Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

yanzu yake gano tarin qatuwar wautar daya ringa tafkawa a rayuwarsa. Ya yarda da gaske ya kasance mutum meson kansa, a koda yaushe buqatarsa ce a gaba be taba duba wani ba idan har ze samu abinda yake so babu ruwansa ko wani yaji dadi ko karya ji muddin buqatarsa ta biya shikenan.

Se a yanzuyake tuno tarin sadaukarwa da tarin soyayyar da Ma’u ta shimfida masa, Mace ce da ta yarda tayi Kuka idan harshi zeyi dariya, ta yarda ta rasa shi ya samu bashi kadai ba duk wani wanda ya shafe shi a duniya Ma’u tana rawar jiki gurin kyautata musu.

Ze iya rantsewa cewar hidimar da take da iyayensa da yan uwansa shi da suka haifa baya yi musu kwatanta. Saboda duk abinda zeyi kafin a buqata ita tayi musu da kudin ta da jikinta hidimta musu takeyi.

A lokacin baya idan Ahajin su yana ce masa ya riqe Ma’u da kyau matar rufin asiri ce da samun irinta a zamanin nan yana da wahala gani yake kawai dai saboda makauniyar soyayyar da Baban yake mata ce tasa baya ganin laifinta shi kuwa gani yake kawai tana amfani da abin duniya da take dashi ne ta siye kowa ta yanda babu me ganin laifinta kowa sonta yake yi.

Idan ya zauna ya nutsu tsaf a zaman su ze iya rubuta sau nawa ta taba kawo masa wata buqata tata na wani abin buqata a matsayinsa na mijinta komai yi take tayi masa tayiwa Yayanta ba kuma ta taba qorafi ko nuna gazawa ba duk a lokutab baya gani yake rainin arziqi ne ya saka take masa haka tana ganin ta fishi wadata dan haka bata taba bashi ma damar da ze tabuka wani abu ba a matsayinsa na Namiji, kodaga baya daya samu Chanjin rayuwa bata sauya zani ba.

Taci gaba dayi se iya abinda ya ga kamatuwar ya dakko ya bata ne ze bata ba kuma ta taba qorafi akai kota raina ba ganin cewar yanzu yana da halin yi a maimakon ya gode mata ya jinjina mata se ya sake qullatarta da ganin tabbas ta rigada ta raina shi, duk tarin Arziqin daze samu tana ci gaba da kallonsa a wannan faqirin data aura ta ringa hidima dashi.

Ya kasa ganin haka a matsayin soyayar da take masa ce tasa take tausayinsa ba kuma ta qyashin hidimta masa ta kowacce siga. Bayan duk wannan sadaukarwar daya tashi ya saka mata da Kishiya irin wacce shi da kansa daga baya seda ya ringa jin kunyar abinda ya aikata mata wanda duk yana cikin irin ingiza me kantun da Bala ya ringa masa a rayuwa.

Shiya fara tunkara da batun abinda ya faraji dangane da Amirah ya kuma nemi shawarar sa akan abinda zeyi dan ya hango tarin rashin da cewa a cikin abinda zuciyarsa take niyyar yi amma Bala ya nuna masa cewar ai ba haramun bane. Kuma daya aurowa Ma’u wadda bata san halinta ba ai gara Amirah da take rainonta tasan bazata cutar da ita ba.

Be zurfafa tunani ba dukda wani bangare na zuciyarsa babu yanda beyi ba na hanashi amma ya dage, sanda ya sanarwa da Dada maganar yana ta taraddadin ya zata karbi Al’amarin ganin irin so da qaunar da take tsakanin ta da Ma’un, a lokacin kullum bata da magana seta ya riqe yarinyar nan da kyau yarinyar kirki kullum yaje gidan nan da sabon abun da zata nuna masa tace Ma’u ta kawo Albarka kuwa baya zaton ko su data haifa tana saka musu ita lodi lodi irin yanda take mata amma daya kai mata zancen Amirah se gashi tashi daya ta amince.

Hartana gaya masa sun dade suna son qulla wannan zumunchin dan da Amiru taso su hada su amma halinsu da banbanci zaman bazeyi dadi ba. Shi kuwa daman shine uban riqonta duk wani hali nata tun yarinta daga shi har Ma’un sun sani dan haka babu komai Allah ya tabbatar musu da Alkahiri.

Yasan ya tafka kuskure na boyewa Ma’u zancen auransa da Amirah da yayi amma ta ina ze fara? Bashi da wannan kwaringuiwar da ze tunkareta yace mata zeyi aure kuma Amirah ze aura.

Ya rubuta Text message yafi sau dari amma ya kasa tura mata, daga baya a takadda ya ringa rubutawa yana ajiye mata amma baya qara ko taku biyu daga gurin yake canza shawara ya dauke dan besan a yanda zata karbi Al’amarin ba.

Sanda au Dada suka kawo Amirah gidan shi kansa yaga rashin dacewar hakan se kuma daya nuna musu kuskuren aikata hakan amma suka qeqashe qasa suka ce ya fita a sabgar babu ruwansa dalilin daya saka shi yanke shawarar biya mata umarah kenan ita da yara suka tafi danharga Allah seda abin yazo dab sannan ya qara ganin kuskurensa.

Babu kuma yanda beyi ba akan afasa amma Su Addah suka ce ata fau babu wannan zance, karshe ma daya matsa seda Dada tayi masa barazanar tsine masa idan ya kuskura ma zancen yaje kunnen mahaifinsa na cewar ya fasa haka ta kuma yiwa su Naziru barazanar da karsu gayawa Ma’u dan daman a wani kalar munafunci suka qulla zancen auran ta yanda hatta da mutanen gari an bagarar dasu kowa se a bazata abin yazo masa bayan da aka daura se gashi tun ba’aje da nisa ba yake karbar sakamakon sa da hannun haqu.

Kyale kyalen daya rude shi ya aurota ashe duk buge ne, matar da yake zaune da ita shekaru Goma sha ta fita ta kowacce siga, shi baze iya cewa ma yau ga wata tsiya daya tsinta acikin auransa da Amirah ba banda tashin hankula da damuwa da take jefashi aciki kala kala qarshe tayi masa me dungurungun, sukayi amfani da halinsa na daukar zuga da zuciyarsa me cike da izza suka raba shi da matarsa da ta so shi tsakani da Allah tun bashi da abinda ze saka a so shin.

Gashi yanzu yanaji yana gani tayi masa nisan da har Abada se dai Idan wata da wata gagarumar qaddarar a gaba ko rabo me tsananida ze sake dawo masa da Ma’u cikin rayuwarsa amma ya tabbata ko haukacewa Yusuf yayi baze sako masa Ma’u ba.

Kai shi shaidane tun a wancan zamanin cikin samarin da sukayi takarar neman auran Ma’u dasu babu wanda yake tsananinsonta saboda Allah kamar Yusuf, a gabansa ta kore shi wanda yake da yaqinin shine haduwar su ta qarshe a wancan lokaci ya kuma tafi bayan yace mata

“Idan har rabuwata dake zesa kiyi Farin ciki Asmy wallahi bazaki sake ganin fuskata ba. Da ina da dama ko me irin sunana dana hana kunnuwanki jinsa saboda kar hakan ya ringa tuno miki dani a rayuwarki ranki ya baci, amma ki sani ina qaunarki saboda Allah kuma bazan cire tsammanin samun ki a rayuwata ba se randa na farka na ganni a cikin kabari tukunna zan haqura dake”

Shiyasa tun daga lokacin kai ko me suna Yusuf yaji an ambata seya tuno shi yana matuqar baqin ciki da kishi da irin qaunar Ma’u dayake gani a cikin idanun sa wanda a haduwar su ta farko bayan shekaru goma sha bakwai ya sake ganin wannan tarin So da Qaunar tata a idon Yusuf, a yau daya sake haduwa dashi kuwa ya tabbatar da ze iya aikata duk abinda ya fada akanta dan ba qarya yake ba yana Son Asma’u, irin son da tayi masa yanzu gashi Allah ya bata wanda yake mata kwatankwacinsa itama.

Seda ya share hawayenda suka ziraro masa kafinya saka hannu ya janyo wayarsa tare da hotonsa da Ma’u da yake kan durowar gefen gadonsa. Hoton ya fara zarewa daga jinin Katakon da yake ya zura mata ido yanda tayi kyau tana wannan murmushin nata da yake nuna irin kyan zuciyar da take dashi se yayi saurin yin a’uziyya tunowa da yanzu fa matar wani ce ba tasa ba.

Durowar ya jawo ya saka hoton tareda katakon, zuwa gobe da safe duk ze fito dasu ya bawa Aliyu dan idan ya barsu tare dashi tabbas baze samu kwarin guiwar chanjinda yake so ya kawo a rayuwarsa ba. Ze cigaba da dakon sabon zunubi ne na kallo da kuma tunanin matar da bata sa ba a yanzu.

Hotonta da yake kan wayarsa ya sauke ya mayar dana yaran da suka dauka wannan qaramar sallar data wuce gaba dayansu wani tausayin su yana ratsa shi musamman Yan biyun sa yanzu duk shine silar komai, ya janyo musu zasuyi rayuwa ba tare da uwar su ba Alhalin tanada ranta ba mutuwa tayi ba.

Doleya jajirce ya inganta rayuwarsu baze bari suyi kukan rashin uwaba dan a yanzu shi kadai ne gatan da zeyi musu, ya koyi darasi daga abinda ya same shi na rayuwar auran sa da Ma’u in sha Allahu kuma ze dauki dangana ze kuma jajirce ya gyara rayuwarsa.

Duk abinda ya zama silar jefa shi a halin da yake ciki yanzu ze kiyaye shi hakan ya zamar masa izina ba kuma ze sake bari ya maimaita kansa ba amma anya ze samu chanjin rayuwa da Mace irin Amirah??

“Kaima kana da taka gudummawar daka bayar gurin lalacewarta ta zama duk abinda ta zama a yanzun” zuciyarsa ta raya masa kuma ya yarda da hakan sannan ya dauki turbar gyara ze yi iya qoqarinsa na ganin ta dawo hanya su lallaba rayuwar su a haka tunda basu da yanda zasuyi da Junansu.

Washe gari kafin Aliyu su tafi makaranta seda ya tabbatar daya ajiyewa Bashir kayan karyawa da magungunan sa akusa dan se da yayi sallar Asuba sannan bacci ya dauke shi dalilin sabon zazzabin daya rufe shi.

Se gurin sha biyun rana ya fito daga dakinsa bayan yayi wanka ya shirya kuma Ahamdulillah ya samu sauqin takurar da zuciyarsa take masa dan yanzu kam ya tabbatar daya rasa Ma’u, duk da baya son ko tuna abun saboda wani daci dayake taso masa kansa yayi zafi har duhu yake gani yana gilma masa duk sanda ya tuna a gabansa jiya wani ya rungumeta kuma yayi kissing nata.

Cikin sanyin Jiki ya fita falo ya zauna, gidan shiru babu Addah babu Amirah yanda kasan ma basu san a halin daya shigo jiya gidan ba cikin su babu wadda ta sake leqowa bare taga yana da rai ne koya mutu.

Yana zaune akan kujera bayan ya kunna Tv ya kai tashar Sunna Tv akaci sa’a Malaminda yake wa’azi a lokacin yana magana ne akan Aureda haqqoqin da suka rataya a kan Miji da Mata.
Nutsuwa yayi sosai yana saurara yana qaruwa da abinda ake fada a ciki. Kusan minti sha biyar da zaman sa sega Amirah ta bude qofar dakinta ta fito.

Turus tayi da ganinsa, cikin wayancewa ta qarasa tana dan sosa kai idonta akan hannunsa da aka nade da Bandeji ta shiga gaishe shi ya amsa mata ba tareda ya kalli inda take ba.

“Uhm daman yanzu nake cewa zan shiga na dubaka, wallahi jiya ina gama shiryawa bacci ne ya kwashe ni shi yasa ban shigo ba” ta fada tana sunkuyar da kai.

“Babu komai ai, ya naki jikin?” Ya tambayeta yana dan kallonta. Cikin mamakinsa dan tayi zaton ze balbaleta da fadane yanda ya saba tafe

“Lafiya lau ai babu abinda yake damuna yanzu”
“Masha Allah, Allah ya qara lafiya. Ina Addah bata tashi bane?” Ya sake tambayarta

Kafin ta bashi amsa Addah ta fito daga daki tana mita
“Ni wallahi na gaji da wannan rayuwa haba gida kamar gidan Haya dan jaraba abinda zaka ci ma seka tashi ka dorawa kanka, naga ni dai zuwan da muka tabayi ba haka aka mana ba Alqur’an Asma’u kafin mu tashi daga bacci yarinyar nana ta hada mana abin karyawa kala kala haka kan ya gama narkewa na Rana ya sauka ga kayan dadi tuli, kai Allah dai ya jiqanta badan ta mutu ba yanzu gashi dan daka haifa ne yake maka baqin ciki kar kaci me kyau shikenan ai nima kwadayina ya zaunar dani”.

Daga Bashir har Amirah babu wanda ya kulata, ta samu guri kusa dashi ta zauna tana cewa
“Au Bashir ya jikin naka? To Allah qara kiyayewa halan Sabon Mijin nata garjejen qato ne kaje ya hada maka jini da majina? Kaima maganin ka kenan ai da naci mace tayi auranta seka qyaleta ai, ni da zaka ji ta tawa ma da ka hada mata yayanta ka bata kasan riqon dan yanzu se uwarsa musamman wadannan marasa mutunchin gara dai can suje su qarata da uwarsu”.

Seda yayi qoqarin gaske ya hadiye bacin ransa kafin cikin dakakkiyar Murya yace mata
“Daga yau gaba daya yaran zasu dawo nan gidan dan haka dole a canza tsarin komai da akeyi kamar girki da sauran abubuwa. Sannan zuwa qarshen satin nan seki shirya komawa Gombe tunda komai ya daidaita”.

“Bangane na koma Gombe ba? Munyi dakai daman idan nazo zan koma ne?” Ta fada tana zate masa ido. Se ya dago ya kalleta dakyau yace

“Ban gane ba, da kinzo gaba daya kenan bazaki koma ba ne?”
“Yo ga amsa nan ka bawa kanka in koma Gombe nayi me? Uwar wa n ajiye a can ko kuwa so kake naje ayita nunani tsofai tsofai dani ana zawarci nake to ba inda zani, kuma koma ba haka ba daga haihuwar tata kwana biyu zaka ce mun na tafi uban waye ze gyaramun yar? salon ta lalace ka sako mun ita na shiga uku to ba inda zani zama daram me naquda ta samu kayifa”.

Shiru ya mata ya ci gaba da istigfarin da yake a zuciyarsa yana kallon Program din da ake a Tv, ta ringa Tijararta wai dan yar uwarka ne yake maka haka, ita dai bata san me tayi wa Nafi data saka yayanta suka raina ta ba idan ba haka ba ko arziqin surukuta ai ya isa ya ringa daga mata qafa idan Nafi ce ze koreta daga gidan sane.

Shidai kamar meyi da dutse har tayi ta gaji tafi ki mutu be ce mata ba dan kanta tayi shiru, se kuma ya dawo zancen tana so ya saka akaita kasuwa akwai abubuwan da zata siyo na amfanin Jegon Amirah. Ganin bazata barshi yayi jinyar zuciyarsa ba yasa ya tashi ya bar mata falon ya koma Daki, babu bata lokaci yayi musu Booking din jirgi su uku shi, Addah da Amirah ranar Juma’a zasu tafi Gombe idan yaso taje cab tayi jegon idan ta gama ta dawo.

ASMA’U

“Yusuf ka bari dan Allah” na fuzgo kalamandakyar ganin dagaske so yake se munyi abin kunya a gaban yara. Saki na yayi ya zauna akan kujera yana qaremun kallo yanda jikina yake rawa kamar wata wadda aka kama tana mugun abu seya saki murmushi me sauti ya miqo mun hannunsa na dama alamar na taho na maqale kafada kamar wata qaramar yarinya ina sakar masa harar da se yanzu na samu ido na ya tuna yanda akeyi ta.

“Ni kike harara ko ki bari na taso sena cinye idonki idan yaso naga da abinda zaki sake hararta ya fada” yana yunqurowa kamar ze tashi ai kuwa na kwas nayi dakina da gudu na rufo qofa seda na jingina kafin takaicin kaina ya kamani, meye haka nakeyi? Ni da ya kamata na fututtuke na nuna masa bacin raina akan me ze saka a daura mun aure ba tarefayarda ta ba shine duk zanbi na wani rude daga ya dantaba ni sekace wata kwaila aikin banza kai.

“Asmy ki bude ina muyi magana” na jiyo yana fada bayan daya kwankwasa qofar a hankali.

“Bazan bude ba ka kuma fitar mun daga gida kaima malam” na fada a tsiwace.

A zatona ze fara roqar na bude qofar ko wani abu se ji nayi yace
“Shikenan toh se anjima” ya fada ba tareda wata damuwa ba kafin nayi wani yunquri najiyo qarar bude qofa da rufewa, se nayi saurin matsawa jikin window na daga labule ai kuwa na hango shi ya shige mota Driver yaja sun qara gaba.

Wani qululun baqin ciki yazo ya tsaya mun a wuya, farawa da Bismillah saboda an bashi aurena a wulaqance shine ze fara wulaqanta ki ya nuna mun cewar su Maza duk halin su daya na wani ne kawai ya fito fili. Idan kina kasuwa kamar zasuyi miki sujjada tsabar tarairaya daga inda kika zo hannu ke da bola banbancin ku kadan ne, se kawai na nemi gefen gado na zauna na fashe da kuka.

Ba laifinsa bane laifin yan uwana ne su suka ja mun da suka nuna masa neman kai suke dani. Wayata ce ta dauki qara na janyota da sauri ganin Yusuf ne yake kira

“Bada amincewata aka dauramun aure da kai ba kuma ni dana ce ka tura ma wasa nake maka saboda kawai na bawa Bashir haushi ne amma shine kaje ka saka aka daura mana aure ko to ni bana so babu kuma wanda zeyi mun dole dan haka ina jiran ka ka dawo ka sawwaqe mun” na fada cikin kuka bayan dana daga wayar.

Shiru yayi na kusan minti biyu dan na zata ma ya kashe wayar kafin naji ya fara magana cikin sauti irin can qasan nan yace

“Nima ban san haka zata faru ba dana dakatar dasu saboda bazan aure ki ba tareda ke da kanki kin yarda ba, sannan ko a yanzu bazan matsa miki ba Asmy, daga nan har zuwa shekara daya kina da dama idan har kika ga bazaki iya zama dani ba zan haqura na sallameki saboda ni ba maye bane da zan auri mace dole bata sona bayan ga masu sona nan birjik a gari suna neman na aure su.

Sannan kuma ina tabbatar miki tunda kika koreni bazaki sake ganina a gidan ki ba idan har ba ke kika gayyatoni da kanki ba. Daga qarshe abinda na kira na gaya miki shine yanzu da da ba daya bane kina amsa sunan MATAR YUSUF ne, ban yarda da fita barkatai ba tareda dalili ba, ki tabbatar duk Namijin dana samu labari kin tsaya kuna maganar da bata aiki dashi ba ko wanene kome kuka hada dashi indai ba jini ba sena dauki mataki akai.

Duk abinda kike da buqata ki turamun da saqo ban yarda ko man mota ki siya da kudin ki ba, idan na samu jirgi zan juya Abuja yanzu idan ban samu ba kuma se gobe da safe” yana gama fada qit ya kashe wayarsa.

Sororo nabi wayar da kallo, Yusuf dai dayake bina yana lallaba ni kamar kwai yau shine yake mun magana cikin isa da bada umarni haka? Ni Asma’u yake cewa baze sake zuwa inda nake ba sena neme shi to na neme shi yayi mun me? Ta yaya ma yake zaton ni zan kai har tsahon shekara da auransa akaina wannan ma zance kawai yake yi ze kuwa san dani yake dan da kansa ba se kowa ya aiko shi ba ze aiko mun da sallamata.

Tunawa da banyi sallar Isha ba yasa na tashi na shiga na dauro Alwala, har na saka hijabi Bashir da jinin dana gani yana zuba a hannunsa ya fado mun se nayi saurin bude qofar dakin na fito daidai sanda Amnah take goge gurin Aliyu kuma ya tattare fasassun Gilasan ya zuba a abun shara.

“Kayi a hankali kar ka jiwa kanka ciwo” na fada ina kallonsa wani tausayinsa yana ratsani dan har ga Allah duk ciki nafi tausaya masa, kamar shi kadai ne ya damu da halin da ake ciki daga kan Jafar zuwa qasa hidimar su kawai suke karma shi Jafar din yaji labari sam na rasa ina wannna qulafucin uban da yake dashi a da? Gaba daya yanzu sabgarsa yake kamar ma ya manta da cewar Bashir ne ya haife su.

Daki na koma na tayar da sallata, seda na idar da shafa’i da wutri na dade sosai ina Addu’a kafin na shafa na tashi ina jina wata iri wai fa a karo na biyu wasu igiyoyin auran sun sake hawa kaina na wani mutum daban ba Bashir ba.

Ina kwance lamo akan gado na tunanina ya kasu gida da yawa, sabuwar rayuwar da nake shirin fuskanta, yaya matsayin aurena da Yusuf yake in karbe shi ne ko kuwa nayi abinda zuciyata take ayyana mun na tilasta masa har seya bani takadda ta amma wai a wanne dalili ma zanyi haka?

Zuwa yanzu idan nace bana son Yusuf har cikin raina nayi qarya dan daman tun Asali ba son sa ne banayi ba, soyayyar da nake yiwa Bashir ce ta shafe ta kowa da har na gaza gane menene so in dai ba akan abinda ya shafe shi ba.

Addu’a dai nayita nasa anyi mun duk akan neman zabin Allah yanzu wannan Al’amari ya kasan ce a haka idan naja dashi ai ya zama butulci ne ga Allah na kuma ja da lamarinsa kenan tabbas baza tayi mun kyau ba idan Allah ya barni da zabi na ina ma da tabbacin idan na kashe auran da ko kwana daya beyi da dauruwa ba zan sake samun wanda ze so ni tsakani da Allah ne harya aure ni?

Wai meye ma laifin Yusuf ne? Koda yake tarihine yake maimaita kansa irin haukan son da nayiwa Bashir ne ya ringa yankwana ni na nace ma liqe shine yanzu Yusuf yake gwada mun na samu dama nima zan shuka tawa tsiyar amma fa banga alamar shi ze jure irin wulaqancin dani na shanye a tawa soyayyar ba, koma dai yaya ne har yanzu ina a kan Batu ma neman zabin Allah, idan aure na da Yusuf Alkahiri ne Allah ya zaunar damu ya dawwamar da farinciki a tsakanin mu har qarshen rayuwa.

Washe gari dole na shirya fita aiki saboda ina da presentation da zanyi yau na wani project, tareda yara muka fita saboda Aliyu ya gaya mun Abbinsu yana kwance bashi da lafiya, na tausaya masa amma abin mamaki banji irin wannan rudu da tashin hankalin da nake shigaa duk sanda wani abu ya samu Bashir ba. Kai gaba daya yau ma ni a karon kaina naji chanji.

Wata kamala naji ta lullubeni, a gurin saka kaya ma yau seda na chanza shigata. Doguwar rigar Atamfa na saka sakakkiya na yafa yalwataccen mayafi daidai da turarena wasu nayi amfani dasu daban irin wanda se mun samu kusanci sosai da mutum sannan zeji qamshin su sabanin kwanakin baya da nake fesa kwalliya ta daukar magana idan zan fita aiki.

Seda na sauke su a makaranta wani tunani ya fado mun, koba komai Yusuf matsayin miji yake a gurina yanzu, Allah babu ruwansa da ina sonsa ko bana sonsa matsayi da hukuncin sa daya ne akaina. Wayata na janyo na tura masa da saqon cewar na fita aiki sannan na biya na sauke yara a makaranta.

“Se bayan da kika fita sannan zaki sanar mun babu komai na yafe miki, kiyi aiki kadan karki wahalar mun da kanki. Yanzu nima zan wuce jiya ban samu jirgi ba, Love you” ya dawo mun da amsa.

Murmushi nayi dan a yanda muka rabu jiya na zata ko ze amsa ni zanga fushi a cikin maganar sa, fatan sauka lafiya na masa na tura se kawai na kashe wayar gaba daya dan bana so wani ya kirani akan maganar auran nan, tun jiya da mukayi magana da Alawa ban sake daga wayar kowa ba dukda se kirana suke nasan wulaqanci ne zasu mun ba wani abu ba dan Khadija harda tura mun saqo wai naqi Allah yaso da baqin ciki se ya mutu ku jifa dan Allah.

Sanda na shiga office dina seda mamaki ya kusan kashe ni ganin yanda akayi wa gurin kwalliya da ballons kamar wanda za’ayi wani qaramin party. Akan teburina naga kati me azabar kyau an rubuta
‘Happy married Life Mrs Asma’u Yusuf Wunti’ da mamaki na kalli sakatariyata data shigo tana dariya kafin nayi magana ta rigani da cewa

“MD dakansa ya saka akayi tun jiya da baki shigo ba, shi ya kawo mana labarin kinyi aure mutane se mamaki suke yi wai dama baki da aure mudai bamu cewa kowa komai ba. Gaskiya na taya ki murna Madam kowa kika aura yana sonki dagaske wallahi Allah ya baku zaman lafiya”.

Kasa ce mata komai nayi dan bakina ya mutu da mamaki haka na karbi System dina data gama gyaramun aikin da zan gabatar muka fita. Duk inda muka wuce taya ni murna ake har abin ya

Please Login or Register in order to submit comment