Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register

“Malam ai ta fita gidan suna itama kuma ka tafi da muqullin shagon ai”
“Anyi haka ya fada yana bude musu kofar suka shiga gaba daya, bayan sun zauna Me Napep yace bari yaje daga waje idan sun gama shima se yazo a bashi taimakon kasuwa.

Malam ya jawo faranti me dauke da yashi ga kuma carbi me dubu ya hau ja yana muimui da baki nan kuma yana faman zane zane sannan ya dago ya kalle su “toh hajia dawa Zamu fara?” Ya tambaye su.

Hajia Balaraba ce ta fara matsawa tace “Malam ni matsalar kaina ce a fara dani dama..” se ya dakatar da ita, “ki bari mu duba abunda bamu fahimtaba se kiyi mana bayani da kuma matakin da kike so a dauka.

Tiryan tiryan ya ringa jera mata zance kamar me gani a film kai har abinda basu fada Me Napep yaji ba seda Wizy ya canka ya fada se kuwa tace kai Malam aikuwa hakane wallahi, yana ta tiqar dariya a qasan ransa to ai labarin duk daya ne dukma wadda tazo indai akan kishiya ne banbancin basu da yawa. Seda ya gama ratta ba mata zance Adda da me gefe ta gama yin Ammana sun zo inda zaa magance musu matsalar su harta gama Ayyano Yanda zasu juya Bashir kaman Tanda a waina.

Tsaf Hajia Balaraba ta gama gaya masa yanda take so ayi nan kuwa ya yanka mata 50k babu neman ragi ba komai ta cake masa su to taji sauqi akan ubannin kudin data ke kashewa babu biyan buqata. Allonsa ya jawo da tawada ya hau rubuta abunda in zaka kashe shi be san menene ba ya gama ya miqa mata da kwano da ruwa yace ta wanke idan taje gida ta guntsi rabi ta fesa a kofar dakin kishiyar ko inda tasan zata taka rabin kuma ta kuskure baki ta zuba a miya kowa na gidan yaci to daga nan babu me jin maganar wani se tata.

Wasu qullin Jan Maganin da kore ya sake dakkowa ya bata su kuma yace ta ringa jiqawa kwana 7 tana sha sannan ya qara mata da wani kuma a jarkoki guda biyu yace ta juye a bokiti ta qara musu ruwa ta ringa sha shima mijin ta san yanda zaayi yasha koda tea ne ta dafa masa dashi sauran aiki kuma karta damu zeyi daga nan shidai idan buqata ta biya kar a manta dashi (kuji dan banza 😂😂Koren Magani na sabara da Jan magani yake ba wa duk wadda tazo se na cikin jarka kuma maganin Basir ne ko banza ai ya temake so ko 😂😂😂😂😂😂).

Adda ce ta matso aka buga mata nata duban se ya kalleta “Wace Mace ce haka gata nan dai Fara kyakykyawa kamar ma bata da lafiya tana gadon Asibiti”
Ai caraf ta amshe “Asma’u ce ita ce kishiyar yar tawa” gyara zama yayi yana ayyano yanda ze tatsi matan nan yace
“Kamar a kudu take fa wannan kai” se yai shiru kafin ya ci gaba
“Tab di hajia akwai babban aiki a gabanki fa dan koma wacece wannan tasha kan shi wannan mutumin sosai dan kuwa Arnan kan dutse ne suke mata aiki an hada shi da gungun Aljanu suna gadinsa gaskiya wannan aiki yafi qarfina”

“Ai Adda kamar zata rushe da kuka tace “haba Malam ba abinda ya fi karfinka ai (haba Adda Allah ne kadai keda maganin komai) ka duba ka taimakamun nidai a tarkato mana hankalinsa ai ko baya auran yata ni me tsayawa na nema masa taimako ce tunda dana ne ai dan yar uwata”.

Zama ya gyara yace “abinda kamar wuya gaskiya kin san aiki da kafiran Aljanu akwai wahala amma in zaki saki kudi ayi musu yanka kinsan su jini suke so to wala Allah a dace”

“Malam indai zaa samu biyan buqata ba matsaka yanzu kamar me zaa yanka?”

“Gaskiya hajia a qalla za’a yanka musu raguna 20” seta dafe qirji tace Malam ina zan samu kudin nan yanzu fa nake maka bayanin na biyan bashi ma nake nema ni a fara rufemun bakin matar nan ma tukunna ta manta da zancen kudin”.

“Wannan duk ba matsala bane kuma zaki iya ringa bayarwa a hankali ai in kin so ma kiringa yankan da kanki amma akwai kalar dabbobin da ake so da kuma abinda ake fada in za’ayi yankan in kina da wanda ze miki duk sena gaya miki ai”

“Aa malam zaa mata komai anan” Hajia Balaraba ta fada
“To ba matsala”
“Kamar nawa kenan Malam” ta tambaya

“To akwai qauyen dana ke siyo dabbobi ana samun qosashshen rago dai daga dubu Arba’in kinga a qalla guda koma dubu Dari hudu kenan amma zaki iya ringayi a sannu in so samu ne dai cikin wata biyu a kammala aikin”.

Nan dai Adda ta zazzage masa dubu tamanin kudin data harhada zata rage biyan bashi tace in an kwana biyu zata kawo abinda ya samu, ita be bata komai ba se wani abu kamar goro yace idan matar tazo ta saka a bakinta ta ringa taunaqmwa tana mata magana kamar remote haka zata controlling nata aikin Bashir kuma Wannan Ze duqufa yai tayi itama Amira jin tana da ciki ya nemo wani garin Maganin zaqi dana sanyi da aka aike shi ya kaiwa Yayar sa da take da ciki ya bata yace ta kai mata tayi tasha zuwa sanda Bashir zezo daya kwanta da ita anci rabin aiki.

Kamar wanda yai musu kyauta suka ringa zabga godiya ya basu Number wayar sa suka fito Me Napep har ya gaji bacci ya dauke shi fitowarsu ta farkar dashi,
“Gaskiya kun dade hajia yau balance kawai zaku bani na maida Machine din nan na huta dan har na gama gajia” ya kunna suna shirin tafiya har sun ja Iliya ya tsaidasu akan Malam yace ya manta da taimakon kasuwar ne, se suka koma ya barsu a cikin mashin ya shiga.

Be zauna ba 40% 60% suke raba duk abinda suka samu Wizy se dauki 50% ragowar 10 ya bawa su iliya da sauran masu yi musu cover a harkar, cas ya cake masa kudin sa tareda bashi wata qatuwar takadda da aka nade kamar laya yace zasuyi waya ya fito, ransa fes suka kama hanya bayan ya saqala Takaddar a gaban mashin wai ta kiran customers 😂😂 ikon Allah kuwa duk inda suka gifta se an tsaidashi yace drop ne har ya ajiye Hajia Balaraba ya wuce Da Adda Fatu dan tace gara taje ta kai mata ta fara sha tunda yau Alhamis a qa’ida gobe Juma’a ze zo

To se muce Allah kauda tsautsayi da Asara 😂😂😂😂https://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS

🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟

Na Maryamah_Mrs AM
(Marubuciyar Rubutacciyar qaddarah)

Page 6

Da Isar Adda gida bata ko zauna ba ta jiqawa Amirah maganin da aka bata tace gashi nan tayi tasha Zuwa goben sega yanda za’ayi.
“Adda kin ganin ze zo ne ko kin manta yanda mukayi dashi jiya da daddare” Amirah ta fada cikin sanyin jiki.

“Ke dallacan barshi ai idan be zo bama baze samu nutsuwa ba saboda sabon malamin nan da muka samu da zafin sa in gaya miki kedai kakarmu ta kusa yanke saqa, ai da lamarin ki sun gama daidaita zan juya kan wannan me baqin jinin itama ai taimaka a samo mata wani zaman ya isa haka” ta fada tana Kallon Ummi. Se Ummi tai zarab ta miqe tana cewa

“Wa ni wallahi na yafe dadai irin Auran Amira kullum kina tafe ba biyan buqata gara in zauna banyi ba duk randa kika gaji kya barni na Auri Auwalu da nake so yake so na”.
Mafice Adda ta cilla mata tana auna mata Ashar
“Shegiya da bata gaji arziqi ba da dai wallahi ki auri wannan faqirin gara kiyi ta zama ina kallonki ba auran, duk yayan gidan nan wa kikaga ta auri ko Malamin Jami’a bare malamin makarantar primary”

“Wato Fatu bazaki dena yin munanan kalamai akan Yaran nan ba ko? Amma ki ci gaba ai kina gani Idan Alkahiri kike shukawa kanki koma akasin haka” Alhaji Murtala da basuji shigowarsa ba ya fada, be ko qaraso ba ya juya kawai dan yasan wani qarin bacin ran ze jawa kansa. Tun kafin ya fito da safe ta bar gidan haka duk a kunnensa Indo Tazo tayi tijarar ta dakyar Yaran gidan Maza suka lallaba ta ta tafi dan shi qin fitowa yayi. Ya gaji da halin masufar da Fatu take jefashi a kullum shi be san Adadin bashin daya biya mata, idan baazo yau ba gobe se anzo to ya gaji.

Yanzu ma maganar ya shigo ya mata akan ta nemi kudin matar ta bata idan ba haka ba tace gobe idan ta dawo da police zata zo to wallahi sedai su kulleta dan shi sisi baze sake biya mata ba ai badan ita kadai yake nema a rayuwarsa ba.
Adda kuwa ko a jikinta ta cigaba da gayawa Amirah yanda sukayi da malami da kuma tabbacin da ya bata da an gama ai Bashir ze dawo hannunsu.

“Amma fa Adda ni bana yarda idan akace wai Anty tana wa Yaya Bashir Asiri ke kanki Adda kin san ba haka bane”
Hararar ta Adda tayi kafin tace “Ji banza, idan tanayi se tace miki zata fito fili a sani ne? Ko kuma ace da batayi to daman me zatawa Asirin bayan kusan ita ce Mijin shi Matar yanzu kuwa daya bunqasa ai bazatayi sanya wata tazo ta taya ta ci ba. Ni in zaki karbi abu kiyi kawai kiyi kafin ki fara saka wasiqasi ki bata mana aiki dama ni ina zargin bakyayin yanda akace shiyasa komai baya tafiyar mana daidai to ke kika sani wallahi kina ji kina gaji zata kado ki waje ki dawo mujere ana mana Dariya” da haka ta shige dakinta dan yin Sallar Azahar da La’asar da suka sameta a tafe ga Magriba an fara kira.

Amirah ma jiki a sanyaye taja jug ta fara bankawa cikinta ruwan magani dukda qasan ranta bata jin Bashir zezo wannan satin amma dai gara tasha saboda tsaro se sannan ta tuna bata gayawa Adda yanda a ka qare da Indo me kaya ba, ta cicciba zuwa dakin Addan ta tarar tana sallah se itama ta wuce nasu dakin dan yin Sallar.

WASHE GARI
Qarfe bakwai a qofar gidan tayiwa Indo ta shiga biga gate baji ba gani dan ta rantse wallahi yau ko ita ko Fatu a garin nan ita zata rainawa hankali lallai bata san wacece Indo ba. Alhaji Murtala da fitowarsa kenan ze tafi wata Jana’iza ya qarasa ya cire sakata ta hankado qofar saura qiris ta bige shi tayi ciki abunta se kawai ya girgiza kai tareda juyawa ya kunna motarsa, Aminu daya daga yaran gidan ya qarasa bude masa gate yai ficewarsa dan bama ze tsaya yaga yanda zata kaya ba.

Adda Fatu da tunda tajiyo bugun ta janyo abinda Malam Wizy ya bata ta bantara se taga kaman Namijin Goro amma kai bashi bane qila kama ce ita dai ta afa baki ta hau tauna harda guara zama akan kujera tana jiran shigowar Indo se kuwa gata kaman an jefota ta fado.

“Fatu bani kudina kafin na yaga miki rigar rashin mutunchi a unguwar nan” ta fada tana huci, se Adda ta miqe tana qara bantarar magani ta tauni ta nufo Indo tana cewa
“Ke Indo fita ki tafi karki sake dawo wa gidan nan ki manta da zancen bashi a tsakanin mu har abada idan ma da wasu kudin a jakarki yanzu cirosu ki bani”

“Fatu hauka ne ya sameki ko to bari kuwa yanzu zan sauke miki shi wallahi ina batun ki bani kudina kina min wata maganar banza harda in qara miki wasu to bari kiga” Indo ta fada tana ja baya ganin Adda ta nufo ta tana sake maimaita kalamanta se zare ido takeyi ai bata yi aune ba se Ji tayi Indo ta dauke ta da wani gigitaccen mari daya sakata furzo da goron ba shiri ta kife gurin tana kururuwa dan ji tayi kunnenta, indo bata haqura ba ta sake kai mata Mahangurba a hanci aikuwa take ya fashe ya fara bulbulo da jini sannan ta bita ta turmushe ta hau duka, Adda ba hakin kwace wa se ihu take tana neman dauki.

Kishiyoyinta uku duk suna tsaye a bakin kofa da yayan su mata ransu qal akan wannan abu se Ummi da Amira a gefe suna taya ta ihun ba damar kai mata dauki 😂. Se da tayi mata lilis sannan Samarin gidan suka kawo taimako dakyar aka kwaceta Indo na jaddada mata wallahi ko kudinta ko kuwa kullum seta zo ta nada mata na jaki dan ta bar maganar police ma da kanta zata kwaci kudinta sannan ta fice daga gidan.

Adda fuska tayi luhu luhu se hawaye da ajiyar rai take ga hanci ya fashe a ranta Allah ya isa take jerawa Malam Wizy akan wannan abu daya bata gashi nan ba biyan buqata se bugu data sha a banza, bari Suga na Bashir idan taga ba nasara dole ta koma ya biyata kudinta dan bazata dauki asara biyu ba. Ita se yanzu ma taji wani tsautsayi ya kaisu yarda da Dan Napep din nan? Anya ma ba hadin baki bane shida Hajia Balaraba suka kaita a cinye mata kudi amma ai itama Balarabar ta bayar. Bari tayi ta kanta yanzu zata kirata taji yanda akayi. Ummi ce ta kamata ta kaita daki ta hada mata ruwan Me zafi a toilet ta shiga dan gasa jikinta, dakyar ta iya watsawa ta samu dai Habon ya tsaya ta dauro towel ta fito ta haye gado kan kace meye wannan zazzabi ya rafke ta se rawar sanyi take.
(To Adda Allah ya qara lafiya ya kiyaye na gaba 😂😂😂😂).

Kafin yamma dai jiki ya qi dadi dole suka kaita asibiti tasha Allurai suka dawo da magunguna gashi har sannan babu Bashir babu labarin sa kuma ta kira Dada ma wayarta a kashe, kukan baqin ciki ta fashe dashi da tsoron haduwarsu da Indo gobe.

Mu koma Lagos

Qiri qiri Asma’u ta qi bari a sallameta acewarta se tayi sati, Dr beqi ba tunda sabga ce ta kudi qaruwar su ce dan haka yace wa Bashir dole ta zauna suyi monitoring Bp nata na wani lokacin kafin a sallame ta. A kwana biyun nan idan kaga Bashir se ya baka tausayi yanda yayi wurjanjan dashi har a office an gane bashi da nutsuwa dole suka bashi leave na 1 week saboda ya samu ya kula da yaran kafin a sallami Asma’u, sauqin sa daya yaran sun rage kokekoken tunda kullum yanzu da safe ze kai su da daddare ma su koma.

Shi ya ma manta da wata Amirah sam bare zancen zuwa Gombe yau ranar Sunday kaman yanda ya saba bayan ya kawo yaran, suna gurinta Abokinsa Abdurrahman da Matarsa suka zo dubata, su suka tafi da yaran gidan su akan da dare idan ya gama se yaje ya dauke su su tafi gida ya dan rage zirga zirga.

Suna zaune kamar kurame bame cewa komai, ita tana chatting a wayarta shi kuma ya tasa ta a gaba yana kallo ganin yanda ta sake wani mugun fresh tayi kyau alamar ta samu hutu ba abinda yake damunta shi kuwa banda uwar rama da baqi da yayi to ga Damuwa ga babu abinci me kyau daya saba kwasa dan yanzu suma yaran mata yassara kawai suke ci dama Mami ce take tsayawa ayi abinci me kyau to bata nan dan haka baya iya ci ko sun dafa in yunwa ta dameshi ne ma zeci Indomie yasa tea in ba haka ba Snacks da lemo ne rabin abincin nasa.

Dagowar da Asma’u tayi tana dan murmushi tareda tsare shi da ido tace “wannan week din bazakaje Gombe bane”
Se a sannan manAmirah ta fado masa ya tuna rabonda suyi waya tun ran Laraba be kiratan ba yasan kuma itama bazatayi gigin kiransa ba tunda ya mata warning. Numfashi yaja kafin yace “Wallahi na ma manta shaf kuma ko waya banyi nace bazan shigo ba gashi har yau Sunday, ya kamata kam na kirata”.

Kishi ne ya dan tsikareta ta wani fannin kuma tana yabawa Bashir dan ba laifi yana kaman ta Adalci wani Sa’ilin. A farko farko se sati biyu yake zuwarwa Amiran ze tafi Friday ya dawo Monday da safe to da aka samu qarin kudin jirgi dole ya chanza tsarin zuwa Qarshen wata, daga bayannan kuma bata san dalili ba wani Sa’in se ya jera sati uku hudu ma duk weekend se yaje duk kuwa da ayanzu kudin jirgin ma yafi da ita dai bata taba tambayarsa dalili ba haka nan ko tare sukaje Gombe ko kwana na wa zasuyi bata da Kwana a yanda suka tsarawa kansu shida Amaryar sa kuma da taimakon Adda to ita hakan be dame ta ba tunda daman idan taje ba zama take ba a lokacin take samun ziyartar yan uwa da sauran abubuwan da akayi bata nan.

Tana kallonsa ya zaro waya ya shiga kiran Amiran ringing biyu kuwa ta daga tana fashe masa da Kuka, kallon Ma’u data juya baya ta kwanta yayi ya tabbatar ta jiyo kukan Amiran se ya miqe ya nufi qofa yana ce mata “kukan kuma Na mene kinsan bana so”

Wani qululu ya tsayawa Asma’u, wato itace banza a wajensa da in zata mutu tana kuka baze ce ta bari ba kenan ashe ita ta zata so ne yasa yake barinta ta fitar da damuwarta ashe tsabar be damu bane kai Anya kuwa Bashir ya taba sonta a ransa??
Abubuwa da yawa da ada take daukar haka yaje se a yanzu take ganin banbance banbance ko kuma dama Haka Mazan suke ko wacce Mace da yanda halayyarsu taje a wajen ta? In kuwa haka ne Sun Amsa sunansu na Hawainiya.

AMIRAH
Sanda Bashir ya kirata suna zaune da Addah da har yau fuska bata daidaita ba ko jiya Indo ta dawo Allah ya taimaketa Alhaji na Nan, shi ya kashe rigimar cikin Kudinta da yake hannunsa yake juya musu da a qalla sun kai 2 Million yau ta kirbi dari gobe Hamsin a wayonta kudinsa take ci da yaga fa da gaske Fatu ba hankali ne da ita ba dole ya saka akayi rubutu kowacce cikin Matan da kudinta dake hannunsa ya kuma gaya musu duk wadda ta nemi kudi indai ba abinda ya zama dolensa ba to a cikin kudinsu suka ce sun yarda kowa ta saka hannu to ita Adda a nata baqin wayon da ganin tasha kansa bata dena ba ta ci gaba dacin kudinta hankali kwance ba tareda ta sani ba shi kuwa yana lissafe da komai ga kuma takaddu saboda Adar rai. To tun jiya daya fita ya yanke shawarar cikin 500 din data rage mata ze biya mata bashin nan dan ba ita kadai ba harda shi take zubarwa mutunci maqota kullum na jiyo an zo karbar bashi gidansa bayan Allah ya rufa masa asiri.

Jiyan Indo na zuwa ya fito a gaban Fatu ya zaro kudi ya bata ta qirga su cif sun cika tace mata “Allah ya taimakeki wallahi da dukan yau se yafi na jiya kuma wallahi ko da wasa karki kuskura naga qafarki kinzo neman abu gida na dan ance ba kunya ce da ke ba se ki dawo” ita dai tayi muqus harda yiwa Alhaji godiya yace mata
“Godiyar me zakimun a cikin kudinki na biya miki ai ba nawa ba tunda haka kika zaba se kiyi tayi wata ran idan ba kiyi hankali ba suturar da zaki daura se ta gagare ki indai baki dena cin bashi ba.

Yana fita wayar Bashir na shigo wa Adda ta zabga Hamdala tace kin gani ko a sannu a sannu komai ze daidaita maza ki daga ki rushe da kuka duk kibi ki hargitsa shi ki samu yazo ko ya turo mana wani abun, haka akayi tana dagawa ta saka kukan.
Seda ta tsagaita ta gaishe shi ya amsa yana tambayarta jikinta tace da sauqi.

“I’m sorry Amirah ranar nayi miki ihu raina ne a bace Wlh ga Ma’una bata da lafiya a lokacin ke kuma kin dame ni da kira”

“Ba komai Yayana ya wuce yanzu ya jikin Antyn? Ban sani ba ai dana kira na mata sannu dukda idan na kirata ma bata amsawa kaga yanzu kosu Aliyu ta hanani magana dasu”

“Qorafi dai qorafi halin daya tsana da Amirah kenan a rayuwarsa” ya ayya a ransa a fili kuwa se yace
“Ta samu sauqi, se zuwa Next week zan shigo insha Allah akwai abinda kike da bugata ne?”

Se Adda ta zungureta tana rada mata tace kudi se tace
“Uhm uhm Ba komai maganar siyayya ne kawai daman se kuma ni Yayana ina so in dawo kusa da kai gaskiya saboda....”

“Amirah I’m looking forward to that ok maganar kudi kuma idan mun gama zan saka miki wani abun kafin End of the month saboda nayi hidimar Asibiti duk na kashe kudaden hannuna yanzu”

“To shikenan amma dai gaskiya Yaya nidai ko wani gidan ne se ka samar min da zan zauna amma irin Na Anty nake so me kyau sannan fa yaya karka manta da zancen canjin kujerun irin natan” ta sake fada dan harga ranta fa ita tunda ta tashi burinta kawai shine ta kamo Asma’u ta ko ina.

“Naji ki gaida su Adda” ya fada yana qoqarin kashe wayar jin tana so ta bata masa rai,
“Bama ta da lafiya bari na bata kayi mata sannu” ta fada kafin ta miqa mata kuwa qit ya kashe wayarsa dan itama Addan haushin ta yake ji dan abu da yawa ita take dora Amiran akai, idan banda bata da tunani kwana nawa basuyi waya ba amma da abinda ya kamata ta tare shi kenan? Bayan haka yanzu fa yake gaya mata bashida kudi amma ita wannan baya gabanta buqatarta ce kawai a gaba. besan dalilin ta na gasa da Ma’u ba komai ta gani a gurinta yunqurinta se itama ta samu, tana mance cewa Asma’u na aiki tana da abin kanta abu dayawa ko beyi mata ba zatawa kanta.

Gudun karta ishe shi ya saka shi yi mata transfer 100k saura 200k kenan kudin siyayyar kayan haihuwa dana fitar suna da tace ya bata, yace sun yi yawa ta ringa masa mita da qorafin bala’i dole ya yarda ze batan kota qyale shi.

shi tunda Asma’u take haihuwa baya tunanin ya taba bata dunqulalliyar dubu Hamsin wai da sunan tayi siyayya shi bata ma taba tambayarsa ba, duk abinda ya dakko ya bata idan yana dashi karba take idan ma bashi dashi haqura take yan uwanta su mata harma ya samu Arziqin shaddar fitar suna shima.

Baze taba manta Haihuwar Abdallah ba da tace ya saka mata sunan Babanta yace mata sedai ta se masa rago hakan kuwa akayi ta siyo raguna har biyu ta kuma cewa Yan uwanta da Nasa shi ya siya har yu har gobe ya kalli yaron se yaji wata kunya da Nauyin sa dana Uwarsa ya kamashi, shi wallahi a duniya in yai wani abun se yaga kamar dai shafar Aljanu yake samu su saka shi yayi abu daga baya yazo yana dana sani (Shafar Aljanu ko iskanci ba 😂😂)

Dakin ya koma Ma’u najinsa tayi shiru kamar me bacci ya gaji da tsayuwa ya qaraso ya mata peck a goshi ya fita yanaso yaje gida ya dan yi bacci tunda yaran basa nan yau shima ya dan huta kafin gobe Monday.

Su Addah kam Kudi na shigowa suka hau Murna “Ke yar nan kinga abu kaman wasa aikin malam ya fara kama Bashir to wannan aka gama aiki kuma ai ban san yanda zamu taka shi ba yanda muke so. Ita waccan shegiyar dama itama ba a zaune take ba dole nata yaqi tasiri amma tunda mun rabu lafiya shikenan, yanzu bari an jima zan kira Malam se ya nada account mu sake tura masa ko kudin biyu ne tunda na bada na biyu ayi a gama aikin nan mu fara shan romon damokaradiyya”

“To Adda amma da mun bari dai akwana biyu a sake samun wani abun wannan mudan rage siyayyar mana” cewar Amira.

“Ke dallacan ba gara a gama ba nasan ko million goma kika ce ya baki kawo wa zeyi”
“Kuma fa haka ne, to ki kira se a tura masa din”

“Allah dai ya kauda bacin rana” Ummi ta fada tana miqewa kafin ta karbi duka ko Ashar daga gurin Adda ai kuwa

Please Login or Register in order to submit comment