Join Our WhatsApp Group


You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register


An dauko wannan littafi daga shafin https://taskarnovels.com.ng ku ziyarci shafin na https://taskarnovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na yake yake dana soyayya




Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,



Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan

Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490



A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci, duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,



Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu



Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai fi kyau ku riga dauko PDF da DOC



Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai wayarku


This hausa novel was uploaded and downloaded from https://taskarnovels.com.ng

You can download more hausa novels there

Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to download it online

It is free we do not charge for uploading novel

Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490 its free we do not charge for our services



Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not blame us



Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day, any time you can visits our site and download it



Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT



This Novel is downloaded from https://taskarnovels.com.ng
to download more hausa novels visits our site at www.taskarnovels.com.ng

For feedback and support

Facebook : https://facebook.com/taskarnovels

Twitter : https://twitter.com/taskarnovels

Telegram : https://t.me/taskarnovels

https://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(Alkhairi CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


Na Maryamah_Mrs AM

Page 1

Lagos Nigeria

Cikin sauri nake har hada takaddun ina qara duba agogon hannuna dukda nasan dakyar idan bazan makara, qarfe Tara jirginmu ze tashi zuwa Kano dan halartar wani conference meeting da aka turani daga office din mu. Gaba daya befi saura 45 mins Taran tayi ba inda na dan samu kwanciyar hankali babu nisan tazara tsakanin unguwar tamu zuwa Airport din. Buda qofar dakina da akayi da dan qarfi ya sani cewa " not now please" azatona daya daga cikin yara nane sedai shirun da naji yasani waiwayawa, megidan ne da kansa wato ENGINEER BASHIR AHMAD da nake Kira da Baban Ali Yara kuma suna ce masa Abbi, Aliyu sunan babban Dana wanda Sunan Amininsa ne ya saka masa da ya rasu sati biyu kafin na haifi Aliyun.

Fuskar sa a hade duk da kasancewarsa dama ba mutum bane me fara'a amma dai ai yanayimun nidai. Kallona yake kamar yanda nima nake kallonsa fuskata dauke da gajeran murmushi nace "Baban Ali ka ganni har yanzu ko? Wallahi Amna ce tayi mun shirme tun jiya da dare nace ta zubamun papers din nan a jaka ashe batayi ba (Amna Qanwata ce kuma Autar mu danake ruqo bayan rasuwar Mahaifin mu da Mahaifiyarmu ta sake aure).

"Uhm" kawai yace mun yana nufar gaban mirror na, ban damuba na qarasa zuge jakata tareda ratayata na dauki wayata dake gefe kafin na nufi qofa da niyyar fita

"Idan kin dawo zuwa end of the month ku fara shirya zaku koma Gombe" muryarsa ta doki kunnena,

"To meya faru kuma? Bari dai in na dawo se muyi maganar a nutse" na sa kai na fice daga dakin. Already Emmanuel Driver office dinmu na waje yana jirana dan haka da sauri na fita ina amsa a dawo lafiyan da yara suka biyo ni suna yimun.

Bayan na nutsu a bayan motar zuciyata ta tafi tunanin me zamujeyi a Gombe kodai wani abune ya faru a bangaren sa? To bangarensa mana dan nidai ko da safiyar nan nayi waya da yan uwana kuma ba abinda akacemun ya faru to ko Matar tasa ta haihu ne? Aa in haihuwa tayi ai kaitsaye zece Amira ta haihu bawai kawai zakuje Gombe ba. Haka dai naita tunane tunane har zuwa Sanda Jirgin mu ya tashi.

A matuqar gajiye na shigo gida kusan qarfe 9 na dare, se yanzu nai dana sanin qin bari na kwana a Kanon dan jirgin 6 na biyo na dawo saboda ban gayawa yarana zan kwana ba nasan bazasuji dadi ba musamman da yake Gobe Saturday ne munsaba zama a gida. Bayan nayi sallar Magriba da Isha naci abincin da Aliyu ya kawo min, ina zaune tsakiyarsu kowa da hirar da yakeyi mun wani irin farin ciki yana cikamun zuciya. Tabbas yaya rahma ne, a duk sanda na kalli yara na ina jin tamkar bani da sauran wani damuwa a rayuwa se fatan Allah ya rayamun su.

Amna qanwata dake matsayin babbar Yata a yanzu nada shekaru 15 tana SS2 se Aliyu shekaru 13 ya shiga SS1 saboda Jumping da makarantarsu suka masa dan Yaro Masha Allah yana da qoqari tamkar Mahaifinsa. Jafar ke bi masa se Farida, Abdallah, se yan biyu na masu shekaru 5 Ahamd da Muhammad su Shidan nan sune rayuwata ban kuma hadasu da komai ba.

Har qarfe 11 muna zaune duk da irin gajiyar da nayi dan har wani ciwo kaina yakeyi, sauqin dana samu tun a kano na aika da report din komai Office dan haka Weekend din nan bacci zan shaqa. Sallamar Baban Ali ce ta katse ni na dago ina kallonsa da mamaki dan Duk hirar da muke a zatona yana Dakinsa dan shi dama be fiya zama ayi irin dogon hirar nan dashi ba, gaba daya muka masa sannu da zuwa ya Amsa yana nufar dakinsa. Se a sannan na tuna ko kirana beyi ba yaji ya na sauka, Se na miqe nima ganin kamar baya cikin yana yi me dadi dan in lafiya seya dan tsaya damu ko ze shige dakin ga kuma fita da yayi da daren nan, tashina yasa suma duk suka miqe mukayi exchanging Hugs kafin Mazan suka nufi dakinsu matan ma haka.

A tsaye na same shi yana cire rigarsa na qara sa taya shi ina cewa "Ashe baka nan, na tambayi yara sukace kamar Zoom meeting kukeyi kana daki"
"Uhm" ya kuma amsa mun. Nan da nan naji raina ya baci dan gaskiya ina da saurin Hasala amma fa ina da sauqin kai rainin hankali ne bana so, to rainin hankali mana ace wani inje kano in dawo a ranar ai ya tambayeni ya hanya koda yake dama duk satin nan tunda ya dawo Weekend naga yana wani fuzga ban kula shi ba nasan qiris yake jira ya sauke abinda ita yar Gwal din baze iya mata ba. A raina naja tsaki tareda cewa "Dan rainin hankali wato ga bolarka can Yarinya ta bato maka rai kazo ka juyemun to bazan tanka ba". Ganin ya shiga Toilet yasa na fita, dakinan yaran na shiga can na tarar da Ahmad da Moh suna kwasar Dambe abun haushi wai Jafar na musu waqa Su Casu bame rabasu, haka suke kamar Kaji kullum fada kamar ko yaushe kuma akan Gado ne saboda Bunk ne dasu Aliyu da Jafar se nasu Muhammad, Ahmad da Abdallah Babban gado suke kwana su ukun to wai se ace A gadon Yah Jafar za'a kwanta shine a sama dan haka yau in wannan ya kwana gobe wannan amma rigima irin ta Ahmad se yace sedai dan uwan ya bashi kwanansa. fada na musu kafin kwantar dasu dukka a gadonsu muka karanta Azkar din bacci naja musu qofa tareda kashe fitila.

Amna da Farida tuni sunyi bacci suma Adduar na qarayi musu ma ja musu qofar na shiga dakina, jikina na qara gyarawa tareda daukar wayata na ja qofar na fita. Har Baban Ali ya kwanta ganin rigima yake nema yasakani kashe fitilar da ya bari a kunne nima na nemi wuri nesa dashi na aje muqamiqina wata gajiya na sake saukar mun.

"Kufa fara Shiryawa Next week zaku koma Gombe" ya sake fada, sena gyara kwanciyata ina cewa "Allah ya kaimu dan wallahi na gaji bacci nake so inyi kuma na biye masa surutu zamuyi tayi dan dai yasan abinda yake fada bame yiwuwa bane tunda na fara aiki ai bama zuwa Gombe se lokacin hutu shima ba kowanne ba se yayi corresponding hutun Yara da nawa ko kuma da wani babban dalili amma rana tsaka ana tsakiyar Term yace wani tafiya ko yar Gwal din ce ta haihu wlh bazan bar aikina na tafi ba duk sanda nai hutu naje mata Barka. Ina wannan mitar bacci yai awon gaba dani da ban farka ba se Qarfe 7 harda Rabi na safe.

Yau Baban Ali halin fulani ya motsa kenan ko ya tashe ni sallah dan gajiya ce ta danne ni banajin ko juyi nayi a baccin nan. A gurguje na dauro Alwala nai sallah bayanna idar da azkar dakyar na miqe dan bawai baccin ya sake ni bane na fito palour, Amna da Farida na zaune Se Ahmad dake bacci a kan Three sitter. A tare suka gaida ni na amsa ina tambayan ina Su Jafar Amna ce tace sun fita Jogging da Abbi
"Kunyi karatun Asuba ne" na tambayesu suka amsamin da eh
Mamaki ya qara kamani amma na dake na shiga kitchen Tea nake so nasha kafin na koma bacci. Kafin na fito sun koma dakin su har Ahmad sun dauke shi daga wurin dan haka na zauna kan Dining ina shan Tea ina tunanin meya ke damun Eng ne haka. Haka na qarasa na koma baccina wanda koda na sake farkawa 12 harta gota na rana.

A dakin nai wanka na shirya kafin na fito ina jin gajiyar ta sake ni. Palour kamar Gidan biki saboda hayaniya Farida da Jafar na musu akan wani film da suka kalla. Da gudu Ahmad da Moh suka nufoni har suna neman kadani na riqe hannayensu muka qarasa cikin palour.

"Ina Abbi" na tambayesu dan koda na farka ban ganshi a dakin ba kuma dai nasan Saturday Sunday yana gida seda babban Dalili yake fita kafin su bani amsa ya shigo da sallama ciki ciki, kallo daya yamun ya dauke kai tareda nufar kan Dining ya aje abunda ya shigo dashi, jin an fara kiran sallah yace su tashi suyi Alwala suka wuce masallaci da Mazan mu kuma muka tayar da tamu a Gida.

Abun mamaki bayan sun dawo kuma se gashi ya zauna a palour tareda yaransa suna hira dan nidai kitchen na shiga na fara qoqarin dora mana abincin rana dan na dare a waje zamu je muci in yaga dama kenan. Da wuri na gama dan Garnished spaghetti na mana se na dumama Grill Fish din daya shigo dashi ko a ina ya samo da safen oho. Farida da Amna na kira suka jera komai akan Dining kafin muka zauna gaba daya banda Abbi dake amsa waya sena dakata har ya gama sannan na masa maganar Abincin.

"Kifin kawai zaki kawomun da juice" ya fada. Ban kawo komai ba dan nasan spaghetti bata wani dame shi ba amma dai yana ci musamman irin wadda nayin, na hada abinda ya buqata na kai masa sannan na koma muka ci gaba da cin abincinmu. Koda muka gama wurinsa Twins suka koma da Abdallah Jafar da Aliyu suka kwashe kwanuka zuwa kitchen tareda wanke wa Amna da Farida kuma daki suka shiga Farida zata yiwa Amna tsifa. Nima palour na koma muka hadu muna yar hira sedai abinda na fahimta Baban Ali yaransa kadai yake amsawa dana saka baki se naji yayi shiru tsam na miqe Ahmad ya tashi shima ze bini dan haka yake indai muna gida da na dauke qafa ze aje tasa nace masa "koma ka zauna aiki zanyi" ban ma shiga dakinsa ba na shige nawa.

Kwanciya nayi kan gadona ina replying whatsapp messages daga nan muka shiga hira da yayata Alawiyya da muke Uba daya, tamu tazo daya nan na shiga bata labarin abinda Baban Ali ya tsiro dashi kuma. Dariya tayi tana cewa "kedai da Engineer Miskili kafi mahaukaci ban haushi" nan muka ci gaba da firar mu ban san lokaci ya tafi ba seda naji ana kiran La'asar.

A dakin nayi sallata ina idarwa na shiga wanka, daidai na fito naji Knocking nasan yaran ne basa shigomun daki sena basu izini koda kuwa Ahmad da Muhammmad da suke qanana. Bayan na amsa Abdallah ya shigo, sak kamanninsa da yanayin Miskilancinsa irin na Bashir ne sedai duk cikin yarana ya fisu haquri wannan kuma halin takwaransa wato mahaifina ya gado. Cikin sanyinsa Yace "Mami Wai Abbi yace kiyi masa text na abinda zamu taho miki dashi".

Se naji wani dus kamar yaya na masa text? Ba tare zamu tafi ba? Har na bude baki da niyyar tambayarsa se kuma na fasa nace masa " Kacewa Abbi ya leqo ina son magana dashi". Da toh ya amsamin kafin ya fita ya barni da mamakin wannan sabon rainin hankalin.


Abbi
Lokacin da yaron ya gaya masa saqon har sun shiga mota ya ma kunnata, ganin idon su ya sahe cewa yana zuwa ya fito yana qara daure fuskar sa. Tana shafa wa santala santalan cinyoyinta mai ya sameta, yaso ya shagala da binta da kallo dan a duniya ASMA'U takai duk inda mace ake so takai, Asma'u mace ce guda harda Rabi wallahi ta ko ina ta hadu bakuma ze taba manta halaccinta a rayuwarsa ba shikansa ya kasa gane dalilin da yasa yake mata wasu abubuwan. Waiwayowan da tayi tana qoqarin sakin towel din jikinta dan sam bata ji motsinsa ba yau saurin juya fuskarsa dan a wannan bangaren baya taba iya tsallake tarkonta. Jikinta tamkar Magnet yake ga idonsa, a kullum gani yake kamar qara mata kyau da sura akeyi Ma'u bata tsufa.

"Au Abbi ka shigo ashe, Ban gane me Babana yake fada ba yau kuma danwaken zagaye zakumin kenan" na fada ina cigaba da zura rigata dan nayi sauri na shirya nasan Bashir baya son jira sam a zatona ma dalilin daya sa zasu fita su barni kenan.

"Nop banyi niyyar fita dake bane, kiyimun text din abinda zaki ci mu taho miki dashi in kuma beyi miki ba shikenan" kawai yasa kai ya fita.

Se na raka bayan sa da kallo kawai kamar wata doluwa, " tofa Baban Ali kodai gamo yai da Aljanu ne" na tambayi kaina ina qara cika da tsabar mamaki.


Share
Share
Sharehttps://chat.whatsapp.com/IcgqoNAQ9V612x1JRXBMVS

🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


WATA KISHIYAR 🥰👹
(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟🌟


Na Maryamah_Mrs AM

Page 2

WATA KISHIYA(ALKAHIRI CE KO SHARRI)


Ni kadai tsuru kamar mayya a gida har qarfe 10pm ga gyangyadi inayi amma na kasa shiga daki na kwanta saboda tsoro gashi har sannan basu dawo ba. Tsayuwar motarsa da naji ta sani miqewa daidai lokacin da Ahmad ya kwaso da gudu yana kwallamun kira "Mami Mami"
"Na'am Ahmad meya faru" na fada ina tare shi, labarin inda sukaje ya fara bani, gurin wasan da ya kaisu, Favorite restaurant dina sukaje suka ci abinci daga nan suka tsaya Cinema sukayi kallo abinda ya saka su yin dare kenan.
Saboda gajiya kowa dakinsu suka nufa, dakaina nayiwa Twins wanka na shirya su kafin 11pm gida yayi tsit duk sunyi bacci sannan na shiga dakina raina yana suya,
Tsabar bacin rai ko takan take away din da sukamun ban bi ba nima wankan na shiga ina sake danne zuciyata na shirya na nufi dakin Baban Ali.

A kan gado na sameshi yayi daidai yana amsa waya fuskarsa dauke da wani shegen murmushin da bazan iya tuna rabonda yayi mun shi ba ko ba'a fada ba nasan da Amira yake waya dan Baban Ali bashida kwashe kwashen yammata, Ada ni kadai ce a rayuwarsa kafin ya kwaso min Alaqaqai.

Wayar dana tarar yana yi ita ta qara bata mun rai saboda wannan ai wulaqanci ne ko? Nasan matar sa ce amma ya kamata nima ya mutuntani idan zeyi wayarsa se ya nemi kebantaccen wuri bawai cikin dakina akan Gado na ba, wannan sabuwar ta'asar da ya samu ta fara kaini bango dan haka ban san sanda na saki wani wawan tsaki ba ina janye ido na daga kansa bayan mun hada ido.

"Ke dawa kike tsaki?" Ya tambayeni still wayar na kunnensa.
"Ni da waye a dakin" na fada raina na qara quna.

"Anty ce ko" na jiyo muryar Amira na tambayar sa daidai sanda na duqa kusa dashi dan na dauke Safar daya ajiye akan gadon sena daga sauti yanda nasan zata jiyo nace "Nice din yar iya ko kina da magana ne"

"A ko yaushe ina gaya miki ki ringa jan girmanki ko? Amma shikenan" ya fada yana miqewa daga kan gadon ya nufi qofa. Wani baqin ciki ya tokare mun wuya, kawai na haye gadon na kwanta tareda fashe wa da kuka.

Duk yanda nake daurewa se Bashir ya qure ni tunda ya auri yarinyar nan ban sakeyin sati ba tare da nayi kukan baqin ciki ba shikenan ni a haka zan qare? Bansan sandaya dawo dakin ba na dai farka cikin dare naji mutum ya kwaqumeni aiko na ingizashi da qarfi har seda ya farka na tashi daga gadon na shige toilet. Fitsari nayi na dauro Alwala, hijabina na zura na fara jero Salloli tare da dogayen Addua.

Kamar kullum a duk sanda muka samu sabani na fara sallar dare nan haka ze zabga tagumi yana kallona in ya gaji shima ya to Alwalar ya tada Sallah (bawai dan banayi ba Aa nafi tsawaita Idan mun yi fada dan karna kwanta kusa dashi dan duk bala'i bama raba gado 😂😂) nasan me yake tunani qila qarar sa nake kaiwa gurin Allah ko 😂😂 wallahi ko daya duk abinda Bashir yake mun ban taba yi masa Allah ya isa ba sedai ma in roqi Allah daya yafe masa ya kuma bashi ikon Yin Adalci a tsakanin mu ya ci gaba da bashi yanda zeyi ya kula damu. Ko ba komai nasan Bashir yana sona nima kuma ina sonsa to ban rabu dashi a lokacin Matsi ba se yanzu da dadi ya samu se in tafi in barwa yar taka haye?? ina ba wannan magana.

Ban sallame ba har seda aka kira sallar Asuba, ina kallonsa ya fita masallaci kafin nima na tashi nayi Raka'atanul fajir sannan na bada Farillah. Rashin samun bacci cikin dare yasa ina idarwa ko Azkar ban samu yi ba na koma bacci, sanda na farka goma harta gota dan haka anan dakin nayi wanka na shirya kafin na fito palour.

Ko ina qalqal sun gyara dan ko kadan banyi wasa wurin koyawa yarana aikin gida ba komai nidasu mukeyi bani da me aiki tunda har kuma yanzu dana ke fita aiki da safe kafin mu fita mukeyin komai tunda kuma ba wuni muke a gidanba baya yin datti. Babu kowa a palor se Baban Ali yana aiki a system dinsa ya dago yai mun kallo daya tareda mai da kai ya cigaba se na qarasa kusa dashi ciki ciki nace masa ina kwana dan har yanzu haushin sa nake ji, se ya amsa ba tareda ya kalleni ba.

A dakin Boys najiyo hayaniya da alama PS sukeyi tunda suna da Tv a dakin nan suke yin Game dukda lokaci da yawa yana dauketa saboda karsu shagala da wasa a qi karatu amma Weekend dama aikin kenan wani sa'in hardashi zasu hada anan palour suyi.
Kitchen na nufa dan naga sun kwashe kayan kan dining, a roba na tarar da dankali ciki ruwa an yanka su, nasan Amnace ta ajiyemun tunda tasan nafison dankali da an kwashe daga wuta nan da nan na maida man da sukayi suya na zuba kafin na debo kwai guda uku na fasa tareda zuba abubuwan da nake da buqata a ciki, ina kwashe dankalin na maida wani pan din na soya kwai, scramble nayi dan ban fiya son me fefe ba na juye akan plate din chips na zuba Ketchup a gefe na fito. Ta gabansa na wuya ina juya jiki tareda baza masa qanshin turarukan dana fesa aikuwa naji yanda yaja numfashi da ajiyar zuciya ina kuma jin idanunsa akaina har na zauna a dining amma kafin na juyo ya dauke idonsa, girgiza kai nayi ina sake cika da mamakin Bashir a raina haka naja kayan tea na hada ina ci ina dan kallon drama da akeyi a Tv.

Har na gama ci babu wanda ya leqo a yaran Gogan ma anata latsa laptop kamar besan Anyi digona a palour ba sena taso na dawo cikin palour na nemi 1 sitter dake facing nashi na karkace ina latsa wayata nima. Whatsapp na shiga group dinmu na Secondary na bude aikuwa na tarar da chats bila adadin, ban samu damar bi ba saboda wasu ne suke qara shigowa se kawai na fara bi daga nan. Ban karanta message din mutum hudu ba na fuskanci dalilin ubannin messages din dana gani ashe Labor zaayiwa kishiya (Labor prefect dinmu da muna school kuma abin dadin qanwar daya daga cikin yan ajin namu qawarta ta hannun dama zaa auro mata, tasan mijin zeyi aure amma bata san yarinyar ba se yau da taje karban lefen Qanwar Qawarta taga dangin Mijinta ne yan kawo lefen 🤣🤣😂😂🤣🤣😂)

Wata muguwar dariya na sheqe da ita har ina kwarewa da ta saka Baban Ali dagowa ya zubamun ido, yasan Ma'u sarai tabbas mugunta ta gano shine dalilin wannan Dariyar. Be gama tunanin kuwa ba na fara voice note still ina dariyata nace "Alhamdulillahi layi ya fara ja ashe? To Allah ya qarawa mazajenmu budi suyi ta auran mana qannemu" na tura ina sake sheqewa da wata dariyar ganin yanda Safiya Sani Labor keta kumfar baki da daukan Alwashi kala da kala ita ma yayar Amarya Zulaiha Balarabe tana aiko da nata.

Masifar da Safiya takeyi seta tunamun da lokacin da za'ayimun tawa kishiyar mun hadu gurin gate together dabanyi niyyar zuwa ba saboda a lokacin bana cikin nutsuwata. A kallo daya zaa gane damuwar da nake ciki duk na hargitse, na tuna yanda ta sakani a loko tana mun wa'azi.


"Wallahi Asma'u kin bani mamaki kin kuma bata wayonki kamar wadda bata san Allah ba, duk ina karatun islamiyyar da kikayi? Kin karanta Alqur'ani tsaf kin haddace da fassara amma kina nema ki kasa aiki dashi. Karin auran nan kinsan umarnine na Ubangiji in har Namiji nada hali da biyu akace ya fara sedai ko in baze iya adalci ba ko kina so kice Bashir ba Adali bane?? Sannan ma ke ai kiji dadi koba komai kinsan wadda za'a auro miki ciki da bai baki da fargabar azo a tarwatsa miki gida tunda Ai Amirah kusan tarbiyyarki ce ma. Haka matar nan ta dage tanamun wa'azi har na sauketa kan layin gidanta mukayi sallama na wuce a raina ina Addu'ar insha Allahu itama se an mata taji in da dadi (Ni fa alokacin duk wanda ya bani haquri se na masa Addu'a Allah yasa shima a masa kuma Alhamdulillah gashi tana karbuwa kuwa 🤣🤣).

Wani mulmulen ashar ta dannomun bayan taji voice dina nan kuwa na samu nayi na ci gaba da kunnata kafin kace me fada yabar kan Yayar Amarya ya dawo kaina harta na jcewa qila dani aka hada baki nace oho dai aikin gama ya gama biki saura 2 weeks , wannan nishadi ya mantar dani wanzuwar Baban Ali a gurin har wurin 12 sannan yara suka fito muka ci

Please Login or Register in order to submit comment