Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

neman cikowa da hawaye.

Zama yayi a gefenta a hankali had'e da rik'o hannunta cikin nasa. "Kibar cewa haka please ni baki yimun komai ba."

"Ban yi maka komai ba?" Ta tambayesa da d'umbun mamaki.
"Ban yi maka komai ba amma auran mu sama da shekara biyu kenan yau baka ta6a tunanin sauk'e mun hak'k'ina da Allah ya d'aura maka ba? Baka ta6a damuwa da wani halin nake ciki ba Afzal. Kana ganin ka kyauta mun kenan?"

"Nazeefah-"

"Amma kar ka damu har ga Allah ni na yafe ma komai saboda bana son Allah ya tsayar da kai ranan qiyama akai na" ta sanar da shi had'e da katse sa sannan ta cigaba. "Nasani ni na bud'e k'ofan duk wani tashin hankali da wulak'anci daga gareka, da tun farko na rik'e mutunci na nayi respecting naka da duk hakan be faru ba I just hope it's not too late to say sorry." Sosai kalamunta suka shigesa ya kuma tausaya mata. Ya sani tauye hak'k'in bawa ba abu bane me kyau musamman ma na tsakanin mata da miji but shima ai ba a son ransa yake hakan ba.

"A tunanin ki a son raina ne nake tauye miki hak'k'in ki? A tunanin ki nid'in zama haka dad'i yake mun ne? Kokuwa kina tunanin ni banida sha'awa ne? As much as you need me as your husband know that I need you as much amma-" se kuma yayi shiru.

"Amma mey? Please talk to me Afzal I can't do this anymore."

"I can't Nazeefah, bazan ta6a iya had'a kwanciya dake ba.l Har cikin ranta taji zafin kalamun nasa ba shiri hawaye ya shiga tsiyaya daga idanunta.

"Afzal meyasa? Me nayi da zaka hukunta ni haka? Dan Allah kayi hak'uri, Afzal bazan iya rayuwa ba kai ba, wallahi da in rasa ka gara na rasa komai ciki harda rayuwa na. I love you Afzal I can't stop saying it no matter what."

"Nazeefah I'm sorry."

"Ni ba hak'urinka nakeso ba Afzal, ka gayamun dalilin da yasa bazaka iya had'a kwanciya dani ba idan wani laifin nayi in baka hak'uri."

"Forget it, just forget it" kafin ya kai ga mik'ewa ta jawo hannunsa tana hawaye sosai "Please tell me Afzal a shirye nake da inyi ta baka hak'uri har se Allah ya huce ma zuciya dan Allah ka fad'a mun." A da ya d'au alk'awarin komin yaya baze ta6a sanar da ita laifin nan da tayi masa ba amma kukan da takeyi ba k'aramin karya masa zuciya yayi ba.

"Please tell me Afzal I can't do this anymore."

"Remember the first day aka kawo ki gidan nan?" Kai tayi saurin gyad'a "Mey kikace wa k'awarki da ta kiraki?" Ya tambayeta, sede ta duba ta duba tayi tunanin gaba da baya amma ta kasa tuna komai. "Afzal wallahi bazan iya tunawa ba dan Allah ka fad'a mun."

"I can't tell you, bazan iya ba Nazeefah saboda kalamun basuda dad'in sauraro zan baki nan da duk lokacin da kike buk'ata ki zauna kiyi tunani idan har kin tuna da kanki then I'm willing to forgive you."

"Afzal please tell me I'm so sorry."

"I'm sorry as well but I can't." Yana fad'in haka ya kuma mik'ewa da niyyan ficewa hannunsa ta sake rik'owa "Nasan kana jin yunwa please ka zauna kaci abinci."

"Karki damu."

"Please Afzal."

"Kefa? Kinci?"

"Ni idan har zaka ci ma hakan ya isa ya k'osar dani don't worry about me."

"I'm not eating unless with you."

"Toh ka zauna please kar ka tafi."

"Toh kibar kukan haka" badan tana so ba ta shiga share hawayen nata seda ta bar kukan ya amince ya zauna nan tayi serving nasu suka ci bayan sun gama ta tattara plates d'in takai kitchen. D'akinta ta wuce dan watsa ruwa shima haka, chan yana shirin kwanciya se gata ta shigo daman ita yake jira. Bayan ta kwanta ya kashe musu wutan. Kan pillonta ta bari ta matso kusa da shi had'e da sauk'e kanta a birnin k'irjinsa tana mey zagaye hannunta akan cikinsa. A hankali taji hannayensa yana kewaye bayanta "Goodnight Nazeefah" ya sanar da ita had'e da sauk'e mata peck a kai.

"Goodnight Afzal I love you." Bada dad'ewa ba yayi bacci itako ta kasa, se tunanin maganansu na d'azu take. Shin mey ta fad'a da ya 6ata masa rai haka har ya gommaci ya tauye wa kansa hak'k'i ya sha wuya da ya kusance ta? Se kusan k'arfe biyu bacci ya d'auketa. Washegari wajajen k'arfe hud'u bayan Afzal ya dawo daga office tayi masa sannu da zuwa had'e da amshe jakansa. Har d'aki ta rakasa ta ajiye jakan nasa a mazauninsa sannan ta shiga bayi ta had'a masa ruwa ya shiga ya watsa bayan ya fito ya sanya shorts da singlet sannan suka fito dining inda suka ci abinci. Bayan sun gama ta tattare wajen tsaf. Har Afzal ya shiga takawa zuwa d'akinsa yaji muryan Nazeefah na kiransa, chak ya tsaya had'e da kewayowa. Mik'ewa tayi ta k'arisa ta samesa.

"Afzal I'm sorry I'm really sorry."

"Why? What for?" Yyi saurin tambaya.

"Bayan tunanin da na yini inayi na tuna abinda na fad'a a daren auren mu dan Allah ka gafirceni, I was young and stupid then, yarinta na yawo a kaina bansan ciwon kai na but tuba nake please forgive me for hurting you like I did, wallahi I didn't mean a word."

"It's okay Nazeefah ya wuce."

"Dan Allah ka yafemun."

"Na yafe miki komai Nazeefah forgive me also."

"You have nothing to be sorry for."

"Toh hawayen ya isa haka" ya fad'a had'e da sa hannunsa yana share mata hawayen nata. Hugging nasa kawai tayi yayinda kukan nata ya tsananta "Thank you for forgiving me Afzal, I love you so much." A hankali ya zagaye hannayensa a bayanta hugging her back.

"Its okay" ya sanar da ita yana shafa bayanta a hankali. Be barta ba seda kukan nata ya lafa hannunta ya ja izuwa parlourn inda suka zauna akan kujera.

"Yaushe zakuyi exams naku?"

"Da d'an saura se nan da two months in shaa Allah."

"Masha Allah shikenan an zama graduate kuma ko?"

Ka manta ne? First semester muke ai? Se mun gama second tukuna."

"Yesh haka My computer scientist" yayi complimenting nata.

"Thank you" ta amsa tana murmushin jin dad'i, har cikin ranta taji dad'in yadda ya kira ta 'his computer scientist.'

"I'm so proud of you Nazeefah Allah sanya albarka acikin karatun."

"Ameen Afzal thank you."

"Ina son mu tafi Umarah tare."

"Umarah?" Tayi exclaiming cike da mamaki.

"Yes just me and you."

"OMG!" Tsalle tayi tare da hugging nasa. "Are you serious?" ta sake tambaya bayan da ta sake sa. "Yes Nazeefah" ya amsa.

"Yaushe toh?"

"I guess se idan kun gama exams naku yanzu kinga ai kina school."

"But ba wani serious lectures ma muke ba."

"A'a Nazeefah bana son wasa da karatu ai 2 months d'in kaman gobe ne karki damu kinji?"

"Toh shikenan Allah kaimu I just can't wait."

****
Haka nan tun daga ranan Nazeefah da Afzal suka soma zaman lafiya a gidan. Kullum shi yake kaita school, idan lokacin lunch yayi kuma ya d'auketa suje su ci da ikon Allah basu ta6a had'uwa da Amal ba sannan duk sanda yake gida baya kiranta gudun kar Nazeefah ta gano wani abun. A satin da ya gabato ne su Abba suka turo gaisuwa gidansu Amal inda su Papi suka amince suka kuma bada Amal. Siyayya sosai su Abba suka yi fiye da wanda Baban Abdul sukayi, kayaki se de ace masha Allah. Kaman yadda Afzal ya buk'ata haka Abba ya sanar da iyayen Amal cewa baya son a d'au lokaci kafin ayi bikin so samu idan Amal ta kammala part three nata batun kayan d'aki da gara kuma yace ya d'auke masu nauyin su kawai su amince ayi bikin ba tare da an 6ata lokaci ba. Papi beyi jayayya da hakan ba shima dama bayi da ra'ayin jan bikin idan ma da akwai abinda ze sasu jan bikin shine shirin yima Amal kayan d'aki amma yanzu da Afzal ya nuna zeyi komai sede suyi musu fatan alkhairi.

Sati uku Papi ya basu a gaba da su dawo kafin nan Amal da mahaifiyarta sun gama yanke hukunci game da ranar da za'a sanya na auren. Sosai su Abba sukayi godiya inda suka sauk'e dubu ashirin da suka tashi tafiya.

****
Haka tafiyan ta cigaba duk da kalan halatayya irin na Amal, Afzal be kariya ba, be fasa kirarta da kuma zuwa gidansu dubanta ba. Gashi duk abinda ya gani me kyau se ya sai mata ita da Nazeefah sosai yake kwatanta yin adalci a tsakaninsu. Nazeefah kuwa har yau bata san meye ake ciki ba.

Ta fannin Abdul kuwa sosai yake kewar Amal, rana baya ta6a wucewa beyi tunaninta ba sede kuma bai fasa tashi cikin dare yana rok'an Allah ya kawo masa sauk'i ba.

****
Yau bayan sallan Isha Afzal da Nazeefah suka shirya tsaf inda suke je sukaci abinci bayan nan ya wuce da ita 3G gallery inda ta sassayi jakukkuna da dama. Bayan ya biya komai sun dawo mota ya sake fita da sunan yayi mantuwa inda ua sai wa Amal tasa itama jakukkunan ya bayar aka sa masa a booth suka k'arisa gida. Project nata ta d'auko suka cigaba da yi mata daga inda suka tsaya jiya, wajajen goma tace su bari haka su kwanta yaso su cigaba gobe. Yau wankan ma a bayin d'akinsa tayi, bayan ta fito shima ya shiga yayi zuwa k'arfe sha d'aya de suka samu suka kwanta. Kaman kullum ta gangara jikinsa sede yau Afzal ya d'au niyyan mayar da Nazeefarsa cikakkiyar mace. Yau fiye da sati biyu kenan tunda ta nemi tubansa amma ba abinda ya shiga tsakaninsu. Tun Nazeefah na sa ran ze nemeta har ta dena saidai ko da wasa bata sake yi masa maganar ba ita de bata fasa da yin addu'an Allah shirya tsakaninsu ba. Kaman acikin mafarki taji ana yi mata wani irin shafa, a firgice ta bud'e ido sede kafin tace zata mik'e zaune ya rik'ota gam a jikinsa.

"Shhh!" Ya buk'aceta se anan hankalinta ya d'an kwanta. A hankali cike da dabara ya shiga sarrafata yayin da take basa had'in kai har yaci nasaran raba ta da kayan jikinta. Wannan dare de da Nazeefah ta dad'e tana jira finally Allah ya kawo mata shi, anci kuka anji dad'i duk a lokaci d'aya. A hankali har bacci me nauyi yayi gaba dasu duka sede duk lokacin da Nazeefah ta tuna yadda Afzal ya riga tarerayarta se ta murmusa acikin baccin. Wani irin gobaran sonsa ne yake ruruwa a zuciyarta ji take idan ba shi bazata iya rayuwa ba.

Kiran sallan Asuban fari Afzal ya tashi, a hankali idanunsa suka sauk'a akan Nazeefah datake manne a jikinsa se bacci take bayan da ya kunna wutan d'akin. Murmusawa yayi a hankali yayinda events na last night suka soma dawo masa ashe de raguwa take se kurun bakin tsiya. Cike da dabara ya raba jikinsa daga nata had'e da lullu6e jikinta da bargo. Bayi ya fad'a yayi wanka sannan ya d'aura alwala ya had'a mata ruwan d'umi tukuna ya fito. Bayan ya sanya jallabiyansa ya nufi kan gadon inda take bacci har yanzun.

Sunanta ya shiga kira a hankali har seda ta bud'e idonta, da sauri ta sake kullesu bayan da suka had'a ido hakan ba k'aramin murmushi ya sanya sa ba, wai kam dama Nazeefah na da kunya? Wai toh idan tana irin wannan kunyan? Amal tasa fah? Amal da ko kalamun soyayya ya fad'a mata bata sake iya kallon cikin idansa. Lallai akwai k'ura a gaba.

Gyaran murya yayi yace, "Tashi haka toh kiyi wanka muyi sallah baccin ya isa."

"Toh ka daina kallo na" tayi maganan idanta rufe gam.

"Yau kuma? Tashi kinga lokaci na k'urewa."

"Toh Ya Afzal ka tashi ni idan da hali ma ka fita idan na kimtsa zanyi maka magana" ta sanar da shi. Murmusawa yayi sosai "Yau kuma nine Yaya saboda kinji wuya jiya?"

"Ya Afzal mana" ta fad'a had'e da jawo pillow tana kare fuskanta.

"Toh naji naji, zan jiraki a parlour."

"Toh ka tafi" mik'awa yayi ya janye pillon a hankali had'e da sanya mata light peck a goshi sannan ya mik'e ya fice. Seda taji k'aran kulluwan k'ofa sannan ta shiga bud'e idon nata a hankali. Haka kawai ta tsinci kanta cikin tsananin farin ciki, se murmushi wa kanta take barin ma idan ta tuna abubuwan da Afzal ya rink'a yi mata daren jiya, yadda ya rink'a binta a hankali yana kashe mata jiki. She felt like a princess, like a baby and all. Aww she's madly in love with him, a hankali ta mik'e ta nufi bayin. Shiganta ba da jimawa ba Afzal ya dawo d'akin, bedsheet d'in ya tattara yayi disposing. Kafin ta fito har ya shimfid'a sabo ya zauna bakin gadon yana jirarta.

"Ya Afzal" ta kirasa lokacinda ta fito tana tsaye bakin k'ofar d'aure da d'an guntun towel. Kafin yayi magana har idonta ya kai ga sabon bedsheet daya shimfid'a kan gadon. "Awwn Ya Afzal ai ko ni ma zan iya canzawa it doesn't have to be you."

"Don't worry sanya kayanki muyi sallah" ya amsa. Nan da nan ta shirya ya jasu bayan sun kammala azkhar nasu suka shiga shirin office da school. Yau ma kaman kullum shi yayi dropping nata. Nazeefah fa ji take tamkar duniyan ma tayi kad'an ta d'auke ta dan murna da farin ciki kawai. Tuni ta sanya hoton Afzal a home and lock screen nata, idan ta isa gida ma zata canza na laptop nata ta sanya hoton nasa.
Da Azahar lectures nasu ya k'are saidai Afzal baze samu daman zuwa d'aukanta ba don haka ya tura driver'n Ummi da ya d'aukota kasancewar yana da meeting. Bayan da ya d'auketa se tayi tunanin ya wuce da ita gida gun Ummi ya kwana biyu basu lek'a juna ba. Sosai Ummi tayi murnan ganinta daman tana da anniyar kai masu visit this weekend saboda shirun yayi yawa. Hira suka sha sosai sekace ba surikai ba, suna cikin cin abinci ne Nazeefah tayi gyaran murya "Ummi?" Ta kirata.

"Na'am Nazeefar Mummy."

"Kai Ummi wai yaushe zaki sauk'e sunan nan ne kam?"

"Ko Nazeefar Afzal ce?"

"Toh ko kefa? Ai hakan ma yafi dad'i" nan suka k'yalk'yale da dariya.

"Ahh lallai soyayya manya wannan kumatu da kika k'ara anya kuwa ba abu a k'asa?"

"Laaa ji Ummi dan Allah ni kinga har zaki sa in mance abinda nakeson tambayarki ma wallahi."

"A'a yi hak'uri tambayan ina jinki."

"Shin mey yafi burge Ya Afzal game da mace?"

"Addini" Ummi ta amsa nan take. "Yana bala'in son mace mey addini."

"Allah Ummi?"

"Sosai ma kuwa."

"Ai kuwa ya zama dole in koma islamiyya kodan shi ma."

"Toh fa mey Prince yayi har ake neman farinta masa rai haka."

Hmm Ummi kenan ai komai ma Ya Afzal na mun jiyan nan ya kaini 3G gallery bakiga jakukkunan dana d'iba ba kuma duk ya biya makaranta yanzu kullum shi yake kaini sede idan banida lectures na safe please ki cigaba da sanyasa a addu'a keda kike mahaifiyarsa, nima inayi masa amman naki daban ne. Allah ya taimakesa ya k'ara masa bud'i."

Masha Allahu sosai Ummi taji dad'in kalamun Nazeefah ashe in de haka ne Afzal yaji fad'an da ita da Abba su kayi masa kenan. Madallah gaskiya tayi wa Nazeefah murna sede kuma alokacin da ta fara jin dad'in aurenta a lokacin Afzal yake shirin k'aro mata kishiya. Oh kowa de da tasa k'addarar, Allah de ya sa ta d'au hakan a matsayin k'addararta ta kar6a hannu bibbiyu.

"A gaskiya naji dad'in kalamanki matuk'a Nazeefah, naji dad'i yanzu da ke da Afzal kuke zaman lafiya Allah yasa hakan ya d'aure ya kuma cigaba da had'a kawunanku."

"Ameen Ummi so bayan addini sey kuma mey yakeso?"

"Addini de itace babba, kika rik'e addini to kin kama k'afansa kenan, inda so samu wannan gyale ma ki daina sanyasu in ba a gida ba, yana son mace me sanya tufafin da ze rufe mata jiki bayan nan kuma mace mey tsafta, mey kunya. Ki zame mey kunya, mey kuma kamun kai ba kowani na miji zakina huld'a dashi a makaranta ba inba wanda ya zama dole ba." Se kai Nazeefah keta gyad'awa wane mey d'aukan lectures "Nake ga idan kika kiyaye wannan ababen da na k'irga miki toh fa kin riga kin mallake Prince kin zama uwar gidansa."

"Thank you very much Ummi in shaa Allah zakiga canji wallahi ina son Ya Afzal and doing just what he likes makes me happy. A shirye nake da in sadaukar da farin cikina saboda nasa, please ki rink'a samin shi acikin addu'a Allah cigaba da karemun shi."




RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:32] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 2⃣4⃣*



"Allah cigaba da baku zaman lafiya Nazeefah ki dage da addu'a, itace komai."

"In shaa Allahu Ummi zan wuce girki na jira na."

"Toh bari ina zuwa." Kitchen ta nufa chan bada dad'ewa ba ta dawo rik'e da wasu robobi a hannunta. "Ga wannan spices ne k'awata take had'awa wannan a pepper soup zaki na sawa, wannan kuma ko a jollof ko fried rice yana gyara girki sosai nima ina amfani dasu."

"Allah sarki Ummi baki gajiya da mun kyauta kullum idan na shigo?"

"Jibeki ko kin manta a matsayin 'yata kike? Hungo kar6i ayi ma Prince girki mey dad'i yaci."

"Toh shikenan Ummi" ta amsa tana murmushi "Nagode sosai akwai leda ne se in juye in baki robobin?"

"Karki damu musamman na sai rabobin dan in zuba miki su aciki."

"Kai Ummi da wahala haka? Nagode sosai zan ko nunawa Ya Afzal bari in wuce." Har wajen mota Ummi ta rakata sannan ta dawo ciki. Driver na sauk'e ta a gida ta rage kayan jikinta ta watsa ruwa sannan ta shiga kitchen bayan ta had'a kan girkin ta d'au wayanta ta kira k'awarta Aisha mey siyar da readymade hijabs akan ta kawo mata tana son siya.

Se wajajen k'arfe biyar Afzal ya dawo gida, lokacin Nazeefah na zaune da Aisha tana kan za6an hijaban. Mik'ewa tayi had'e da yi masa sannu da zuwa, bayan sun gaisa da Aisha, ya k'arisa ciki. Nan da nan Nazeefah ta gama za6e three quarter hijabai masu hannu kusan kala goma sha biyu. Duka-duka de ya tashi N21,600 kasancewar N1,800 ne kowani guda amma k'awar nata tayi mata ragi akan N20,000.

"Toh nagode zan miki transferring kud'in banida enough cash a wajena."

"Ba komai toh zan wuce."

"Yauwa nagode" bayan tayi mata rakiya ta tattara hijaban ta wuce d'akin Afzal dasu. A lokacin yana mik'e kan gado yana latsa wayansa. A kan gadon ta jibge kayakin yayin da ya kafa mata ido yana kallonta da mamaki.

"Wad'annan fah?" Ya tambaya.

"Na wa ne" ta amsa tana jin dad'i.

"Toh kuma" ya furta yana mamakin ina zata kai hijabai dayawa haka, inde don na sallah ne kam ai sunyi yawa.

"Starting today zan soma sanya hijabi ban sake fita da gyale" ta sanar da shi tana k'ok'arin sanya d'aya daga ciki. Da mamaki cike da jin dad'i ya tsaya yana kallonta ba k'arya kuma hijabin ya mugun amsanta.

"Ya mun kyau?"

"Sosai ma kuwa RABB'ATUL BAIT (sarauniyar gida)" ya amsa yana bata full attention nasa. Sosai taji dad'in sunan dukda cewan bata san meye ma'anar ba amma ta de san abun arziki ne. "Duka wannan kika saya?" Ya tambayeta.

"Eh zan zo in k'ara ma daga baya."

"Wow! I'm really impressed Nazeefah, Allah yayi miki albarka."

"Ameen Ya Afzal."

"So duka-duka nawa ne?"

"N21,600 amma tabar mun akan N20k."

"Alright zanyi miki transferring kud'in."

"A'a kar ka damu inada enough kud'i a waje na."

"You shouldn't bother as well kiyi amfani da kud'in ki sai wani abu daban zan biya na wannan d'in kinji?"

"Toh shikenan thank you so much Allah k'ara bud'i."

"Ameen my Rabba'atul bait." Dad'i sosai ta kuma ji sede ta kasa hak'ura taji ma'anan sunan dan haka ta tambayesa. "Ya Afzal meye ma'anar Rabba'atul bait d'in?"

"Wai ashe matar tawa bata jin larabci" ya shiga neman tsokanarta.

"Kaga nifa shiyasa banason tambayar ka abu seka gama yi ma mutum dariyar mugunta tukuna amma karka damu kwanan nan zanyi joining islamiyya zaka sha mamaki."

"Dagaske zakiyi joining Islamiyya?" Ya tambayeta cike da k'in yarda.

"In shaa Allah idan muka samu hutu, ko baka so?"

"Taya bazan so matata ta shiga neman k'arin ilimin addini ba? I'm very happy in fact nima zan nemo miki islamiyyan da kaina."

"Awwn Ya Azal da gaske?"

"Sosai ma Rabba'atul bait."

"Toh gayan mey ma'anan sa?"

"It means The queen of my home (sarauniyar gida na)" bata san sanda ta shiga blushing ba. "Am I really?" Ta tambayesa cike da kunya da kuma jin dad'i.

"Yes Nazeefah you are."

"Awwn Ya Afzal thank you so much I really am in love with the name."

"You're welcome" ya amsa yana mayar mata da murmushin shima.

"I feel honored kaima ka jira nan da lokaci kad'an zan nemo maka romantic name in baka."

"Toh shikenan ina jira."

"Yau baka jin yunwa ne? Naga ko tambaya na abinci bakayi ba."

"Ai nasan food will always be ready as long as kina gidan nan so yau mey aka girka mun?"

"Fried rice ne da pepper chicken."

"Wow! Har wani fitinannen yunwa ya kamani, let's go?"

"Let's go" takawa yayi ya k'arisa inda take, da hannunta rik'e acikin nasa suka k'arisa dining d'in inda tayi serving nasa saidai spoon d'aya ya kai baki ya tsaya yana exaggerating girkin wai yayi dad'i murmusawa tayi sirrin Ummi ta fad'a a zuciyarta. Seda suka gama ci take fad'a mishi dalilin daya sa abincin yayi dad'i sosai yau, spices da Ummi ta bata ne. Sosai yaji dad'in zuwa duban Ummi da tayi ba tare da ya sanar da ita ba.


**** ****

"Abba ai wannan kaman tonawa Baby asiri ne" Mami tace da Papi yayinda suke zaune a d'akinsa.

"Kaman
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment