Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

se na gama had'a miki kayan fad'an kishiyanki ne, auran namu is in three weeks time in Allah ya yarda."

"No!" kai ta shiga kad'awa yayinda take k'aryata duk wani abinda ya fad'a, take wan irin sharp headache ya kamata. "This can't be possible" ta shiga cewa "It can never be possible dan Allah kace wasa kake mun Ya Rouhi" ta rok'esa yayinda take hawaye sosai.

"Dan Allah kibar kukan haka Nazeefah."

"Aure fa kace Ya Rouhi? Mey nayi maka da zaka auro mun kishiya? Idan wani laifin na maka wanda ban sani ba dan Allah ka sanar dani a shirye nake da in baka hak'uri amma please let this be a joke."

"It is no joke Rabba'atul Bait and ni baki yi mun laifin komai ba, I love you, you know that right?"

"No" ta katsesa "You don't love me Ya Rouhi, you've never loved me, inda kana so na da baza ka ta6a tunanin yi mun kishiya ba, why? Why?" Tuni ta rushe da wani irin masifaffen kuka. Rungumota yayi niyyan yi amman sam ta hanasa da k'yar ya samu ya rufe ta gam ajikinsa yayinda kukan nata ya tsananta. Sun dad'e a hakan yana ta bata hak'uri amma ina ta kasa hak'uran se kuka take. Chan ya d'agota daga jikinsa ya shiga share mata hawayen nata "Come with me" ya buk'aceta. Batayi gardama ba ta bisa a baya yayinda ya rik'e hannunta cikin nasa ya jata izuwa parlour inda D'anladi ya jera akwatunan nata.

"Do you believe it's not a joke now?" Ya tambayeta a nitse.

"Mey wannan d'in?" Ta tambayesa a hankali.

"Kayan fad'an kishiyanki Nazeefah." Bata iya k'ara yin magana ba yayinda ta rushewa da wani fitinannen kuka mey tsuma zuciya. Shikenan ya tabbata aure Afzal zeyi amma ko be kyauta mata ba, na mey zeyi mata kishiya bayan duk wani abinda yake so tana mishi, bayan nan ace seda aure ya rage sati uku ze sanar da ita? Me tayi da za ta fuskanci hukunci me tsauri haka daga garesa? Bazata iya zama da kishiya ba, da ta zauna da kishiya gomma ta rasa ranta.

"Ya Afzal you're such deceit, ka cuceni kaci amanata kuma ka sani I'll never forgive you, I'll never forgive you for tricking me that you did. For all these while you made me believed you loved me ashe ba haka bane wasa da hankalina kawai kake chan a waje kana da wacce kakeso kake kuma son ka aura ka kasance da ita, me na ta6a yi maka da zaka mun wasa da hankali haka? Ashe k'arya kake mun duk sanda ka ce ka yafemun."

"Ko da wasa Nazeefah, ki yarda da ni idan nace miki na yafe miki na kuma mance da duk wani abinda kikayi mun da a baya, I'm terribly sorry Nazeefah bazan gaji da baki hak'uri ba ki sani ina sonki, I really do love you."

"No you don't love stop lying to me" Hannayenta biyu ya had'a acikin nasa "I'm not lying to you Nazeefah, I really do love you wallahi I do."

"Wallahi k'arya kake you don't love me you've never once loved me" ta k'aryatasa cikin tsananin kuka. Tausayi sosai ta basa barin ma ganin yadda hawayen ke tsiyaya daga idanunta, na matuk'a ta basa tausayi.

"Nazeefah please stop crying" yayi maganan yana k'ok'arin rungumarta sede tak'i barinsa. "Don't you dare touch me!" Be saurareta ba haka na k'arfi yayi hugging nata ya shiga shafa bayanta a hankali yayinda yake showering kisses akanta. "Shhh! I've got you, I love you so much."

"Idan da har kana so na da baza ka fara tunanin k'aro aure ba" tayi maganan had'e da raba jikinta da nasa tana share hawayenta "Mey yayi zafi da zaka yi mun kishiya Ya Rouhi? Mey ka ta6a nema a gidan nan ka rasa, girki ne inayi maka, ina respecting naka ina tsaftace maka muhalli baka ta6a neman hak'k'inka a guna ka rasa ba, duk abinda kace kana so shi nakeyi wanda baka so kuwa koda hobby na ne ina k'ok'arin dainawa, mey yayi zafi da har seka k'ara aure?"

"Nazeefah kin manta ni miji ga mata hud'u ne? Bayan nan bakisan mata sun fi maza yawa a al'umma ba yanzun? Idan kowani na miji yace mace d'aya kacal ze aura sauran kuma waze auresu? Bakiya son 'yar uwarki ta raya sunna itama ta cika umarnin anmabin mu SAW?" Nasiha ya shiga yi mata sosai saidai ina kishi ya riga ya rufe mata ido bata jin kira.

"No Ya Afzal! Bazan bari ka auro wata muddin ina raye, bazan zauna da kishiya ba."

"Wayace kishiya zan auro miki Nazeefah? Abokiyar zama zan kawo miki."

"Bana sonta bana so."

"Nazeefah please calm down kiga baki ma santa ba fa amma kike cewan baki sonta, Amal is a very nice girl ina da tabbacin you two will get along."

"Bana son sanin ko ita wacece ina ji ina gani bazan bari wata ta sace mun kai ba Ya Afzal, I'll do whatever it takes in tabbata wannan aure be auku ba you'll see."

"Nazeefah-"

"Kuma ka tattara kayakin fad'an kishiyanka or whatever you call it bana buk'ata" tana kaiwa nan ta nufi d'akinta ko amsa kiran da yakeyi mata batayi ba. Hijabinta ta sanya ta d'au makullin motarta yana ganinta yasan fita zatayi be hanata ba saboda yasan ba amfani ko da yayi maganan ma ba sauraronsa zatayi ba. Kad'an ya rage bata take k'afan D'anladi ba da ta zo fita daga gate d'in, gida ta wuce direct se d'akin Mummy.

Khalifah ta tarar mik'e kan gado se faman latsa wayansa yake.

"Ya Nazeefah" ya kirata had'e da mik'ewa zaune.

"Ina Mummy?"

"Tana wanka" ya amsa take.

"Jeka d'auko mun ruwa" tayi maganan tana cire hijabinta.

"Ni shikenan kinzo ki fara aikan mutum ba" ya watsa mata harara.

"Nace kaje ka d'auko mun ruwa wallahi kar ka bari in sauk'e haushin da nakeji akanka."

"Ki sauk'en mana a jinki zaki iya duka na ne?" yayi maganan had'e da mik'ewa, daga bakin k'ofa ya wulla mata gorar ruwan da ya d'auko matan sannan ya haura sama d'akinsa. Kad'an tasha ta rufe ta ajiye, bada dad'ewa ba sega Mummy ta fito.

"Ha'ah Nazeefah ce a gidan namu yau."

"Mummy" ta kirata tana turo baki tamkar wacce zatayi kuka.

"Meya faru?"

"Mummy kina jin Ya Afzal wai aure ze k'ara."

"Dama bakida labari ne?" Mummy ta tambaya tana mey zama a gefenta.

"Aww kina sane dama?"

"Eh though nima ban dad'e da sani ba be sanar dake bane ke?"

"Wallahi se yau yake fad'amun."

"Ai na d'au kina da labari auran sauran sati biyu ne ko uku nema."

"Wallahi Mummy bazan yarda ba adalilin mey ze auro mun wata? Wai harda akwatin fad'an kishiyansa."

"Guda nawa?"

"Ni nama irga ne amma yafi shida de naga kaman."

"Toh ai ki godewa Allah."

"In godewa Allah fa kika ce Mummy? Uwar mey zanyi da kayan fad'an kishiyan nasa? Tsirara nake yawo ne?"

"Kiga Nazeefah kowa yasan kishiya da zafi amma idan Allah ya k'addaro maka toh fa dole ne ka hak'ura banda ke da abin ki an riga an sa rana, rana ya gabato ajinki akwai borin da zakiyi ne da ze hanasa yin auren?"

"Wallahi auren nan bazata saku ba komin yaya ne se nasan yadda zanyi in hana aukuwan hakan."

"Uhn uhn fa Nazeefah kar ki bari kishi ya kaiki ga halaka ki kwantar da hankalinki don za ayi maka kishiya bawai hakan na nufin mijinka baya sonka bane, kefa da bakinki kikace yayi miki kayan fad'an kishiya ai yaci ace kin hak'ura Afzal na sonki ke kanki kin sani, a zamanin nan ba kowani na miji bane ze yiwa uwar gidansa akwati dan wai ze k'ara aure. Ga akwati ba d'ayaba ba biyu ba keda kanki kikace zasu fi shida."

"Son banza so a baki, wallahi baya sona da yana sona da baze ma fara tunanin yin wani auren ba mene bani yi masa da zece seya sake aure. Ke yau shekara nawa kuke tare da Daddy meyasa bece ze sake yin wani auren ba? Idan ba fitina ba mata nawa yaga Abbansa ke da daze kama yace shi se yayi mata biyu."

"Kowa da ra'ayinsa Nazeefah. Kisani Afzal daban yake da Abbansa ko ni dake nan ba d'aya muke dake ba. Shi kishiya kuma tana kan kowa wallahi ko ni nan ban isa in bugi k'irji ince Daddy'nku baze k'ara aure ba, a yau d'innan yaga dama ze k'ara auransa, hak'uri ya zama dole."

"Ni wallahi bazan yarda ba auren namu dududu shekara nawa ne befa kai uku ba, ya bari ma idan na gama haihuwa na mana amma ko k'wark'wata ban ajiye ba har ya fara tunanin yin wani auren, Allah bazata saku ba."

"Ta ma riga ta saku ne fah Nazeefah don banga abinda ze hana aukuwan auran nan ba idan ba mutuwa ba. Dan Allah ki rufa min da Daddy'inku asiri ki d'au hakan a matsayin k'addarar ki, ni kaina zan saki a addu'a Allah ya sa hakan shi yafi alkhairi."

"Amma Mummy kin ban dariya har akwai alkhairi ne acikin kishiya?"

"Toh kije Nazeefah kiyi duk abinda kika ga ya dace amma idan kika zo kika rasa auren naki daga k'arshe kar kiyi blaming d'ina nide na fad'a miki" bata sake cewa komai ba ta ja hijabinta ta fice. Gidan k'awarta Suwaiba ta nufa da ikon Allah kuma mijinta baya gida. Zama tayi ta irga mata halin da ake ciki, sosai Suwaiba ta ji mata takaici amma ta nuna mata lokaci ya riga ya k'ure ba yadda za'ayi a hana aukuwan auren.

"Taya zakice haka Suwy? Nida nake cewa zaki share mun hawaye idan nazo."

"Wallahi ba yadda za'ayi saidai idan malamai zaki fara bi."

"Malamai? Wasu irin malamai kenan?"

"Malaman tsibu nake nufi."

"Subhanallahi Suwy! Kin san ko yin hakan shirka ne?"

"Tabbas na sani amma kuma idan bada su ba mutum baze ta6a iya mallake mijinsa ba kinga Ibrahim (mijinta) idan nace masa zauna ya zauna se abinda nakeso yakeyi I can't bear the risk of sharing my husband da kowata shegiya idan a shirye kike gobe goben nan ina iya kaiki gidan malami na ya share miki hawaye."

"A'a kam gaskiya zan zauna inyi tunani am sure akwai wata hanyan da zanbi in hana aukuwan auren nan ba tare da na fita daga musulinci ba."

"Toh sani de ya rage wa me shiga rijiya kije kiyi shawaran anytime your mind is made up, gidan malam kullum a bud'e yake yana maraba wa bak'i."

"Toh ni zan wuce."

"Bari in raka ki."

"A'a yi zamanki keda kikayi nauyi, Allah de raba lafiya."

"Ameen toh se anjima." Maimakon ta zarce gida ta wuce gidan wata k'awarta Maimuna har bayan maghrib tak'i dawowa gida. Tun Afzal na trying numbanta har ya gaji ya dena don kashe wayan tayi gabad'aya don kar ya tak'ura mata. Se wajajen k'arfe tara ta dawo gida. Tana shiga sega Afzal zaune kan kujera kallonsa tayi sannan ta kawar da kai ji take kaman ta nad'a masa duka don takaici. Daga bisani ta shiga takawa bata kai ga shiga corridorn da ze kaita d'akinta ba ya kira sunanta. Banza da shi tayi se akaro na biyu sannan ta tsaya had'e da kewayowa.

"Ina kikaje?" Ya tambayeta. Shiru tamai ko ta kallesa ma bale wai tasan yanayi.

"Magana nake miki Nazeefah ina kikaje? I've been trying to reach you but am sure da gan-gan kika kashe wayan naki don kar in sameki, yeah?"

"Gida naje, wayana kuma ya mutu ne ba charji" ta amsa sama-sama.

"Don't think of lying to me, na kira Mummy tace tun La'asr kika bar gida so where did you go?"

"Gidan k'awata excuse me" bata kai ga juyawa ba ya dakatar da ita mik'ewa yayi ya tako zuwa inda take tsaye. "Da izinin wa kika fita sannan ya dace a matsayin ki na matar aure ki fita se cikin daren nan ki dawo?"

"Kayi wa kanka fad'a kafin kayi mun Malam, ya dace a matsayin ka na magidanci amma kana neme neman mata? Bayan nan se three weeks to d'aurin aurenka zaka sanar da ni a matsayina na matarka?" Sosai ransa ke 6aci duk lokacinda ta kwatantasa da mey neme nemen mata sanin ba halinsa bane amma ya ya iya? Dan dole ya danne zuciyansa, yasani duk acikin zafin kishin ne don haka yayi mata uzuri.

"Look Nazeefah" yayi maganan had'e da aza hannunsa a kafad'unta "I know this's not going to be easy on you, I know how it must hurt, ina sane da komai shiyasa nake rok'anki da kiyi hak'uri dan zan k'ara aure bawai hakan na nufin mabud'in wahala maki bane kokuwa wai zan mance dake ko in walak'anta ki. Nazeefah I love you, I'm proud to have as my Rabba'atul bait, Amal might be my bride but kece uwar gida na, which applies being my soul. Please karki bari kishi ya rufe miki ido yayi destroying relationship namu, I love you Nazeefah and I don't wanna lose you."

"Duk k'arya ne" ta fad'a had'e da sauk'e hannayensa daga jikinta "wallahi duk k'aryar banza ce inda kana so na da bazaka ta6a tunanin k'ara aure ba."

"Nazeefah dan zan k'ara aure ba wai hakan na nufin na daina sonki bane, zan k'ara aure saboda sunna ne, ki d'au Amal a matsayin 'yar uwarki ba kishiya ba."

"'Yar uwa fa kace? Kar ka sake kwatantata da 'yar uwata dan duk mutumin dake shirin sace maka miji ba d'an uwanka bane, Amal mak'iyata ce bana k'aunarta, bazan ta6a sonta ba kuma muddin ka auro ta a gidan nan toh wallahi kaida kwanciyan hankali kunyi sallama sena tabbata na tada maka hankali fiye da yadda ka tadamun nawa yanzu mu zuba da kai a gidan nan muga" tana kaiwa nan ta wucesa ta shige d'akinta had'e da sa key. Ruwa ta watsa ta sauk'e sallan Isha sannan ta fito in search of what to eat. Afzal ta tarar zaune kan dining yana shan corn flakes ko ta kansa batayi ba ta zarce kitchen ta shiga dafa indomie. Bayan da ya gama sha ya shiga yayi joining nata a kitchen d'in.

"Ni baza a dafa dani ba?" Ko juyawa ta kallesa batayi ba wai gani yake kaman wasa take ko? Ze gani.

"But I'm hungry."

"Kula da yunwan ka ya tashi daga kaina ya koma kan na amaryar ka. Idan har bazaka iya jure yunwan ba your bride is just a call away kana iya fita kaje ka sameta daman ka saba" ta basa amsa ba tare da ta koda juya ta kallesa ba. Be sake cewa komai ba ya jira ta, bayan data gama girkin yabita har cikin d'akinta. Duk yadda takeson ce masa ya fita haka ta hak'ura, tasan da gan-gan yake hakan don ya sata yin surutu. Bayan da ta gama ci ta sinche bathrobe dake jikintan ta sanya kayan baccinta ta feffeshe jikinta da turare sannan ta kewayo garesa "Malam kana iya bar min d'akin zan kwanta."

"Yau kuma nine Malam? Ba Ya Rouhi?" Shin wai ya d'au wasa take? Ze sha mamaki na lahira seya fisa jin dad'i.

"Ka de jini ka fice mun a d'aki."

"Naji anan zamu kwana yau?"

"Malam am damn serious ka fice mun daga d'aki zan kwanta."

"In kinga nabar d'akin nan to dake ne in fact hak'k'i na ma nakeso, I need my wife."

"Idan a garinku ana kusantar matar da take haila toh bismillah" ta sanar dashi cike da rashin kunya. Duk yadda yaso 6oye dariyansa ya kasa "Baby kin manta yanzu kika idar da sallah ne?" Yayi maganan yana nuni da sallayar da tayi sallan akai. K'aramar tsuka taja "seka cinye d'akin idan ya zama abinci" sannan ta janye pillonta ta fice. Bayanta yabi izuwa d'ayan d'akin data shiga, haka suka tayi k'arshe tazo ta kwanta a parlour akan d'aya daga cikin couches d'in. Sarai yasan kujeran ba iya d'aukansu zeyi duka ba amman ya bita har kai dan neman magana, kusan rabin jikinsa akan nata yake.

"Wai don Allah meye haka?" Bata kaiga mik'ewa ba ya jata nan ya samu ya baje akan kujerar had'e da aza ta akan k'irjinsa. Gagam ya matseta yadda ko k'wak'k'war motsi bazata iya ba.

"Malam ka sakeni!"

"Shhh let's sleep baby."

"Ka sakeni ko sena shak'e tukun?" Adjusting nata yayi yadda zata na iya nishi da kyau amman bawai ya saketa ba. Duk kalan suratan da tayi-tayi hakan besa ya saketa ba, dan kanta ta daina surutun sabida yadda ta galabaita. Acikin awa d'aya bacci mey nauyi yayi awon gaba da ita, seda Afzal ya tabbata baccin nata yayi nauyi sannan a hankali ya sauk'eta daga jikinsa. D'agata yayi cike da dabara ya kaita d'akinsa ya shinfid'a ta akan gadon had'e da gyara mata kwanciya. Bayi ya fad'a ya watsa ruwa sharp-sharp sannan ya fito ya kwanta a gefenta had'e da kashe musu wuta. Pillonsa ya kawo kusa da nata sannan ya zagaye hannunsa a jikinta wane wanda wani ke shirin k'wace masa ita, a hankali bacci ya d'aukesa.




RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:33] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 2⃣6⃣*



Asuban fari alarm na Afzal yayi ringing, bayan ya kashe ya kunna bedside lamp ya kewayo yana kallon Nazeefah dake ta bacci a hannunsa cikin kwanciyan hankali. Peck yayi placing mata a goshi had'e da furta "Allah sassauta miki wannan kishi Rabba'atul Bait, I love you" cike da dabara ya rabata daga jikinsa ya sauk'a daga kan gadon ya nufi bayi. Bayan ya fito yayi shirin zuwa masallaci sannan ya shiga tayar da ita.

"Ta shi kiyi sallah zan wuce masallaci" yana tabbatar da ta tashi ya fice.
Dawowansa ya tarar Nazeefah bata d'akin dama yasan za ayi hakan. Kwanciya yayi kan gadon ya koma bacci kasancewar yau Asabar ne ba aiki. Se wajajen goma sha d'aya ya tashi bayan yayi wanka ya d'au wayansa ya fice parlour inda ya tarar da Nazeefah zaune kan kujera tana faman latsa wayanta. K'amshin turarensa ne ya buga mata hanci, ba shiri ta d'ago kai tana kallonsa ba k'arya yayi kyau ina irin morning shower glow d'innan? Se wani k'yalli fatan jikinsa yake k'ark'ashin ranan dake haskowa ta window. Daga bisani ta kawar da kanta badan wai kallon sa ya isheta ba se don haushinsa da take ji.

"Rabba'atul bait yau ba gaisuwa?" Ya tambayeta yayin da yake takowa zuwa inda take. Shiru ta mai ko kallonsa bata sake d'aga kai tayi ba. "Good morning Babe" ya gaisheta had'e da sauk'e mata light kiss a gefen baki. Hannu tasa ta dirje cike da takaici wanda ya mugun basa dariya amma ya dake tare da yin tari dan korar da dariyan.
"Islamiyya fa yau bazaki je ba?" Shide a dole seya sata magana.

"Mallam kana damuna da surutu please."

"Rabba'atul Bait please kiyi hak'uri haka nan" ya fad'a had'e da zama a gefenta "Nasan nayi miki ba dai-dai ba and I'm sorry bazan gaji da baki hak'uri ba but please kar ki 6ata tsakanin mu saboda Amal."

"Seka fasa aurenta tunda baka son tsakanin mu ya 6aci as simple as that."

"Tayaya kike tsammanin zan iya fasa aurenta bayan an riga an gama komai, mey kikeson incewa iyayenta bayan nan duk hidiman da Abba da Ummi suka yimin ya tafi a iska kenan?"

"I don't care, kade sani zaman lafiyanka da na ita karuwar taka yayi depending akan hakan."

"Subhanallahi! ki daina kwatanta Amal da karuwa Nazeefah tunda bata yi miki komai ba kuma baki ta6a ganinta tana wani alfashan ba."

"Bata yi mun komai ba?" Ta tambayesa yayinda take k'yalk'yalewa da dariya. "Bata yi mun komai ba fa kace? Tana shirin k'wace mun miji ka ce bata mun komai ba?"

"Amal bata da shirin yin hakan Nazeefah, wannan abu da kikeyi shi ze sa in nisantar da kaina daga gareki please cut it out."

"Oh really? So what do you expect me to do then? To fold my arms? K'ara aure fa kake shirin yi, kuma se three weeks to auren kake sanar dani how do you expect me to act? Ince Allah sanya alkhairi?"

"Hak'urin nan dey shi zan cigaba da baki I know am at fault but abinda kike yin nan kuma ba shi ze hanani fasa auren nan ba kisani fa kaman yadda nake son kasancewa dake haka nakeson kasancewa da Amal, nasan da zafi amma idan kika hak'ura komi mey wucewa ne Nazeefah, I'm never leaving your side and as far as am concerned kece Rabba'atul Bait d'ina not Amal."

"K'aryar banza kawai" tayi maganan had'e da mik'ewa "Ni zan fita ina iya kai yamma kumma kafin in dawo kuma."

"Breakfast d'ina fa?"

"Ban girka ba kana iya samun karuwar taka aww sorry amaryar taka ta girka maka" bata kai da jin abinda zece ba ta wuce d'akinta. Nan da nan ta fito sanye da hijabi shide Afzal bece mata komai ba banda binta da ido da yayi. Gabad'aya ya rasa mey ke masa dad'i Nazeefah isn't at all ready to understand him, anya kuwa ze iya da wannan bala'in da yake neman afka masa?

Gidansu aminiyarta Rumaysa ta taje inda take bata labarin abinda ya faru.

"Kar ki gaya mun Babe!" Tayi exclaiming.

"Wallahil azeem aure Ya Afzal ze sake yi, ga chan akwatunan fad'an kishiyansa ko kallonsu ma banyi ba."

"Chab! Amma shiko meyayi zafi da ze k'ara aure? Kode kun samu matsala ne?"

"Wallahi lafiya k'alau Babe ni daya sanar dani ma na kasa yarda I can't believe for all these while he's been deceiving me."

"Ai na miji bashida guarantee komin dad'in ki dashi idan be ci miki amana ba baya jin dad'i yanzu ya zakiyi?"

"Wallahi ban sani ba jiya ina gidan Suwy nake tambayarta mafita tace wai mafitar d'ayace."

"Wai meh?"

"Malaman tsubu."

"Boka de!" Rumaysa tayi exclaiming.

"Hmm ai nima nace ba dani ba a iya fahimtan addinin da nayi Allah na yafe ko wani irin zunubi amma banda shirka har mey yayi zafi akan wata shegiya in jefa kaina ga halaka."

"Gaskiya kam wannan shawara batayi ba amma shin wacece yarinyar wai?"

"Ina ko zan sani yanzu haka wata banza ce."

"Kode ze iya yuwawa yarinyan nan da muka gansu tare ranan a Unimaid garden ne?"

"Waya san masa ne
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment