Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

manta mey likitanka yace? Bana son in rasaka Yaya, bana son a sanadi na ka rasa raywanka."

"Karki damu dani Amal ai ciwo ba mutuwa bace."

"In your own case mutuwa ce Yaya, bazan iya ba, bazan iya yafewa kaina ba idan har a sanandi na wani abun ya kuma samunka."

"Abdul fa? Don't you love him?"

"Yaya I'm sorry" kawai se ta rushe da kuka "But I do love Ya Abdul, I really love him so much" ta sanar dashi cikin tsananin kuka. Har cikin zuciyarsa yaji zafin kalamun nata yayinda sautin kukanta ke tada masa hankali. Mey matakin da ya kamata ya d'auka? Yana son Amal yana son kasancewa da ita amma meye amfanin ajiyeta a gurinsa idan har zuciyarta na tattare da wani daban? Sosai ya tausaya mata barin ma da yaga yadda take kukan cira rai. Ji yayi gabad'aya ya tsani kansa na jefata cikin wannan hali da yayi. Da ya sani da tun farko ya sanar da ita abinda yake zuciyansa kokuwa da ya gano tana da wanda takeso ya tattara ina inasa yabar musu garin inda hali k'asar ma gabad'aya. Sautin kukan ne ya ishesa ya shiga kiran sunanta a hankali.

"Yaya I'm sorry but I don't think I can do this" tana fad'in haka ta mik'e a guje ta wuce ciki ko ta kan su Mami batayi ba ta nufi d'akinta had'e da sa sakata ta kwanta kan katifarta ta shiga rera kuka.



RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 02:18] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 2⃣0⃣*

_My dearest Aunty Sis where're you? Here's a page I'm devoting in your honour, know that your daughter loves you hell much, Xx._ 😘



Sosai kan Mami da Papi ya d'aure barin ma ganin yadda ta shigo a guje da sukayi ko amsa kira batayi, toh kode wani abun ne ya bita? Da wuri Mami tabi bayanta ta lek'a waje don tabbatar da me ke faruwa chan kawai ta hango Afzal zaune kan benchi ya had'a tagumi. K'arisawa tayi ta zauna a gefensa sede har anan be lura da cewa ma wani ya zauna kusa da shi ba. "Afzal?" Ta kira sunansa se a karo na biyu ya amsa a firgice.

"Lafiya?" Ta tambayesa. Sam be 6oye mata mumunan halin da yake ciki ba. "Ba lafiya ba Mami" ya amsa tamkar wanda zeyi kuka.

"Meya faru? Kai da Baby ne? Yanzu naga ta shiga ciki a guje wani abun ne?"

"Mami Amal bata sona sam bata sona Abdul take so it breaks my heart watching her cry like this I can't take it anymore."

"Laaa! Bade kukan kai ma zaka yimun ba?" Ta tambaya da mamaki.

"Mami no."

"Toh ya kakeson ayi kenan?"

"Ni zan hak'ura yaso ta auri Abdul d'in kawai, farin cikinta ya fiye mun komai."

"Kaman yadda kaima lafiyarka ya fiye mata komai ba."

"Mami she's hurting alot please ku barta ta auri wanda zuciyanta keso."

"Yaushe ne zaka gane kaine za6in da Allah yayi mata Afzal? Kuma yanzu da kake biye mata d'in kai kuma ya zakayi da naka ran? Idan ban manta bafa likitanka ne yace rashin magance maka wannan matsala yana iya saka rasa ranka koba haka ba?"

"But Mami Amal's happiness comes before anything my life included."

"Kar ka kariya Afzal kar ka bari tausayinta ya rufe maka ido tabbas Amal abar a tausaya mata ce amman kai be kamata ka kariya haka gabad'aya ba. Amal na buk'atanka yanzu. Idan har bata sonka ya zame dole kenan ka koya mata. Mu mata munada laushin zuciya garemu, abu kad'an yakan karakato mana da hankali hak'uri zakayi ka nuna mata tsan-tsan so hakan ne kawai zesa ta iya mancewa da Abdul ka kuma maye gur6insa a zuciyanta amma idan ka kariya haka ai kaman ka bata dama ne ta cigaba da kewan Abdul d'in koda yaushe, Amal taka ce Afzal."

"Mami bana son ina ganinta cikin k'unci da hawaye haka duk laifi na ne gashi yanzu Amal ke shan wuya."

"Ka dena cewa haka Afzal kuskure de an riga anyisa ba kuma amfanin nanatasa kaide yanzu ne ya kamata ka nuna jarumtakarka wajen tabbatar da cewa Baby ta mance da Abdul idan ko kayi sakaci..."

"Thank you Mami."

"Karka damu duk lokacinda kake buk'atan wani abu kar ka 6ata lokaci ka taho ka sanar dani damuwanka ina nan zan kuma yi iya k'ok'arina inga na magance ma wannan matsala kaji?"

"Thank you so much."

"Ba komai zaka shiga ciki kokuwa?"

"A'a zan wuce gida but please ki samu Amal ki bata hak'uri tabar kukan haka nan."

"In shaa Allah" da haka ta rakasa gun motarsa bayan ya fice ta dawo ciki ta wuce d'akin Amal sede duk suratan da take tayi Amal tak'i tasowa ta koda bud'e mata k'ofar se kuka kawai take, k'arshe seda Papi yace ta hak'ura ta barta kawai. Tambayanta yayi ko meke faruwa inda ta zauna ta zazzage masa komai. Sosai ya tausayawa Afzal d'inma kansa tabbas ya cika masoyi na k'warai shima da har yake tunanin saudakar da rayuwansa gabad'aya saboda farin cikin Amal sede kaman yadda Mami ta fad'a kada ya kariya ya cigaba da nuna mata so a hankali zata koyi sonsa shima ta kuma manta da Abdurrahman.

Tun isan Afzal gida Nazeefah ta lura da yanayinsa gabad'aya ba walwala tattare da shi sa6anin yadda ya fita. Ko da tayi masa tayin dinner ma cewa yayi a k'oshe yake baze ci ba ya wuce d'akinsa amma bata sauraresa ba ta d'iban masa abincin ta d'au ruwa a fridge ta nufi d'akinsa. Knocking tayi bayan ya amsa ta shiga ciki. Tsince akan gadonsa ta samesa da wuri ya 6oye wayansa dayake ta faman kallon hotunan Amal k'ark'ashin pillow. Bayan ta k'ariso ta ajiye masa abincin akan side drawer tare da buk'atansa ya tashi ya ci. Beyi musu ba ya mik'e ya zauna.

"Wani abun ne yake damunka Afzal?" Ta tambayesa cikin siririn murya. "Feel free to talk to me kaji? I'm here."

"Ba komai Nazeefah" ya amsa a sakalce.

"Taya zakace ba komai bayan gabad'aya ba haka ka fita kabar gidan nan ba."

"Just pray for me kinji? Allah shige mun gaba."

"In shaa Allah I'll ga abincinka kaci kar ka kwanta akan yunwa."

"Thank you."

"You're welcome akwai wani abinda kake buk'ata?"

"Not at all."

"Alright ina parlour idan kana buk'atan wani abun." Kai zalla ya gyad'a mata yayinda ta mik'e ta fice. Abincin ya janyo ya shiga ci a hankali yayinda yake ta tunanin Amal.

Washegari...
GIDAN ALHJ A. ZARMA.

"Assalamu alaikum" Abdul yayi sallama cikin parloun Baba inda shi da Mama suke zaune.

"Wa'alaikumus salam" duka shi da Mama suka amsa. K'arisowa cikin parlourn yayi sannan ya zauna a inda ya saba zama kullum "Sannu Mama"

"Yauwa Abdul har kun taso?"

"Eh, sannu Baba ka kirani."

"Eh Abdul ya office?"

"Alhamdulillah."

Gyaran murya Baba yayi ya cigaba "D'azu manager'nku yake mun wata magana akan yana son yi maka transfer zuwa Canada ko ya gaskiyan al'amarin yake?"

"Tabbas yamun maganan amman ban kar6i transfer letter d'in bama bana so I'm not interested."

"Dalili?" Ya tambaya da mamaki.

"Baba banason inyi nisa da gida most importantly bana son inyi nisa da Amal."

"Ya kake magana haka Abdul sekace idan ka tafi ba za ka sake dawowa ba?"

"Baba duk da hakan bana so I'm okay with my job in here."

"Ka dubi kyan aikin fa Abdul ka kuma sani dama sau d'aya yake zuwa a rayuwa. Shi kansa manager'n naku cemun yayi dayawa sun samesa suna rok'ansa da ya basu aikin amman ya duba zumuncin dake tsakani na da kai ya d'auka ya baka amma kace kai baka so? Gaskiya be kamata kayi wasa da wannan damar ba, aikin tana da kyau albashi hud'u zuwa biyar fa shikenan ka zama DON (mey bala'in kud'i) na kanka ka sake tunani ai idan mu kake gudun yin kewar mu bature yayi video call idan ma Amal takan ce kuna iya yin video call da ita ko ba haka ba?"

"Hakane Baba amma ai aikin nan nawa ma nada kyau."

"Bance batada kyau ba amma sanin kanka ne ai bazaka had'a kyan albashinsa da shi na Canada d'in bako? A gaskiya tunaninkan nan beyi ba koba haka ba Hjy Binta?"

"Hakane Alhj, Babana Abdul?" Ta kirasa.

"Na'am Mama."

"Kabi shawaran Babanka kar ka bari wannan dama ta wuce ka this is your chance to build yourself into the millionaire you've always wanted zamu baka nan zuwa jibi ka zauna kayi tunani kaji?"

"Toh Mama nagode Baba zanyi tunani in shaa Allah I'll get back at you."

"Allah yima albarka Abdul."

"Ameen Baba nagode zan wuce site d'ina."

"Toh ka huta gajiya ko?" Yana ficewa Baba ya sauk'e nauyayyar ajiyar zuciya "A gaskiya keda Amal kunyi gaskiya Hjy Binta yanzu fa saboda yarinyar nan ne bayison tafiya bawai saboda mu ba."

"Ai na fad'a maka he's so attached to her Allah kawo masa sauk'i."

"Ameen."

"Amma Alhj idan har yak'i amincewa fa? Ya zamuyi? Plan namu beyi ba fa kenan."

"In shaa Allah zeyi ai aikin na da kyau."

"Toh Allah yasa, kaga idan muka samu ya tafi yanzu se ita Amal d'in ta canza layinta gabad'aya yadda komin ya yakeson samunta baze iyaba ita kuwa Maamah komin ya zeyi da ita akan ta nemo masa new line na Amal zance kar ta basa, this's the only way nake ganin ze iya rabuwa da Amal cikin sauk'i."

"In shaa Allahu wannan shawara taki tayi Hjy Binta Allah sak'a maki da mafificin alkhairi."

"Ameen Alhj"****

Bayan sallan Isha Abdul da gabad'aya kansa ya d'aure ya d'ago wayansa da aniyan kiran Amal. Shi kansa yana son aikin saboda kyansa amman kuma baya son yayi nisa da Amal baya son tafiyansa ya zame sanadin rabuwansu gashi idan ya tafi ze iya d'aukan kusan shekara ko biyu ma halan kafin ya dawo. Kai baze iya ba. A karo na biyu Amal ta d'aga wayan nasa.

"Halo Baby na?" Ta soma cewa.

"Na'am My Princess ya kike?"

"Lafiya k'alau ya office I missed you two days."

"I missed you even more office na shiga miki hak'k'i ko?"

"Sosai ma."

"Toh ya zamuyi? Gashi na samu promotion a office this time har Canada sukeson tura ni Baby."

"Har Canada?" Jin hakan kawai ta gano iyayensa has something to do with this, Allah sarki ta inda suka 6ullo masa kenan so that idan ya tafi a hankali har ya soma mancewa da ita.

"Eh Baby kuma idan na tafi I might take a year or two kafin na dawo."

"Babe congratulations nayi maka murna sosai this is such a massive promotion."

"Yes it is amman ni nak'i amincewa nama k'i kar6an transfer letter'n."

"Meyasa Baby?"

"Toh kuma haka kawai se in tafi in barki har na tsawon shekara Baby? Kina tsammanin zan iya rayuwa ba ke ne?"

"Baby yanzu danni kakeson barin wannan dama ta wuce ka?"

"I can sacrifice the whole world for you darling."

"Allah sarki Baby please don't do this, our love for one another is enough balle ma ai zamu na waya har har video call ma idan kana so amma please kar ka bari daman nan ya wuce ka saboda ni."

"Baby bana son inyi kewarki."

"I'm just a call away my Prince Charming kaji? You don't have to miss me."

"Duk da hakan my Princess nifa bazan tafi ba."

"Baby mana yanzu so kake kace zaka bar daman nan ta wuceka?"

"Ni tama riga ta wuce dan bazan tafi Canada ba tare da ke ba."

"Kana nufun idan zan bika zaka tafi?"

"Mey ze hana ni?"

"Toh Baby makaranta ta fa?"

"Ai muna iya kar6a miki transfer letter se muyi aure mu wuce chan d'in tare." Ba k'aramin hawaye kalamun sa suka sanyata ba da wuri ta share kafin ya gane kuka takeyi. Ina ma ace hakan is possible, ina ma ace za ayi musu aure su tafi Canada and start a new life together, tana ganin da duk duniya ba wanda ze kaita jin dad'i amman Yaya fa? Shin ta kyauta masa kenan idan haka kawai ta tashi ta tafi ta barsa da ciwo? Upon all the hidimomin da yayi mata a baya?

"My Baby kinyi shiru."

"Ya Abdul I want this morethan anything, ba abinda ze fiye mun kwanciyan hankali kamar rananda za'a d'aura mana aure in kasance mallakinka."

"Then let's get married princess let's do and fly to Canada together zan d'au nauyin komai karki damu kawai ki amince don Allah."

"But Ya Abdul su Mami bazasu amince ba."

"Meyasa? Ina iya turo su Baba suyi masu magana ke kawai ki amince."

"Ya Abdul kasan ina sonka ko?"

"Yes Baby I do ai kema kin san ina sonki."

"Sosai Sweetheart shiyasa nakeson ka kwantar da hankalinka, ina nan ba inda zani har kaje ka dawo ina jiranka, kaga idanma a shekara d'aya zaka dawo by then na kammala part 4 d'ina clinicals kawai ze rage mun idan kuma in two years ne kaga ma na kammala karatun kenan gabad'aya se muyi auren mu cikin kwanciyan hankali ba hanzari ba komai."

"Princess why not now?"

"Baby bana son had'a aure da karatu ne banason school yana shiga maka hak'k'i idan munyi aure."

"Princess ni ban damu ba as long as zaki amince ki tafi dani Canada."

"Baby please listen to what I told you, ina nan ba inda zani zan jiraka har kaje ka dawo, I'm yours alone."

"Meyasa nake ji ajikina bayan tafiya na wani ze min gaba dake?"

"Kuma har kake tsammanin zan amince in auri wani sama da kai? Baby shin baka yarda da soyayyan da nake yi maka bane?"

"Of cours not Princess I trust in your love but-"

"Them you don't have to worry Baby I will wait for you ko shekara nawa ne zan jira ka kaji? I love only you."

"Promise?" Hawaye na d'iga daga idonta tace, "I promise."

"Thank you Princess zan yima Baba magana suzo su samu Papi suyi masu bayani ko?"

"Baby ba amfanin hakan."

"Princess what if suka ji shirun nawa yayi yawa sukayi deciding su ba wani ke? I think is better su Baba su samesu suyi musu bayanin ina nan tafe kar su d'ay Princess d'ina suba wani chan."

"Toh shikenan Baby tunda kayi insisting seka turo su Baban suzo."

"That's my Princess."

"Tafiyan yanzu ne?"

"Eh baze fi nan da one month ba."

"Ayyah I'll miss you so much."

"I'll do that even the more Princess." Hira suka sha sosai sannan tayi masa seda safe. Washegari yaje ya samu su Baba ya musu bayanin shawaran da ya yanke, sosai suka ji dad'in amincewan da yayi amman ya nuna masu shi lalle fa se anje gidansu Amal an sanar dasu Papi batun tafiyan nasa kar bayan tafiyansa su aura mata wani. Basu masa musu ba suka amince duk dan son su 6atar da sahun abun. Koda labari ya iske Maamah, bata sha mamaki sosai ba saboda a karo na farko data fara ganin Afzal ta tabbatar da soyayyan da yakeyi wa Amal ita Ya Abdul kawai take tausayawa yanzu na k'arfi da yaji ana son turasa Canada.

Washegari kaman yadda Abdul yaso haka iyayensa suka shirya suka sake zuwa gidansu Amal duk se zolayansa suke.
A cikin wata d'aya da sati visan Abdul ya fito ya gama shiri tsaf sauran tafiya. Cikin wata d'ayan nan Amal bata ta6a d'aga waya ta kira Afzal ba saidai idan shi ya kirata shima befi sau biyu zuwa uku ya kirata ba don ya gane kaman tak'ura mata yake. Ko daga yadda take mai magana ma. Don haka se be sake kiranta ba haka kuma be sake taka k'ofar gidansu ba amma kullum da tunaninta yake kwana da kuma shi yake tashi. Sau dayawa suna fita tare da Nazeefah se yayi dropping nata a school sannan ya wuce office rananda yake da meeting d'in safe kuwa ita da kanta take tafiya. Lafiya k'alau suke zama a gidan rannam ma a d'akin Afzal ta kwana, suna cikin hira bacci yayi gaba da ita shiko be tada ita ba instead seya gyara mata kwanciyar suka yi kwanciyar su tare. Da Asuba da ya tada ita sallah kawai se ganin kanta tayi cikin d'akinsa, mamaki ne da farin ciki ya rufeta a lokaci d'aya bata d'au har Afzal ze barta ta kwana d'akinsa ba. Lallai idan mutum yayi hak'uri komai ma is possible, aiko hak'urin zata cigaba da yi har se ta gama karkato da hankalinsa akanta gabad'aya. Tana cikin sallan Asuba Afzal ya dawo daga masallaci bayan da ta idar suka gaisa sannan ta d'aga pillonta. "Ina kuma zakije?" Yayi saurin tambayarta.

"D'akina" ta sanar dashi tana kallon k'asa.

"A ina kika kwana?"

"I'm sorry ai da ka tadani jiyan."

"Ajiye pillonk kinji? You're sleeping in here." Dad'i kaman ze kashe Nazeefah mayar da pillon tayi ba musu ta kwanta chan shima yayi joining nata, bargon yaja ya rufesu suka koma bacci.

***
Ta fannin su Amal kuwa, ba k'aramin shareta Maamah ke ba, se wani kaffa-kaffa takeyi da ita sam bata sakewa da ita kaman da seda Amal ta zauna tayi mata bayanin komi dallah-dallah sannan ta kuma nuna mata how sorry she is Maamah ta amince suka sake dawo da k'awancensu na da.

Kasancewar tafiyan Abdul gobe ne yau tun da Azahar ya taho ya d'auki Amal suka wuce yawo ba shi ya dawo da ita ba se chan yamma bayan sun fito daga motan ya sa yara suka shiga mata da ledojin siyayyan da yayi mata sannan ya kira sunanta alokacin idon Amal ya cike dam da hawaye tasani daga yau kuma se idan Allah ya sake had'a su she's sure kafin ya dawo an yi mata aure da Afzal.

"Princess bade kuka kike ba?" Ya tambaya da mamaki. Kanta tayi saurin juyawa yayinda ta shiga share hawayenta. Zagayowa yayi ta gefenta "Princess so kike kisani kukan nima?" Kukan ne yaci k'arfinta sosai kawai ta fad'a jikinsa tana kukan tsuma zuciya. Tasan yin hakan haramun ne amman bazata iya jure rashinsa ba, mutuwan tsaye Abdul yayi wajen ko rik'eta ya kasa yi. Wai Amal da ko hannunta bata barin a ta6a ne ta fad'a jikinsa haka? Tunani ya fara yi anya ko lafiya? Ya yake ji kaman wannan ne had'uwansu na k'arshe? A hankali ya zagaye hannayensa a bayanta yayinda kukan nata ya tsananta, hak'uri ya shiga bata sannan ya d'agota a hankali ya shiga share mata hawayenta da handkerchief.

"Princess kukan ya isa haka kinji?"

"Ya Abdul dan Allah kar ka tafi, I can't do without you I really can't" ta fad'a cikin tsakankanin kuka.

"Amal I'm sorry but I have to, we'll keep in touch kinji? Kukan ya isa haka, idan fa kika cigaba nima zanyi" Kalamai masu kwantar da hankali yayita fad'a mata har ya samu kukan nata ya lafa a hankali har ya d'auke gabad'aya.

"That's my Princess smile toh kinji?" Sede ta kad'a masa kai da nufin a'a.

"D'an murmushin ma yau bazaki yi mun ba? Sena kira Babana na fad'a mishi" Yayi maganan had'e da turo baki wane d'an yaro. Bata san lokacinda ta fashe da dariya ba, she'll surely miss him kodan sanyata dariyan da yake yi. Hira suka sake ta6awa kad'an gun sannan ya buk'acesu da suyi last selfie, suyi a wayanta suyi a wayanshi haka suka tayi har seda suka gaji.

"Toh Maghrib ya kusa muje muyi niyya ko Baby?" Yace da ita. "Ki gaishe mun da su Mami sosai sosai."

"Toh my Baby semun sake waya ko?"

"In shaa Allah I love you so very much" ya sanar da ita.

"I love you too baby" ta amsa, a hankali ya mik'a yayi placing mata light kiss a goshi "Keep yourself safe for me okay?" Kai ta gyad'a cike da kunya ta juya ta k'arisa ciki. Washegari da safe kafin jirin su Abdul zuwa Abuja ya tashi ya kirata yayi mata sallama haka itama da suka isa ta kirasa tayi masa sannu.

The next day international flight nasu ya tashi tunda ya kira Amal don suyi sallama take faman yi masa kuka a wayan haka har ya ajiye bata fasa kukan ba. Tun Mami na bata hak'uri har tagaji ta barta. Haka nan tun tafiyan Abdul Amal ta koyi sabon sana'an kulle kanta a d'aki tayita kuka. Sau biyu Afzal na kiranta amman bata d'aga wayan nasa, yau bayan ya tashi daga office ya biya ta gidansu. Mami ya tarar a tsakar gida tana surfan wake. Bayan sun gaisa yake tambayarta ko Amal na gida.

"Gata chan a d'aki tun safe da ta fito ta karya ban sake jin motsinta ba."

"Meya sameta? Bata da lafiya ne?"

"A'a Abdul d'inne ya tafi."

"Ina?"

"Canada kode baka da labari ne?"

"Sam" ya kad'a kai. Nan ta basa labarin duk yadda akayi, ashe de dalilin daya sa ko ya kirata kwana biyu bata d'auka kenan, Allah sarki.

"Toh ni zan kai markad'e nan mak'ota zaka jira in dawo?"

"Eh Mami Allah kare."

"Ameen" ta amsa tare da ficewa. Nauyayyan ajiyar zuciya ya sauk'e sannan ya mik'e ya nufi k'ofan d'akin Amal d'in tare da placing gentle knock sede shiru tak'i amsawa. Sallama yayi next se ji tayi kaman muryansa shiru tayi ko ze sake magana don ta tabbatar.

"Lily?" Ya kirata anan ta tabbatar da cewan shi d'inne. "Lily fito kinji?" Manna masa tayi duk suratan da yata yi hakan besa ta fitowa ba daga d'akin, don kansa ya fito waje ya d'auko ledan da ya d'an yi mata sayayya tare da attaching note ajiki ya koma ya ajiye mata dab bakin k'ofan nata sannan ya fita waje ya jira dawowan Mami, tana k'arasowa yace ze wuce, se anjima tayi masa sannan ta k'arasa ciki. Chan da Amal ta tabbata Afzal d'in ya tafi wajajen Maghrib ta bud'o k'ofan d'akin nata inda ta tarar da farar leda tsugunawan da zatayi ta d'aga se note d'in ya fad'i d'agawa tayi ta karanta kaman haka;

'Here're your favorites to light up your evening, I love you Xx.'

Lek'a cikin ledar tayi taga favorite ice cream flavors nata ne da har sunyi melting da kuma chocolates, ciki ta koma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment