Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

"Ko kad'an nide kawai na fad'a miki ne."

"Akwai wacce kake so a waje kake nufi?"

"Yes."

"Wacece ita?"

"I'm sorry Ummi but I can't tell."

"Hmm yaron nan ina tausaya maka, ina rabaka da ciwon zuciya, ba shakka kana bin soyayyar yarinyar nan ne a zuciya har ka rame kayi bak'i haka kwana biyu. Afzal ka tausayawa kanka ka dena rik'e abu a zuciya haka uhn uhn fa!" Ta ja masa kunne. Shi de shiru yayi zaune a gun yana sauraronta dan kuwa bashida abin fad'a mata, soyayyar Amal ne de baze ta6a furtawa ba.




RANA D'AYA!💖
#RD

Love... Miemiebee👄✨
[13/08, 00:39] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣5⃣*



Yana dawowa gida ya tarar da Nazeefah zaune a parlour ta sha wanka tayi kwalyanta ras tana kallo. Sannu da zuwa tayi masa tare da mik'ewa. Shiru yayi yana nazarin amsawa kokuwa chan de yace "Yauwa sannu."

"Food is ready, zaka ci anan ko in kai maka d'aki?"

"A k'oshe nake" yace da ita sama-sama yayin da ya shiga tafiya.

"Afzal shin baka jin hak'uri ne kam?" tayi sauri ta sha gabansa "Me kakeson inyi ka hak'ura?"

"Nifa ki dena bani hak'uri don bance miki ina buk'ata ba."

"Then me ke hana ka cin girki na?"

"A jinki zaki je ki samu Unmi a bayan idona ki had'a mata k'arya da gaskiya sannan kizo nan kina proving min innocence? LOL" ya sa dariyan rainin hankali. "Try harder."

"Wallahi ni ban yi maka sharri gun Ummi ba."

"Ohhh!" ya numfasa had'e da zaro lumsassun idanunsa waje "So kike kice Ummi na k'arya kenan?"

"Ni ba haka nake nufi ba kawai ce mata nayi ta baka hak'uri nothing more."

"Toh nak'i, nak'iyin hak'urin just let me."

"Afzal please mey kakeson inyi maka ka hak'ura ka dena d'aura mun fuska haka? In hak'uri ne kakeso zan yita baka shi I'm sorry but please let's put a stop to this, shin zama hakan be isheka bane?"

"Be isheni ba infact yanzu ma ya soma min dad'i, excuse me" yana kaiwa nan ya wuce d'akinsa. Sosai jikinta yayi sanyi amman dukda hakan bata kariya ba, dining ta nufa ta d'ibar mar abincin a plate ta d'au goran ruwa tayi d'akinsa luckily ta samu a bud'e. Shiga tayi taga ba kowa aciki da ta kasa kunne setaji alaman mutum a cikin bayin. Zama tayi daga gefen gadon nasa tana jiransa, be dad'e ba se gashi ya fito d'aure da towel a iya kunkuminsa yayinda droplets na ruwa ke d'iga daga kansa yana bin well defined abs nasa, omo Nazeefah ta kasa d'auke idonta daga kansa, ko kyaftawa ta kasa, yadda skin nasa ke wani glowing k'ark'ashin ranan da ya hasko d'akin kad'ai ya sata mance ina take, burinta a lokacin kawai ta aza hannunta akan jikinsa.

Ta fannin Afzal kuwa mamaki sosai ya sha da ya ganta a d'akinsa, a d'akin ma wai akan gadonsa. Gadonsa de! Shin waya bata izinin? Banda nan ga wani mayen kallon da takeyi masa wane zata cinyesa, ganin kallon nata ba na k'arewa bane yayi gyaran murya hakan ne ya dawo da ita daga duniyan tunanin data fad'a. Kanta tayi saurin sauk'arwa cike da kunya tare da mik'ewa "Dama abincin naka ne na shigo maka dashi" bata jira jin mey zey ce ba ta fice binta da kallo yayi sannan ya nufi kan abincin ya tsaya yana k'are mai kallo.

Toh kode wani abun cutarwan ta sanya masa aciki yadda ta k'osa seya ci? Yayi tunanin hakan a ransa. D'agawa yayi ya kai hancinsa dukda cewa yasan shunshuna abinci haramun ne. K'amshin spices zalla yaji ke tashi sede hakan be sanya sa cin abincin ba. Miyarwa yayi ya nufi wardrobe nasa ya ciro shorts da singlet, yana cikin sanya singlet nasan ne wayansa ya shiga ruri k'arisawa gefen gadon yayi ya d'aga ganin Amal ke kira se yaji gabad'aya jikinsa yayi sanyi ya mutu kaman wanda baze d'aga ba ya amsa.

"Halo Yaya?" Ta soma da cewa.

"Na'am Lily" ya amsa.

"Yaya are you free today?"

"Wani abu ne?"

"Na had'a maka Aldeb ne nake tunanin ko zaka zo ka d'auka."

"Kash wallahi ban tsammanin zan iya zuwa aiki ya rik'eni yanzu haka ina shirin zuwa meeting ne" yayi mata k'arya.

"Toh Yaya ya zamuyi kenan?"

"Se zuwa wani lokacin in shaa Allah Lily thank you."

"Toh ba yadda za'ayi in kai maka ne ko a gida?"

"Kibari zuwa wani lokacin kawai kinji?" Ba don tana so ba kawai tace masa "Toh shikenan Allah kaimu" da haka ta kashe wayan ta sauk'e.

"Ya wai?" Falmata da ke shirin rakata office na Afzal ta tambaya.

"Wai baze yuwu ba seko wani lokacin."

"Baze yuwu ba kuma? Wani irin juyayyan magana ne haka?"

"Wallahi ban sani ba Falmata, ban san meke damun Yaya ba ina fad'a miki tun kan lokacin da ya gane cewa Ya Abdul saurayina ne ban sake gane kan sa ba."

"Hmmm Baby kenan ke yanzu har se an zauna an fad'a miki abinda ke faruwa?"

"Abinda ke faruwa kaman ya kenan?" Ta tambaya cike da rashin fahimta.

"So kike kice wai baki san dalilin da yasa Ya Afzal ke nuna miki wannan halaye ba?"

"Wallahi ban sani ba Falmata dan Allah ki fad'a min" ta amsa tana me tattaro hankalinta duka a gareta.

"Kin deji rantsuwa ba kaffara ko? Wallahi son ki Ya Afzal yake" dum Amal taji zuciyarta ta buga, yadda kuka san an sanar da ita mutuwan Mami haka jikinta ya mutu a wajen ko k'wak'k'warar motsi ta kasa tafi minti biyu zaune shiru a wajen sannan daga bisani ta shiga kad'a kanta tana k'aryata batun Falmata "K'arya ne hakan baze ta6a faruwa ba. Ba yadda za'ayi Yaya ya fara sona, Falmata it doesn't even make sense."

"Ko meyasa? Meyasa Afzal baze fara sonki ba Amal bayan kullum kuna tare?"

"A'a Falmata dan Allah kibar zancen nan ko matan duniya sun k'are Yaya baze ta6a cewa yana son k'waila kamata ba. Ke ni bama tsarirsa bace har mey Yaya zeyi da mace kamar ni? Kiyi tunani mana."

"Shikenan Baby ki k'aryatani iya son ranki amman de gaskiya d'aya ce wallahi Ya Afzal sonki yake idan ba kishinki yake ba har mey yayi zafi don yaji kina da saurayi ransa ze 6aci yayi fushi dake? Bayan nan keda bakinki kikace tun lokacin chan har izuwa yanzu baki sake gane kansa ba kiyi tunani mana akwai 6oyayyen al'amari anan."

"Tabbas akwai amman ba wai Yaya sona yake ba."

"Toh shikenan amman de ki zauna kiyi tunani da a banza ne zeyi maki duka wannan d'awainiyyar da yake mikin Baby? Haba mana ai ko ba a fad'a miki ba yaci ace kin gano hakan da kanki ko shi d'in ki mayara dashi baho ne wanda be san meye zeyi da kud'insa ba? Kin deji rantsuwa ba wallahi ba mey maki wannan d'awainiyyar a banza in ba mahaifanki ba."

"Ni nasan Yaya, nasan abinda ze aikata da abinda baze iya ba. Komi da kika ga Yaya namun tsakaninsa da Allah ne, idan da har so na yake kaman yadda kika fad'a da idan munyi waya baze na tambaya na ya Ya Abdul ba."

"Aikin banza, wallahi 6ad'da k'afa yakeyi."

"Falmata idan har da sona Yaya yake ina da tabbacin daya furta min idan ko beyi hakan ba ze samu Papi ya fad'a masa amman beyi ko d'aya ba taya kike tsammanin zan kawo tunanin hakan a raina? Kamar yadda nasan Yaya baze kalleni da idon so ba nima wallahi bazan iya kallonshi da hakan ba so please bana son sake jin maganan nan kafin har magana ya iskesa kisa ya fara min kallon wacce bata da godiya batin duk abinda yayi min in bud'i baki ince ina sonsa."

Duk yadda Falmata taso fahimtar da Amal lamarin ina abun ya gagara ita k'wak'walwarta ma ta kasa d'aukan mata maganan, wai taya za'a ce Yaya yana sonta? Yaya deh? K'arya ne.

Chan dare wajajen k'arfe tara Amal na mik'e akan katifar ta tun tafiyan Falmata take ta tunanin abinda ta fad'a mata, ta kasa daina tunanin hakan. Wayanta dake gefenta ne ya shiga ruri yana me tsamurota daga duniyar tunanin data fad'a. Lek'awan da zatayi taga Ya Abdul ke kira ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga.

"Halo Baby?"

"Na'am My heartthrob" ta amsa. "Ya kake?"

"I miss you" yayi admitting.

LBaby I missed you too se yaushe ne zasu dawo min da kai?"

"Se ko next week."

"Har next week? Shi d'inma under question mark? Gaskia ni zan nemi wani saurayin shikenan kai kana cikin tafiye-tafiye kullum?"

"Haba girlfriend yi hak'uri mana nima ba a son raina bane, guess what?"

"Tell me."

"Akwai tsarabar dana tanadar miki."

"Kai Baby? Na meh fah?"

"Toh kuma ana sanar da mutum tsaraba ne?" Ya had'e rai tamkar tana gabansa.

"Ai ni baby'nka ce zaka iya sanar dani ko ba haka ba?"

"Kuma haka ne fah."

"Yauwa dearest ome tell me toh."

"Ina bracelet nan da Daddy ya saiwa Maamah kika ce kinason irinsa?"

"Eh Baby bear" ta amsa anxiously.

"Toh wanda Baby'nki ya saya miki har ya fi nata kyau."

"Kai Baby! Dagaske!" Tasa ihu.

"Yes Love."

"Awwwnn I love you soo much nima ina kan tanadar maka da tsarabata."

"I trust my Baby."

"Your baby is honored."

"Toh ya kike yasu Mami?"

"Lafiyansu k'alau ya chan d'in? Ina fatan ba wacce tasa maka ido kasan fa kullum se nayi maka add'ua."

"Kai Baby karki damu I'm safe."

"Ahtoh duk wacce tace maka tana sonka ma kace mata kai anyi maka mata a gida."

"An gama Baby" yayi assuring nata.

"Yauwa Baby na" hira kad'an suka k'ara tayi masa seda safe. Tana ajiye wayar tunanin Afzal ya sake dawowa mata, daga k'arshe de ta d'au wayarta ta kirasa sede har ya tsinke be d'aga ba se a karo na biyu.

"Yaya?"

"Na'am Lily" ya amsa yana mik'e akan gado daman tunaninta yake shima se gashi ta kira.

"Yaya muna fad'a ne?" Ta tambayesa.

"Kaman ya fad'a kuma Lily?"

"Yaya ai ka fini sani."

"Ban fahimce kiba Lily."

"Yaya idan wani laifin ne nayi maka ka sanar dani in baka hak'uri wallahi I miss you, Yaya ko kirana baka yi sede idan ni na kira ka, rabonka da ka kawo mana gaisuwa har na manta daga yau kace ba kada lafiya se gobe kace aiki ya rik'e ka, Yaya what is happening? Wani laifin ne nayi maka ya 6ata maka rai haka wanda ni ban sani ba?"

"Lily-"

"I'm sorry" ta katse sa "It's just that I miss you so much. I've had sleepless nights thinking about where and how I've wronged you amman nakasa figuring out komai" ta sanar da shi sincerely. Shiru Afzal yayi na d'an lokaci, gabad'aya se yaji ba dad'i tabbas yasan be kyauta mata ba kuma ko shi d'inma bawai yana jin dad'in zamansu hakan bane. He misses her dearly, he misses being with her, he misses her smiles and laughter, he misses picking up fights with her. A takaice yayi missing komai dangane da ita amman ba yadda ya iya ne. Ya zame masa dole ya nisantar da kansa daga gareta saboda gudun 6acin ransa da kuma jefa kansa acikin damuwanda yafi wannan da yake ciki yanzu. Baze iya jure ganin Amal da wani d'a na miji ba shi ba, baze iya jure ganin minti-minti wani na kiranta yana tambayan lafiyanta ba a takaice baze iya jure ganin wani d'a na miji da ba shiba yana sanya Lilirsa farin ciki, gara suyita tura tafiyan haka.

"Yaya baza kayi magana ba?" Tayi maganan yayinda idanunta ke cikowa da hawaye.

"I'm sorry kinji?" Ya tsinci kanta yana fad'a mata dan ko besan mey zey ce bayan hakan ba.

"Yaya ni ba hak'uri nakeso ba just tell me mey nayi maka in baka hak'uri wallahi bazan iya yafewa kaina ba idan har na 6ata maka rai ba tare da baka hak'uri ba" kawai seta sa kuka. "Yaya I'm sorry please forgive me."

"Lily bade kuka kike ba?" Ya tambaya da mamaki.

"Yaya taya bazan yi kuka ba bayan kana fushi dani har nagaji da had'awa Papi k'arya kullum se yace mun kunyi waya kana lafiya amman ya rasa dalilin da ke hana ka zuwa, gani yake kaman ni nayi maka wani laifin, haka sede inyi masa k'arya ince aiki ne ya rik'e ka please forgive me."

"Ya isa haka kinji? Ya isa bar kukan haka."

"I can't bazan iya ba."

"Are you free gobe?"

"Eh" ta amsa tana share hawayenta.

"Toh shikenan share hawayenki, se na shigo."

"Dagaske Yaya zaka zo?"

"Everything for my Lily. Zanzo muje duk inda kikeso."

"Toh Allah kaimu" ta amsa cike da jin dad'i.

"Ameen."

"Amma bazaka sanar dani abinda nayi maka ba ko?"

"Lily bakiyi mun laifi ba ai na sha fad'a miki Lily bata laifi."

"Toh shikenan nagode sosai ka gaishe da Nazeefah." Washegari kamar yadda yayi mata alk'awari bayan da ya dawo daga sallar jum'ah ya canza kaya ya sanya wata burgundy half jamfan daya mugun amshe skin colorsa da kuma figure. Wankan turare yayi ya sanya accessories nasa sannan ya d'au wayarsa ya fice. Yana cikin locking d'akinsa ne wayansa dake aljihu ya shiga ruri da sauri ya sa key'n ya zaro wayar se gani yayi Amal ke kira da alama don taji sa shiru ne takeson jin ko lafiya. Murmusawa kad'an yayi tare da sliding ya amsa sannan ya shiga tafiya.

"Halo Lily?"

"Yaya naji shiru kode ka canza ra'ayinka ne?"

"Na isa?"

"Toh gashi har k'arfe hud'u baka zo ba" ta amsa had'e da zum6uro baki.

"Gani nan zuwa yanzun nan ki bani like 20 minutes okay?"

"Alright toh seka iso" cike da farin ciki ta katse wayan. Nazeefah dake zaune kan kujera a parlour tuni ta cika dam da kishi, zuciyarta ta gama ta fasa sauran k'onuwa kawai. Wato duk uban wankan nan gun karuwarsa zasa ko? Da kyau ai bata basa izinin k'arisawa bakin k'ofa ba ta sha gabansa.

"Lafiya?" Ya tambayeta da mamaki had'e da d'age gira d'aya.

"Se ina kuma?" Ta tambayesa cike da kishi.

"Wai tsaya ni dake wake zaman wani ne kam a gidan nan?" Shi dariya ma ta basa.

"It doesn't matter, taya ina ji ina gani zaka gun wata daban?"

"Aww ashe kinsan inda zani" yayi maganan cike da rainin wayo.

"Wallahi bazaka ba" tasa rantsuwa.

"Hana ni zakiyi?"

"Wallahi idan ta kama zan hanaka ita karuwar taka bata san kana da aure bane?"

"Nifa na gaya miki ki dena kwatanta yarinyar nan da karuwa."

"Da malama kakeson in kwatanta da? Haba mana Afzal yanzu duk hak'urin da na baka da wanda Ummi ta baka be isheka ba, bazaka dena neme nemen matan nan ba?"

"Kar ki sake kwatantani dame neme nemen mata kuma koda nayin ma you think kina da right na min magana ne? Look at you" ya tsaya yana k'are mata kallo "Tun yaushe kika fara regarding d'ina as your husband and incase you forget I'm a husband to four wives."

"Wato ko kunyan ido na ma bakayi gar da gar kake fad'a min kana da budurwa ko?"

"Lmao kunyan mara kunya asara ko inji bahaushe?"

"Wallahi Afzal ka cigaba kuma kaji rantsuwa ba kaffara wallahi ko 'yar gidan ubanwa kake nema muddin na samu information akanta believe me sena rabaku ka nemi waje ka rubuta."

"I would love to see you try" yayi maganan disgustedly yana mey watsa mata mumunan harara sannan ya fice. Rushewa tayi gun tana kuka na hak'ik'a bata san ya akayi soyayyar Afzal ya kamata haka ba, gani take kamar idan be zame nata ba tana iya rasa rayuwarta. Oh Allah ya kawo mata sauk'i.

**
Yana isa gaban gidan nasu yayi ma Amal waya, nan da nan tayi touching over 'yar kwaliyarta ta sanya hijabinta sannan ta cire sim nata ta ajiye a gefe gudun kar Ya Abdul yazo ya kirata suna tare da Afzal hakan ya sake janyo mata wata matsalar. Da farin ciki kwance fal a ranta ta fice taje ta samesa, kamar yadda take masa fara'a shima hakan yake mata, ba k'arya sunyi kewar junansu. Hira sosai sukayi sannan ya tambayeta inda takeson suje ita dan murna ma kawai ce masa tayi suyita zagaya garin Maiduguri har se sun gaji. Haka suka d'au hanyan federal low cost chan farin Maiduguri suka kai suka sake d'auko hanyan University dake k'arshen Maiduguri daga chan suka bi ta gidan madara ya sai mata chocolates da dama. Bayan ya dawo da ita gida ta buk'aci ya jirata tana zuwa, fitowanta ta taho masa da aldeb da ginger. Sosai yaji dad'i danko yayi missing had'ad'd'en aldeb natan nan ba k'arya. Ba gardama ya amsa yayi mata godiya sannan ya tambayeta ko su Mami suna gida ya shiga su gaisa. Sosai su Papi suka ji dad'in ganinsa, sunyi hira kad'an Afzal yace ze tafi Maghrib ya gabato har waje duka suka raka sa sukayi sallama.

Haka Amal keyi duk sanda Afzal zezo mata seta cire sim nata ta ajiye, da ikon Allah kuma Afzal be sake d'auko mata maganan Ya Abdul ba, a hankali shak'uwa ya sake shiga tsakaninsu as duk abinda Amal tasan ze 6atawa Afzal rai gamw da Ya Abdul tana avoiding. Nazeefah bak'in ciki kaman ze kasheta ta rasa ya zatayi da ranta gashi har yau ta rasa information akan Amal ko idan Afzal ya fita tace zata bi bayansa kullum seya kamata seya canza gun zuwa kokuwa ya shiga nan ya shiga chan har se tayi losing track nasa. A haka ne har aka bud'e makaranta, su Amal 'yan part two. Wannan karan da kanta tayi registrations nata, koda Afzal yace ze taimaka mata ma k'i tayi tace zata iya da kanta. Bada dad'ewa ba suka fara lectures.

Yau bayan lectures ya k'are, Amal da Maamah suna zaune akan slab suna jiran Ya Abdul yazo suje su ci abinci sega Afzal na sauk'owa daga kan stairs tare da wani abokinsa wanda ya kasance assistant lecturer. Amal na ganinsa zuciyarta ta fad'i kafin tace zata tare fuskarta inaa Afzal har ya hangeta. Suna sallama da abokin nasa ya shiga dosan inda suke zaune da Maamah sede beyi nisa ba sega motan Ya Abdul yazo dai-dai gaban su Amal ya tsaya hakan yasa Afzal dakatawa shima se gani yayi mutumin ya fito cike da farin ciki ya tsaya akan su Amal. Wani irin k'ona zuciyansa ya shiga yi masa bade wannan bane saurayinta Abdul d'in ya tambayi kansa. Se chan yaga Amal ta mik'e sede har yanzun ta kasa juyawa ta kalli Afzal da k'afafunsa ke kakkarwa. Ba haka taso abun ba, bata som abinda ze 6ata wa Afzal rai. A hankali ta juyo tana kallonsa, excusing kanta tayi daga gun Ya Abdul akan tana zuwa, nan ta nufi gun Afzal yayinda shi da Maamah suka zuba mata ido. Tana k'arisawa ta la6e daga jikin wata bishiya.

"Yaya" ta kirasa cike da kunya ko kallon cikin idanunsa ta kasa. Danne zuciyarsa yayi da k'yar ya iya amsata "Na'am Lily."

"Yaya good afternoon."

"Afternoon ya lectures?"

"Alhamdulillah Yaya shine zaka shigo school ba zaka sanar dani ba?"

"Ba zama zanyi ba shiyasa lemmi get going" ya sanar da ita yana neman juyawa.

"Yaya bazaka tsaya ku gaisa da Ya Abdul ba? Tun ba yau ba yake son ku had'u."

D'aga ido yai ya kalli Ya Abdul dake kallonsa shima, kau da kansa yayi take yace da ita, "Maybe next time Lily I'll be late for the meeting" be bata daman sake magana ba ya fice ya nufi motarsa tare da bata wuta. Kaman wanda k'wai ya fashewa a ciki Amal ta k'arisa gun su Maamah da suke kallonta har anan.

"Omg! Amal kinga ban yi mana submitting assignment namu ba, lemmi hurry" Maamah ta fad'a kafin Amal tace mata ai nayi d'azu har ta fice dama da gan-gan tace hakan don ta basu daman yin magana ne don tasan ko ba'a tambaya ba Ya Abdul na da abin cewa game da wannan abinda ya faru yanzu.

"Amal?" Ya kira sunanta a hankali bayan ficewan Maamah sede sam hankalinta yabar jikinta. "Amal?" Ya sake kirarta se a karo na uku ta amsa a firgice. "Amal meya faru?"

"Babu I'm sorry mu tafi ko?"

"Ba inda zamu sekin fad'amin abinda ke damunki."

"Allah babu komai Ya Abdul lets go yunwa nakeji." Hijabinta ya ja seda ya zaunar da ita sannan ya zauna agefenta tare da barin rata a tsakaninsu. "Meya faru tell me kinji? Waye wancan da ya tafin?"

"Ina Yaya na da nake fad'a maka? Shine ya tafi yanzun." A lokaci guda Ya Abdul yaji zuciyansa ya tsinke karde d'an wannan ne yayan da Amal ke damunsa da shi kullum? Lallai akwai k'ura shi a iya tunaninsa wani babba ne da ya girmesa ashe de yaro ne, ai ko be tambaya ba yasan ya girmesa. Inko wannan ne yayan nata shikenan ya tabbatar da zarginsa batun lokacin da Amal tace masa yayanta yayi fushi saboda yaji tana da saurayi.

"Baki fad'a masa ina son mu gaisa ba?"

"I told him yace wai yana da meeting seko wataran" amsanta ne ya sake tabbatar masa da zarginsa ba shakka kaman yadda yake gudu wannan yayan nata sonta yake. Shin ita Amal bata sani bane? Kokuwa bata son shi ne? Amman kuma daga yadda take mganansa mutum ma ze san tana sonsa. Yau ya zeyi? Baya son ya rasa Amal baze iya jura rashinta ba.
Ka kwantar da zuciyanka wata ra'ayin tace dashi dan kawai be k'ariso kun gaisa ba doesn't mean yana gaba da kai ne ko wani abun ze iya yuwu wa meeting d'in zasa dagaske. Hakan ne ya d'an kwantar masa da hankali amma fa still hankalinsa be bar tashi.

"Tashi muje kici abinci toh, you're hungry aren't you?" Kai ta gyad'a masa "Maamah fah?"

"She'll catch up with us mu tafi" ba gardama ta mik'e ta bisa a baya sede tun da ta shiga motar har suka isa restaurant d'in Amal shiru take a motar gabad'aya hankalinta ya duk'ufa akan Afzal. Duk yadda yaso 6oye haushi da kishin daya tokaresa yau da ya ga Ya Abdul abin
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment