Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

sabida wa amininsa Sultan kad'ai ya fad'awa damuwansa ba yadda bamuyi da shi ba ya fad'a mana meke damunsa amman yak'i da k'yar muka samu abokin nasa ya bamu had'in kai ya kawo mu gidan naku." Nauyayyar ajiyar zuciya both Papi da Mami suka sauk'e as suna mamakin wannan al'amari ashede kukan da Amal ta yini take tayi kenan tun jiya na zafin rabuwa da masoyinta ne, hak'ik'a tana son Abdul. Shi ko Afzal har yanzu sun rasa dalilin da ya hanasa sanar dasu cewan yana son Amal bayan yasan ba wanda ya cancanci soyayyarta sama da shi kodan hidimomin da yake mata. Sau dayawa Papi kan zauna yayi tunanin nan na cewa anya ba son Amal yake ba shiyasa yake mata wannan hidimomi sede tun yana sa ran wataran Afzal zeyi masa maganan Amal har ya dena saboda koda wasa Afzal be ta6a d'auko masa zancenta ba. Toh meyasa? Meya hanasa? Ko gani yake ko da ya furta masu kud'urina zasu hanasa Amal d'inne? Ai shima yasan baza a ta6a yimasa haka ba toh meya hanasa sanar dasu?

"Shine muke neman alfarma a gareku, ku kad'ai keda ikon ceto mana ran d'annan idan har Allah ze baku iko, shi kad'ai ne garemu bama son mu rasa sa kuma munsan yadda tambayan hakan agareku ya nuna tsan-tsan san kanmu amman ina da tabbacin duk iyayan da suka tsinci kansu acikin halin da muke ciki haka zasuyi suma" Ummi ta sake fad'a.

"Tabbas haka yake Ummin Afzal" Mami ta nunfasa "Nima koda nice na tsinci kaina acikin halin nan da kuke ciki bazan fasa ba har se inda k'arfi na ya k'are. Abu d'aya ne ya d'aure mun kai, dalilin da ze hana Afzal sanar damu k'udurinsa akan yarinyan nan bayan yasan baza a ta6a hanasa ita ba kuma a fari ita kanta Baby nasan bazata k'i sa ba, yanzu gashi tun tafiyanki jiya ta kulle kanta a d'aki tana ta aikin kuka ko ni tak'i sanar dani meke faruwa harta Papinta ma ce masa tayi babu da aka tak'ura mata ne se take ce mana wai Afzal ne bashida lafiya likita yace yana iya rasa ransa dalilin da ke sata kukan kenan amman dukkanmu ba wanda ya yarda da hakan saboda kukan yayi yawa. D'azu shi Abdul d'inma ya shigo kuma ya nuna a shirye yake da ya turo magabatansa anytime aka basa daman hakan, a gaskiya ban san ya zamu 6ullowa al'amarin nan ba. Yaran nan sunyi nisa ba adalci bane mu raba su, ta fannin Afzal kuwa ya cancanci komi a garemu ko saboda halaccin da yayi mana ko duniya yake buk'ata inde muna da ita ya zamo dole mu basa." Sosai Ummi suka ji dad'in maganan Mami suka shiga yi mata godiya.

"Toh yanke hukunci de ba namu bane" cewan Papi "Mude zamuyi k'ok'ari muga mun karkato da hankalin ita Baby da Abdurrahman d'in idan sun amince zasu iya yin shahada su ceto mana ran Afzal walillahil hamdu amman nikam bazan iya tilasta Baby auran wanda bata so ba, shi auren dole ba shida amfani kuma kun sani."

"Wannan haka yake Alhj Muh'd" cewan Abba "Kuma a hakan ma muna godiya sosai and we pray for nothing but the best Allah sak'a muku da gidan aljannah."

"Ameen wa iyya kum" ya amsa.

"So zamu wuce duk abinda akwai dan Allah ga number na" yayi maganan had'e da zaro card nasa daga aljihunsa ya ajiye a gaban Papi "Ka min waya."

"Toh toh shikenan Allah sa mu dace."

"Ameen ameen" da haka suka musu rakiya.

"Ai dama na fad'a miki iyayen Afzal ne" fad'in Amal dake la6e jikin k'ofansu Falmata tare da ita Falmatan. Tuntuni taso komawa gida amman cin karo da tayi da motar seta fasa gashi kuma kamar yadda ta fad'an ne su Ummi ne.

"Yanzu har sunzo sun sami su Papi kenan? Amal ki hak'ura da Ya Abdul kawai nasan da k'yar ki kasance tasa."

"Falmata I love him I can't do without him."

"Ya Afzal fa? Kina nufin duk halaccin da ya miki da butulcin nan zaki sak'a masa kenan?"

"Falmata ban sani ba sun tafi barin k'arisa gida duk abinda akwai zan sanar da ke."

"Toh se anjima." Tana isa gida Papi ya kirata ta k'arisa ta zauna a tsakankaninsa da Mami. "Uwata ina kika shige?"

"Na jeni gidansu Falmata ne."

"Toh tafiyanki iyayen Afzal suka zo suka kuma sanar damu dalilin kukan da kika kwana kinayi a gidan nan tambayata itace meyasa? Meyasa kika k'i sanar dani ko Maminki halin da kike ciki kika gwammace kisha wahala ke kad'anki?"

"Papi I'm sorry ban san ya zan fara sanar daku bane shiyasa."

"Ko tunani kike zamu bada ke ga Afzal d'in ko kink'i ko kin so?" A hankali ta gyad'a kanta. "Ko kad'an Baby se wanda kike so zaki aura kinji? Alk'awari na d'auka tunda Maminki ta haife ki na cewa zan kula dake tamkar nine mahaifinki kuma bazan bada ke ba se ga wanda kikeso."

"Papi ina son Ya Abdul bana son rabuwa da shi" ta fad'a yayinda ta shiga kuka.

"Shi ko zaki aura in shaa Allah kinji? Se wanda kikeso zaki aura ki kwantar da hankalinki."

"Toh Papi Yaya kuma fah? Ya zamuyi da shi? Kana ganin munyi mai adalci kenan bisa ga duk ababen alkhairin da yayi mana a gidan nan? Ace buk'atansa ya tashi amman mun kasa biya masa saboda son kai namu?"

"Uwata meke tafe a k'wak'walwarki? Kina son Abdul?" Kai ta gyad'a take "Ba kiya kuma son Afzal ya rasa ransa?" Nanma kai tayi saurin gyad'awa "Amma kinsan bazaki iya auran maza biyu ba ko? Dole cikinsu d'aya ya hak'ura koba haka ba?"

"Hakane Papi."

"Toh wa zamu ba hak'uri? Dan ni se abinda kikeso zanyi miki."

"Papi ban sani ba nima I don't want to lose them both."

"Amman ya zama dole Baby, hungo Jamila ku shiga daga ciki duk hukuncin da kuka yanke shi zamuyi aiki akai." Yace da Mami ba gardama taja hannun Amal suka yi ciki kaman yadda Papi ya buk'ata sede banda kukan da Amal keyi ta k'i cewa komi. Daga k'arshe de Mami ta yanke hukuncin Amal zatayi istikharan kwana uku duk za6in da Allah yayi mata shi zata bi. Amal batayi musu ba ta amince da shawarar cikin dare yau ta fara.


2 days later...
"Assalamu Alaikum" Mami ta fad'a tare da sa kai cikin d'akin Amal. Hawayenta ta shiga sharewa da wurwuri sede ina Mami ta riga ta ganta. K'arisowa tayi ta zauna a gefenta had'e da kiran sunanta. "Na'am" ta amsa sama-sama.

"Yau kika kammala istikharan ko?" Kai ta gyad'a a hankali.

"Wanne cikinsu yafi kwanciya miki a rai?"

"Mami..." sekuma ta rushe da kuka, rungumota tayi tana shafa bayanta tana bata hak'uri har seda kukan nata ya lafa. "Waye ne ki gaya mun kinji?"

"Mami it can't be Yaya it just can't! What of Ya Abdul? Bana son in rasa sa" ta kuma rushewa da wani kukan.

"Afzal?" Mami ta ambata da mamaki "Shi hankalinki yafi kwanciya da?"

"Mami zan sake yin wani istikharan what of Ya Abdul? Me ze sameshi? Waze aure shi?"

"Baby za6in Allah shine mafi alkhairi idan har hankalinki yafi kwanciya da Afzal toh shine za6in da Allah yayi miki ya zamo dole ki hak'ura da Abdul nakin."

"But Mami I can't, I love Ya Abdul wallahi ina son sa kuma banjin zan iya rayuwa ba shi dan Allah karki fad'awa Papi wannan za6in zan sake yin wani istikharan."

"Baby ai ba ayin istikhara sau biyu akan matsala d'ai kuma ina da tabbacin koda kin sake d'inma still Afzal Allah ze za6a miki."

"Mami dan Allah ki bari in sakeyi please don't tell Papi."

"Baby-"

"Mami please" ta rushe jikinta tana kuka, sosai Mami ta tausaya mata daba don za6in Allah yafi ba da se suyi ma Papin k'aryan cewa Abdul ne yafi kwanciya mata a rai a shafe zancen Afzal. "Shikenan bar kukan haka zan sake baki kwana uku ki k'ara yin wani istikharan tunda abinda kikeso kenan."

"Thank you Mami."

"Shikenan toh kukan ya isa haka" tayi maganan tana share mata hawayenta. Bayan fitan Mami sega Ya Abdul na kiran Amal, hawayenta ta share ta gyara muryanta sannan ta d'aga.

"Halo my princess?"

"Na'am my Baby good morning."

"Morning ya kike?"

"Lafiya k'alau ya office?"

"Alhamdulillah baki fita school bane yau?"

"Eh."

"Baby why?"

"Gobe zan fita in shaa Allah."

"Toh Allah ya kaimu, Baby har yau bazaki bani date in turo su Baba ba? Ni ko formal introduction akayi I'm satisfied, bana son wani yazo yayi mun awuf dake."

"Bayan kasan ni kai kad'ai nakeso?"

"Even still my Princess, du da hakan inason iyayena suzo su sami su Papi."

"Ya Abdul kad'an k'ara hak'uri kad'an kaji? In shaa Allah very soon zan kasance mallakar ka kaji?"

"Promise?"

"In shaa Allah Ya Abdul."

"Thank you my Amal, I love you so much."

"I love you even more you take care."

"You too, bye" da haka sukayi sallama. Kwanciya tayi akan wayan yayinda wasu zafaffun hawayen suke shiga gangarowa akan kumatunta. Tasan 6ata lokacinta kawai take koda ta sake yin wani istikharan still Afzal Allah ze sake za6an mata but why not Ya Abdul? Ta fi son Ya Abdul akan Yaya a tunaninta kodan wannan Allah ze za6an mata shi akan Yaya but why?? Why Yaya? Kuka ta shiga yi a hankali.

****
Kwana biyar kenan yau su Abba suna sa ran kira daga gun Papi amman shiru, gabad'aya shida Ummi sun k'osa a fari ma shikam cewa yayi ko zasu sake komawa gidan nasu ne amman Ummi ta ce su k'ara hak'uri su bari zuwa gobe ko jibi idan har basu kirasu ba se su san nayi. Afzal kuwa har yau besan me ake ciki ba, lafiya k'alau suke zama da Nazeefah a gida. Kasancewar be fara fita office ba kafin ta fita school take shirya masa breakfast da lunch idan rana yayi se yayi heating a microwace yaci.

Washegari...
Tun shigowan Mami da tayi taga Amal ta baje kan sallaya tana kuka kawai ta yanke hukunci. K'arisawa tayi tare da hugging nata tana bata hak'uri "In shaa Allah Afzal shine za6i mafi alkhairi a gareki hak'uri ya zama dole kinji?"

"Mami Ya Abdul fah?" Ta d'ago daga jikin Mami tana kuka sosai idanun nata sun kunburo sunyi ja wur. "Shikenan shi ko wacce budurwa yayi ta ringa tafiya tana barinsa kenan? What if shima ciwon zuciyan ya kama sa fa? I'm sure idan ya gano for all these while I've been deceiving him ze kamu da ciwon zuciya kokuwa yayi hauka."

"Wa yace deceiving nasa kikayi Amal? K'addarace ta rabaku bawai ke kika yi niyyan barinsa ba saboda haka ki kwantar da hankalinki in shaa Allah shi Abdul d'in ze miki kyakkywar fahimta."

"No Mami no matter what karku sanar da Ya Abdul zan auri Yaya banason ya rasa hankalinsa a sanadin hakan dan Allah kar ku fad'a mishi."

"Toh ya kikeson ayi Baby? Ayita yaudararsa kenan? The earlier the better."

"I know amman karku sanar da shi direct I don't care how you do it amman karku fad'a mishi cewan zan auri Yaya wallahi ina gudun abinda hakan ze iya haifarwa."

"Shikenan zan yima Papinki bayani za'a san yadda za'a sanar da shi amma kibar kukan haka kinji?" Kai zalla ta gyad'a. Isan Mami d'akin Papi ta sanar da shi halin da ake ciki da kuma alfarman da Amal ke nema na cewa kar a sanar da Abdul direct bata son wani abun ya samesa. Dabara ce ta fad'o wa Papi bayan ya kira Abban Afzal ya sanar da shi outcome da suka samu bayan istikharan da Amal tayi Abba yayi ta godiya yace zuwa anjima ko gobe ma zasu shigo. D'akin Amal ya nufa ya buk'aceta numban Abdul inda take sake rok'ansu da komin yaya ne ita kar a sanar da Abdul direct cewa Yaya zata aura. Kwantar mata da hankali Papi yayi akan ta bar masa komi yasan yadda ze 6ullowa al'amarin. Bayan ya amshi lamban nasa ya kira sa tare da masa bayanin shi waye, bayan gaisuwa yake ce masa yana son ganin mahaifinsa idan da hali har ita mahaifiyarsan ma.

"In shaa Allah zanyi musu magana duk abinda akwai zan sanar da kai Papi nagode."

"Nine da godiya Abdul Allah yima albarka."

"Ameen" ya amsa "Toh se anjima." Isanaa gida can yamma ya watsa ruwa yad'an huta bayan sallan Isha ya samu mahaifinsa a site nasa yake sanar da shi halin da ake ciki. Sosai mahaifin nasa ya masa murna tun ba yau ba yake jiran wannan rana da Abdul ze ce masa gashi ya samu wata se gashi nan Allah ya k'addaro masa da ranan ashe da rabon zega auran d'ansa. In shaa Allahu gobe nida mahaifiyarka zamu je gidansu yarinyan kaji?"

"Toh Baba nagode."

"Yauwa d'an albarka ko 'yar wace gida ne?"

Ba 'yar babban gida bane Baba amman she's from a well respected home."

"Madallah, zamu je gobe in shaa Allah ko akwai wata matsalar?"

"A'a shikenan." Da haka yayi masa seda safe ya wuce 6angarensa. Amal ya kira yake ta faman yi mata godiya a tunaninsa gabad'aya wai ita tabada daman ayi wannan formal introduction. Itako bata nuna masa komai ba, hira suka shafa kad'an tayi masa seda safe akan gobe tana da school. Washegari iyayen Abdul sukayo gaggarumin shopping na kayan abinci yadda al'ada ya kawo suka iso gidansu Amal har da shi Abdul d'in. Bayan gaisuwa da hiran da suka d'an ta6a Abdul yayi tunanin basu waje su tattauna dan haka ya fito waje ya shiga mota yana jiransu. Anan ne Papi ya samu daman yin magana.




RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 02:16] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣9⃣*



Gyaran murya Papi yayi sannan ya numfasa "Iyayen Abdurrahman ku gafirceni, ba abinda kuke sa ran ji daga gareni nake da shirin sanar daku ba" ya ce dasu. Sosai suka shiga cikin rud'ani suka ma kasa cewa komi daga k'arshe de cikin tsan-tsan rashin fahimta Baba ya tambayesa "Ko game da mey Malam Muh'd? Ban fahimceka ba."

"Zan fara de da neman gafararku nasan ni mey laifi ne amman ku sani banida wata mafitar ne shiyasa, har cikin raina banso hakan ya kasance ba sede k'addara ta riga faruwa."

"Wannan haka yake" Baba ya amsa dukda cewan ba wai ya fahimci inda Papi ya dosa bane.

"Tabbas Abdurrahman yaro ne mai hankali da ladabi da biyayya da kuma sanin ya kamata, d'a ne da kowani mahaifi zeyi kwad'ayin samunsa a matsayin surki sede kana naka Allah na nasa. Da mahaifiyar Amal ta sanar dani batun za6in Amal akan cewa Abdurrahman ne wanda takeso take kuma son ta aura, wallahi nakega ba wanda ya kaini yin farin ciki. Sosai nayi murna saboda yadda ita Jamila ta yaba wa hankalinsa, sede wani hanzari ba gudu ba kwatsam sega wannan yaro Afzal wanda tun kamin had'uwan Amal da Abdul suke tare da Amal bawai as masoya ba a'a yadda dey kuka san shak'uwan dake tsakanin wa da k'anwa, tamkar d'an gida haka yake a gidan nan kusan kullum suna tare da Amal da Maminta. Sau dayawa nakan zauna inyi tunanin anya ko ba son 'yar nan yaron nan yake ba? Amman dai-dai da rana d'aya Afzal be ta6a nuna mana ko ita kanta Amal d'in alamomin da zema nuna cewa yana sonta ba banda hidimomin da yakeyi mata. Sati biyun da suka wuce muke samun labarin cewa ya kamu da ciwon zuciya a sanadin son Amal wanda be ta6a furtawa kowa ba. Na tsawon lokaci ya kasance masoyinta na 6oye amman ba wanda ya samu ya sanar da shi ko iyayensa ya 6oye musu zancen. Haka abun yayita cinsa barin ma idan yazo nan d'in ya tarar da ita Amal da Abdul, sau biyu yanzu kenan yake samun attack wanda shi likitansa ya nuna cewa idan har ba a magance masa wannan matsala ba to yana iya rasa ransa. Satin da ya wuce iyayensa sukazo sukayi mana bayanin halin da yake ciki suke kuma neman alfarma daga garemu na cewa a taimaka musu a had'a shi d'an nasu da Amal don ceto ransa, kar ku manta har anan shi Afzal d'in be san mey ake ciki ba. Da magana ya iske Amal kuwa ta nuna tsan-tsan rashin son rabuwanta da Abdurrahman. A matsayina na me kula da ita yazamo dole ne inyi mata abinda takeso don haka na baiwa iyayen shi yaron hak'uri akan cewa bazan iya tilasta mata auran wanda bata so ba tun farko Afzal d'in shi ya janyo komai da tuni ya d'au mataki akan soyayyar da yake yiwa yarinyar nan da anjima da wuce gurin don ba wanda ze hana sa ita kuma koni na tabbata a fari Amal bazata k'isa ba amman seda ya bari soyayyar wani ya shiga zuciyanta sannan kuma za'a zo a fara tunanin raba masoya biyu? Gaskiya na nuna musu hakan ba mey yuwu ba ne ni iyakan abinda zan iya yi shine in gwada karkato da hankalin Amal da na masoyin nata idan har sun amince zasu iya saudakar da son da suke yima junansu suyi shada su ceto masu ran d'a toh walillahil hamd amman de nikam bazan shiga tsakanin masoya biyu ba. Ita Amal da kanta tazo tayi tunani daga baya ta kuma yi la'akari da kalan hidimomi da d'awainiyyan da shi Afzal d'in yayi mata a baya taga kaman ba a kyuata masa ba idan har ba'a share mai da iyayen nasa hawaye ba. Gabad'aya de ta zamo confused ta rasa me take ciki, gashi bata son rasa Afzal alokaci d'aya kuma bata son rabuwa da masoyinta. Mahaifiyarta nan ce ta kawo shawarar cewa Amal tayi Istikhara duk za6in da Allah yayi mata se ayi amfani dashi. Idan har Abdul ne alkhairi a gareta walillahil hamd dama abinda akeso kenan se a baiwa iyayen Afzal hak'uri idan ko Afzal d'inne alkhairi a gareta se ta rungumi k'addara ta bawa Abdurrahman hak'uri. Yin hakan shine adalci saboda cikin duka 6angare biyu ba wanda zeyi jayayya da za6in Allah. Bayan da Amal ta k'are istikharan ta se za6in ya kasance Afzal amman haka nan yarinyar nan tak'i amincewa da sakamakon ba dan komi ba kuwa se don tsan-tsan son da takeyi wa Abdurrahman da kuma gudun rabuwa dashi. Kuka take tana rok'an mahaifiyarta da a sake bata wani daman ta kuma yin wani Istikharan. Yaushe akeyin istikhara sau biyu akan matsala d'aya inba abunku da yaron da soyayya ya rufe mai ido ba?" Ya tsaya tare da sakin murmushin takaici sannan ya cigaba "Haka nan aka zuba mata ido ta kuma wani istikharan sai dai still za6in d'aya ne Afzal. Gata chan har yau ta na rufe a d'akinta tana kukan rabuwa da Abdurrahman ko makaranta tak'i fita kwana biyu haka nan zata yini a d'aki tana kuka. Yanzu haka ita ta kawo shawaran kar mu sanar da Abdurrahman gaskiyan al'amarin gudun abinda hakan kan iya haifowa gwara idan ku iyayensa ku mai bayani, bata son sanadin hakan wani abu ya samesa. Dalilin da yasa na kira Abdurrahman na buk'aci idan da hali ina son ganinku kenan, nasan ba k'aramin karya muku zuciya wannan labari yayi ba amma dan Allah kuyi hak'uri ku sani bawai nuna banbanci muka soyi ba saboda munga Afzal d'an gida ne ko makamancin hakan kokuwa don kwad'ayin abin duniya muka raba Amal da Abdurrahman, kun deji rantsuwa ba kaffara wallahi da ba don wannan istikharan da 'yar nan tayi ba da ba abinda ze hanani had'ata da masoyinta don a fili ta nuna tafi son Abdul akan shi Afzal d'in dukda kalan hidima da d'awainiyan da yake yi mata hakan be rufe mata ido ba. Ina fatan zaku san yadda zaku sanar da Abdurrahman wannan labari ba tare da tsinka mai zuciya ba kamar yadda Amal ta buk'ata."

Shiru kukeji a wajen Mama kanma ta kasa magana tsan-tsan tausayawa situation da d'anta ze shiga kawai da takeyi. Ta sani idan har ya gano gaskiyan al'amarin abun bazeyi kyau ba. Wannan karo na uku kenan da yake yin rashi, jikinsa har rawa yake idan yana bata labarin Amal tsabagen yadda yake sonta yake kuma sa ran finally ya samu sanyin idanunsa kwatsam kuma se gashi. Shi de tasa k'addarar kenan, akan 'yan mata to ita fatanta Allah yasa rabuwansa da Amal shine alkhairi a garesa. Baba da jikinsa ya mutu ne shima ya numfasa yace, "Mungode Malam Muh'd da har ka sanar damu gaskiyan al'amarin baka bari kwad'ayin abin duniya ya tsole maka ido ba kayita ja mana rai da d'an namu gabad'aya. Fatana Allah yasa rabuwnshi da Amal shine mafi alkhairi a garesa itako Amal da Afzal Allah basu zaman lafiya."

"Nagode sosai da kyakkyawar fahimtar da kayi mun dukda cewan nasan hakan da ciwo nima sam ba haka naso abun nan ya kasance ba amman ku k'ara hak'uri abin ne nima yafi k'arfi na wallahi banso sake karyawa d'anku zuciya ba barin ma da Amal take cemun 'yan mata biyun da yayi a baya ma duka bezo ya k'are dasu ba d'aya mutuwa ya rabasu d'aya kuma abin bezo yayi ba, dan Allah kuyi hak'uri."

"Ba komai Malam Muh'd k'addara ta riga faruwa kuma bazamu iya ja da za6in Allah ba in shaa Allahu zamu san yadda zamu sanar da shi. Abdul yaro ne mey tawakkali ina da tabbacin zeyi muku kyakkyawar fahimta ya mik'a komi wa Allah."

"Godiya nake Alhj Zarma, Hajiya ina me sake baki hak'uri don Allah" yace da Mama da tayi lamo tun d'azun.

"Hajiya kiyi hak'uri na gane yanayin da kike ciki amman kiyi hak'uri" Mami da tun da aka fara maganan batace komi ba ta fad'a.

"Ba komai Allah sa hakan ne mafi alkhairi ga kowa."

"Ameen ya Allah" duk suka amsa.

"Toh bari zamu wuce sede akwai kayakin da suke acikin mota idan da almajirai kusa sesu shigo muku dasu" Baba ya fad'a.

"Kayaki kuma? Wasu irin kayaki kenan?" Papi yayi saurin tambaya.

"Kayan abinci de da makamancinsu."

"Ko meyasa Alhj?"

"Ji Malam Muh'd kuma da wata tambaya, yadda al'ada ya kawo de muka d'an yo cafani sede kuyi hak'uri ba yawa."

"Haba! Haba Alhj! Ai idan har muka kar6i kayan nan kuma ya zamo bamuda kunya kenan, baza ayi haka ba yadda kuka taho dashi haka zaku koma dashi mungode sosai da fahimtar mu da kukayi."

"Kaya an riga an siyo dan ku taya kuma kakeson mu koma da su? Dan Allah kar kace haka."

"A'a Alhj wallahi bazamu kar6a ba ai be ma yi fasali ba, bayan aure baze auku ba
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment