Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yake ta faman chatting da Nazeefah k'ark'ashin pillow yana pretending kaman yana bacci. "Habib Albi?" Ta kirasa shiru yayi yak'i amsawa a hankali yakejin takunta har lokacin da ta k'ariso kan gadon ta zaune gefensa.

"Habib Albi bazaka ci abinci ba?" Nan ma shiru yayi mata sarai kuma tasan ba bacci yake ba. Hijabinta ta cire ta kwanta a d'an space dake gabansa had'e da kwantar da kanta a k'irjinsa tana mey zagaye hannunta kan cikinsa sannan ta ja musu bargo ta rufesu. "Goodnight Habib Albi I love you" ta furta a hankali bacci me wuya ya d'auketa chan tukuna shima Afzal baccin ya d'aukesa.
Kasancewar tana da morning lectures washegari se suka gama shiri kusan a tare, dukda cewan se shareta Afzal yake. Yau kwata-kwata ma k'in karyawa yayi wai ze fita da azumi. Gano itama school zata se yayi mata k'arya wai bazeyi ya kaita ba yana da meeting driver ya kaita kawai. Kud'in makarantar ta ya ajye mata ya fice ko kiss daya saba yi mata beyi ba yau haka ma jiya. Na matuk'a hankalin Amal ya tashi ta rasa mey tayi Afzal yake yi mata haka, Maamah ce ta karanci yanayinta a makaranta ta tambayeta ko lafiya.

"Babu" ta amsa.

"Taya zakice babu Amal? Tun d'azu fa na lura banda tunani ba a inda kike tayi mey ne?"

"Maamah it's Yaya."

"What about him."

"Wallahi ni kaina ban sani ba, na rasa gane meke damunsa kusan sati kenan yau idan yazo baya sakewa dani seda yata d'aura mun fuska ko girki na baya son chi d'an tsaraban daya saba siyo mun idan ze dawo gida ma ya daina I don't know why."

"Subhanallahi Ya Afzal d'in?"

"Wallahi aka ce mun Yaya zemin haka wataran bazan yarda ba kinga tun da ya fita office jiya be dawo ba se kusan goman dare nasan sarai ba wani meeting da sukayi k'arya yake mun gashi ba kiran duniyan da ban masa ba haka yata ignoring calls d'ina maganan da nake miki haka yanzu ko nema na bayayi."

"Ikon Allah this's serious toh ke mey kikayi masa? Am very sure Ya Afzal baze fara shareki haka kawai ba dole da akwai sila."

"Wallahi ban yi masa komai ba Maamah I can't take this anymore bana jin dad'in yadda Yaya yake fushi da ni haka wallahi ko karatu na kasa yi jiya gashi muna da test gobe I can't stop thinking about him, I miss him so much bazan iya rayuwa ba shi ba" ta k'are maganan idanunta na cikowa da hawaye.

"Ke kuwa kar kiyi kuka mana" Maamah tayi maganan tana kwantar da ita a jikinta "Yi hak'uri don't cry komi mey wuce wa ne."

"Har zuwa yaushe toh Maamah?"

"Kiga toh kiyi confronting nasa mana ki tambayesa mey kikayi yake shareki haka talk to him Amal silence is never a solution."

"Maamah bana son hakan ya 6ata masa rai."

"Toh haka zaku cigaba da zama ne? Har zuwa yaushe? Kiyi masa magana dole da akwai abu a k'asa tunda shi yak'i yayi confronting naki ai ke se kiyi hala wani laifin kikayi masa baki sani ba."

"Bazan iya ba mey zan fara ce masa? Bana son yaga kaman rashin kunya nake shirin yi masa I respect him alot."

"Ai ba rashin kunya aka ce kiyi masa ba Amal cike da kissa zaki tambayesa idan laifi kikayi masa ya yafe miki da haka har ze sanar dake abinda kikayi masa seku daidaita tsakaninku."

"Okay I'll try."

"Yauwa yanzu tashi muje muyi karatu nasan idan kika je gida ba iyawa zakiyi ba in shaa Allah everything will be fine."




RANA D'AYA!
#RD

Love... King MiemiebeeπŸ‘„βœ¨
[13/08, 09:38] β€ͺ+234 907 483 8352‬: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
πŸŽ€β£πŸŽ€
❣❣

πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
*RANA D'AYA!*
πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
August, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by MiemiebeeπŸ‘„_


*PAGE 3⃣3⃣*



Se yamma Amal ta dawo gida bayan sun k'are karatu da Maamah. Driver na sauk'eta ta zarce d'akinsu inda ta tarar da Afzal yana shirin komawa gun Nazeefah ko sannu da zuwa beyi mata ba hasali yi ma yayi tamkar be ganta ba. Itace tayi gyaran murya ta gaishesa tukun ya amsa sama-sama.
"Zan koma gida gun Nazeefah ga kud'inki ajiye a gaban mirror" ya sanar da ita.

"Habib Albi tun yanzu zaka tafi?" Ta tambayesa tana mey duban agogo dududu 5:17 ne amma yake zancen nan bayan se pass 6 yake tafiya kullum.

"Eh wani abu ne?"

"Habib Albi ko ka mance da alk'awarin da kayi mun?"

"Na mey fa?"

"Kace kafin ka tafi zamuyi wanka tare I miss bathing with you Habib Albi, I really do" tayi admitting abun tausayi. Kau da kansa yayi gudun kar tausayinta ya kama sa.

"Nata jiranki baki dawo ba Amal ni kuma sauri nake maybe next time."

"Abinci fa kaci? Nasa Safiyya ta maka microwaving sauce d'in ta dafa maka white rice tayi?"

"A k'oshe nake karki damu na wuce."

"Yaya" ta kira sunansa da sauri lokacinda ya shiga takawa chak ya tsaya had'e da kewayowa.

"Wani abu ne?" So take tayi masa magana kaman yadda Maamah tace da ita amma inaa bata jin zata iya, mugun nauyinsa takeji bata son a sanadin hakan yaga kaman rashin kunya take son yi masa don haka kawai tayi shiru. "Sauri nake" ya sanar da ita.

"Ermm nace Allah dawo da kai lafiya ka gaishe da Nazeefah idan ka isa."

"Kaman dagaske" ya furta chan ciki-ciki.

"Na'am?" Ta tambaya kasancewar bata jisa da kyau ba.

"Nace naji" da haka ya fice Allah kare Safiyya dake sharan parlour tayi mishi sannan ya k'arisa.

Safiyya na ganin fitansa tayi hanzari ta kammala sharan nata da wuri ta wuce d'akinta inda tasa key ta danna wa Nazeefah kira bayan sun gaisa take ce mata, "Aunty bazaki amince da abinda nake shirin fad'a miki ba."

"Mene meya faru?"

"Hmm yanzun Uncle ya bar gida toh kafin ya fito ina cikin share corridon d'akinsu naji su suna magana da Aunty."

"Wai mey suke cewa?"

"Nide ban gane kan zancen nasu ba amma naji tana ce masa wai yayi mata alk'awarin zasuyi wanka tare se gashi kafin ta dawo daga makaranta har yayi wankansa ya gama shiri."

"Wanka tare?!" Nazeefah ta tambaya da d'umbun mamaki "Wanka tare de?" Ta sake nanatawa yayinda ta kasa amincewa da hakan.

"Wallahi Aunty."

"Kaiiii inaaaa! Baki ji su da kyau ba, wannan k'arya ne."

"Wallahi na jisu da kyau Aunty kuma daman tun ba yau ba ina zaton hakan dan akwai ranan da abokin Uncle yazo Uncle Sultan se yace inje inyi ma Uncle magana toh dana k'arisa d'akin nasu sena tarar da k'ofan a bud'e nayita sallama amman shiru chan dana kasa kunne najiyo hayaniyansu acikin bayin."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un wallahi Amal mak'ira ce, shegiya 'yar asiri toh dan ubanta bazeyi wankan ba kiji mun karuwanci fah! Wato har wanka ma sukeyi tare? Chab!"

"Hmm wallahi ko amma kuma kinsan tun dawowan Uncle wannan karan ko fita sau d'aya basuyi ba? Jiya kanma da tayi masa breakfast k'in ci yayi yace wai nice zan yi masa baya son nata. Bayan nan zama da sukeyi a parlour suyi kallo ma basuyi yanzu gashi banda d'ad'd'aure mata fuska ba abinda yakeyi yau tana da makaranta da safe amma yak'i kaita sa6anin kullum yace se de driver ya kaita shi yana da gun da zasa. Maganan da nake miki yanzu ko tsinke ban ga ya siyo mata ba tun zuwan sannan."

"Ai kibari kad'an ta gani da izinin Allah se Ya Afzal ya tsani taka k'afa acikin gidanta kede kiyi k'ok'ari ki sato min littafin makarantar ta guda d'aya mu samu copy na handwriting nata, zata gani ba har wanka sukeyi ba? Allah kawo shi gida."

"Zanyi k'ok'ari in samo miki bari in gudu ina kan aiki."

"Jeki Safiyya aikin ki na kyau se anjima."

"Toh se anjima" da haka sukayi sallama.

Fresh flowers Afzal ya tsaya ya amsa mata a florist shop sannan ya k'arisa sede har ya shigo parlourn bata mik'e tayi masa sannu da zuwa ba ko sallamansa ma k'in amsawa tayi. Da mamaki kwance a fuskansa ya k'arisa kan kujerar da take zaune ya zauna daga gefe.

"Rabba'atul Bait I'm home" ya sanar da ita.

"Sannu da zuwa" tace da shi zalla ba walwala tattare da ita.

"Rabba'atul Bait what's wrong?" Hannunta ya gwada rik'ewa wanda tayi saurin wabcewa "Sweetheart please talk to me keda nake marmarin in dawo wajenki saboda ki cire min bak'in cikin da 'yar uwarki ta cusa mun kuma kike haka? What have I done this time?"

"Ai mey hali bai ta6a fasawa amma nagode." Cike da rashin fahimta ya tambayeta "Mey kike nufi Rabba'atul Bait please talk to me."

"Ni de wallahi na gaji bazan iya ba da rashin mutuncin nan da tokari tunda baka sona kawai ka sallameni in tafi gida gun Mummy yaso ka cigaba da sha'aninka da amaryarka."

"Wani irin magana kuma kike haka Rabba'atul Bait sanin kanki ne ina sonki kuma bazan iya rayuwa ba ke ba."

"Wallahi baka sona Ya Rouhi" ta fad'a tana cika idonta da hawayen munafirci.

"Please don't cry darling."

"Ka daina kira na darling tunda ba sona har zuciya kake ba, idan da har ka d'auke ni da muhimmanci kaman yadda na d'auke ka da Amal baza tana kirana tana mun gori ba."

"Amal?"

"Eh ita."

"Oh Dear! Mey wancan ta kira kuma ta sake ce miki? Wallahi we're not on good terms with her girkinta haka ban d'ana ba tun zuwa na, mey tace miki?" Ya tambayeta ransa na 6aci.

"Ni baza ka ji komai daga bakina ba har ga Allah bazan so in had'a kanku ba amma de ka cigaba wallahi ranan da komi ya isheni tattara kayakina zanyi in koma gida inyi ma Daddy magana asan ya za'ayi tunda gashi a fili ka nuna baka sona kuma baza ka iya yin adalci a tsakanin mu ba. Ka nunawa Amal ni ba kowa bace banida daraja a idonka idan ba haka ba taya zata na kira na tana gaya mun magana iya son ranta?"

"Nazeefah please calm down ke kanki kinsan I'll never do this to you, I love and respect you alot, dan Allah ki daina magana haka kiyi hak'uri mey yayi zafi da zakice zaki koma gida? Believe me duk abinda Amal ta kira tace miki nayi mata wallahi k'arya take don ko tsinke ban sai na bata ma tun komawa na."

"Ai idan da har ba kayi mata abubuwan dagaske da koda wasa bazata kira tace mun gashi ba nasan ba k'arya take mun ba."

"Ni ke miki miki k'aryan kenan Rabba'atul Bait? Please tell me what is it that Amal told you."

"Ka kirata ka tambayeta da kanka ni bazan had'a kanku ba."

"Ita d'in ba so take ta had'a kanmu ba take kiran ki take miki k'arerayi a waya? Please tell me."

"Dan tamun haka nima senayi mata? Ai ko addini cewa yayi karka sak'a wa mutumin da yayi maka sharri da sharri Allah ma shaida ne ni da zuciya d'aya na d'auki Amal amma ita kam ba haka bane."

"Rabba'atul Bait wallahi ba k'arya nake miki ba I and Amal aren't even speaking to each other ko tamun magana shareta nake saboda na gaji da kalan abubuwan da take yi miki, I'm tired."

"I'm not buying any of your lies again Ya Rouhi zaka ce mun bakuwa magana da Amal bayan d'azun nan na kirata dan mu gaisa take ce min kana jiranta a tub zakuyi wanka tare."

"Amal d'in?"

"K'arya zanyi maka ne?" wayanta ta janyo ta shiga call logs ta nuna mai wayan da sukayi da Amal d'in. Kuma tabbas ta kirata d'azu sun gaisa amma bawai Amal tayi mata magana makamancin haka ba.

"Innalillahi!" Ya furta cike da tashin hankali "Wallahi tallahi k'arya take yi miki Nazeefah-"

"A'a Ya Afzal" tayi saurin katsesa "Karka 6ata lokacinka, ba seka mun bayanin komai ba na riga na fahimceka na sani kafi son Amal akai na dama idan ba ni da shashanci bama taya zan had'a soyayyan da kake mun da wacce kake yima Amal ita da take matar so a gareka bayan ni auran had'i akayi mana? Ni abu d'aya nake buk'ata kawai ka sawwak'e mun in koma gida bazan iya ba da wannan walak'anci da cin fuska" ta k'are tare da rushewa da kuka. Sosai ransa ya mugun 6aci yayinda wutan tsanan Amal ke sake ruruwa a zuciyarsa. Gabad'aya ji yayi ta fita masa a rai, amma ko tana tattare da babban asara.
"Rabba'atul Bait" ya kira sunanta cike da tausayi yana mey k'ok'arin rungumarta sede tayi saurin janye jikinta yayinda ta cigaba da kuka.

"Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri kibar kukan haka I'm dearly sorry."

"Ka rik'e hak'urinka Ya Afzal ba laifinka bane don zuciyarka ta fi kwanciya da Amal akai na, ni kawai ka sawwak'e mun zey fiye mun kwanciyan hankali idan ina gida gun iyayena."

"Please don't talk like this wallahi k'arya Amal take yi miki you have to believe me" a hankali ya janyota jikinsa yana hugging nata "Idan kika tafi wa ze zame Rabba'atul Bait d'ina? Please stop crying I love you and you know it isn't that all that matters Sweetheart? By Allah duk abinda Amal ta ce miki nayi mata k'arya ne ki yarda da ni" be d'agota ba seda tabar kukan munafircin nata. Hak'uri yayi ta bata ranan throughout chan dare da yazo yin wanka yace suyi tare Nazeefah tana so tana kaiwa kasuwa wai ita baza tayi ba. Lalashinta yata yi har seda ta amince suka shiga bayin wasa suka yita yi sannan sukayi wanka a k'arshe ya sanyata sukayi alwalan bacci kaman yadda Amal ke tunasar masa kullum. Da kansa ya sanya mata kayan baccinta sannan suka kwanta inda yata tattalinta yana mata wasu irin abubuwan da tuni yasa ta fita daga hayyacinta. Wani irin so na musamman Afzal ya shiga nunawa Nazeefah na d'an kwana biyun da sukayi, ji yayi kaman kada ya tafi da kwanansa ya k'are sam baya sha'awan komawa gun Amal gabad'aya ta fita akansa da abubuwan da takeyi.

"Ya Rouhi har six baka fara shirin tafiya ba ka manta yau kwanan ka ya k'are anan?"

"Ba se gobe ba?"

"Gobe kuma? Da Allah ka tashi ka shirya kar mu shiga hak'k'in Amal."

"She can wait se bayan Maghrib zan tafi."

"Ni baza ayi rashin adalcin nan da ni ba gaskiya."

"Tashi ka shirya Ya Rouhi."

"Zo ki d'agani toh."

"Ni da kai wa ze d'aga wani?"

"We wouldn't know until you give it a try so zo ki d'agani" bata sake musu ba ta k'arisa kan gadon. Hannun sa ta kama ta shiga ja sede ko motsawa baiyi a lokaci d'aya ya jata bata sauk'a ako ina ba se akan jikinsa inda sukayi gware.

"Awch!" Ta furta tana murza goshin nata "Ya Rouhi!" Tayi exclaiming.

"Toh ai na fiki jin zafi."

"Tayaya?"

"Ba goshinki yafi nawa tudu ba."

"Wallahi k'arya ne banida goshi" ta fad'a had'e da kai masa bugin wasa a k'irji.

"Mu gwada ne?" Yace yana mata dariya.

"Ban sanin ba ni ka sakeni" ta fad'a tana k'ok'arin mik'ewa, kankameta ya sakeyi a jikinsa tare da placing mata kiss a gefen baki hannu tasa ta dirje ita a dole tayi zuciya yace mata mey goshi at once yayi flipping position nasu ya zammana shi a sama ita a k'asa.

"Babe you're the most beautiful girl I've ever seen."

"Ba wanin nan nice mey goshi ba? Tashi ka barmun gida jeka samu amaryarka."

"Haba Rabba'atul Bait idan kika koreni gun wa zanje?"

"Amal mana of course."

"Nifa nace ki daina kawo mun magananta."

"Nide d'agani."

"Haba my beautiful Rabba'atul Bait" yayi maganan had'e da matso da fuskansa gab da nata yayinda ta zagaye hannayenta a wuyansa "I love you Babe" ya sanar da ita.

"I love you too Darling" a hankali ya sauk'e lips nasa akan nata ya shiga kissing nata yayinda take miyar masa da martani kaman wasa suka fara wuce gona da iri kafin su hankara har sun wula wani duniyan daban. Bayan sun gamsar da juna suka yi wanka tare Nazeefah na mik'e akan gado tana kallon Afzal cike da adoration da soyayya yayinda yake faman neman kayan da ze sa a wardrobe. Wayansa dake kan gado ne ya shiga ruri ko motsawa Nazeefah dake kan gadon batayi ba ina irin ita ba ruwanta da yi mai shisshigi d'innan shi da kansa yace "Who's calling?"

"I don't know" ta mayar masa tana gyara d'aurin towel nata.

"Duba" ya umarceta. Lek'awa tayi taga Kittenβ€πŸ’πŸ” na flashing akai ga picture'nsu da yayi saving contact natan dashi wani selfie'nsu ba hassada sunyi kyau.

"Amal ce" ta amsa tana k'ok'arin 6oye kishin daya rufeta lokaci guda "Ayya taji shiru."

"D'aga kice mata idan nayi sallah zan shigo."

"Ya Rouhi kana ganin yin hakan ya dace?"

"Toh ki bari seta ga shigowa na kawai" ya amsa tare da juyawa yana mey cigaba da neman abinda ze sa. Bada dad'ewa ba sega Amal na sake kira wayan ta d'aga tayi answering had'e da yin shiru.

"Halo Habib Albi?"

'"Yar uwa Nazeefah ce" ta sanar da ita.

"Oh Nazeefah, ina yini?"

"Lafiya k'alau, kinji Ya Afzal shiru ko? Yana hanya abu ne ya rik'esa."

"Ayya ba komai seya shigo toh."

"Aha seda safe" da haka sukayi sallama sauk'e wayan tayi tana ma Afzal murmushi yayinda shima ya miyar mata yana mey mamakin hali irin na Amal ace duk yadda Nazeefah ke sonta har take kirarta da 'yar uwa amma se tana kiranta tana irga mata ababen da tasan zasu 6ata mata rai. Seda sukayi sallan Maghrib sannan Afzal ya tafi yau har doubling kud'in daya saba ajiye musu yayi wa Nazeefah ita kam dad'i kasheta she can't wait ta gama aikin ta akan Amal ta fiddata daga gidan finally.

Yana isa gida Amal ta bud'e k'ofa tayi masa sannu da zuwa tana cewa bari tayi hugging nasa yaja da baya. Dama a cike take dam tunda ta kirasa taji Nazeefah ta d'aga wayansa gashi yau se bayan maghrib ya shigo abinda be ta6a yi ba. Kuka kawai ta rushe da sede da mamaki taga ko d'aga kai Afzal beyi ba bale yasan tanayi. "Excuse me" yace da ita yana neman wuceta hannu tasa ta dakatar da shi.

"Yaya mey nayi maka haka ka za6i kana shareni kana wulak'anta ni a gidan nan? Idan wani laifin nayi maka dan Allah ka fad'a mun a shirye nake da in baka hak'uri" ta sanar da shi cikin tsan-tsan kuka. Shi dariya ma ta basa bayan duk rashin hankalin da take tafkawa still tana da bakin da zata tambayesa mey tayi? Lallai she thinks she's smart. Kallonta kawai ya tsaya yi ko uffan bece mata ba.

"Yaya please talk to me I can't do this anymore yau kwana nawa idan ka shigo mun sede kayita d'aura mun fuska, ka daina cin girki na, d'an gifts da ka saba siyo mun ka daina, ka daina kwanciya da ni yanzu ko jikinka kana neman hanani ta6awa baka tunanin hukuncin nan da ka yanka yayi tsauri dayawa?"

"Yayi tsauri fa kikace Amal? I'm truly disgusted at you I never expected this from you how could you stoop this low? Tell me mey kikayi benefiting da wannan abun kunyan da kikayi mun kika kuma yi wa kanki?" Ya tambayeta cike da tsiwa. Hawaye take sosai yayinda kanta ya d'aure shin mey yake fad'i? Wani abun kunyan tayi masa?

"Yaya wani irin magana kakeyi? Wani abun kunya nayi maka please talk to me ban fahimce ka ba."

"Ai dama baza ki ta6a fahimta ta ba Amal you know what? I don't have time for this idan kinsan k'arya zaki tsaya kina mun just forget it."

"Yaya dan Allah kar kayi mun haka I beg of you wallahi ba k'arya nake maka ba" ta rok'esa cikin tsananin kuka.

"Ohhh itace take k'arya kenan?"

"Ita wa?"

"Seriously Amal? Har tambayana kike ita wa? Kin d'au magana baze zagayo kunne na bane? Kede ki cigaba."

"Wallahi ban fahimceka ba Yaya bansan akan mey kake magana ba kuma a iya sani na ban yi maka wani abun ba sede ban sani ba ko a bisa rashin sani yet still zan baka hak'uri dan Allah kayi hak'uri ka rage wannan hukunci wallahi yayi mun tsauri dayawa Yaya can't you see? I'm slowly losing my mind and going crazy fushinka a gareni ba k'aramin tashin hankali bane please kayi hak'uri ka gafirceni I'm dearly sorry."

"Idan ba kiya son ina fushi dake se ki iya bakinki ki koyi rik'e sirrin gidanki ki dena buga waya tako ina kina irga wa mutane abinda mijinki yake miki, how could you Amal? I thought kina da hankali kuma kinsan abinda ya kamata ashe ba haka bane, wallahi ba halin ki bane ban san ki da halin nan ba."

"Ni Yaya? Wa na kira na sanar dashi sirrin gidan nan? Wallahi ban buga wa kowa waya ba ko Mami."

"Kiji I don't have time to listen to your lies because a sane nake da komai don haka ba abinda zakice da zaisa in amince dake I've heard enough and I'm very disappointed with you ban ta6a sanin kina da wannan mumunan hali ba amma ki cigaba ni bazan miki baki ba sede inyi miki fatan shiryuwa idan ma k'awaye kike bi suke rud'anki suke d'aura ki akan gur6arcacciyar hanyan nan gara tun wuri kin rabu da su ina Safiyya!" Nan Safiyya dake lek'ansu ta koma cikin d'akinta a 360 seda ya sake kiranta a karo na biyu sannan ta fito tana wani hamma irin bacci takeyi ya kirata d'innan.

"Ina yini Uncle?" ta gaishesa.

"Lafiya ki dafa mun indomie biyu da k'wai biyu kiyi sauri I'm hungry."

"Akwai abinci fah Rice and Stew Aunty ta girka."

"Ina sane ai nace ki dafa mun indomin."

"Toh" da haka ta wuce kitchen d'in wani pathetic look ya bawa Amal ya wuceta ya shige d'akinsu. Har k'asa ta sauk'a tana kuka wajen gabad'aya ta rasa mey ke mata dad'i sam bata da masaniya ga abinda Afzal yake cewa mey yake nufi da ta daina kiran mutane tana yad'a musu sirrin aurenta a ina tayi hakan? Ita da ko da iskokai suka shafeta ma bata kira Mami ta sanar da ita ba wani
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment