kafin ya tafi ya turamun zunzurutun miliyoyin kudade na a account da seda jikina yayi sanyi da ganinsu.

Rayuwa kenan, shi wanda ya tara su yanzu tasa ta qare muma da muka samu wata rana haka zamu tafi mu barsu, shawara muka yanke akan gidan mu kar a tabashi, abar shi a yanda yake tunda kowa sun san kason su kowa mahaifiyarsu tana ciki sannan muka samu Qaton fili muka siya akayi Babbar Makarantar Islamiyya da masallaci Muka kuma bude foundation ta tallafawa Marayu da mabuqata me sunan ABDULLAHI TUKUR KUMO FOUNDATION ladan Allah ya kaiwa Baffan mu.

Duniya sabuwa tuni al’amura suka daidai tar mana. Na bawa Bashir mota daya sannan na hada masa da kudade masu nauyi, Alkahiri babu wanda na manta dashi dan hatta su Fainusa da suka yanke alaqa dani yanzu sun dawo kuma ban qisu ba na karbe su da hannu biyu ba wai dan bani da wayo ko ban san me nake yi ba, Aa shi wanda kafi a rayuwa har abada ka fishi arziqi kuma kashi ne kowa yazo ya dangwala.

Har sannan Bashir na zama a shago amma ba na qofar gidan mu ba dan a cikin kudi na na bude babban super market acan kan titi shine manager muka dauki ma’aikata tsohon kuma na barshi a hannun Shafi’u da sabon yaron daya samo yake tayashi saboda na mayar dashi makaranta se da yamma yake zama a Gurin.

Bayan fitar Su Goggo takaba kawai ta taso da wata maganar wai zata koma Yola ta daura aure da Baffa Sama’ila. Qiri qiri muka nuna qin Amincewar mu gaba daya seda Alhaji Qarami ya tsawatar mana sosai akan me yasa mu zamu haramta abinda Allah ya halasta, babu wanda ya isa ya hana mahaifiyarsa qara aure a cikin mu gaba daya ko da kuwa cewa sukayi zasu kawo mazan cikin gidan mu tunda dai suka da kason su.

Haka muna ji muna gani aka daura musu aure da Baffa Sama’ilan ta shirya komawa Yola nan na tada sabuwar rigimar sedai ta bar Amna bazata tafi da ita ba a wannan karon dai na samu goyon baya se kuma rigima ta koma tsakanin manyan cikin mu mu Ashirin da bakwai a sannan maza da mata masu aure kowa yace shi ze riqeta daga qarshe dai nayi nasara riqon Amna ya dawo hannuna wanda Bashir da kansa ya goya mun baya aka bani ita.

Riqon Amna da na karba wane tudu wane gangare se ganin Amirah nayi da faggon kaya Addah ta kawo ta wai Addahn zasuyi tafiya zata je Niger, daga tafiyar sati biyu taji dadi da su Addan suka dawo se cewa tayi bazata tafi ba, Bashir zeyi fada nace ya barta ta zauna zan riqe dan har ga Allah ina son yarinyar kuma ina so naga tarbiyyarta ta inganta dan duk in tazo mun sena ga abinda beyi mun ba a cikin halayyarta wannan shine mafarin dawowar Amirah hannuna.

Sosai Allah ya sanya Albarka a cikin kasuwancin mu, kudin da na bawa Bashir a cikin super market din shima ya saka ake juyawa, wata dabara da nayi masa muka zauna akayi rubutu kudinsa da yake ciki nace masa ya cigaba da juya su duk ribar daya samu ya barta a ciki karya cire sannan za’a ringa biyansa a matsayinsa na manager kamar sauran ma’aikata, da Allah ya sakawa abin Albarka se gashi muna neman yin kankan kan dashi a mallakin shares na super market din.

Salin Alin muke zaune rana daya Bala da rabon dana ji duriyar sa har na manta yazo mana ziyara. Faran faran muka gaisa na basu guri shida Bashir na koma ciki, bansan me suka tattauna ba bayan tafiyarsa na fara ganin chanjin fuska a gurin Bashir.

Kwanaki biyu a tsakani ya dena fita super market, a rana ta uku ne nayi masa magana se ce mun yayi

“Akwai sauran Ma’aikata nasan zasu kula da komai”

“Amma baban Ali kasan dai yanda mutane suke yanzu idan babu idon ka zasu iyayin yanda suka ga dama, ka manta rungon lissafin da suka ringa yi mana

Please Login or Register in order to submit comment