Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

don yadda mamaki ya mamayeta tama kasa magana banda zuba ma kayakin ido da tayi tana mey mamakin anya kuwa ita zata sa kayakin nan? "Baby bakiga kayaki bane da baza ki bud'e baki ba kiyi godiya?" Papi ya tambayeta.

   Kai ta kad'a tana mey dawo da kanta asalin rayuwa daga duniyar tunanin data fad'a.
"Yaya?! Duka wannan namu?" ta tambaya tana mey nuna kayakin.

  "Ji Amal" ya fad'a had'e da murtuk'e gira "Kin ta6a jin inda babban yaya yasai wa kansa kayan sallah be yi wa k'anwarsa ba?"

  Cike da kunya ta kad'a kanta "Yaya mun gode sosai Allah k'ara bud'i ya kuma miyar maka da gidan aljannah."

  "Ameen" Papi ya amsa a fili a yayinda Afzal ya amsa a zuciya.

   "Gaskiya Afzal ba muda bakin yima godiya sai dai muce Allah ya biya ya k'ara bud'i godiya ba adadi Allah ya sak'a ya shige maka gaba aduk abinda kake ciki kake kuma nema."

  "Ameen Papi please godiyan ya isa haka ana tare ai."

  "Toh masha Allah, Baby mai da kayakin ciki kinji kar k'ura ya 6ata" ya sanar da ita a yayinda yake k'ok'arin mik'ewa "Zan fita zani kasuwa sena dawo" ya sanar da Afzal.

  "Papi idan ba sauri kake ba daman inaso muyi wata magana da kai ne" Afzal yayi saurin tanka shi.

  "A'a ko kad'an Babana bismillah" nan ya koma ya zauna.

  "Thank you, dama batun Amal ne munyi magana da ita kuma tace tana son ta koma makarantar boko idan har kaga hakan ba matsala I am willing to provide for her education se tayi sitting jamb muyi mata applying jami'a nan Unimaid."

  "Jami'ah! Allah sarki babana nauyin baze zo yayi maka yawa ba kuwa? Dan Allah karka damu nima ina kan tara mata kud'i ne ko nan Ramat ta shiga don Allah karka tada hankalinka."

  "Papi ni izinin ka kawai nake nema karka damu da komai."

"Baby zaki deyi karatu baza kisa Yayan ki asaran kud'in makaranta bako?" Ya juyo yana kallon Amal data had'e gira. Lalle ma Papi sekace besan k'ok'arinta ba yake fad'a mata haka gaban Afzal, ai se Afzal ya d'au ita d'in doluwa ce.

   Daga bisani tace, "Papi da gan-gan ka fad'i hakan donka kunyatani idon Yaya ko? Allah se in d'auko report sheets d'ina tun daga JSS1 in nuna mishi kaima kasan bana wasa da karatu."

  "Ah ah mamana na kaina yi hak'uri maida wuk'an wasa nike." Murmushi Afzal ya saki yana mey sha'awan relationship dake tsakanin Amal da Papinta.

  "Toh Afzal nide ba abinda zance sede muyi ma addu'a Allah ya biyaka. Rashin shiganta babbar makaranta ba k'aramin damuna yake ba a matsayina na mey kula da ita barin ma yadda take da son karatu, tun tana damuna da cewa tanason ta shiga jami'a har tagaji ta dena saboda rashin samu, ba yabon kai ba amman uwata akwai ja inada tabbacin cewa bazata baka kunya ba, kuma nima zan sa ido sosai akanta inga ta cika maka burin ka nason ganin tayi karatun nan, Allah sak'a maka da alheri."

  "Ameen Papi nine da godiya daka amince da wannan k'udiri nawa zan d'anyi tambayoyi kad'an in shaa Allahu duk abinda akwai zan sanar dakai."

  "Toh toh Babana mungode mungode sosai Allah kad'ai ze biyaka shikenan ko akwai wata maganar kuma?"

  "A'a Papi kana iya tafiya nagode da ka bani lokacin ka."

  "Toh madallah madallah" ya fad'a yana mik'ewa.

  "Toh a dawo lafiya" cewan Afzal.

  "Allah tsare Papi" inji Amal.

  "Ameen Afzal ameen uwata, mungode sosai sosai ka gaishe da gida idan ka koma."

  "In shaa Allah" Da haka ya fice ya rage Amal da Afzal kad'ai kasancewar Mami ta shiga mak'ota.

  "Yaya wanne ne nawa?" Ta tambayesa cike da jin dad'i tana mey zazzago da kayakin. Murmusawa yayi ganin yadda ta kasa 6oye farin cikinta. Atamfan Mami yaja gefe da kuma shaddan Papi sannan yace, "Duka wannan naki ne."

  "Dagaske Yaya? Da wannan da wannan da wannan duka?" Ta tambaya cike da k'in yarda tana mey bin kayakin da yatsarta tana nunawa.

  "Sosai ma."

  "Yaya you're truly an angel thank you so much."

  "You're welcome Lily" ya amsa yana mey miyar mata da murmushin da take masa.

  "Toh ni da irin abubuwan nan da kake min dasu Papi me muke dashi da zamu iya baka in return?"

  "Addu'o'in ku kad'ai ya isheni Lily."

  "Are you sure Yaya?"

  "Absolutely sure Lily."

  "Toh shikenan Yaya ga addu'o'ina na yau da kullum a gareka; Allah sak'a maka da alheri, ya k'ara maka bud'i yasa ka cimma duk wani burinka a doron k'asa, Allah ya baka mace ta gari da 'ya'ya nagari ba masu rashin kunya da taurin kai kaman ni ba fa" Dariya sosai Afzal ya tsaya yi a yayinda ta cigaba "Allah sa ka gama da duniya lafiya, ya baka gidan aljannah kuma, kai Allah ya baka duk wani abinda kakeso tun a zuci ba seka furta shi waje ba." Shiru ta yi don jin yadda Afzal keta dariya tun zamansu dashi bata ta6a ganinsa yana dariya haka ba, ashe de haka dariya yake kar6ansa shine baya yi? Cankwad'i! aikuwa ta rik'a sashi dariya kenan kullum yanayi.

  "Ka gama dariyar baka amsa da ameen ba."

  "LOL ameen Lily kema Allah ya miyar miki da duka addu'o'in da kikayi min."

  "Hmm ameen da babban murya kaga barin surfa waken nan kafin Mami ta shigo ta balbale ni tun d'azun tace inyi na tsaya ina shirme."

  "Kafin nan Ummi tace tanason ki koya mata yadda akeyin aldeb d'innan Lily na rage mata na jiya bakiga yadda tayita santinsa ba."

  "Kai Yaya dagaske?" Gira ya d'age mata "Wai yayi dad'i tace?" Ta tambaya zealously.

  "Sosai ma."

  "Ai dama nasan na iya girki Mami ce kullum ke kusheni."

  "LOL that is because tanaso ki k'ara himma ne don't blame her it's what mothers do."

  "Hmm toh kasan me za'ayi? Barinje in kira Mami nan mak'ota tayi hak'uri tayi sirfen waken sena had'a wa Ummi da kai aldeb d'in ai idan nayi a gabanka zaka gane procedures d'in idan ka koma gida se kayi mata bayani ba?" Shiru Afzal yayi yana nazari shi banda dafa indomie, tafasa ruwa, farar shinkafa ko spaghetti da macroni anya akwai wani abinda ya iya?

  "Kode Yayana be iya girki bane sam?" Ta tambayesa cike da neman tsokana.

  "Waya fad'a miki?" Ya wani 6ata rai yana cin fuska.

  "Toh naji kayi shiru."

  "Of course, how do you expect me inje in fara yima Ummi bayanin yadda ake had'a aldeb mace ne ni? Kede yanzu ki bani number'n Mami in naje gida sena had'aku kiyi mata bayanin ta waya."

   "Haha nide na gane Yaya ajebo ne be iya komi a harkan kitchen ba."

"Na yarda fad'i koma mey ba shi zey sa in amince da k'udirinki ba."

  "Toh shikenan Yayana na kaina ai ni duk abinda ka fad'a ya zauna se ayi hakan." Bece da ita komi ba yayin da ta shiga ciro ingredients da zata buk'ata tsakar gidan, tana cikin taran ruwa daga famfo sega Mami ta shigo. Sosai tayi murnan ganin Afzal, bayan sun gaisa Amal ta fito mata da kayakin da Afzal ya kawo musu ta nuna mata, da godiya na kisa kam daya kashe Afzal a wajen saboda kalan godiyan da Mami tayita masa.

   Bayan ta mai da kayakin ciki ta fito ta tarar da Amal na aiki daban maimakon sarrafa musu waken da zatayi. Ta soma k'orafi kenan Afzal ya shiga bata hak'uri had'e dayi mata bayanin lamarin cewa Ummi ce keson aldeb d'in. Ba tare da 6ata lokaci ba ta shiga surfen da kanta yayinda Amal ta cigaba da had'a aldeb d'in. Ido Afzal ya k'ura mata yana mey sa hankalinsa sosai game da duk wani abinda takeyi ko da ze iya fahimta yayi ma Ummi bayani ko dan kar Amal tayi underestimating nasa.

   Abu d'aya daya karanchi tattare da Amal shine kominta tsaf-tsaf take yinsa ba dotti bale k'azanta hakan ba k'aramin burgesa yayi ba, a rayuwa ya washi mutum me shegen daud'a da k'azanta kasancewar acikin tsafta ya girma, mutane har suna cewa tsaftan Ummi yayi yawa, shara idan batayi atleast sau biyu ko uku a rana ba bata jin dad'i.

   A haka har Amal ta samu ta gama ta d'ura masa cikin manya-manyan silver flasks guda biyu d'aya nasa wai d'aya na Ummi.

Kud'i ya k'irga yasa a hannun Mami cewa suyi d'inkin kayakin nasu dashi. Wayyo Mami ta ma rasa ina zata sa kanta, albarka tayita sa masa sannan suka rakasa har inda yayi parking motarsa, bayan ta mishi asha ruwa lafiya ta koma ciki ta barsa shi kad'ai da Amal.

"Here press Mami's number bayan ansha ruwa zan had'aku da Ummi se kiyi mata bayani" ya fad'a yana mey mik'a wa Amal wayansa da ta amsa da 'Toh.' Hannu na 6ari ta mik'a ta amsa tana mey fatan Allah ya kawo mata ranar da zatayi wayar kanta me k'aton screen kaman wannan ko shegiyar Bintun ajinsu na islamiyya zata shiga hankalinta ta daina yi musu yanga da wata k'aramar infinix nata da bai iya zama cikin jaka ba sede akan table don a nunawa 'yan aji ana da waya. Bayan ta zuba ta miyar masa da wayan inda yayi saving.

"Toh Lily ba-bye."

"Mungode Yaya asha ruwa lafiya."

Murmushi kad'ai ya saki mata yayinda ya bud'e murfin motan ya shiga, se da taga ficewansa sannan tabi lungun gidansu ta koma.

****
BAYAN SHAN RUWA, GIDAN ALHJ AHMAD AMIN.

"Ni fa ban yarda ba kuma bazan yarda ba in zaka kira min yarinya kawai ka kira tayi min bayani da kanta dududu banda tafasa ruwa mey ka iya da zaka wani cemin ka iya had'a aldeb me dad'i irin na Amal in yarda" Fad'in Ummi dake zaune a gefen Afzal akan kujera a parlourn site nasa.

"Am serious Ummi a ido na ta had'a and I did observed her closely."

"Oho nide kiramun ita se naji daga bakinta zan amince, ba ka amshi lambarta kona mahaifiyarta ba? Call her up for me."

"Fine!" Ya fad'a aggressively tare da dannawa lamban Mami kira saida ya kusan tsinkewa aka d'aga. "Assalamu alaikum" yaji siririyar muryar data d'aga ta fad'a. For a moment ya shiga duhu yade san muryan Mami ba haka yake ba, na Amal shigen hakan ne seda kuma wannan d'in har yana son fin natan zak'i.

"Yaya?" Ta kirasa wanda hakan ya tabbatar masa da kokonton da yake.

"Na'am Lily" ya amsa yayinda Ummi ta zura masa.

"Ina yini? An sha ruwa lafiya?"

"Lafiya Alhamdulillah ya gida?"

"Lafiya k'alau ya Ummi?"

"She's okay ita ma ke son miki magana kafin nan Lily aldeb d'innan bada tsamiya, sugar, ruwa..." nan ya shiga irgo duka ingredients d'in sannan kuma da procedures d'in, sosai Amal ta sha mamakin yadda ya rik'e komi dai-dai dukda fad'in sau d'aya aka ta6a had'awa a gabansa.

   "Wow! Impressive kai Yaya na akwai k'ok'ari ai kuwa ka bada procedures din dai-dai sede tsamiyan da ruwan zafi ake jik'a sa kuma sugar'n ma ba raw one ake sawa direct a ciki ba se an narkar dashi."

"Ai na fad'a seda na fad'a maka narkar da sugar'n nan ake kak'i yarda Pff" nan Ummi ta shiga yi masa gwalo.

"Whatever ai nayi k'ok'ari for goodness sake yau fa na fara ganin yadda akeyi."

"Eh sugar'n ma ana iya sa shi direct amman narkekken yafi fita ne" Amal dataji Ummi sama-sama ta waya ta amsa. Gwalo ya shiga yima Ummi shima "Pff to you! Kin deji da kunnen ki a hakan ma ana iya sawa."

"Kai Yaya bade gwalo kake yima Ummin namu ba?" Ta tambayesa "D'an bata mu gaisa."

"Barshi Amal 'yata gwalo yake min" Ummi ta amsa tana matsowa kusa da wayan.

"Toh bata mu gaisa."

  "Nak'i, ke bakiji sanda take min gwalon ba itama?"

"Yi hak'uri toh ka bata" ba gardama ya mik'awa Ummi wayan inda suka gaisa take ta yaba aldeb na Amal wanda har ahakan yasata kunya sosai.

"Ai da na bi procedures na Prince da nayi kwa6a" For a moment kan Amal ya d'aure karde sunan da ake kiran Yaya dashi kenan a gida Prince? Ta tambayi kanta, lallai kuwa d'an gata ne. "Kai Ummi ai yayi k'ok'ari" ta amsa cike da wasa.

"Bani waya na Ummi bani!" Ya fad'a trying to sound serious. Da sauri ta tare hannunsa "Kinsan kuwa banda tafasa ruwan zafi ba abinda ya iya? Taya mutumin da ko jollof be iya dafawa ba ze ce min ya iya had'a aldeb kuma in yarda, 'yata is it possible?" Dariya sosai Amal tasa har tana sark'ewa Afzal da ya kai har maqora se harara yake dannawa Ummi yayinda take tayi masa gwalo. Taya zata fad'awa Amal bai iya girki ba? So take ta raina sa?

"Ai fa ba laifinki bane nine nan na had'aku ai" yace da ita yana girgiza kai.

"Kinji Yayanki yamun fushi ko ki basa hak'uri" Ummi tace da Amal dake ta faman yi musu dariya tun d'azu.

"Laaa yayi mana hak'uri don Allah ai bamu iyawa da fushin Yaya, Yaya?"

"Gashi amshi k'anwarka na son yi maka magana."

"Nak'i" ya amsa ba walwala "Ni d'agani in mik'e idan kun gama wayan naku ki kawo min wayana ciki ko ki kirani inzo in kar6a." Kafin ya kaiga mik'ewa Ummi ta danneshi "Haba Prince yi hak'uri mana."

"Toh Ummi seda safe, ki sake yiwa Yaya godiya sosai dan Allah munga kaya mun gode Mami tac-" wabce wayan yayi daga gun Ummi da sauri kafin Amal ta k'arisa zancenta had'e da katsewa yana mamakin dogon baki irin na Amal se kace bata san halin Ummi ba.

"Ya haka Prince?"

"Babu d'agani nikam."

"Tsaya ma tukun wato ba wa ita kad'ai ka sai wa kayan sallan ba harda iyayenta ko?" Shiru yayi tamkar be jita ba, "Hmm su Prince an fad'a kogin soyayya."

"God help me! Ni wallahi saboda irin suratan nan naki nak'i nuna miki kayakin duka baga irinta ba" ya fad'a a tak'ure.

"Aww ashe da gaske ne ka sai wa iyayenta kayan."

"Eh na sai musu shikenan kin huta?"

"Prince jokes aside kode son yarinyan nan kake ne amman ka kasa ganewa har yanzu?"

"Haba Ummi! Taya zan so Amal please? Ai banyi adalci ba kenan."

   "Kamar ya bakayi adalci ba?"

  "For goodness sake a matsayin yayanta ta d'auke ni, ta na gani na da k'ima da daraja tana girmama ni kawai don ni na kawo rashin halacci da kunya duniya se in hau sonta? It's not possible."

"Kana nufin in ba don wannan dalilin ba zaka iya sonta kenan?"

"God help me!" Ya furta unbelievably "No that is not my point you know what? Let's just drop this topic" ya fad'a ransa na soma 6aci.

"Hmm tayi tsami maji."

"Ummi please kidena blabbing d'innan haka Amal is just my sister there is no any other feeling attatched to it" ya fad'a cikin tattausar murya. Shiru Ummi tayi bata kuma cewa komi ba ganin yadda ransa ke 6aci.


  ~•. .•~        ~•. .•~        ~•. .•~      ~•. .•~

     Bayan Sallah da k'imanin wata biyu dai-dai da lokacin watan Zul~Hijjah ta kama kenan Afzal da Ummi suka wuce Saudi wanda tafiyansu yazo dai-dai da na Nazeefah, Mummy da Khaleefah. A hotel d'aya duk suka sauk'a inda Khaleefah da Afzal suka had'a d'aki, Mummy, Ummi da Nazeefah ma haka. Kusan kullum tare suke fita suyi Ibadunsu har Allah ya kawo su k'arshen aikin Hajji. Ana jibi zasu juya ne Ummi tayita insisting cewa se Afzal ya kai Nazeefah shopping kar Mummy tayi zaton lallai-lallai tilasta masa akayi batun auren. Seda suka kusan haurawa sama Afzal ya amince. Bayan ya fito daga wanka, ya shafa lotions nasa sannan ya zira d'aya daga cikin expensive jallabiyan daya sissiya ya feffeshe jikinsa jak'ab da turare sannan ya tattara wayoyinsa.

"Khaleefah kace bazaka bimu ba? Da Nazeefah zamu fita fa" ya sanar da Khaleefah dake mik'e akan gado se faman buga game na world tip yake.

"Friend d'ina zezo za muje muyi playing video game kuje sekun dawo."

"Alright make sure you lock the door idan zaka fita."

"Toh Uncle Afzal Allah ya kare." Da haka ya fice ya sauk'a reception a k'asa. Numban Nazeefah da Ummi tayi masa saving about last two weeks yayi scrolling yakai kai amman bai jin ze iya kiranta. Bayan tsawon lokacin daya d'auka yana nazari k'arshe ya yanke hukuncin kiran Mummy. Bayan ta d'aga sun gaisa yake sanar da ita cewa yana reception yana jiran Nazeefah yana son su d'an fita yau, yayita trying layinta amman bai shiga.

"Allah sarki halan network ne don gata ma a gefe na bari yanzun nan zata sauk'o sannu ko Babana."

"Yauwa Mummy thank you" da haka ya katse.

"Nazeefah maza tashi ki shirya Afzal na jiranki a reception."

"Mey zey min?" Tayi saurin tambaya had'e da d'ago kanta.

"Jimin tambaya yace yana son ku fita go meet him downstairs."

"Mummy ni wallahi da kince mishi na fita bana nan."

"Dalili? Yanzu har yaro yayi creating time miki ki tsaya kina batun banza?" Itade Nazeefah bata kuma cewa komi ba amman tasan tabbas inma Ummi ce tasa sa na dole kokuwa yana shirin yi mata wani mumunan abun. "Ba zaki mik'e bane?"

"Ba naji ba" ta amsa a tak'ure. Da haka ta kimtsa ta fice inda ta tarar da shi da wasu yaran larabawa se faman wasa sukeyi. Sallama tayi masa wanda se da ya gama 6ata mata lokacin duniya sannan ya amsa. Maimakon ya sallami yaran su tafi inda zasu, no wasan suka cigaba dayi yabar Nazeefah tsaye gun kaman ta6arya, seda ya tabbata ta gaji sannan ya sallami yaran ya mik'e. Don kanta ta shiga bin bayansa dan kuwa beyi niyyan yi mata magana ba.

   A mall suka tsaya inda ya d'au trolley tare da ce mata "Pick whatever it is you want I'm doing this because of Ummi so karki kawo tunanin wani abun a ranki." Daga fad'in haka yaja nasa ya fice ya shiga shopping. Tafi minti biyu tsaye wajen sannan daga bisani taja trolley'n ta shiga kwasan duk abinda yazo hanyarta da abinda zatayi amfani da shi da wanda bata ma san meye shi ba komi kawai d'auka takeyi har Afzal ya gama kwasan abinda ze kwasa Nazeefah bata gama ba se chan ana cikin billing masa abubuwan da ya siya se gata nan cike da trolley tazo ta tsaya bayansa. Murmusawa yayi ba tare da yace da ita komi ba.

Kayakin nasa ta leqa ciki sede da mamaki taga yawancin kayan 'yan mata ya kwasa wanda ta nada tabbacin bana Ummi bane gashi bawai k'anwa ko ya yake dashi ba bale ace nasu ne, toh na waye ne? Kode budurwa yake dashi?? Toh ma ina ruwanta? Kanta ta kawar ta maido da kallonta akan wayarta har izuwa lokacin da billing ya iso kanta. Kud'in abubuwan data siya yayi ninkin na Afzal biyu, da gangan tayi hakan dama, fatanta kawai ace kud'insa ya kasa ta biya wa kanta tasasa jin kunya cikin mutane sede kash! Credit card nasa kawai taga ya zaro ya mik'a wa mutumin inda yayi debiting nasa suka miyar masa da abunsa, har maqora abin ya kai Nazeefah sam ba haka ta so ba. Acikin manya-manyan shopping bags aka sanya musu kayakin nasu suka fito. A bakin k'ofar Nazeefah ta tarar da beggers masu rok'o d'innan tsaye suna neman taimako, ledojin nata gabad'aya ta dank'a musu lokacinda taga Afzal ya kewayo yana kallonta.

Ya sha mamaki sosai amman yayi k'ok'arin 6oyewa, taxi d'in ya bud'e ya shiga tare da cewa driver'n su tafi, sa6anin tahowansu a rarrabe suka koma. Ko a babu itama tasan tayi mishi ba dad'i yau, a cigaba a hakan aga wa ze yi surrender.

***
Afzal ne mik'e kan gadon d'akinsu da Khaleefah se tunanin abinda Nazeefah tayi masa yake yana mey nazarin mey zeyi mata wanda zataji zafinsa haka itama a yayinda wata zuciyar ke cey masa kawai ya barta yaci girma sede yana ganin da k'yar idan ze iya. Ana cikin haka ne wayansa dake kife akan cikinsa ya shiga ruri, duban wa da zeyi ya tarar da Nigerian number, be kawo wani tunanin ba a ransa ya d'aga a tunaninsa gabad'aya ma Sultan ne sede ya tarar da muryar mace, macen ma Amal.
Yau akeyinta, bema san ta ina ze fara yi mata bayani ba saboda ko sanar da ita cewa zasa aikin Hajj beyi ba rabonsu tun kafin ya taho Saudi yau kusan sati uku kenan. Ma ya akayi ta samu numbansa? Katse wayar yayi gudun kar kud'inta ya k'are sannan ya kirata back.

"Lily?"

"Na'am Yaya ka kyauta min kenan? Ai kam yanzu na tabbata ni ba Lilir ka bace kamar yadda kake fad'a tunda har zaka aikin Hajji amman baka sanar dani ba."

   "Lily ba haka bane."

  "Toh yaya ne Yaya? Kawai sena dena jinka ga layinka kullum switched off hankalina du yabi ya tashi haka su Papi ma gashi ban san gidanku ba, last week naje office naka nake tambayarka sukace kayi tafiya se yau kawai Allah ya had'a ni da Ya Sultan yake fad'a min wai Hajj ka tafi sannan ya bani numbanka truly am very disappointed."

"Yi hak'uri kinji Lily? I know I've offended you ni kaina bansan meya hanani sanar dake ba but I'm sorry."

"Saboda baka damu dani bane mana inda kayi ai da ka sanar dani."

"Kema kinsan that's not true I do care about you Lily."

"Uhmm" tace kad'ai.

   "Baki hak'ura ba?"

  "Ai Yaya baya laifi" ta fad'a tana murmushi.

  "Masha Allah that's my Lily ya kike toh?"

"Lafiya Alhamdulillah ya Ibada kun kammala ko? Allah yasa kar6e66iya ce."

  "Eh Lily ameen, jibi ma in shaa Allah zamu juyo, anyi sallah lafiya?"

  "Lafiya k'alau though I miss having you around."

  "I miss you even more Lily yasu Mami da Papi?"

  "Duk lafiyansu suna gaisheka."

  "Ina amsawa my regards, ya karatu?"

  "Gashi muna ta fama da tilawa."

  "Allah ya taimaka guess what?"

  "Ameen, tell me Yaya I'm a bad guesser."

  "Alright digital Qur'an na sai miki na k'ira'a Al~Sudais complete."

   "Kai Yaya! Dagaske!" Tayi exclaiming yayinda ta tsinci kanta cikin farin ciki maras misaltuwa. "Kaman kuwa kasan k'ira'an Sudais nake bi nake kuma son koya."

   "Ai kin riga ma kin iya Lily sede kice kina son sake k'warewa."

  "Kai Yaya! Har yaushe ka sani?"

"Am serious, there was a day naje gida na tarar dake kina karatu so I stayed back and listened to you as you recite."

  "Kai Yaya har kasa naji kunya."

  "Sosai fah Lily nan na gano k'ira'ar Sudais kike bi and masha Allah kin iya sosai."

  "Thank you Yaya."

  "You're welcome karatun boko fa kina d'an tab'awa ko?"

  "Eh wai February zamuyi Jamb ko?"

  "Eh in Allah ya yarda."

  "Ina d'an ta6awa amman akwai wasu abubuwan dana d'an manta a physics da chemistry kasan it's been long banbi ta kansu ba."

  "Don't worry idan na dawo I'll help you out."
 
  "Toh Allah ya dawo mana da ku lafiya."

  "Aameen."
  
  "Amman Yaya dama ba commercial class kayi ba?"

  "Waya fad'a miki? I was once a science student."

  "Shine kuma kake aikin banki?"

  "Ai kowa ma zey iya aikin banki Lily ba se lalle wanda ya karanta accouting ko economics ba kuma kinga ni da bank of agriculture nake aiki."
 
  "Agric ka karanta kenan?"

  "Yes se nayi specializing a Horticulture and Agronomy."

  "Wow! I'm impressed" hira sosai suka tayi se
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment