Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya gagara har seda Amal ta d'an gano wani abun don haka ta fara kawo tunanin abinda Falmata ta ta6a fad'a mata sede kuma gabad'aya abun be yi making sense mata ba. Taya wai Yaya ze fara sonta ne? Maybe kawai ya damu ne kar Ya Abdul ya d'aukar mata da hankali daga kan karatu. Amma kuma meyasa jikinsa yayi sanyi yau tun ganin Ya Abdul da yayi?
Haka har Ya Abdul yayi parking motar ya fito ya bud'e mata k'ofar Amal bata ma san yayi hakan ba.

"Baby?" Ya kirata a firgice ta d'ago kai "Sorry" wur-wur tayi ta fito suka k'arisa ciki. Bayan orders nasu sun iso Ya Abdul ya shiga ci Amal kam se ido.

"Tunaninshi kikeyi?" Ya tambayeta a hankali yana mey tsamota daga duniyan tunanin data fad'a.

"I'm sorry" ta furta tare da d'ago spoon nata.

"Fad'amun Amal mey tsakaninki da wannan Yayan naki?"

"Wallahi Ya Abdul ba komai kar kayi tunanin wani abun" tayi saurin basa amsa.

"Taya bazanyi ba Amal bayan tun da ya ganmu tare kika rasa nutsuwar ki."

"Ya Abdul wallahi ba haka bane kaima kasan kai kad'ai nakeso kai kuma zan aura kawai Yaya is a part of me ne, ya zama wani sashi a jikina wanda farin cikinsa matters to me alot bana son ganinsa a damuwa."

"Kina ganin kuma kallon mu da yayi tare ya sanya sa a matsala?"

"I fear so" ta amsa a hankali.

"Kina son shi kema?" Ido ta d'ago a razane tana kallonsa bata ta6a tsammanin irin wannan kalamu daga bakinsa ba. "Ya Abdul wani irin magana ne kuma haka?" Abinda bakinta ya iya ya furta kad'ai kenan yayinda mamaki ya gama mamaye mata zuciya.

"It's a question Amal answer me do you love him too?"

"Ya Abdul gaskiya banji dad'in wannan kalamu daga bakinka ba, bayan kasan kai kad'ai nakeso kuma kace ko ina son Yaya? I told you ni ba komai tsakani na da Yaya ko shi Yayan ne ya sameka yace maka yana so na da har zaka tambayeni ko nima ina sonsa? I'm very upset with you right now."

"I'm sorry I'm just curious, yadda yake kallona d'azu was more of na sace masa sanyin idanunsa da farin cikin rayuwansa, naga soyayyar ki a cikin idonsa Amal don't blame me." Ran Amal in yayi dubu be 6aci ba, abubuwanta ta shiga tattarawa taya akan kowa Ya Abdul ze ce mata ko tana son Yaya? Ai wannan ma iskanci ne. "Ina kuma zakije?" Yayi saurin tambayarta.

"Anywhere better than here" ta fad'a cike da 6acin rai. Hijabinta yayi saurin rik'ewa "I'm sorry I take whatever I've said back kiyi hak'uri kinji?"

"Na rasa appetite d'ina ni zan tafi gida."

"Shine nace kiyi hak'uri, yi hak'uri ki zauna kinji? I'm sorry" hak'uri yayi ta bata da k'yar ya samu ta koma ta zaunan chan bada dad'ewa ba sega Maamah ta shigo d'adi sosai Ya Abdul yaji inda yayi mata fillanci (yaransu) kan ta bawa Amal hak'uri ze koma office. Ko da yake yi mata sallama ma tak'i amsawa sam bata ji dad'in maganan da yayi mata ba.

"Meya faru ne Amal?" Maamah ta tambaya bayan ficewan Ya Abdul. "Ya na ganki haka?"

"Meya ce miki da yaren naku? Gulma ta kukayi ko?"

"Taya kuma gulmar ki? Wallahi hak'uri zalla yace in baki."

"K'arya kike na sanki da Ya Abdul nakin ai."

"Wallahi hak'uri ce zallah, tell me mey ya had'aku?"

"Yayanki ne mana" se kuma tayi shiru.

"Yayi mey?"

"Taya ze kalleni yace mun wai ko ina son Yaya ne bayan yasan sarai shi nakeso."

"Ayyah Amal kiyi hak'uri shi ba da wata manufa ya fad'a hakan ba gani yayi kaman shi Yayan naki na sonki ne."

"Aww kema abinda zakice kenan? Wai yaushe ne dukanku zaku gane cewa Yaya ba so na yake ba he's just being overly protective of me a matsayina na k'anwarsa, yanzu ko ke Ya Abdul ya ganki da wani baze had'a mishi rai bane?" Cikin 6acin rai take maganan hakan yasa Maamah ta soma bata hak'uri.

"Tabbas ze ji haushi Amal amma kuma" se kuma tayi shiru sakamakon mumunar kallon da Amal ke watsa mata.

"Amma kuma mey?" Ta tambayeta a fusace.

"Amma bakiga kallon da Yayanki yayi wa Ya Abdul ba wallahi dole Ya Abdul yaji wani iri a matsayinsa na wanda yake sonki Amal."

"Wani irin kallo yayi masa?"

"Wannan ma a gefe a tunaninki haka ne kawai Yayan naki yak'i k'arisowa su gaisa da Ya Abdul? I'm sorry to say amma Amal komin ya kika musanta Yayan nan naki sonki yake ni yanzu ba abinda yafi damuna kaman Ya Abdul, wallahi shi nake tausayawa bana son ki tafi ki barsa Amal."

"Shaidan da zaki yimun kenan Maamah a matsayinki na very close friend d'ina? So kike kice duk soyayyan da nake yi wa Yayanki na k'arya ne kenan? Wow!" Ta numfasa "I'm totally speechless dake da Yayan naki duk haushin ku nakeji yau" tana kaiwa nan ta fishe jakanta ta fice, da wuri Maamah tabi bayanta tana k'wala mata kira amma ina tak'i koda juyawa. Keke ta tsara ta wuce park daga chan ta tsari na gida. Akan gadon d'akinta ta fad'a yayinda ta shiga yin kuka. Haka kawai taji komi ya dak'ule mata kuma kuka ne kawai solution, wayanta dake ringing ta zaro daga jakarta dubawan da zatayi taga Ya Abdul ke kira dan haushi ma hanging tayi gabad'aya be dad'e ba se gashi yana sake kira nan ma kashewan ta kuma yi se a karo na biyar ta d'aga. Hak'uri ya shiga bata amman tak'i hak'uran seda yayi dagaske har kaman zeyi mata kuka a wayan sannan ya samu ya shawo kanta, yazo ma tace ita kar yazo she wants to be alone da haka sukayi sallama akan ze kirata anjima.

***
Ta fannin Afzal kuwa ikon Allah kad'ai ya kaisa gida sabida tuk'in gangancin da ya rink'ayi a hanya. Gabad'aya ji yayi rayuwarsa bata da wata ma'ana ashe haka kullum shi Abdul d'in yake kaiwa Amal ziyara makaranta? Time d'in da ya kamata shida Amal su sake shak'uwa da junansu Abdul ke amfani da ita yana matsowa kusa da zuciyar Amal? Oh Allah! D'akinsa ya zarce ko ta kan Nazeefah dake yi masa sannu da zuwa beyi ba yana isa ya fa'a kan gadonsa had'e da rik'e dai-dai saitin zuciyansa inda keyi masa k'una sosai. A d'akin ya yini ranan, k'arshe sallah ma a zaune yazo ya k'arisa saboda wani irin zazza6in daya rufesa lokaci guda. Wajajen goman dare Amal ta kira layinsa sede wayan yata ringing Afzal be d'aga ba, ko energy'n da ze mik'e ya d'au wayan daga wardrobe nasa ma bayi da shi kuma yana da tabbacin cewa Amal ce ke kira, ko mey zata fad'a masa? Haka tayita kiran nasa har ta gaji ta hak'ura. Washegari ko office Afzal ya kasa fita saboda tsananin da jikinsa yayi.

Chan Azahar Nazeefah taji shirun yayi yawa don haka tayi tunanin gwada lek'asa kode lafiya dan ko breakfast be fito yayi ba. K'ofan nasa ta gwada turewa taji a rufe da key, knocking tayita yi amman ba response. Bata 6ata lokaci ba ta zagaya ta window inda ta tarar da sumemmiyar jikin Afzal a kan sallaya. Wani irin d'ankaren ihu tasa tuni me gadi yayi kanta yana tambayarta ko lafiya. Tsabagen yadda ta tsure ta kuma rikice ko magana ta kasa banda nuni da takeyi masa da cikin d'akin da yatsa. A guje suka yo ciki ya shiga k'ok'arin 6alla k'ofar sede ina security door ce hakan seya gagara daga k'arshe welder aka kira yazo ya cire lock d'in gabad'aya, da haka ne aka samu akayi waje da Afzal. Nazeefah se kuka, ko kiran Ummi ta kasa.

Suna isa asibitin akayi emergency room da Afzal yayin da aka bawa Nazeefah wasu papers tayi signing da k'yar ta iya tayi signing d'in se anan ta shiga neman wayarta ashe ko fitowa da ita ma batayi ba. Takalman k'afaya ya duba taga ashe sawu d'aya ma na Afzal tasa. Wayan wata nurse ta ara agun ta zuba layin Mummy sannan ta kira. A karo na farko Mummy ta d'aga.

"Mummy" ta kirata cike da tashin hankali.

"Nazeefah?" Mummy ta tambaya.

"Mummy kizo kizo da sauri dan Allah" tayi maganan tana kuka.

"Meya faru? Kina ina?"

"Afzal."

"Meya samesa?" Ta tambaya take.

"Mummy kizo kawai muna TH shi kad'ansa ya sume wallahi bani bace ni ban yi mishi komi ba wallahi."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Mummy ta furta cike da tashin hankali "Shikenan ina zuwa" tana sauk'e wayan ta cigaba da salati yau Nazeefah ta gama da ita shikenan ta kashe wa mutane d'a yau ina zata sa kanta? Hasbunallahi wa ni'imal wakeel. Hannunta na kakkarwa ta nemi lamban Ummi ta shiga kira bada dad'ewa ba sega Ummi ta d'auka.

"Halo In law?" Fad'in Ummi.

"Hajiya Mariam."

"Na'am Hajiya Fatsuma ya kike?"

"Hajiya Mariam ki shirya ki taho TH yanzun ba lafiya."

"Subhanallahi waye ba lafiya? Bade autan mu ba?"

"Afzal ne kiyi sauri."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta furta yayinda zuciyarta ta tsinke "Afzal?! Afzal d'ina?? Meya samesa?"

"Wallahi nima ban sani ba yanzun Nazeefah ke sanar dani kiyi sauri kekam." Take Ummi ta ajiye wayan ta janyo hijabinta da hanzari tayi waje tana k'walla wa driver kira. Kusan a tare ita da Mummy suka isa asibitin suka nufi emergency ward inda suka tarar da Nazeefah zaune kan benci ta had'a tagumi se aikin kuka take. Da hanzari suka nufi kanta suna tambayarta ina Afzal d'in. Wani sabon kukan tasa musu a wajen tare da hugging Mummy, d'agata Mummy tayi take daga jikinta had'e da kifa mata wata zazzafan mari. Tunda Nazeefah tasan kanta ba a ta6a marinta a fuska ba se yau. Rikicaccen ihu tasa yayinda Ummi tayi sauri ta shiga tsakaninsu.

"Haba Hajiya Fatsuma! Meyayi zafi haka?"

"Kin kyauta min kenan Nazeefah? Da abinda zaki sak'a min kenan? Ai kin huta yanzu da kika tura shi har gadon asibiti burin ki ya cika."

"Mummy wallahi ni ban yi mishi komai ba Ummi wallahi bani ce sanadin halin da Afzal ke ciki ba, dan Allah ki yarda da ni wallahi a sume na tarar da shi a d'akinsa" ta jero amsa tana kuka sosai.

"K'arya kike! Nace k'arya kike" Mummy ta k'aryatata tana me sake k'ok'arin kai mata wani marin yayinda Ummi ta tareta.

"Ya isa haka please ya isa mu jira muji fitowan likitocin" da haka ne su uku suka koma suka zauna kan benchin d'azu. Nazeefah bata bar kuka ba har yanzu sede abinda ya k'aru ba wanda yayi ta kanta kuwa as duk tunanin wani hali Afzal ke ciki suke barin ma Ummi dake jin tana iya rasa ranta idan Afzal ya rasa nata. Chan red globe na d'akin ya mutu yayinda k'ofan ya bud'u revealing a doctor with two nurses behind him. A gigice su Ummi sukayi kansa suna masu jero masa tambayoyi, da k'yar ya samu sukayi shiru sannan yayi gyaran murya.

"Ko wacece mahaifiyarsa a cikinku?"

"Dukan mune" Mummy ta amsa. Kallo yayi mata na d'an lokaci sannan ya gyad'a kai "Wannan kuma fa?" Yayi nuni da Nazeefah.

"Matarsa ce" Ummi ta amsa "Please Dr ka fad'a mun ya condition na d'an nawa yake."

"Hajiya bazan 6oye miki ba amman condition na d'anki ba kyau, rayuwansa yana cikin matsala."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" dukansu uku suka furta a tare yayinda Ummi ta shiga nanata hasbunallahu wa ni'imal wakil gabad'aya hanjalinta ya fita yabar jikinta.

"Dr meya samesa?" Mummy da tayi k'arfin hali ta tambaya.

"D'anki ya kamu da ciwon zuciya, base on gwajin da muka d'auka sakamako ya nuna cewa ya samu heart attack ne dalilin sumewanda yayi kenan."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" suka kuma furtawa yayinda idanun Ummi suka kad'a sukayi ja nan take. "Heart attack? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" A raunane ta juyo tana kallon Nazeefah.

"Nazeefah mey kikayi wa Afzal? Me kikayi wa d'a na? Mey kika masa?" Take ta rushe da kuka.



RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 00:44] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣6⃣*



   Rawa bakinta yake tana kakkarwa tace, "Ummi wallahi ban yi mishi komai ba wallahi bani bace."

  "Da Allah rufa mana baki!" Mummy ta katse ta. "A jinki bama sane ne da kalan rashin hankalin da kikeyi masa a gidan? Tun yaushe yaron nan yake hak'uri dake? Gashi nan k'arshenta kin sanya masa ciwon zuciya amma karki damu komi yazo k'arshe Allah tada kafad'an shi ya rubata miki takardan sakinki ki huta shima ya huta kowa ma ya huta."

  "Mummy dan Allah kar kiyi mun haka wallahi inason Afzal kuma wallahi ni ba ni bace sanadin wannan rashin lafiyan nasa Ummi you've got to believe me" ta juyo tana kallon Ummi a raunane "Ku tambayi D'anladi me gadi wallahi ahaka muka tsince sa a d'akinsa dan Allah ku yarda dani" sede ba wanda yako kalleta a cikinsu ita kanta Ummi kuka takeyi. Mummy ko ta had'a tagumi tana tunanin yadda zata fara sanar da Daddy wannan labari me d'aci.

  "Dr dan Allah kuyi duk abinda ya kamata ku tabbata d'ana ya rayu shi kad'ai gareni bazan iya rasa saba dan Allah kuyi mun rai."

  "Karki damu Hajiya we'll keep him under an intensive care da ikon Allah ze samu sauk'i sede ku sanya sa a addu'a abu da zuciya ba guarantee, Allah de ya bashi lafiya."

  "Ameen amma Dr dakata dan Allah, shin baku gano ko mey ya jawo masa wannan ciwo ba?"

  "Tukuna muna kan jiran sauran sakamakon su fito amma ina da tabbacin cewa tunani ne yayi masa yawa dake BP nasa ma ya hau, tabbas akwai abinda yake damunsa na tsawon lokaci wanda ya rik'e a ransa yake kuma bi da zuciya."

  "Ai na fad'a" Mummy tasa baki "Bin duk kalan halayya da rashin hankalin da fand'ararriyar 'yarnan keyi masa ya jawo mai wannan ciwon zuciyan. Kinyi asara wallahi Nazeefah kinyi asara." Banda kuka ba abinda Nazeefah ke iya yi, k'iri-k'iri tasan ba ita bace da laifi amma ake blaming nata ya zatayi idan wannan labari ya iske Daddy? Wayyo nata ya k'are.

  "Nagode Dr zan iya shiga ganinsa?"

  "Sosai ma kuwa excuse me." Yana ficewa Ummi ta shige d'akin Afzal a karo na farko da idanunta suka sauk'a akansa ba se hawaye ba, kuka ta shiga yi na sosai da k'yar k'afafunta suka iya takata izuwa gefen gadon nasa. Hannu ta aza akan oxygen supply da aka sanya masa sannan ta koma gashin kansa tana shafawa a hankali yayinda take zubda hawaye sosai.

  "Afzal Ummi ce" ta furta yayinda kuka yaci k'arfinta. "Afzal Baba na Allah tada kafad'anka in shaa Allahu zaka samu sauk'i sede na rasa dalilin da zaisa kana da uwa a raye amman ka gwammaci ka rik'e damuwanka wa kanka kai kad'ai. Meyasa Prince? Idan Nazeefar ce bakaso a yau ka sanar da Abbanka wallahi mey hana raba auren nan se Allah why do you have to do this to yourself?" Rungumosa tayi tana kuka na hak'ik'a se chan ta iya ta fito daga d'akin ta nufi inda Mummy ke zaune itama ta zauna. Nazeefah dake tsaye daga gefe ne ta k'araso ta durk'usa gabanta.

  "Ummi dan Allah kiyi hak'uri kibar kukan nan haka."

  "Mey kika ma Afzal Nazeefah? Na d'au da kikazo kika sanar dani halin da kuke ciki zaki canza al'amuranki ne ku soma zaman lafiya a gidan meya faru?"

  "Ummi wallahi bani bace, duk abinda nasan ze 6ata wa Afzal rai ina k'ok'arin dainawa, wallahi ba nice sanadin rashin lafiyarsan nan ba. A sume haka muka samesa a d'akinsa da D'anladi daman tun jiya daya dawo gida ya rufe kansa a d'aki ban kuma jin motsinsa ba you have to believe me."

  "Hmmm I wish I could Nazeefah" amsan da Ummi kad'ai ta bata kenan sannan ta kau da kanta. Gun Mummy takeso ta nufa amman bata shirya shan wata marin ba dan haka ta tattara kanta taja gefe. Satan idonsu tayi sid'ak-sid'ak ta shige d'akin Afzal d'in. A hankali ta k'arisa gefen gadonsa ta tsuguna yayinda take zubda hawaye sosai. Hannunta dake kakkarwa ta d'aga ta sauk'e akan fuskarsa tana shafawa a hankali yayinda wani irin so da tausayinsa yake sake shiga zuciyarta.

  "Afzal?" Ta kirasa a raunene tana shafa gashin kansa.

  "Afzal wai nice sanadin rashin lafiyarka? Wai nice na janyo maka wannan ciwon? Dan Allah ka farfad'o ka fad'a musu ba ni bace. Afzal suna shirin rabani da kai, Afzal bazan iya rayuwa ba kai ba dan Allah ka tashi ka musu bayanin komai Afzal I love you, I love you so much and I'm not willing to let you go, I'm here, I'll always be by your side dan Allah kar ka bani kunya ka tashi." Kanta ta sauk'e akan k'irjinsa a hankali tana me cigaba da kukan tsuma zuciya. Ta dad'e a hakan badan tana so ba ta tashi ta fice se don kar azo a kamata.
  
   Abba dake Morocco Ummi ta kira ta sanar dashi halin da ake ciki. A karo na farko kan ma yak'i amincewa don yadda kansa ya d'aure. Ciwon zuciya de? A dalilin mey? A iya zamansa da Afzal be ta6a sanin Afzal nada zurfin ciki ba toh meya faru? Kode zancen Ummi gaskiya ne, Nazeefah ce ke k'untata masa shiko yake bi a rai har abun ya kai ga haka? Aiko ya zama dole a d'au mataki dan akan zumunci baze rasa ran d'ansa guda ba. Ba shiri ya shiga booking flight of return.

  Wajajen k'arfe takwas na dare likita ya dawo ya duba Afzal sede har yanzu ba cigaban da aka samu hak'uri ya basu kan su bari zuwa gobe. Ummi kam ba aikinta se kuka, har da Daddy yazo dubata ya tafi bata bar kukan ba. Ran Daddy ya matuk'ar 6aci, ya sani duk hakan na faruwa ne saboda laifin daya ta6a aikatawa, alhak'inta ne ke binsa shiyasa Allah ya basa 'ya gagararriya kamar Nazeefah. Oh Allah! Ko kallon Nazeefah da ke ta faman rantsuwa beyi ba ya fice. Sauk'a har k'asa tayi gun tana kuka me tsuma zuciya.

  Wajajen k'arfe goma Mummy tace zata tafi, Ummi na jiran tafiyan Nazeefah amma shiru koda ta tambayeta se yaushe zata tafi kuwa tace mata ita anan zata kwana sede Ummi ta hanata bata son ko cikin dare idan Afzal d'in ya tashi ganin Nazeefah akansa kuma hakan ya sake haifar masa da wata rashin lafiyar dan su duk sun gama yarda cewa Nazeefah ce sanadin komai. Haka badon tana so ba aka sa driver ya dawo da ita gida, ko abinci ta kasa ci sallah kawai tayi ta kishingid'a jikin sallaya tana kuka har bacci yayi awon gaba da ita.

  Washegari Mummy ta shirya breakfast ta kai wa Ummi haka Nazeefah ma, sede har izuwa wannan lokaci Afzal be farfad'o ba basu Ummi kad'ai ba harta shi kansa likitan ma jikinsa yayi sanyi har ya soma tunanin ko Afzal d'in ya shiga state of comma ne. Sultan da se a yau labari ke iskesa ne ya shirya ya taho. Ko daga jin batun yasan ba komai bane ze jawo wa abokin nasa ciwon zuciya banda tunanin Amal. Sosai ya tausayawa Afzal da yaga irin critical condition da yake ciki yayinda yake jin haushinsa kuma, ai dama seda ya fad'a masa ba inda zurfin ciki ze kaisa banda halak'a amman yak'i ji. Yana zaune a d'akin ne shida Ummi da Mummy Nazeefah tayi sallama zata shiga don ajiye masu basket na abincin ranan data dafa.

  "Ban ce miki kar na sake ganin kin tako k'afar ki cikin d'akin nan ba? Duk abinda kikayi masa be isheki ba nan d'in ma sekin biyosa kin k'arasa sa?" Mummy ta kurarata. Magana ma ta kasa kawai maida k'ofan tayi ta fice ta nemi gu ta zauna ta shiga kuka, shin yaushe ne zasu amince akan cewa ba ita bace sanadin wannan rashin lafiya?

  Sultan da kansa ya d'aure ne ya juyo yana kallon Mummy da tayi maganan "Aunty me kuma had'in Nazeefah da condition na Afzal? Bade ita kuke zargi ba?"

  "Da wa kakeso a zarga idan ba ita ba Sultan? Abokin naka be ta6a baka labarin kalan zaman da sukayi da ita a gidan bane?" Ta tambayesa.

  "Sure yana bani kawai de I don't think itace ta janyo masa wannan ciwo besides ai zatto ma zunubi ne kamata yayi ku jira ya farfad'o ya sanar daku da bakinsa kafin ku hau tsagwamanta haka."

  "Ko wa kakeso mu zarga? Idan ba Nazeefah ba to waye ne? Dan Allah ka sanar dani idan ma mutanen office ne I am ready to deal with them tell me Sultan" cewar Ummi.

  "Ba mutanen office bane."

  "Then waye ne?"

  "Nima bansani ba amma kam ba Nazeefah bace."

  "Allah farfad'o da Afzal d'in koma wanene ze sanar dani" cewar Ummi had'e da cigaba da shafa gashin kansa. Sallama yayi musu akan yana zuwa ze dawo anjima. Yana fita ya kira numban Amal wanda ta d'auka bada dad'ewa ba.

  "Assalamu alaikum."

"Wa'alaikumus salam" ya amsa.

  "Ya sultan ina yini?"

  "Lafiya ya kike? Kina gida?"

  "Eh lafiya?"

"Ki jirani ina zuwa" batayi musu ba tace "Allah kawo ka" ta sauk'e wayan. Anya kuwa lafiya? Yau Ya Sultan ne bashida fara'a haka ko kad'an?? Numban Afzal data gaji da kira ne ta sake gwadawa sede kaman yadda take tsammani haka ya gama ringing be d'aga ba toh meke faruwa ne? In minutes like 30 sega Sultan ya iso k'ofan gidansu. Fitowa yayi ya mata waya kan gashi bata 6ata lokaci ba ta sanya hijabinta ta fito.

  "Ya Sultan yau kaine a gidan namu?"

"Eh Amal dalili ya kawo ni" ya sanar da ita straight forward.

  "Toh ina jinka."

  "Kin ko san Afzal ba shida lafiya yanzu haka as we speak? Yana kwance a gadon asibiti rai na a hannun Allah."

  "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" tasa salati yayinda ta nemi duk wani nutsuwarta ta rasa. "Ka ce mey????" Ta tambaya bayan tsawon lokacin data d'auka.

  "Afzal na gadon asibiti haka as we speak fighting for his life" ya sake nanata mata. Take idanunta suka ciko da hawaye ashe dalilin daya sa ko ta kira baya d'agawa kenan toh meya samesa? Meya samu yayanta? Innalillahi!

  "Ya Sultan dan Allah ka fad'a min wasa kake hatsari yayi ne? Meya samesa?"

  "Wasa kuma Amal? Ana wasa da rashin lafiya ne? Ko baki gwada layinsa bane tun jiya?"

  "Wallahi kona gwada baya d'agawa se nayi tunanin ko yayi fushi dani ne."

  "Mey ya had'aku? Fad'a kukayi ne?"

  "Ya Sultan ni ba wannan ba meya samu Yaya? Hatsari yayi ne?"

  "Ko d'aya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment