Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yana jiran ta soma magana dukda cewan yayi mamakin ganin kirarta amman dake yasan halin matar nasa, tunaninsa gabad'aya yayi kan ko so take ta sanar dashi kud'inta ya k'are ne ya hankad'o mata wasu.

Ganin ba mahalicci se Allah mutumiyarku tayi gyaran murya had'e da cewa "Halo?"

"Yes?" Ya amsa cikin sleepy husky like voice nasa. Rasa na cewa ma tayi, tace ya isa lafiya ne? Toh ai tun shekaran jiya yayi tafiyar chan de ta gaishe sa kawai "Ina yini?"

"Lafiya" ya amsa casually, "Ya kike?"

"Lafiya k'alau ya aiki?"

"Alhamdulillah."

"Dama nace in ji ko kana lafiya."

"Toh thank you I'm good ba wata matsala dai ko?"

"Babu."

"Toh yayi kyau."

"Nace gobe zan fita gidan k'awata, ina neman uzuri."

"Kikace?" Afzal da mamaki ya rufesa ya tambaya tun yana a mik'e akan gadon nasa har ya tashi ya zauna besani ba, kode gizo kunnensa ke masa ne? Har Nazeefah ce zata kira waya ta gaishesa musamman don ta tambayesa izini? Lallai yau za ayi ruwan mutane.

"Nace zani gidan k'awata gobe, am I permitted?"

"Sure you're, kikaje ki gaisheta."

"Toh seda safe."

"Yauwa Allah tashe mu" da haka sukayi sallama. "Phewww!" Ta sauk'e ajiyar zuciya yayinda shima yayi haka ta d'ayan 6angaren. Afzal yana mey mamakin anya kuwa wannan Nazeefah ce yayin da ita kanta take tambayar kanta anya kuwa itace??

Ranan da Afzal ze dawo ne Nazeefah ta fad'a cikin kan zata mai girki sede da zaran ta motsa d'auko tukunya se wata ra'ayin ta hanata kan cewa har na me zata masa girki? Ai seya d'au sonsa take, yayinda wata ra'ayin ke ce mata mey aciki don tayiwa mijijta girki, besides ma ai ya sanar da ita ranan da ze dawo. Haka dey tayi nan tayi chan daga k'arshe girkin da ba azo anyi ba kenan. Haka nan ya dawo gidan dry ta nad'e k'afa a kan kujera tana kallo. Sannu da zuwa kad'ai ta masa ya amsa ya wuce d'akinsa. Yana watsa ruwa ya canza kaya ya fito se buga k'amshi yake, ko bata tambaya ba tasan gidansu Amal ze wuce. Wani irin zazzafan kishi ne ya tokareta ji take kaman ta rik'o k'afarsa ta hanasa fitan.

Da ta zauna tayi nazari kuma se taga ai duk laifinta ne da ace ta dafa masa abinci da sede tace yaje dining yaci hakan baze ma samu daman fita ba. Holy sh*t.

Kaman Nazeefah ta sani gidansu Amal direct Afzal ya wuce inda aka shirya masa abinci kala-kala ga smoothies d'innan ba wanda Amal bata had'a ba su Ginger ne, zo6o da kuma Aldeb nasa. Sosai ya ji dad'i, dalilin da ya hanasa cin abinci kenan through out yau saboda yasan Amal bazata taresa da dry hannu ba. Zama yayi ya gabza abincin sosai har ya buk'aci a sa masa ragowar a kula ya tafi dashi gida. Amal se dariya take tana neman tsokanansa tana kiransa glutton. Da yazo tafiya ne ya ciro masu tsarabar laces daya musu ita da Mami.

****
Haka nan tafiya ta cigaba har hutun su Amal ya k'are suka shiga second semester. Ita da Ya Abdul fa se abinda yayi gaba shi de har yanzu be furta mata kalamun so ba, but with the way he's being so extra ita kanta Amal tasan relationship nasu ya tashi daga friendship ya koma wani abun daban. A rana se suyi waya sau biyu zuwa uku, har Mami ta fara sa mata ido tana zata k'wace wayan idan batayi hankali ba. Ana nan ana nan kwatsam rana d'aya Ya Abdul ya fad'awa Amal abinda ya juma yake son sanar da ita kan yana sonta, so kuma na aure. A wannan lokaci itama Amal ba k'arya ta fad'a kogin sonsa, saboda ko be kirata a waya ba, ita zata d'au wayarta ta kirasa. Tunda ya furta mata wannan kalamu ta daina d'aga wayansa ko message ya mata bata responding, ba k'aramin tashin hankali ta sanya sa ciki ba gabad'aya ya rasa meke masa dad'i. Gun k'anwarsa Maamah ya nufa yayi mata bayanin abinda ke faruwa kan dan Allah ta taimaka masa. Kwantar mai da hankali tayi ta kuma tabbatar masa da cewa in shaa Allah Amal ta sa ce saboda ita ta riga ta gane Amal na sonsa. Washegari ko school Amal tak'i fita sanin the moment ta fita zasu had'u da Maamah itako zata kira Ya Abdul ta had'asu don haka ta fake a gida da cewan cikinta na ciwo.

Da misalin k'arfe goma Afzal ya kirata bayan sun gaisa yake tambayarta lectures take ce mai bata ji dad'i ba yau tana gida amman da sauk'i yanzu haka. "Se yau za'a same ki kenan Lily" yace da ita afterwards.

"Kamar ya Yaya?" Ta tambayesa cike da rashin fahimta.

"Throughout last week koda na kiraki kullum line busy nakeji wa muka samu haka?"

"Kai Yaya ba kowa fa idan ka kira kaji line busy to da da Maamah nake waya."

"Anya kuwa Lily?"

"Dagaske Yaya."

"Toh shikenan Allah k'ara sauk'i."

"Ameen thank you." Da haka sukayi sallama bata kaiga ajiye wayan ba se ga call na Ya Abdul kaman wacce bazata d'aga ba seda call d'in ya kusa tsinkewa ta d'aga had'e da yin shiru.

"Alhamdulillah" ta ji ya furta "Amal?" Shiru tayi "Amal kuma bazaki amsa ba?"

"Ina kwana?" Ta gaishesa a hankali.

LAmal mey nayi da zan fuskanci wannan hukunci daga gareki? Don't you think hukuncin nan naki yamin tsauri dayawa?"

"I'm sorry."

"Amal in sona ne bazaki iya yi ba you could have simply told me, I was worried sick about you gashi yau ko school kin k'i fita duk don gudun karki had'u da ni ne?"

"Nifa ba haka bane, cikina ne yake ciwo."

"Why do I feel like you're lying?"

"I'm sorry" haka kawai ta tsinci kanta tana basa hak'uri ba gaira ba dalili ko de don ita kanta tasan abinda tayi masa bata kyauta masa bane?

"Look I take back what I said to you kinji? Na gane you can't love me back but please karki 6ata friendship dake tsakanin mu I cherish our friendship alot Amal."

"Ya Abdul ka dena magana haka."

"Toh ya kikeson inyi Amal? Haka kawai kika dena recieving calls d'ina kina ignoring d'ina anyhow."

"I'm sorry."

"It's okay abu d'aya nakeson tambayanki Amal please give me a sincere answer."

"What is it?"

"Who's the lucky guy da ya rigani sace zuciyarki? I'm sure this's all about him."

"Wallahi ba kowa Ya Abdul I just need some space."

"You mean I still have hope?"

"In zaka iya jira" ta amsa bayan tsawon lokacin da ta d'auka.

"Amal I'm ready to wait for eternity for you, Amal ba zaki gane irin soyayyan da nake miki ba, it's been long since I felt this. Amal out of the blue kika sace min zuciya, I love and adore everything about you and I'm willing to wait for you for as how long it takes until you're ready. Amal I love you."

"Ya Abdul..." se kuma tayi shiru.

Yes Amal I love you and am not ashamed of it ko a gaban waye zan fad'a, I love you Amal."

"Thank you Ya Abdul."

"Gobe ki fita school kinji?"

"Ni banida lafiya" ta fad'a stubbornly.

"Haba beautiful? Duk don gudun kar inzo d'aukan Maamah mu had'u ne? Ki kwantar da hankalinki ni gobe ma zanyi tafiya."

"Tafiya kuma Ya Abdul?" Alokaci d'aya se taji kuma tana missing nasa.

"Ba abinda kikeso ba kenan."

"A'a fa ni bance ba."

"Toh zaki fita school gobe inzo in kun tashi?"

"Eh kazo."

Does this means you missed me too?"

"Ya Abdul yes, I missed you" ta amsa cuke da kunya ita kad'ai ce a d'akin amman tana kare fuskarta da pillow.

"Wow!" Yayi exclaiming cike da murna da farin ciki "That's my girl, I miss you even more, so se na zo ko?"

"Toh Allah kaimu"

"Ameen, you take care okay? I love you."

You take care too" da haka ta karse wayar tare da rungume ta. Haka kawai ta tsinci kanta tana murmushi ita kad'anta there's no denying itama tana son Ya Abdul halan fiye da yadda yake jin yana sonta ma kawai de as a lady her ego comes before her feelings.

*****
Mu kwana mu tashi be ragar da komi ba, haka tun Amal tana 6oyewa Ya Abdul soyayyarta ta shiga nunawa, haka zata la6e a d'aki kaman tana bacci amman waya take. A school kuwa yawancin in sun fita break shima Ya Abdul seya kar6i excuse a office ya fito su had'u su sha firarsu. Afzal kuwa kasancewar ya samu cigaba a office, daga Assistant manager ya koma manager sam baya samun zama kullum cikin aiki yake da tafiye-tafiye hakan ya bawa Amal da Ya Abdul daman sake shak'uwa sosai.

Yau bayan juma'a Amal na karanta suratu Kahf wayarta ya shiga ruri dubawan da zatayi taga Afzal ke kira, wai wata sabon gani. D'agawa tayi take had'e da cewa, "Yau Yaya ya tuna dani kenan."

"In ban tuna dake ba ai ke bakida niyyan kira na."

"Inji wa Yaya? Wallahi kullum kana raina banason tak'ura maka da kira ne saboda naga kaman aiki na maka yawa yanzu."

"Toh ya kike?"

"I'm fine just that am missing you."

"I miss you too Lily ya school?"

"School lafiya k'alau."

"Ki fito ina bakin k'ofa." Dum taji zuciyarta ta buga a tunaninta gabad'aya Afzal baya gari ne, dan kuwa yanzun sukayi waya da Ya Abdul yace mata yana tahowa ya zatayi idan yazo ya iskesu da Afzal? Yau nata ya k'are me hana afzal kurara ta se Allah motan wani kawai ta shiga seda ya kusan cinyeta bale ace har ta kawo saurayi gida?
"Halo Lily? Fitowan ne baza kiyi ba sena k'ariso ciki da kaina?"

"A'a Yaya gani nan fitowa" daga nan ta ajiye wayan. Zagin kanta ta shiga yi, meyasa bata ce masa bata gida ba? Sede sarai tasan halinsa yana iya cewa bari ya k'ariso su gaisa da Mami, daga nan kuma Mami ta fallasheta. Numban Ya Abdul ta kira take don sanar dashi kar yazo yanzu ya bari se anjima zata fita sede kash two missed calls ta masa amman bai kusa. Yau akeyinta! Ta furta a ranta.

Qur'anin ta mayar mazauninsa ta d'an shafa powder da jan baki taja hijabinta ta sanya ta d'an feffeshe da turare sannan ta fice. Tun da ta fito Afzal dake zaune cikin motansa yake binta da kallo yayinda ya tsinci kansa cikin wani irin walwala da farin ciki maras misaltuwa. Se gani yake kaman yau ya fara sanya ta a idanunsa, tana k'arisawa cikin motan k'amshin turarenta ya mamaye ciki. "Kyau kenan Lily?" Ya ce da ita yana murmushi sosai.

"Kai Yaya" ta amsa tana kare fuskanta da hijabin nata "Dan Allah ka dena sani jin kunyanka."

"Ai kuwa sede ki dunga cin kunyan nawa don bazan fasa fad'a miki kinyi kyau ba Lily."

"Toh ai kaima kayi kyau in fact kullum ma cikin baza kyau kake."

"Hakane?"

"Sosai ma Yaya."

"Toh tsaya in d'aukeki hoto."

"Yaya wai kai se mutum yayi muni zaka ce zaka mai hoto?"

"Kika sake cewa kinyi muni zamuyi fad'a."

"Toh na dena amman d-" flash na cameran daya haskata ne y rufa mata baki. "Haba mana Yaya!"

"Tsaya mana kiga kinyi kyau" tsayawan tayi ya nuna mata se kuma taga batayi muni ba "See? I told you tsaya mu k'ara miki d'aya." Daidaita zamanta tayi daram tayi posing yayin da ya haska mata flash ras ta fito ta kuma yi bala'in kyau.

"Toh saura kai, kaima ka tsaya a d'aukeka."

"Ce miki akayi maza suna hoto?"

"Yimin yanga de Yaya" ta kai ga d'aukan wayanta a inda ta ajiye kenan sega Ya Abdul na kira kafin tace zata janye inaa har idon Afzal sun karance mishi sunan wanda ke kira as
"LOML❤🔐" meaning 'Love Of My Life' danqaree! Ba zuciyan Amal kad'ai bane ya buga harta na Afzal, infact nasa ma yafi nata tsinkewa take wajen yaji jikinsa yayi sanyi lissss. A hankali ta janye wayan, yadda ta kasa d'agawa haka ta kasa katsewa ta bari se ringing yake, yana tsinkewa Ya Abdul ya shiga kira again se a karo na biyu ne ta katse.

"Mey na katsewa kuma?" Afzal ya tambayeta yana me k'ok'arin 6oye kishi, k'unci da bak'in cikin da ya fad'a aciki.

"Ba important call bane" ta fad'a a hankali, gabad'aya kunya yabi ya mamayeta ba haka taso sanar da Afzal batun Ya Abdul ba.

"Love of our live yana kira kice ba important call ba Lily?"

"Yaya please-" tana cikin maganan ne Ya Abdul ya shiga kira again bata kaiga katsewa ba Afzal yace, "You're excused, jeki amsa ina jiranki."

"Yaya I can call him back later."

"Ni nace ai kije Lily kar ki damu" kallonsa tayi one last time sannan ta sauk'a daga motan ta ke6e gefe guda. Afzal da yake ji tamkar na lahira ma yafisa jin dad'i besan lokacinda ya tada motan ba ya fice a guje ji kawai Amal tayi iska ya wuceta, juyawan da zatayi taga motan Afzal ne bata san lokacinda ta bawa Ya Abdul hak'uri akan anjima zasuyi magana ba ta katse wayar.

Yau kashinta ya bushe!


RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨

[13/08, 00:36] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣4⃣*



Tuk'in ganganci Afzal ke wane wanda ke shirin afka hatsari da gan-gan, ikon Allah ne kawai ya kaisa gida nan ma da yayi parking ya fito ko ta kan motan beyi ba bale ya zara key har ya rufe k'ofar, a wangale ya barota ya k'ariso ciki. Yana bankad'e k'ofan ciki se ga Nazeefah a shirye tsaf da alama ma fita take shirin yi.

"Yauwa Afzal zani suna ina buk'atan 5k" ta tambayesa ba tare da ta karanci halin da yake ciki ba, don 6acin rai Afzal ko kallonta beyi ba bale ma ya amsata, yazo wuceta kenan ta kira sunansa "Afzal magana fa nake."

"Nace bani da shi!" ya sanar da ita a tsawa ce. Ranta ne ya mugun 6aci dan rainin hankali banzan 5k ne ze tsaya yana mata walak'anci akai? Ai ba wai ta rasa 5k d'in bane itama kawai de don tana neman k'ari ne, ma ba laifinsa bane ita ta tambaya. "Wallahi kama kanka izinin ma na fasa tambaya" tace dashi yana cikin tafiyar.

"Karki tambayan kuma dan Allah in kin fitan karki sake tako k'afarki gidan nan aikin banza kawai" yana kaiwa nan ya wuce d'akinsa bang! Taji yayi banging k'ofar kad'an ya rage bata ci tuntu6e ba don yadda ta firgita.

Anya kuwa lafiya? ta tambayi kanta. K'arisawa waje tayi garin fito da motarta daga parking lot taga k'ofan motan Afzal a bud'e, lek'awan da zatayi taga motar ma a kunne ya barta nan ne ta tabbatar da cewa lallai-lallai something went wrong somewhere. Key'n ta zara ta kashe motan ta dawo ciki ta ajiye mai sannan tayi ficewarta.

Tun shigansa ciki ya fad'a kan gado ya kwanta can anjima ya mik'e ya shiga zagaya d'akin yayi nan yayi chan ba tunanin da be yi ba akan Amal da wannan mutumin da yaga tayi saving lambansa as 'LOML❤🔐', gabad'aya ya rasa meke masa dad'i. Hannunsa da ya d'aga kawai yakai jikin bango, blow ya rink'a kai wa bangon yadda kuka san baya jin zafin a jikinsa, kafin ace me hannun nasa duk ya faffashe yana yoyon jini, ana cikin haka ne wayansa dake aljihunsa ya soma ruri, be damu ya cie bale ma ya duba wa ke kira ba se a karo na biyu. Ganin Amal ke kira kawai yaji zuciyansa ya sake 6aci yayin da ya shiga tafasa yana masa wani irin k'ona wurgi yayi da wayar seda ta rugurguje a k'asa (Allah sarki iphone 7) sauk'a har k'asa yayi yana wani irin kakkarwa. Mutum na iya rantsewa aljanu ne suke aiki a kansa. Idonsa ya rufe gam bud'ewan da zeyi sega hawaye na tsiyaya. Yau ran maza ya 6aci! Yafi minti goma durk'ushe a wajen, jini se tsiyaya yake daga hannun nasa, a takaice de yayi staining kan tiles d'in gabad'aya. Daga bisani ya mik'e ya shiga bayi ya bud'e tap tare da sa hannunsa k'ark'ashin running water d'in. Kun de san yadda sabon ciwo ke rad'ad'i idan ruwa ya ta6a toh k'una da rad'ad'in da zuciyan Afzal keyi masa kwatankwacin hakan ne. Bayan da ya wanke ciwon ne ya rage kayan jikinsa ya watsa ruwa sannan ya fito yayi dressing hannun nasa ya mik'e a kan gado.

Ta fannin Amal kuwa hauka ne kawai batayi ba layin nasa ta cigaba da kira ammana inaa se switched off yake ta cemata, private number'nsa da take kira shima switched off ke cewa dake layin a kashe ne. Gabad'aya ta rasa me ke mata dad'i, ashe da tun farko ta sanar da Afzal d'in batun Ya Abdul, a ganinta da abubuwa bazasu cha6e haka ba dan kuwa ita ko da wasa bata kawo a ranta wai kishinta Afzal yake ba, a nata tunanin ta d'au kawai he's being over protective of her ne as her big bro. Ta d'au wai haushi Afzal yaji saboda bata sanar dashi kan cewa wani ya nemeta ba har sun daidaita, little did she know shi kansa Afzal d'in sonta yake. Har dare yayi har washegari bata fasa kiran layin nasa amman inaa se switched off yake ce mata, bayan data tashi daga school yau ta biya ta office nasa sede da mamaki securities suka ce mata ai be fito aiki ba yau kwata-kwata akan bey ji dad'in jikinsa ba. Wani sabon tashin hankalin ta fad'a, mey ke damun sa? Shin jikin yayi tsanani ne kokuwa? An rik'eshi a asibiti ne kokuwa yana jinya a gida? She needs to find out. Sede kamar yadda bata san gidansa ba haka kuma bata san gidansu ba balantana taje gun Ummi taji meke faruwa. Office nasu Sultan ta wuce chan ma ta tarar baya nan wai sun wuce meeting, zama tayi kusan na awa tana jiran dawowansa amman shiru dan haka kawai ta hak'ura ta komo gida. Tana isa gida ta watsa ruwa tad'an huta chan ta d'ago wayarta ta sake gwada numban Afzal luckily private line nasan ya shiga sede har ya tsinke be d'aga ba, a karo na biyu data gwada kuwa se yake ce mata number cannot be reached ko meye dalili? Ashe blocking contact natan Afzal yayi yasa a call divert yadda baza ta ta6a iya samunsa ba.

The following day still Afzal be fita office ba. Nazeefah kuwa ta rasa dalilin da ke sanya sa ababen da yakeyi kwana biyu, ko abincin da ya saba fita yana saya ma bata ga yayi ba yau, bayan nan ga bandejin data gani nannad'e a hannunsa. Ta duba dustbins na gidan kap bata ga fasassun glass ba bale ache ko yanka ya samu shin meke faruwa ne? Tun da ya kulle kansa a d'aki bey sake fita ba se zuwa masallaci kad'ai ke fitar dashi. Gwada tambayansa meya faru tayi inda sukayi baram-baram. Akan me don ta damu dashi tana tambayansa meke damunsa ze tsaya yana mata masifa? Aikin banza. Bayan kwana biyu da faruwan abun ne Afzal ya soma fita office, hannun nasa da sauk'i kam amman still be since d'aurin ba saboda ba k'aramin ciwo ya jima kansa ba.

"Triple A ina ka 6oye ne wai kam kwana biyu?" Kafin Afzal ya amsa idon Sultan ya kai ga bandejin dake d'aure a hannun Afzal "Tsaya bandejin mey haka?" ya tambaya nan take.

"Babu banji dad'i bane kwana biyu."

"Afzal I've known you for morethan 20 years kar kayi tsammanin zaka iya 6oye min abu. Amininka ne ni idan baka fad'a mun damuwanka ba mawa zaka fad'awa?"

"Maza ba wani abu serious bane ciwon ciki ne ya rik'eni two days se kuma jiya na yanke da glass that's all."

"Toh Allah sawwak'e ya cikin naka?"

"Da sauk'i ya office?"

"Alhamdulillah dama nace barin dubaka kwana biyu lines naka duka basu shiga."

"An sace wayan ai sena sai sabo tukun."

"Subhanallah private line naka fa? Har shima switched off yake cemun idan na kira."

"Kasan ban cika kunnasa ba shi" Sarai Sultan yasan k'arya Afzal ke masa kawai baya son yayi pushing nasa ne saboda yasan halin abokin nasa abu kad'an kan 6ata masa rai kafin su hankara se suyi kaca-kaca anan. "Toh lemmi go back to work."

"Alright take care" da haka sukayi sallama Sultan ya fice. Da yamma Sultan na zaune a office nasa PA'nsa tayi knocking ta shigo take ce mai yayi bak'uwa.
Bak'uwa de ya tambaya inda take jaddada masa eh. "Toh ki shigo da ita" yace mata. Ko da yaga Amal ce beyi mamaki ba saboda yasani dama komin rinsti da Amal Afzal ya samu matsala, yana da tabbacin ita kad'ai ce zata iya d'agawa Afzal hankali haka saboda tun ba yau ba ya karanci Afzal nason Amal.

"Amal?" Ya kirata.

"Na'am Ya Sultan" ta amsa tare da k'arisawa ciki ta tsaya. "Ina yini?" Ta gaishesa "K'ariso ki zauna kinji?" Ba gardama ta k'arisa ta zauna inda suka gaisa. "Yau kuma kin tuna dani kenan" yace da ita tamkar besan meke tafe da ita ba.

"Ai Ya Sultan kullum sede bamu had'u da Yaya ba se nace ya gaishe ka."

"Toh nide sak'on ki be ta6a iske ni ba."

"Afuwan toh."

"Ba komai, meke tafe dake ko de gaisuwa ce kawai?"

"Eh toh duka biyu" ta fad'a tana nazari.

"Toh ina sauraronki."

"Ya Sultan taimakonka nake nema don Allah."

"Game da mey kenan?"

"Yaya, Ya Afzal."

"Meya faru?"

"Yau kwana hud'u kenan ko biyar bana iya samunsa ta waya, koda naje office nasa kuma se acemun baya nan ya fita meeting dan Allah ka taimakeni."

"Wait hold on, mey ya had'aku? Fad'a kukayi ne?"

"Wallahi sam" se kuma tayi shiru bata san ta ina zata fara masa bayani ba tace mishi saurayinta ya kirata a gaban Afzal ne shikenan shi kuma ya hau zuciya yayi fushi da ita ko mey? Yau tana cikin wani yanayi.

"Feel free to talk to me kinji?"

"Ya Sultan wallahi da nasan ransa ze 6aci da tun farko da Ya Abdul ya tinkareni da kalman so da bazan amince ba kokuwa da zan sanar da shi Yayan wallahi bansan ransa ze 6aci haka ba."

"Hold on,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment