Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

mahaukata se anyi da gaske ake iya raba su da Yayan su bare ita yar tilo haihuwar farko ko nicefa bazan baka ba.

Idan Dan rashin lafiyar ta ne Allah ya hore maka ai ka barta a Asibiti suyi ta kula da ita har zuwa sanda suke ganin tayi kwarin da zata juri ko wanne kalar yana yi amma ba maganar ka bani ita, nawa ma idan za’a ragi wasu aciki bayarwa zanyi”.

Shiru yai yana kallona harna dasa aya ina sake turo dankwalina gaban goshi, ajiyar zuciya yayi kafin yace “yanzu dai bazaki karba ba kenan?”

“Allah me iko, da Hausa fa nayi maka jawabi dalla dallah amma kake sake tambaya ta kuma?”

“Eh saboda kinsan ni bana son dogon surutu, amsa daya nake buqata Eh ko Aa kawai” ya fada a dan hasale alamar ya fara barin cool site dinsa ze koma Bashir dinsa na gaskiya, se kuwa na tura baki gaba nace “Toh a taqaice dai bazan karba ba”.

“Shikenan, amma ina da ikon da zan kawota cikin gidan nan ko tunda gida nane” ya fada yana miqewa, nima sena miqe tsaye jin wani qundumemen rainin wayo,

“Tabbas gidanka ne ka isa ka dakko kowa nene ka kawo shi ciki, zaka iya kawo ta tunda itama gidan ubanta ne ai se ka hado dame kular maka da ita, ko kuma kai zaka aje aikin ka ka zauna rainon duk ba matsala ta bace ni” na fada ina dauke kai gefe, ina jin yanda yake qare mun kallo kafin yaja tsaki tareda sakin kwafa ya shige daki na rakashi da harara ina cewa a fili

“Wallahi ba tsaki ba kome zakayi sedai kayi, bazan karbi raino ba, rainon ma yar Amirah yarinyar da duk zamana da ita idan dana ze tsaga guri saboda kuka bazata dauke shi ba balle aje ga tsarkin kashi ko wanka shine ni ga jaka yanzu ta haifa za’a dakko a kawo mun in riqe mata toh ko daga turu aka kuntota qarewar rashin nutsuwa sedai duk handa za’ayi ayi”. Tsaf nasan yaji ni dan da qarfi nayi saboda yajin, na koma kan kujera na zauna, se kuma na miqe na dakko wayata na dokawa Dadar su kira dan fa karma inji wata magana daga baya.

Ringing biyu ta dauki wayar, a taqaice na gaisheta ta amsa kafin na shiga koro mata jawabin yanda mukayi da Bashir, na rufe da cewa “Iya gaskiya ta na fada ko bana aiki bazan riqe mata ya ba kowa ya kula da nasa Allah ya taya masa, idan kuma Ya dage akan hakan to sedai na bar masa nawa nima ya nemo wadda zata riqe masa su ni intafi”. Shiru Dada tayi har na kai qarshe sannan ta numfasa tace

“Ya kirani ya gayamun kuma na gaya masa wannan ba me yuwa bane, todai yanzu duk se hankalin ku ya kwanta tunda Allah ma ya raba muku gardamar ya karbi abarsa, se kowa yayi haquri ya maida wuqar” Dadan ta fada cikin sanyin murya,

“Hasbunallahu wani’imal wakeel, ta rasu jikin ne ya sake tashi?” Na tambayeta a rude dan maganar ta dake ni dagaske, “ta rasu yanzu Likitan ya kira Naziru yake gaya masa lafiya lau dan yau sukayi niyyar sallamarta ma har an yi mata wanka ma sun bata madara tayi bacci to daga baccin ne kuma bata farka ba”.

“Allah yasa me ceto ce, ya musanya mana da wadda tafi ta Alkahiri” Na fada a sanyaya tareda sauke wayar daga kunne na, ina dagowa muka hada ido da Bashir daya fito kamar wanda aka koro.

“Se ki zuba ruwa a qasa kisha, da baki karbeta ba ta mutu” ya fada yana jifana da wani irin kallo kamar ni na kashe masa ita. Sena miqe na nufe shi ina cewa “karbarta ko akasin haka be isa ya chanza hukuncin Allah akanta ba tunda babu dayan mu daya halicceta ko kuma ranta yake hannunsa dan haka ko tana gidan nan tunda wa’adinta yayi dole ta mutu, in zuba ruwa a qasa nasha kuma bani zaka gayawa ba Uwarta da tai sanadinta can zakaje ka gayawa dan ita ta nuna a fili bata damu da ita ba” na wuce shi na shige dakina tareda banko qofa, in banda ma rainin hankali ji abinda fa yake cewa fa.

Ina ciki naji tashin motarsa alamar fita yayi a raina nace a sauka Lafiya Allah ya gani qilan zamanta ze iya zama fitina shiyasa Allah ya karbi abarsa, Har qarfe biyar ina dakin fito ba, gaba daya zuciyata a jagule take ga alhinin rasuwar Iman ga soki burutsun Bashir na sake kiran Dada nayi musu ta’aziyya ta cikin wayar ina iya jiyo kururuwar Amirah da muryoyin mutane wasu na tausarta wasu kuma suna mata fada akan kukan da takeyi.

Na tausaya mata harga Allah Kuka kam dole tayi shi wannan duka wani kan wani amma yata iya haka Allah ya tsara abinsa masu samari da yammata ma ake dauka bare ita jaririyar da ba dadewa tayi ba.

Har na miqe da niyyar zuwana dora abinci wani tunani yazo mun, ta yuwu fa Bashir ya tafi Gombe be gayamun ba ga yara a makaranta lokacin tashin su tuni ya wuce, Hijabi na na dauka da wayata na fita, bari naje na ari motar Anty na dakko su dan tawa tana gurin Service ba’a dawo da ita ba, ina kulle qofar gidan motar sa na tsayawa da yaran ya dakko su se na bude na koma ciki ina jiransu.

“Mami ina zakije” Abdallah ya fada bayan daya rungume ni, “Da zuwa zanyi na dakko ku na zata Abbi ya tafi Gombe” na fada ina kallon Bashir daya shigo a sanyaye kaman wanda aka sheqawa ruwan sanyi.

“Abbi yace Baby Iman ta rasu wai Mami” Farida ta fada fuskarta kaman zatayi kuka, sena riqo hannunta ina cewa “ta rasu Farida” kaman tana jira kuwa ta saka kuka tanacewa “kenan banida sister mace yanzu har fa na fadawa friends dina yau a school step mum din mu ta haifo mun baby sis”

“Dallah malama yi mana shiru, kina kallon yarinya kamar mage dama ai kinsan mutuwa zatayi kuma ai ma...”

“Shut up You are very stupid Aliyu” Bashir da yake shan ruwa a dispenser ya katse Aliyu cikin tsawar da harni seda na tsorata amma ko gezau yaron nan beyi ba sema ido daya zubawa uban suna kallon kallo kamar wasu zakaru.

“Zaka wuce daga nan ko sena zo na same ka wawan yaro har fada kake daman mutuwa zatayi kenan so kake ta mutu koh” Bashir din ya sake fada cikin bacin rai, se na saki hannun Farida da Abdallah na miqe da niyyar yin magana Aliyu ya rigani yana cewa

“Toh ni Abbi me nace kawai dan na fadi gaskiya wayace su jagwalgwalata sannan su sakata a sanyi ai dole ta mutu....” be rufe bakinsa ba Bashir ya dauke shi da mari da har seda gefen bakin sa ya fashe kafin ya fizgo shi ya hau dukansa.

Kuka yaran suka saka gaba daya ganin abinda be taba faruwa ba a gidan yau Bashir ne yake dukan Aliyu kamar wanda ya samu jaki, tsakiyar su na shiga ina qoqarin kwatar Aliyu da ko gezau sema cewa da yake yi

“Ai daman seda nace miki ki koreta daga gidan mu muguwa ce kika qi seda ta aure shi, gashi nan yanzu yafi son su akan mu tunda ta haifi yarinyar nan kina kallo yanda hankalinsa ya koma kanta komai ita har comapany da ze bude da sunan Farida ma ya chanza na gani sunanta ya saka, shi yasa kullum nayi sallah sena yi Addu’a Allah yasa ta mutu dan akan Abbi ze iya yin komai gashinan kuma kina gani”.

Bige bakinsa nayi ina fashewa da kukan nima dan na kasa tare dukan da Bashir yake masa shi kuma yaqiyin shiru nasan kalaman sa ne suke qara tunzurashi seda ya gaji dan kansa kafin ya kyale shi ya shige dakinsa ya banko qofar ya barmu muna rusa kuka kamar nan ne gidan mutuwar.

Wannan wane irin bala’ine, ni na kashe yarinyar ko Yara na da ze huce akan mu? Ai kuwa wallahi da sake zan dauki komai amma banda irin wannan dukan da kalaman da basu dace ba akan yarana.🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah Farouk
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)


Wattpad @MaryamahMrsAm

Page 25

Ina kuka ina gasawa Aliyu fuskarsa da ta kumbura sosai saboda marin daya sha a hannun Bashir, tausayin sa ya cikani tabbas be kyauta ba amma ai dukan yayi yawa, Yanda ya zage ya ringa dukansa kamar wanda yake dambe da sa’ansa.

Gaba daya yaran suna tsaye sunyi cirko cirko kowa fuska da hawaye kana kallonsu kasan a tsorace suke, bude qofar da Bashir yayi da qarfi yasa suka zabura kafin kace meye wannan sun maqalqaleni wani kan wani Jafar yana cewa “kice masa yayi haquri Mami dan Allah karya doke mu”.

Tausayinsu da matuqar takaicin Bashir ya sake qume ni, na daga idanuwana da har sun qanqance saboda kuka na kalleshi yana tsaye shima mu yake kallo, fuskarsa a daure tam haka idanunsa sun kada sunyi jajir har wata jiniyace ta fito a goshinsa. Daga tsayen yace mun “Ina kika saka mun folder dana ajiye akan Gado”.

Ayanda nake jina Banyi niyyar tanka masa ba amma saboda yaran da suke gurin bana so na bada qofar da zamu ringa raba hali a gabansu dan hakan ze shafi tarbiyyar su, “Ina zuwa” nace masa kafin na miqe na kama Aliyun da zuwa sannan jikinsa ya rufe da zazzabi me zafi amma saboda dakiya da taurin kai har sannan ko digon kwalla babu a idonsa.

Dakinsu na rakashi, ina tsaye ya shiga ya watsa ruwa a jikinsa ya fito dakyar ya kwanta akan gadonsa. A cikin first Aid box dinsu na ciro masa Paracetamol na bashi yasha, ina zaune a gefen kansa nace

“Aliyu kana babba kai kake so ka raba kan qannenka ko, irin abinda na koya muku kenan ka tsaya mahaifinka yana fada kana fada Aliyu?”

Se a lokacin ya saka kuka yana cewa “Mami Abbi ya canza wallahi ya dena son mu, da bakwayin fada amma yanzu kullum se sukunyi kuma duk akan Anty Amirah ne. Mami yanzu fa da muna tahowa yana waya da Abokinsa Uncle Bala yana ce masa daman bakya son yarinyar yace ze kawo miki ita kinqi yanzu gashi ta mutu hankalinki seya kwanta ai”.

Shiru nayi ina shafa kansa, wato a gabansu ma ya fadi haka kenan, tabbas shi ya bada qofar da yaran zasu ga baqin sa ko bayan haka yana sane Aliyu ai photocopy dinsa ne daman, duk wani hali daya ke taqama dashi Aliyun ya kwasa harda qari dan badan ma Irinta Allah ya bawa Aliyun a matsayin uwa ba da ba qaramin wuyarsa za’a sha ba.

Numfashi naja kafin nace “koma menene karna sake gani, Abbinku yana sonku ka sani irin son da yakeyiwa Iman, ba fata ba yau ko daya daga cikin mu ya rasa irin damuwar da ze shiga kenan kasan halinsa kuma idan yana cikin damuwa Fada yakeyi da kowa. Dan haka ka kiyaye Aliyu karna sake jin wata magana irin haka kaine babba komai kayi qannenka suna koyi da kai ko so kake Allah yayi fushi daku kuna sabawa mahaifinku?”

Girgiza kai yayi a sanyaye, na ci gaba da cewa “yawwa Haidar dina kar a sake, gobe kuma ka same ahi ka bashi haquri kaji ko dan yanzu dai be huce ba”

“Insha Allah Mami bazan sake ba” ya fada.

“Yauwa Allah yayi muku albarka ya kulamun da rayuwarku”
“Amin Mami, I kove you”
“I love you more” na fada tareda kissing goshinsa kafin na ja masa bargo na fita.

Seda na lallaba sauran suka cire uniform na dora farar shinkafa dan ina da miya na barwa Amna ta duba sannan na tafi dakin nasa.

Ina tura qofar yana sako kai ze fito, ya watsamun kallon banza na mayar masa da martani na shige se ya biyo ni yana cewa “Wato daman abinda kike gayawa yaran nan kenan kina koya musu mugun hali har Aliyu yana fadar na fi son Amirah akan su ko?”

Banza na bawa ajiyarsa, na jawo drawer dana saka folder na dire masa akan gadon kafin na miqe na nufi qofa.

“Ma’u” ya kira suna na kafin yaci gaba da cewa

“Wato Ma’u kin rainani, saboda wulaqanci da rashin mutunchi ina miki magana shine kika sa kai zaki tafi bayan tara yayana da kike yi kina cusa musu tsana ta a zuciyar su ko?”

Tsabar mamaki daskarewa nayi a guri daya na kasa gaba na kasa baya, wace kalar kwaya Bashir yasha ne? Ko kuma rasa Ÿa hauka ne ko a kansa aka fara, kai da alama dai kawai Bashir ya shirya ci mun mutunchi ne idan ba haka ba ya gama jibgar mun Da sannan ya kalleni yace wai ina masa wulaqanci da rashin mutunchi, waiwayawa nayi na gyara tsayuwata sosai ina kallonsa

“Wulaqanci ko rashin mutunchi ba tarbiyyata bane dan da ace na iya da bamu kai shekara goma sha shida tare da kai ba, batun in tara yaran ka kuma in cusa musu tsanarka..” na dan dakata tareda qara taku biyu na dawo gabansa sosai, murmushi nayi me kama da yaqe kafin na ci gaba da cewa

“Base na zugasu akan ka ba, yanda kyakykyawar mu’amalarka gare su ta sa suke sonka haka sababbin halayen daka tsiro dasu zasu bi su goge duk wannan so da shaquwar da kake gani a tsakanin ku, sannan kayi a hankali duk abinda yaro ya gani a gurin iyayensa tarbiyyar da ze tashi da ita kenan musamman kai me Ÿaya maza zasu tashi su zata abin kirki kake aikatawa kaga haka zasu tafi da matan da.....”

“Ya isheki Asma’u” Bashir ya katse ni cikin hargagi tareda daga hannunsa ya nufoni da niyyar mari, sedai ko me ya tuna ya janye tareda kaiwa Bangon dayake bayan mu naushi sannan ya juya ya dafe kansa yana huci kamar wanda ya hadiyi kunama.

Tabbas na tsorata, na kuma saddaqar sheya shararamun mari a yanda ya nufo ni amma taurin zuciya da dakiyar dana dorawa zuciya ta bata sa baki na ya mutu ba,

kallonsa nayi da kallon da ni kaina bazan iya fassara shi ba, na tsana ne ko na takaici da baqin cikin abinda Bashir yakeyi mun nace

“Nima dukana zakayi kamar yanda ka kusa illata danka gashi can kwance, to ka tabbata hakan shine abu na qarshe da kwakwalwarka zata raya maka akaina dan wallahi Bashir sekayi dana sanin dora hannunka a jikina da sunan duka, har Mahaifina ya koma ga Allah ban taba ganin ya dagawa daya daga cikin matansa murya ba ballantana har ya dake su se kai kake tunanin zaka daki yar sa? Toh bismillah” na fada ina zare masa ido kamar wani dana.

Naga alamar se nayi masa haukan gaske sanann ze shiga hankalin sa, wata irin tsanar Amirah ce tayi mun dirar mikiya dan itace sila, ita ta janyo komai da yake faruwa da be aure ta ba da haryanzu muna cikin zaman lafiyar mu da qaunar juna amma tunda ta shigo rayuwar mu abubuwa suke rinchabe mana bamu taba rufa sati ba tareda munyi tashin hankali da Bashir ba.

Shiru mukayi gaba daya, ni ina jiran ya sake wata magana ko yunqurin marin nawa dan wallahi sena gwada masa nima yar buyagi ce yau amma se yai shiru, kiran Sallar Magriba ya sakashi shigewa Toilet ya bugu qofar da qarfin gaske se na bishi da harara kafin na ja dogon tsaki na fice daga dakin.

Seda na tashi Aliyu na sake bashi awa paracetamol bayan yaci abinci yayi sallah kafin bacci ya sake dauke shi, gaba dayan su basu da walwala haka na daure na ringa tausarsu har sukaci abinci sunayin sallar isha kuwa kowa ya nemi makwanci sa har yan biyu da suke qanana sun shiga nutsuwarsu dan Muhammad dayaga Bashir ya fito daga dakinsa ze shiga Kitchen ma kuka ya saka ya rirriqe Jafar.

Ina kallon yanda yai turus yana kallon yaron, duk da fuskarsa bata nuna ba amma jikinsa yayi la’asar daga gani cike yake da nadamar abinda ya aikata amma izza irin tasa bazata barshi aga gazawarsa ba.

Palour na dawo na zauna bayan duk sun shiga daki ina jiran kota kwana, jira nake naji ko Bashir zece na bashi abinci ko ya sake gayamun wata maganar banza a daren nannayi masa wankin babban bargo amma shiru har sha daya ina zaune ban sake jin motsinsa ba.

Dakina na shige nayi wanka, Idona sun soye bana jin bacci dan haka nayi Alwala nayita jera salloli ina kaiwa Allah kukana har seda gabbaina suka gaji kafin na kwanta ina ci gaba da jan carbi.

Nayi niyyar washe garin na kira Amirah da Addah nayi musu gaisuwa amma wallahi na fasa, na kuma shirya duk wanda ya sake bude baki ya gayamun zancen banza a gidan nan bazan daga qafa ba sena gaya masa na wofi.

Da safe ban jira shi ba na shirya yara na kaisu Makaranta a motarsa daya bar Key akan Dining be dauke ba. Tare muka fita da Aliyu bayan na bada excuse din bashida lafiya na wuce dashi Asibiti aka sake duba shi suka rubuta masa magani muka dawo gida.

Ina Kitchen ina dama masa wa Aliyu custard naji fitowar Bashir daga daki, sena dawo bakin qofar na leqa tareda kasa kunne ina jin Aliyun yana gaishe shi, se ya amsa harda tambayarsa yaya jikinsa yace da sauqi.

“Abbi kayi haquri bazan sake ba” naji Aliyun yana fada, se Bashir yace

“Ya wuce Aliyu kaima kayi haquri ina cikin fushi ne na dake ka gashi har naja maka ciwo, kaci abinci muje na kaika Asibiti a duba ka” Bashir ya fada, se Aliyun ya nuna masa ledar magungunan da muka siyo yace

“Mami ta kaini yanzu ga magani ma an bani”

“Ok Allah ya qara sauqi, ka huta sosai kaji bari naje office nakai papers din nan.

“Yawwa yaron kirki ga shi tashi kasha” na fada ina ajiye masa.

Nida Aliyu muka wuni a gidan ya warware har yana tayani aiki munata hirar mu, qarfe hudu har na kira Uber zan tafi dakko yara se gasu sun shigo wai Driver Office dinsu Abbi ne ya dakko su.

Bashir ne dawo gidan ba se 9 na dare, muna zaune muna kallo ya shigo da sallama hannunsa dukka biyu da ledoji, Kallon cikin ido mukayiwa juna kafin na janye nawa ina tabe baki yara suka tashi suna masa sannu da zuwa ya amsa ya basu ledojin hannunsa manya guda biyu ya wuce da qaramar dakinsa.

Be dade da shiga ba ya kwalawa Aliyu kira ya tashi ya tafi sauran suka bude ledojin, tarkace ne kowa Abinda yafi so ya siyo masa, indai yaudara ce ya kware daman, ya zuga rashin mutunchi sannan ya siye ka da abinda yasan kana so. Ina jinsu suna tsallen murna banbi takansu ba.

Aliyu ne ya fito ya debi abinci a plate ya hada da ruwa da cup akan Try yaje ya kai masa ina kallonsa ban ce masa komai ba ya sake dawowa ya debi zobon dana hada ya kai masa.

Da gudu ya fito daga dakin yana tsalle da ihun murna na waiwaya ina cewa “kai meye haka zaka zo kana mana ihu akai”

“Kukalla ku kalla” ya fada yana daga kwalin wayoyi iphone X guda biyu, Amna ya jefawa daya kafin ya zauna cikin zumudi ya shiga bude ta hannunsa.

“Yaya waya aka siya muku” Jafar ya fada yana komawa kusa dashi,

“Wallahi Mamai waya ce, yeee munzama yan gayu muma Faree mun samu tayim snap” Amna ta fada tana daga wayar tata Fara ta Aliyu Baqa. Duk su biyun suka dawo kusa dani suna nuna mun, na karba ina cewa “iye yan gatan Abbi gaskiya kun gode Allah ya sanya Alkahiri ya sa lafiya ta kashe”.

Gaba daya sun cika gurin da ihun murna, sun dade suna nacin a siya musu waya amma yaqi yace se sun gama secondary school idan zasu kira abokansu sedai su karbi tawa ko tasa kowannensu dai yana da Laptop itama dan dokar makarantar suce amma yanzu da yake neman shiri yake da yaran shine ya siyo musu da kansa, Bashir kenan.

Ana tsaka da murnar ya fito da plate din abincin, Jafar ya tashi da gudu ya karbo yana cewa “Abbi mufa, se yaushe za’a siya mana?”

“Ba yanzu ba Sheik baku isa riqe waya ba amma zan chanza muku PS 5 gobe kuma za’a kawo muku” ya fada yana zama akan kujerar da take kallon wadda nake kai. Sabon ihu suka dauka harda yan biyu dan suma sun koya musu Game, ba damar a samu zama a gida anyita buga PS sena gaji wani lokacin na dauke.

Ina kallon yanda yake ta wani murmushi yana jin dadi ganin yaran na murna an shirya kenan, yana kallona na sake hade girar sama data qasa, sen miqe ma ina cewa Farida idan sun gama tura hotunan da sukeyi daga wayata ta miqomun na shige dakina a jikana ina jin yanda ya bini da kallo amma ban waiwaya ba.

A dakin ma ban zauna ba, wanka na shiga nayi shirin bacci, sena dakko Backpack din da nake zuwa office da ita na fito da kayan ciki ina dubawa dan nima ranar Monday zan koma aiki in Allah ya kaimu, gajiya da jiran Farida nayi sena leqa dan ina so na kwanta har sannan suna zaune Bashir na nuna musu ko menene oho a wayarsa.

“Farida bani wayata, bazaku tashi kuje ku kwanta ba ko gobe akwai school fa” na fada daga bakin qofa. Seta taso da gudu ta bani ta sake komawa,

“Oh ina magana duk kunyi mun shiru ko” na sake fada, se Bashir ya dago yace
“Babu aiki gobe Workers day”
“Au toh, seda safen ku” na fada ina juyawa ciki.

Harna kwanta naji message ya shigo wayata, kamar bazan duba ba sedai na janyota, Bashir ne
“Ina son magana dake” ya rubuta. Guntun tsaki nayi na maida wayar na ajiye naja bargo na,

Befi minti uku ba tsakani kira ya shigo, sauri nayi na sakata a silent, ina kallo seda yai kira uku nai likimo abuna dan bazan dauka ba, wato nice baze lallaba ba tunda ya shirya da yayansa shikenan ba ina cikin wannan tunanin naji an turo qofa.

Luqus nayi harda wurga qafa gefe dan fitila a kashe take ni a dole bacci nakeyi, ina jinsa ya kunna hasken ya tsaya akaina yana kallona.

“Ma’u Ma’u” ya fada yana bubbuga pillow da nake kai, senayi miqa tareda qantsarewa ina salati irin an tashen nin nan nayi mici mici da ido ina kallonsa nace “Lafiya zaka zo kana tashina a bacci”.

Seda ya zauna gefen qafafuna ya wani kumbura baki yace “baki ga message dina ba da calls dina ba?”

“A mafarki ka turomun halan” na fada ina tura baki gaba. Se da yayi kwafa sannan yace “saboda abinda ya faru yasa kika dauki fushi dani, naga wanda na doka din ma mun shirya se kece zaki ci gaba da gaba dani”

“Ni kuma inyi fushi dakai ana me Baban Ali space dai na baka ka gama zaman makokin idan ka dangana kayi tawakkali se mu ci gaba da magana” na katse shi ina gyara kwanciya, gajeran tsaki yaja kafin yace

“Oh banida tawakkali kenan”

“Ni awa ince baka da tawakkali, hausa nayi maka bawai abinda nake nufi kenan ba” na fada ina danne dariyar dake neman kufce mun ganin yanda yai kinini da fuska yana jan iska.

“Gobe da asuba zamu tafi Delta inaga zamuyi kwana biyar ko sati saboda tafiyar nema yasa ban tafi Gombe ba”

“Allah ya kaiku lafiya ya dawo daku lafiya” na fada a qagare dan na fara jin baccin gaske, se ya miqe yana cewa “ta so muje can, ban hada kaya ba kuma ina so nayi bacci kinga fitar Asuba zamuyi”.

“Yi gaba gani nan” na fada ina miqewa kamar zan shiga bandaki, yana fita na rufe qofar na murza key, a fili nace “Dan rainin wayo sedai ka tafi babu kayan kuwa” nai hayewata Gado na kwanta ina jinsa yana kiran suna na yana kwankwasa qofar a hankali nayi biris dashi harya gaji ya tafi, duk randa ya koyi karbar laifinsa, ya iaya bada haquri ma shirya.

Please Login or Register in order to submit comment