Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

zata dawo gidan nan kuma a sannan baki isa ki koreta ba" kalaman Addah suka dawo mun a kwakwalwa ranar da na kori Amirah daga gidana a Gombe. Ashe abinda suka shirya yi mun kenan daga ita har Dadan suka dakko kishiyata suka kawo mun da nufin na gyarata su kuwa wasu irin mutane masu saka Alkahiri da sharri ta ina na kuskure musu a rayuwa da suka zabi hukunta ni ta irin wannan hanyar?

Kuka na ringayi wanda tun likitocin da suka dubani suna bani haquri har suka haqura sukayi shiru, bana buqatar sauran bata lokaci a qasar tunda daman ba dan Allah ya turani ba dan ya aiwatar da nufin sa ne to yaci galaba amma nima dole na koma Nigeria muyi wacce zamuyi da Bashir dan bazan taba hada miji da Amirah ba.

Yana da damar ya auro mun mata uku mu zauna amma ba Amirah yarinyar da nakewa Kallon Yata ita ce ze hadani kishi da ita baze sabu ba.

Sanda na koma Hotel din da muke na tarar da yara zuru zuru dan da aka kaini Asibiti can suka koma saboda a qa'idar su ba'a barin dan jinya.

"Ku hada kayan ku yau zamu tafi" na fada ina hargitso duk abinda hannuna ya kai kansa ina sakawa a jaka. Seda na gama sannan na tuna da ai Passport dinmu ma baya hannunmu yana gurin Agent din da Bashir ya hadamu dashi, wayata na dauka na shiga kiran nayi sa'a tana shiga ya daga.

"Malam Isah kayi mana booking jirgi idan da akwai Yau ka, ka fada mun kudin ko nawane zan biya wani abu ya taso mun bazan iya jira har se gobe ba" na fada ba tareda na amsa gaisuwar daya fara mun ba.

"Amma Hajia me ya faru haka, bayan haka kuma ai Ticket din ku bana komawa Nigeria bane Dubai zaku wuce daga nan na zata ai Engineer ya gaya miki ma"

"Isah dakai da Dubai din da Engineer kunci abu ta kazan ubanku" na lailayo wata Ashar me maiqo da ni kaina bansan na iya ta ba na kora masa kafin na ci gaba da cewa

"Ka kawo mun passport din mu nan da Awa daya idan ba haka ba wallahi se nayi qarar ka nace safarar mu kayi, kasan ina da duk wasu bayanai naka da zan bayar ka kuskure lokacin baka zoba ka gani".

"Kiyi haquri hajia ku shirya yanzu zan turo mota da zata kaiku Jiddah ni ina can yanzu haka akwai jirgin da ze tashi yau da daddare bari na bincika idan da akwai guri se a siya" Isah ya fada jin abin yafi qarfinsa.

A dakin muka bar kusan rabin kayan mu dan bana buqatar abinda ze bata mun lokaci bate har aje ana maganar wani awon kaya ko wani abu muka hau mota se Jiddah gaba daya ma gani nayi motar bata sauri, ina ma ace zan iya rufe ido na ganni a Nigeria, ina buqatar naje naga da wadanne idanu Bashir da danginsa zasu kalleni.

Mun samu jirgi amma se munyi jiran Awa goma sha biyu kafin tashinsa, haka Isah ya nema mana hotel gaba daya ya rasa meya faru haka gashi kiran duniya Bashir yaqi dagawa daga qarshe ma ya kashe wayar gaba daya Asma'u kuwa bega fuskar da ze mata tambayar abinda yake faruwa ba ma dan haka yaja Aliyu yana tambayarsa ko mutuwa akayi

"Nima ban sani ba, kawai daga Masallaci aka kaita Asibiti kuma data dawo mun kasa tambayarta abinda ya faru idan mukaje gida koma menene se mu gani" Aliyun ya bashi amsa.

Haka muka hawo jirgi se Nigeria ya sauke mu a Kano,Asuba ranar lahadi muka sauka tun a AirPort na samu shatar mota ta kwashe mu kafin Goman safe mun sauka a Gombe muka ci burki a qofar gidan su Bashir cikin Sa'a nayi kyakykyawan gamo da Ango Bashir da tun daren Alhamis rabon da ya sake daga wayata.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 39

A qofar gidan motar mu ta tsaya, idona akan Bashir da suke tsaye tareda wasu mutum biyu da ban gabe su waye ba.

“Ku jirani karku fito” na fadawa yaran, seda na yi kokawa da duk wani rauni da karayar zuciyar daya taso mun kafin na bude motar na fito ina gyara mayafin kaina gaba daya mutanen gurin suka bini da kallo banda Bashir da tunda muka hada ido ya maida kansa qasa kaman wanda aka kama yayi qarya.

Kai tsaye cikin gidan na shiga, nayi sallama ina jiyo hayaniyar su daga cikin dakin Dada amma ba’a Amsa ba dan haka na nufi can din, har na kai bakin qofar naji an kira sunana, sena waiwaya.

Alhajin su Bashir ne yana tsaye daga qofar dakinsa ya yafito ni da hannu sena juya na koma gurinsa.

Ina durqushe a gabansa kusan minti biyu kafin yaja numfashi yace dani

“Asma’u kiyi haquri nasan an cutar dake amma zan roqeki Arziqi kar kice musu komai yanzu, ki barsu akwai ranar da su da kansu zasu maidawa junan su martanin abinda sukayi miki.

Na sani Qarin aure ba haramun bane amma ta yanda aka shirya naki sam be kamata ba. Ya zama zamba cikin aminci. Ki sani Ita Amana daya ce kuma wanda yacita baya taba zama lafiya, idan har Bashir da uwarsa sun qulla wannan aure dan su ci mutunchin ki Asma’u in Allah ya yarda muna raye ko mun mutu se sunga sakayyar cin Amanar da sukayi miki.

Ina qara roqonki da kiyi haquri, ki qara akan wanda kike yi in sha Allahu bazaki tabe ba, duk me neman gazawarki akan idonsa zakiyita ci gaba da yardar Allah”.

Kuka nakeyi dagaske a raina ina hasaso irin tarin qaunar da na nunawa Bashir da Ahalinsa, a tsahon zamana dashi kusan shekara goma sha uku yanzu bazan iya cewa taka maimai ga wani abun laifi daya taba hadani da wata daga cikin su ba, a kullum cikin kyautata musu nake iya qarfina kuma duk albarkacin so da qaunar da nakeyi wa Bashir din ce ta shafi su amma ace a gurinsu basu da abokin hamayya seni.

Sosai nasha kuka na ba tareda Baba ya hanani ba in banda “kiyi haquri Asma’u” babu abinda yake cewa.

“Naji zan haqura Baba bazan tanka musu ba amma kayi haquri bana jin zan iya ci gaba da zama da Bashir. Bazan iya ci gaba da zama cikin Ahalin da basa qaunata ba Baba. Sannan Baba Amirah fa, yarinyar dana raina da hannuna ita zan hada miji da ita wallahi bazan iya ba.

“Zan bi umarnin ka a yanzu zan koma ba tareda na cewa kowa cikin su komai ba amma Baba karka roqeni ci gaba da zama da Bashir saboda ina girmamaka bazan iya tsallake unarninka ba amma tabbas zan cutu. Zuciyata zata iya bugawa a dalilin haka muddin zan zauna inuwa daya da Amirah a matsayin kishiyata” na fada cikin sheshsheqa me qarfi.

Se Baba yayi murmushi wanda da ganinsa na takaici ne kafij yace
“Asma’u ke Yarinyar kirki ce sannan abar Alfaharin duk Miji me hankali da yayi katarin samun irin ki sannan ko wanne uba zeyi alfaharin zamtowarki Suruka a gare shi.

Bazan so na rasa nagartacciyar suruka irin ki a cikin zuria’ata ba domin ke din mayafi ce da kika lullube Bashir duk kuma ranar da wannan mayafin ya yaye ba baki nayiwa Bashir ba tabbas se rayuwar sa ta shiga cikin gararin rayuwa.

Idan har ki ka ce bazaki ci gaba da zama da Bashir ba ni me tsaya miki ne in tayaki kwatar yancin kanki amma yanzu kije ki samu nutsuwar zuciya, karki yanke hukunci cikin fushi idan kika nutsu duk abinda kika yankewa zuciyarki ki dawo ni ki gaya mun in Allah ya yarda zan baki goyon baya dari bisa dari ki share hawayenki yanzu”.

“Baba bana tunanin ina da buqatar yin wani dogon nazari ka taimakeni kawai kasa Bashir ya sawwaqe mun dan ina da yaqinin ko ba yanzu ba watarana se sunyi nasarar fiddani daga dakina” na fada cikin kuka, se ya tare ni da cewa

“Haba Asma’u ke da na sanki jaruma ya zaki karaya tun yanzu ki bada qofar da za’a ci galaba akanki? Maganar su fitar dake daga dakinki kuka babu wanda ya isa yayi Abinda Allah beyi ba, kije gida ki huta ki bawa zuciyarki haquri idan kuma kinga bazaki iya karbar Al’amarin ba ki dawo zan tsaya miki”.

“Shikenan Nagode Baba Allah ya qara girma”
“Nima na gode Asma’u Allah yayi miki albarka keda zuri’arki gaba daya”. Haka mukayi sallama da Baba seda yasakani na share hawayena tas yace naje na dauraye fuskata a bayin da yake cikin palour sa kafin na fito.

Ina fitowa naci karo da Dada da yayanta sun fito daga dakinta, Yanda kasan anyi ruwan sama an dauke haka sukayi shiru gaba daya suka zubo mun idanu kamar wanda sukaga wata sabuwar Halitta nayi musu kudin goro gaba dayabna watsar na nufi qofar fita.

Sanda Na fita ban tarar da Bashir a waje ba se Naziru suna tsaye a jikin motar da muka zo tareda yara. Kallo daya nayi masa na kama murfin motar na bude se ya riqe yana cewa

“Wallahi Anty babu sa hannuna basu gayamun ba se ana gobe za’a daura, da nace zan gaya miki Dada tace duk wanda ya kuskura ya sanar dake wallahi se tayi masa baki shiyasa ko Yaya Amiru da kika kira jiya ya kasa gaya miki komai” ban bi takansa ba na cewa me motar muje na nuna masa hanya ya qara sa damu gidan mu gidan Baffana. A waje na barsu ana sauke kayan mu bayan na sallame shi na wuce ciki.

A yanzu babu abinda nake buqata sama da na kebe ni kadai a inda zan sha kukana kar wani ya rarraahe ni. Dakin Hajia Babba nayi masauki na haye can qarshen gadonta na saka kaina a cinya na ringa rirgar kukan da wadda akayi wa irin abinda akayi mun ce kawai zata fahimce ni, tambayar kaina nakeyi me nayiwa Bashir a rayuwa daya qullaceni yaga ta haka kadai ya kamata ya rama.

Ina jin matan gidan mu suka ringa shigowa suna bani baki amma na toshe kunnena, nasha kukana seda naji Numfashi shina yana barazanar daukewa kafin na bawa kaina haquri na koma sauke ajiyar zuciya kawai ga wani masufaffen ciwon kai daya dirar mun maqogarona kuwa kamar ze tsage saboda bushewa dan in ban manta ba rabonda ko ruwa ya wuce ta cikinsa tun kafin na samu wannan baqin labarin.

Har dare ina cikin dakin sallah kadai na tashi nayi na koma na kwanta ba tareda na ko kalli kayan abincin da Hajiyar ta kawo mun ba. Haka ta zauna akaina tana ta faman yi mun nasiha dana gaji da jinta sena sa mata kuka dole ta tashi ta bani guri, qarin abinda yake damuna ganin har zuwa sannan banji komai daga Bashir ba, be zo ba be kuma kirani a waya ba haka na kwana kafin safiya jikina ya rijice dole se da aka danganani da Asibiti.

Gwajij farko likita ya tabbar mun da jini na ne ya hau sosai abinda ya saukar mun da mugun ciwon kai kenan ga kuma zazzabi me zafi, shawara ya bani da koma menen yake damuna nayi haquri na kuma fawwalawa Allah domin lafiyata tana gaba da komai, duk wani al’amari na rayuwa baze tafiyar mun daidai ba idan babu lafiya daga nan yayi mun Allurai da zasu taimaka mun zafin jikin ya ragu da ciwon kan ya bani magunguna muka tafi gida.

Seda akayi mun wuqa wuqa sannan naci abinci nasha maganin ban dade ba bacci ya dauke ni seda na shafe awanni ina yi kafin na tashi.

A yammacin ranar Alhaji Qarami yazo, bashi kadai ba kusan yayyena dukka seda suka zo gida aka taru masu tsinewa Bashir nayi masu bani baki sunayi. A bakin su nakeji wai ashe jiya da daddare ma yazo gidan ma, nidai ina kwance ina jinyar zuciyata.

Seda muka kwana biyu da dawowa a daren ranar da daddare ina kwance a daki da carbi a hannuna ina ja Jafar ya shigo yace wai naje inji Dadyn Abuja. Da dogon Hijabi na har qasa nayi sallama a Palour Hajia Babba kaina a qasa seda na kai tsakiya sannan ido na ya sauka akan Bashir da Bala se Abdulkarim Dan Qanin Baban su ne, ba tareda na qara ko taku daya ba na juya da niyyar fita Alhaji Qarami ya dakatar dani dole na koma na samu can gefe kusada qofa na zauna ina jin zuciyata kamar an watsa fetur an cinna mata wuta.

“Asma’u mijinki ne yazo bada haquri shine nace a kiraki tunda ke akayiwa laifi ke ya cancanci abawa haquri ko” Alhajin ya fada yana kallona, kafin ya miqe yana sake cewa”ki matsa ciki kin zauna a bakin qofa ga dare idan kun gama ki same ni gurin Hajia Umma ina son ganinki”.
naji shi sarai amma ban dago ba ban kuma matsa daga inda nake ba ya tsallakeni ya fice daga palour, be san jira kawai nakeyi ma na samu wata dama na fice na bar musu gurin dan bazan iya musa masa ba tun farko dalilin da ya sa na zauna ma kenan.

“Gamu munzo guiwoyin mu a qasa Asma’u munsan ba’a kyauta miki ba ni kaina wallahi bansan abinda ya faru ba kenan se daga baya amma ki dubi girman Allah kiyi haquri, kuskure dai an rigada anyi shi sedai muyi fatan Allah ya kiyaye na gama amma yanzu kiyi haquri ku karbi qaddara a yanda tazo muku” Abdulkari ya fada, se na daga kai na kallesu ina shirin buda baki nayi magana Bala ya rigani da cewa

“Allah ya huci ran uwar gida sarautar mata, kinsan fa kinsha kan mutumin bala’in tsoronki yakeyi shiyasa ya kasa gaya miki zancen auran nan. Kuma ma ni gani nayi ai ba wani abu a ciki tunda qanwarki ce daman da aje a dakko miki Bare wadda baki san halin ta ba Uwargida ai gara ta gida ko, easy kawai ki shanye a koma a ci gaba da gashi”

“Sedai a koma a ci gaba da gasa ubanka Bala” na fada a fusace ina miqewa tsaye kafin na nuna Bashir da yai tsamo tsamo kamar kazar data sha dukan ruwa ya zate ido yana aikawa Bala da mugun kallon katobarar dayayi nace

“Kai kuma tun da sauran burbudin mutunta juna a tsakanin mu ka rubuta takaddata ka aiko mun da ita dan wallahi Bashir kayi kadan ka wulaqanta ni kayi mun kishiya ta rashin mutunchi, idan kuma kaqi tabbas kotu ce zata raba auran mu da kai” ina fadar haka na juya amma kafin na kai waje Bashir da bansan tasowarsa ya riqe ni kamar dansanda da Barawo yana cewa

“Bazan iya ba Ma’u, na sani nayi kuskure amma wallahi rashin sanin ta inda zan fara gaya miki maganar yasa na aikata haka. Basan a ya zaki kalleni ba Ma’u idan nace miki zan qara aure. Ni kaina na rasa ta yanda Al’amura suka juya har na fara son Amirah na yarda kiyi mun duk irin hukuncin da kikaga ya dace komai tsananinsa zan dauka amma bazan taba iya rabuwa da ke ba Ma’u”

Wani tuquqi ne ya taso mun, yanzu har Bashir ya iya kallon tsabar idona yace dani wai yana son Amirah lallai na yarda In da ranka zaka sha kallo. Hannayensa daya riqeni na banbare daga jikina ina cewa

“Tunda kana sonta seka je ka zauna da ita amma ni dai wallahi na gama zaman aure dakai ko kaine autan maza Bashir kaje ka zauna da matar so tunda na gamayi maka rana”

“Kiyi haquri dan girman Allah Ma’u ki yafe mun ki bani dama na wanke kaina nayi miki Alqawarin babu abinda ze chanza a tsakanina dake saboda wannan auran, Ina sonki ina qaunar ki ki dauka wannan abun yana cikin qaddadarar mu daga ni har ke” ya fada yana qoqarin sake kama hannuna nayi baya ina cewa

“Qaddarar ka dai kai kadai kuma ka matsa karka sake rabar jikina idan ba haka ba Bashir sena kwada maka mari wallahi”. Sosai na birkice nayi masa tijara yanda ne taba tsammani ba a rayuwar sa, na hada da Balan da Abdulkarimun nayi musu zagi na tsamar nama kafin na jadda da masa akan ya kawo mun takaddata dan wallahi na gama zama da Bashir na yarda su Addahn suci galaba a kaina. Dana hada miji da Amirah gara na fita na bar mata gidan ta zauna dashi ita kadai.

Bangaren Hajia Umma na wuce gurin Alhaji Qarami, banko bashi dama yayi magana ba na fashe masa da kuka ina rantsuwar bazan komawa Bashir ba ya saka shi ya kawo mun takaddata na tsane shi na tsani zama dashi. Haka yayita bani haquri ya kuma tabbatar mun da cewa tilas Bashir ya sake ni tunda har na nemi hakan amma yanzu na kwantar da hankalina kodan jinina da akace ya hau a samu ya sauka kar kuma na sake janyo wa kaina wata matsalar.

Haka na kwashe sati biyu cif a gida muna kan wannan danbaruwar, kullum Bashir se ya zo kamar maye haka ze durqusa yana bani haquri nima kuma ban fasa ci masa mutunchi da jaddada masa cewa ya bani takaddata ba tunda ba’a aure dole nace na gama.

Gashi makarantar yara kullum se kiran waya sukeyi an koma tuni lafiya basu dawo ba nace musu mun bar gari ne za’a zo a fada officially a cire su haka gurin aikina ma da suka tuntubeni tunda hutun sati uku na dauka gashi na haura kawai se nanemi takaddar hutu ba tareda biyan Albashi ba, dan bazan bar aiki na ba saboda a yanzu ne nafi buqatar sa Idan Bashir ya sake ina da buqatar neman hanyoyin da zan ruqe kaina da Yayana dasu.

Bazan manta ranar da Dada da Addah suka wanko qafarsu wai sunzo biko na ba, na yaba da tsantsar rashin kunya irinta mutanen nan. A ranar nayi musu abunda Bahaushw yake cewa idan Malam beji kunyar hawa Jaki ba to shima Jakin baze ji kunyar kada shi ba.

Na fito musu a yar zamani na wanke su tas da soso da sabulu na kuma sake jaddada musu da idan sunji haushi su saka Dan su ya sake ni su gani tsakanij ni dashi waya rasa na raka su da Allah ya isar abinda sukayi mun kuma in sha Allahu nan kusa zasu ga sakayyar yaudarata da sukayi haka suka kwashi kafafu a sanyaye dan ba Dada ba Addah kanta da bata raina abin kunya tayi mamakin yanda na sakawa idona toka nayi musu tas.

Daukata sukeyi a duk yanda suka takani zan biyune shiyasa ma yanzun suka zo saboda horon da Bashir yaje yayi musu akan kodai suje su bani haquri na koma dakina ko kuma ya saki Amirah tunda ita ce duk musabbabin tashin hankalin da akeyi.

Wai mutane saboda qin Allah se kaga sun kirani da sunan wai ban kyauta ba abinda nayi wa iyayen Bashir tunda auren daya qara ai ba haramci bane da zance ni bazan zauna da kishiya ba.

Har da wadda take cemun ilimina be amfana mun komai ba ina Karatun islamiyyar da nayi ina Bokon nawa zan zauna ina ja ina jayayya da abinda Allah ya halasta, ban dagawa ko wace yar iska qafa ba na kuma roqi Allah duk wadda tace nayi Haquri Allah yasa ayi mata abinda yafi nawa muni idan yaso se taji in ma rashin tawakkalin me ya sakani yin haka ko yaya.

A cikin wannan yana yi wata rana muka samu baquncin Goggo da tunda aka fara wannan abun sau daya mukayi magana da ita shima ni na kirata kuma tace mun nayi haquri daga haka bata qara komai ba.

Ina kwance a daki aka kirani a lokacin idan ka ganni se na baka tausayi, na rame na fige fuskata babu komai daga ido se dogon hanci ina shiga palour idona ya sauka akan Bashir daje zaune a qasa, ban lura da sauran mutanen da suke ciki ba na hau kansa da masifa ina cewa

“Wallahi ko maye ne kai Bashir haka zaka ganni ka kyale tunda nace banayi banga wanda ya isa ya tilastani ci gaba da zama da kai ba, ka tashi ka tafi tun kafin nasa azo a fitar dakai mara zuciya kawai”

“Idan baki saka an fita dashi ba baki isa fitsararriya mara mutunchi ba Asma’u” muryar Goggo da ban san da zuwan ta ba ta katse ni kafin ta ci gaba da cewa

“Ashe duk rashin mutunchi da diban Albarkar da akace kinayi dagaske ne kuma a gaban ku Hajiya kuna kallo aka rasa wanda ze tsawatar mata. Saboda bakida mutunchi Mijin naki kike sakawa a gaba kina fada masa irin wadannan maganganun ku to bari kiji shi Allah babu ruwansa ze hukuntaki ne akan laifin ki na sabawa miji da ci masa mutunci babu ruwan Allah da cewar Bashir ya auro miki wadda bakya so anyi miki ba daidai ba dan haka tun wuri ki dawo cikin hankalinki kafin ki kanki wuta da qafafunki.

Sannan saboda kin zama yar kanki se abinda kika tsarawa ranki zakiyi shine kike iqirarin zaki kashe auranki saboda kanki farau kishiya ko kuma kece ta qarshe da za’ayiwa ko?

Ki idan kina da hankali ma ya kamata ki tashi jiniyoyij wuya akan za’a miki kishiya, gidan mu mata nawa Ubanki ya aura gamu nan mu Hudu ya mutu ya bari kin taba gabin wata tayi tashin hankali da yar uwarta a cikin gidan nan?”

“Amma Goggon su bazaki hada mu dasu ba, ko bayan haka hanyar da Bashir yabi tayin qarin auransa ce bata dace ba kuma ko wacce mace akayiwa irin haka dole ranta ya baci ai” Hajia Anjin ta tare Goggo jin yanda take ta surfa fada, se Goggon ta kalleta tace

“Saboda ya auri yar uwarsa ne take tashin hankali dan ba’a gaya mata ba, ai ba kansa aka fara ba tunda ubanta ma a sanda ya auro ni ai baku sani ba tafiya yayi bikin abokinsa ya dawo muku da ni a matsayin kishiya me yasa a sannan ku baku yi tashin hankali kunce bazaku yarda ba?”

“Aa Maryam Allah ya jiqan Alhaji bazaki taba hadashi da wannan yaron ba domin Alhaji Adali ne gamu nan dukka bari kiji kafin A daura auran ku da Alhaji seda ya kira mu a wayar landilayin da daddaya ko waccen mu seda ya gaya mana abinda ya faru ya kuma sanar mana da cewa ze aureki bisa wasiyyar Sama’ila dan haka da yardar mu da Amincewar mu Alhaji ya auro ki, sannan tunda tace bazata koma ba ai Asma’u ta wuce yarinta bare ace za’a zabar mata abinda zatayi”
Hajia Babba ta fada sauran suka amsa da “kwarai haka aka yi.

“To shikenan tunda kun daure mata gindin tayi duk rashin mutunchin da take so kun bata goyon baya ni baza’a hada kai dani ba, Ke Asma’u idan na isa dake ki tattara ya naki ya naki yanzu ki bi mijinki, kuma diban Albarkar da kikayiwa uwarsa da yayarta kije ki basu haquri, dan cikin matan yayyen ki kaf babu wadda ta taba duban idon mu ta gaya mana maganar banza balle mu yayanmu suje suyiwa na wasu”.

Tunda suka fara mahawarar na durqushe a gurin ina Kuka, wato qarata Bashir ya kai gurin Goggo ita kuma ta goya masa baya. Da sauri na daga kai na kalleta hankali tashe jin irin umarnin data bani, se nayi saurin matsawa kusada ita ina cewa

“Amma Goggo...”
“Karki ce mun komai sedai kuman idan kin shirya nuna mun ban isa dake din ba shikenan” ta yi saurin katse ni, se na mayar da kaina qasa na ci gaba da kuka me ciwo, ya zalunce ni kuma ha hadani da mahaifiyata Bashir wane irin mugun mutum ne a rayuwa.

Haka naja qaqafuna na koma daki na shiga tattara kayana ina kuka yarana da suka biyoni suna tayani. Ina cikin hada kayan Hajia Babba ta shigo dakin,

“Ki bar shirin yanzu Asma’u tace ku bari zuwa jibi se ki koma. Kiyi haquri ita rayuwar Ya mace daman haka da qalubale wata rana komai ze zama tarihi in sha Allahu” haka tayi ta bani baki har seda naji zuciyata tayi sanyi na kwanta a kan Gado ina saka da cin alwashin

Please Login or Register in order to submit comment