Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ko daman magana bata basa ba tace, "Alhj ka juyo ka juyo da wuri Nazeefah ta yanke kanta."

"What?!' I'm on my way" U-turn yasha nan take ya dawo ba tare da 6ata lokaci ba akayi da Nazeefah nearest clinic inda akayi emergency room da ita.

_53 minutes later_
Da wani irin gudu Afzal ya shiga haraban asibiti sannan ya nemi waje yayi parking ya fito ya k'arisa ciki. Tsaye a inda akayi mai kwatance ya same su da tashin hankali bayyane karara a fuskokinsu.

"Afzal?" Daddy ya kirasa yana mey mamakin yadda akayi yasan halin da suke ciki.

"Afzal waya sanar da kai muna nan?" Mummy ta tambaya.

"Mummy nine" Khaleefah ya amsa.

"How's she?" Afzal ya tambaya. Shiru ne ya d'auki wajen se chan Mummy ta amsa "Muma jira muke likitocin su fito tukuna."
15 minutes more sega emergency room d'in ya bud'u nan duk suka duk'ufa sukayi wajen kowa da abinda yake tambaya. Nan Dr'n ya musu bayanin komai yakuma tabbatae musu cewa cut d'in beyi affecting Radial artery nata ba in less than an hour zata farfad'o. Godiya suka masa sannan ya fice.

"Daddy, Mummy I'm so sorry I'm terribly sorry nasan duk laifi na ne."

"Ko kad'an Afzal" Daddy yayi saurin katsesa "you're not to be blamed for anything, idan har akwai mey laifi anan toh nine so kabar damuwa."

"Mummy I'm sorry."

"Don't be Afzal mungode da kulawanka in shaa Allahu zan sanar da Nazeefah zuwanka."

"Thank you Allah ya bata lafiya."

"Ameen mungode Khaleefah ka rakasa" cewan Mummy.

"No don't bother" Afzal yayi saurin amsawa sannan ya fice. Gida ya wuce direct sede tun shigansa Amal ta karanci yanayinsa wani iri. Bayan ta mar sannu da zuwa ta d'auko masa ruwa ta zauna a gefensa. "Ya Omri lafiya?"

"Babu" ya amsa sama-sama.

"Kaman ya babu Ya Omri? Tell me kaji."

"Nagaji ne kawai barin je in watsa ruwa in huta" hannunsa tayi saurin kamawa" kafin ya mik'e "Please tell me Ya Omri nasan akwai abinda yake damunka."

"Rania I'm sorry."

"Why what for?"

"Rania it's Nazeefah tana kwance a asibiti yanzu haka as we speak."

"Subhanallahi meya sameta?"

"Yanke kanta tayi."

"Nazeefan? Dalili?"

"Batun takardan ta, yanke kanta tayi in attempt to kill herself."

"I want to go and see her Ya Omri."

"Rania-"

"Please" tayi saurin katsesa "Ya Omri ji nake kaman duk laifi na ne, komin mey Nazeefah tayi laifi na ne."

"Kar kiyi magana haka Rania, in har akwai wanda za ayi blaming anan mahaifinku ne and he's sorry mu taya Nazeefah da addu'a kawai Allah yasa ta gane gaskiya da wuri."

"Ameen but I still want to go and see her please kar ka hanani Ya Omri." Hannunta ya d'au ya rik'e a cikin nasa "Okay zanyi wa Mummy magana se muje."

"Thank you."

"Don't mention so me kika girka mana? I'm hungry."

"Spaghetti ne kawai nima ban dad'e da dawowa daga school ba."

"Oh! Muje toh."

****
Bayan Maghrib Afzal yayi wa Mummy waya inda ya tabbatar da cewa ba a sallamesu ba har anan sannan yace mata suna shigowa shi da Amal. Acikin k'ank'anin lokaci suka isa inda Mummy ta taresu ta k'arisa ciki dasu. Nazeefah na ganin Amal taji tsikan jikinta gabad'aya na tashi yayinda ta shiga yi mata wani irin tsananin tsana.

"Mey wanann take mun a d'aki Mummy? Send her out send her out!"

"Nazeef-"

"Bana k'aunan ganinta a kusa dani ku fitar mun da ita daga d'aki" ta katse Mummy da hanzari.

"Nazeefah please" Afzal ya sa baki. "Kiyi hak'uri."

"Hak'uri Ya Afzal? Da abinda zaka sak'a mun kenan? Ashe for all these while k'arya kake mun? I never expected this from you, I thought you love me ashe ba haka bane, ka sani daga kai har matar taka bazan ta6a yafe muku wannan abu da kuka mun ba Mummy send them out."

"Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri" Amal tace da ita.

"Ko da wasa karki kuskura ki sake kiran suna na Amal saboda keba 'yar uwata ba ce. You ruined my life, first you stole my father away from me and then now my husband, meyasa kike nok'e-nok'e? Ki fito fili kice kina son ki zama ni kina son ki sace nun rayuwa. Amal na tsaneki, na tsani duk wani mey sonki, ba kuma abinda ze fi mun nishad'i da jin dad'i kaman inga gawanki bana k'aunanki in har kina son kanki ki ficemun daga d'aki you have absolutely no right to speak to me get out." Hawaye Amal ta shiga yi yayinda Afzal ya janyeta jikinsa "Ku fice mun daga d'aki bana k'aunan ganinku duka."

"Nazeefah meyasa bakida mutunci ne?" Mummy ta tambayeta tana mey tsananin jin takaicin abinda Nazeefah ta aikata.

"Shikenan Mummy zamu koma" fad'in Afzal "Nazeefah Allah ya baki lafiya we mean you no harm" daga fad'in haka ya sauk'o da ganinsa akan Amal "Let's go Amal." Badan Amal na so ba ta amince ya jata waje se kallon Nazeefah take tana kuka itako Nazeefah ko sake kallon 6angarensu batayi ba.

"Meyasa baku barni na mutu ba Mummy? I hate my life I hate Amal."

"Nazeefah it pains me as a mother ace ni na tsuguna na haifeki, Allah ma shaida ne ni ba tarbiyyan dana baki ba kenan, bansan a ina kika d'auko wannan banzan hali ba dan bazan ce na mahaifinku bane saboda koda wasa be ta6a gigin d'aukan ransa da kansa ba. Kuma Amal da kike gani kika raina wataran zaki nemata hannu bibbiyu ki rasata kuma ko kin k'i kin so 'yar uwarki ce ba abinda zaki iyayi da ze canza hakan. Ki tashi ki ci abinci yanzu za'a sallameki zamu koma gida."

"Wani gida?"

"Ban gane wani gida ba gida gida mana."

"Meya samu hotel da muke zaune aciki?"

"Zamu koma gida gun Daddy'nku nide na fad'a miki."

"No Mummy ni bazan koma gun Daddy ba, a dalilin mey? Bayan duk bak'in ciki da k'uncin da nake ciki shine sanadi."

"So? He's still your father nothing can change that."

"Ni gaskiya bazan bi ku ba."

"Ni na fad'a miki" tana kaiwa nan ta fice had'e da rufo mata k'ofan.

****
Tun da suka shiga mota har suka isa gida Amal take ta kuka.
"Amal it's okay with time in shaa Allah Nazeefah zata fahimci komai kukan ya isa haka" Afzal yace da ita bayan sun k'arasa ciki yana mey share mata hawayenta.

"Yaya I feel so responsible for everything Nazeefah is going through, Nazeefah tana sonka har yau har gobe tana sonka she can't ever stop loving you."

"And you too Lily, you love me don't you?"

"I do Yaya amma Nazeefah kuma fah? Yaya har ranta fa ta so d'auka akan soyayyar ka."

"Amal you matter to me more than anyone morethan Nazeefah kibar tada hankalinki kinji? I love only you" rungumeta yayi a hankali itama ta zagaye hannayenta a bayansa tana mey lumewa acikin rik'onsa yayinda kalamun Nazeefah suke faman yi mata wasa a kai.

****
Washegari...
Dawowan Daddy daga gidansu Mami kenan amma sam babu walwala tattare da shi. Yana shigowa Mummy da ta karanci yanayin nasa tayi mai sannu da zuwa.
"Tak'i amincewa?" Ta tambayansa a hankali.

"Hjy Surayya ko bani dama in nemi tubansu sun hanani bale in sanar dasu k'udurina, Jameelah tana matuk'ar fushi dani haka ma mahaifinta. Ban san ya zanyi ba muddin tak'i yafe mun, alhak'in ta ya cigaba da bina kenan idan da ma akaina kad'ai ze tsaya da da sauk'i amma har ku baku tsira ba, bana k'aunan sake ganin ku cikin k'unci Hjy Surayya bana son abinda ze sake raba kanmu yadda na samu da k'yar Nazeefah ta amince ta biyoki kuka dawo mun."

"Ka kwantar da hankalinka Alhj."

"Ta yaya Hjy Surayya? Ta ina hankalina yaga ta kwanciya bayan rayuwan mu duka yana cikin gwagwarmaya."

"Ni da kaina zanje in samu Jameelah gobe muyi magana in shaa Allahu zata yafe maka komai ta kuma amince da k'udurinmu."

"Keda kanki?" Ya tambaya yana mey kasa 6oye mamakin da ya sha.

"Baka yarda bane?"

"Hjy Surayya a ina aka ta6ayin haka? Dan Allah karki baiwa kanki wahala-"

"Kabar zancen nan Alhj" tayi saurin katsesa "Ai mun wuce haka yanzu try not to worry Allah kaimu goben."

"Ameen Hjy Surayya banida bakin yi maki godiya, Allah saka ya biyaki da gidan Aljannah."

"Toh kuma godiyan mey kake? Muje kaci abinci."

"Ya jikin Nazeefah?"

"Da sauk'i tana kwance a d'aki tana bacci."

"Toh madallah".****

Tamkar mey ta6in hankali haka Nazeefah ta zame musu a gidan ko abinci tak'i ci tun dawowansu daga asibiti jiya da dare har izuwa yinin yau. Allah ma yaso ana sa mata ruwa. Banda kuka ba aikinta a gidan, Mummy tayi mata nasiha tayi mata fad'a amma ina tak'i ji haka zata kafa hotunan auransu da Afzal tayita kalla ba fashi. Washegari kamar yadda Mummy ta d'au alk'awari ita da Daddy suka jesu gidansu Mami inda ya tsaya daga waje ita kima ta k'arasa ciki. Sallama tayi yayinda take sa kai cikin gidan, Mami dake gida ita kad'ai ce ta amsa. Kallo d'aya tayiwa Mummy ta tabbata mahaifiyar Nazeefah ce saboda tsan-tsan kaman da sukeyi.

"Mahaifiyar Nazeefah?" Ta tambaya. murmushi Mummy ta saka had'e da gyad'a mata kai. "Bismillah ki shigo" tabarma ta shimfid'a musu inda suka zauna sannan suka gaisa.

"Bari in kawo miki ruwa."

"A'a 'yar uwa ba amfani."

"Toh lafiya dai ko?"

"Lafiya k'alau batun Abdallah nazo muyi magana."

"Kiyi hak'uri maman Nazeefah amma in har abinda ya kawo ki kenan saidai ki koma."

"Nasani 'yar uwa nasan abinda Abdallah yayi miki da zafi da ciwo amma abu ne ya riga ya faru ba abinda zamu iyayi da zai canza hakan saidai muyi gyara. Kiyi hak'uri ki yafe masa, shi yafiya ba kowa bane Allah yake basa iko da zuciyan yi amma na tambayeki ne saboda nasan zaki yafe masa saboda ko ban tambaya ba nasan a wajenki 'yarki Amal ta yo gadon kyawawan d'abi'unta. Idan muka ce zamu biye ta zuciyoyin mu toh wallahi ba abinda zamu tsinana wa kanmu na arziki. Ko ban fad'a miki ba nasan kinsan irin tsanan da ke tsakanin yaran mu Nazeefah da Amal. Duk yadda Amal ke son shirya tsakaninta da 'yar uwarta hakan ya gagara kuma ba wanda ze iya had'a mana kawunan yaran nan sama da ke."

"Ban fahimce kiba Maman Nazeefah ta yaya zanyi hakan?"

"Ki amince ki auri Abdallah."

"Iyyeh?" Mami ta zaro ido wuru-wuru waje. "Kikace?"

"Eh, ki amince ki auri mijina ta hakan ne kawai zamu iya gyara zuri'ar mu mu had'a kawunan yaran nan dan Allah ki amince."

"Kiyi hak'uri Maman Nazeefah amma bazan iya cika miki wannan buri naki ba, bazan iya auran Khaleefah ba bazan iya ba."

"Zaki iya 'yar uwa muddin kika yarda da hakan, dan Allah karki bari tsanan dake tsakanin yaran nan yayi tsamari iche tun yana d'anyensa ake iya tank'warasa, muddin ba'a sa musu a jiki cewa mun zama abu d'aya ba yanzu toh wallahi gaba tsanan da zasu tashi dashi a cikin zuciyoyinsu baze so yayi kyau ba ki taimaka."

"Maman Nazeefah tunda nake ban ta6a jin inda uwar gida tazo taya mai gidanta k'aro aure ba ko da kuwa a radio ne, saboda haka ban san abinda ke cikin zuciyarki ba keda mijinki, bansan mey kuke shirin yi mani ba amma koma menene kuyi hak'uri ku janye ni daga cikin matsalarku tunda na samu auren 'yata be mutu ba Alhamdulillah koni na mutu a haka bazan damu ba."

"Jameelah da zuciya d'aya nazo na sameki bada wata manufa ba, Jameelah har yau har gobe nasan Abdallah yana sonki, kema kin sani ba sena fad'a miki ba, ni kuma har ga Allah har cikin zuciyata tun cemin da Abdallah yayi bakida aure naji tausayinki ya shige min zuciya nasan ba komai ya hanaki yin aure ba illa idan kika juya baya kika ga abinda Adallah yayi miki, shi ya lalata miki rayuwa dan haka kuma shi ya tantanci yayi making everything right don haka na basa goyin baya na bashi shawaran ya auro ki. Kuma kinga ta hakan ne kawai zamu iya had'a kawunan yaran mu. Zan barki kiyi tunani anytime your mind is made up ga lamba na" ta fad'a had'e da ajiye mata wani gajeren paper data rubuta number'nta ajiki "Seki kirani, hope to hear from you soon ni zan wuce."

"Toh bari in rakaki."

"Ba amfani 'yar uwa yi zamanki nagode da wannan lokaci da kika bani se anjima." Tun fitan Mummy Mami ta shiga tunani, gabaki d'aya kanta ya d'aure se bata jikinta yake trap su Mummy suke shirin shirya mata in ba haka ba har a ina uwar gida ta ta6a aran bakin mijinta dan nema masa mata?

Daddy kuwa a gida ya sauk'e Mummy ya wuce gidansu Amal, yasani it's now or never. Bayan mey gadi ya bud'e mishi gate ya k'arasa ya samu gu yayi parking sannan ya fito ya nufi entrane door inda yake ta knocking amma ba response kasancewar bacci da suke duka daga ciki. Ganin ba mahalicci se Allah kawai seya kira wayan Afzal. Kaman a mafarki Afzal ya soma jin ringing na wayansa dake ajiye akan side drawer'n kansa kafin ya mik'a hannu ya d'aga har Amal itama ta farka. Sorry go back to sleep" ya sanar da ita rik'e a hannunsa yana mey sake daidaita kanta a k'irjinsa sannan ya d'au wayan inda ya tarar da missed call na Daddy nan take ya kirasa back, "Halo Daddy?

"Na'am Afzal gani a bakin k'ofan gidanku fa amma shiru ko bakuwa nan ne?"

"Afuwan Bacci ne ya d'auke mu bari inyi ma mey gadi magana ya bud'e maka."

"No already ina ciki ya riga ya bud'e mun ina bakin parlour ne."

"Sorry bari ina fitowa yanzu" ya fad'a had'e da kashe wayan sannan ya sauk'o da kallonsa akan Amal "Rania bari in fita Daddy yazo yana waje." Kai zalla ta gyad'a masa sannan ta koma gefe ta cigaba da kwanciyanta. Jallabiyansa ya sanya ya fito ya bud'e wa Daddy yana mey sake basa hak'uri. Ruwa da juice ya d'auko masa inda suka gaisa yake tambayansa ya jikin Nazeefah.

"Da sauk'i Alhamdulillah."

"Toh Allah k'ara mata lafiya."

"Ameen yaya Amal kuma?"

"Lafiyanta itama."

"Ina sake baka hak'uri game da abinda Nazeefah tayi muku ranan, ni kaina I'm having a hard time with her kuyi hak'uri kuyi mata uzuri."

"Ba komai Daddy duka nan mun san what she's going through is not easy fatan mu Allah kawo mata sauk'i."

"Ameen Afzal thank you."

"Ba komai Daddy."

"Yauwa dama batun Amal nazo ne Afzal, ina son muyi magana da ita in kuma bata hak'uri gameda duk wani abinda nayi mata, Afzal ka sani a addu'a I want to make everything right I want to marry Amal's mother." Mamaki da dad'i ne ya ziyarci zuciyan Afzal wanda ya kasa 6oyewa "Tabbas kayi tunani Daddy, Allah sanya alkhairi acikin hakan ya biya maka buk'atunka na alkhairi."

"Ameen Afzal zan iya yi ma Amal magana."

"Sure tana bacci bari in tayar da ita."

"No no in tana bacci ka barta kawai ko gobe ina iya dawowa."

"A'a don't worry." D'akin nasu ya koma yaje ya samu Amal ya shiga tada ita. "Rania?"

"Uhmmm?"

"Daddy yazo."

"Uhmm?"

"Yana son ya ganki kuyi magana." A hankali ta bud'e idanunta "Yaya I don't want to face him ban san mey zance mishi ba."

"I know Rania, I know kiyi hak'uri kije kiji mey zai ce miki."

"Yaya-"

"Kar muyi haka dake kinji? Tashi hungo kayanki kisa" da kanshi ya mik'ar da ita zaune ya sanya mata kayan da hijabi suka fito suka zauna a kan two seater.

"Ina yini Daddy?" Ta durk'usa har k'asa ta gaishesa.

"A'a please Amal koma ki zauna Afzal ce mata ta zauna" duk da haka Amal tak'i mik'ewa seda ya amsa tukuna. Gaisawa sama-sama sukayi sannan ya fayyace mata dalilinsa na zuwa dan ya nemi tubarta.

"Nasan na cuceki a rayuwa Amal, nasan nayi depriving naki duk wani right da gatan da kika cancanta a rayuwarki, nasan ban kyauta miki ba ban kuma kyauta wa mahaifiyarki ba amma gani yau nazo neman tubanki" ya k'arasa had'e da sauk'a k'asa akan guiwoyinsa. "Daddy please ka tashi" tayi saurin cewa amma yak'i. "I'm dearly sorry Amal, kiyi hak'uri ki yafe mun I'm here and ready to take full responsibility for everything ki bani dama in cika aiki na a matsayina na mahaifinki, ki bani dama in kula dake in soki a matsayina na mahaifinki da jini na ke gudana a jikinki. Amal I'm so sorry" Afzal be ji tashin Amal ba kawai ganinta yayi gaban Daddy tana k'ok'arin d'agosa "Don't be Daddy komai ya riga ya wuce ka kuma sani ni na riga na yafe maka komai da jimawa Allah ya yafe mana gabad'aya."

Rungumeta tsam yayi a jikinsa cike da farin ciki yayin da duk suke zubda hawayen jin dad'i "Oh Amal thank you so much Allah cigaba da yi miki albarka bansan da wani bakin zan yi miki godiya ba." Itama a hankali ta zagaye hannunta a bayansa "Ameen Daddy ka daina yimun godiya." Se murmushi Afzal dake ganin komi kaman a mafarki yake faruwa, this's all he's ever wanted, ranan da Allah ze bayyana musu mahaifin Amal ya nemi tubanta su shirya se gashi Allah ya kawo musu ranan.

"Amal?"

"Na'am Daddy" ta amsa.

"Amal nasan kinsan yadda Mahaifiyarki ta tsaneni ko?" Shiru tayi bata ce komai ba. "Amal I need your help, Mahaifiyarki tak'i ta bani dama in bata hak'uri bale in nemi tubanta Amal a shirye nake da in auri Mahaifiyar ki in har zata amince."

"Zaka auri Mami?" Ta tambayesa d'auke da d'unbun mamaki.

"In har zata amince, eh."

"Mummy kuma fa? Bana son abinda ya faru tsakani na da Nazeefah ya faru dasu suma, in har Mummy bata goyi bayan zancen nan ba babu amfani Daddy."

"Hasali Mummy'nku nema ta kawo shawaran nan Amal, Mummy'nku batada matsala da hakan idan har keda mahaifiyarki kun amince."

"Kayi wa Mami magana ne?"

"Naso amma tak'i bani dama d'azu nida Mummy'nku mukaje tayi mata magana sede har yanzu bata shirya bamu had'in kai ba please help me Amal nasan bani da daman tambayan hakan daga gareki but Amal I love your mom, har yau har gobe ina sonta kuma ina son in aureta." Na matuk'a Amal taji dad'i ta juma tana mafarkin rananda Mami zata shiga d'akin mijinta itama koda sau d'aya ne taji dad'i a rayuwanta. Inde hakane kuwa se inda k'arfin ta ya k'are inshaa Allahu bazata gaji ba seta shawo kan Mami waya sani ko da haka Nazeefah zatayi accepting nata ta bata chance suyi working out relationship nasu.

"Amal? Bazaki iya ba ko? Bakiya son mahaifiyarki ta kasance tare dani ko? Look I'm terribly sorry wallahi nayi nadaman abinda nayi muku please forgive me."

"Ko kad'an ba haka bane Daddy hasali nayi murna da farin cikin wannan labari in shaa Allah kuma zan tayaka yima Mami magana."

"Nagode sosai 'yata Allah miki albarka sak'a miki da alkhairi."

"Ameen Daddy."

"Toh ni bari zan koma."

"Da wuri haka Daddy?" Fad'in Afzal "kabari mana muci dinner."

"A'a karka damu."

"Please stay Daddy" Amal ta sanya baki.

"Tunda 'yata tasa baki na isa ince a'a? Se in jira d'in." Dad'i sosai both Amal da Afzal suka ji haka Daddy ya yini musu koda Mummy taji shiru ta kira ta tambayi dalili kuwa ce mata yayi se zuwa dare ze shigo, zeci dinner a gidansu Amal. Kafin su dawo daga masallaci Amal har ta gama tsara kan dining da had'ad'd'un dishes ta bi gidan da turaren wuta. Nan tayi musu magana suka k'ariso se yaba abincin nata Daddy yake Afzal na ta jin dad'i ana yaba girkin matarsa. Hira suka sha kaman ba gobe anan Daddy ya gano ababe da dama tattare da Amal, he's in every way submissive to be a great Dad to Amal. Da yazo tafiya kuwa har wajen motansa suka rakasa sannan Amal tace a gaishe mata da Nazeefah.

Washegari...
Wajajen sha d'aya Amal ta dawo daga school bayan morning lectures nata ya k'are. Tana dawowa ta kama shara bayan ta gama ta aza tukunyan tuwo sannan ta d'au waya ta kira Mami wacce ta d'aga a karo na farko.

"Halo Mami."

"Na'am Amal ya kike?"

"Ina yini Mami? Ya kike ya Papi?"

"Lafiya k'alau ya Afzal?"

"Yana office."

"Makaranta fah?"

"Alhamdulillah ban jima da dawowa bama kinsan mun kusa fara exams."

"Aww haba? Se part 4 kuma ko?"

"Eh in shaa Allah."

"Toh Allah sanya alkhairi ya bada sa'a mamana."

"Ameen Mami."

"Ba wata matsala dai ko?"

"A'a ba komai."

"Toh madallah."

"Mami jiya Daddy yazo."

"Wani Daddy d'aya?"

"Daddy mahaifin Nazeefah."

"Kuma mahaifinki ba."

"Eh" ta amsa tana murmushi "jiya yazo muka yini se bayan Isha ya tafi."

"Allah sarki."

"Yazo ya nemi tuba na."

"Kin yafe masa?"

"Eh Mami."

"Madallah toh yayi kyau."

"Mami kefa?"

"Baby-"

"Mami kiyi hak'uri komi ya riga ya wuce Daddy yace min yana son ya aureki."

"Baby ke kanki kinsan baze yiwu in auri mahaifinki ba ko?"

"Dalili Mami? Hasn't it always been your advocate to get married someday?"

"Yes Baby amma ba ga mahaifinki ba."

"Meyasa Mami? Didn't you loved him? Dan Allah kar kiyi ma Daddy haka."

"Baby bazaki gane bane."

"Toh meneh Mami? Daddy yana sonki har yau har gobe kema kin sani."

"Baby ba wannan bane matsalar."

"Toh meye ne?"

"Mahaifiyar Nazeefah."

"Mummy? Me tayi?"

"Baby bakiya ganin kaman wani muguntan suke shirin yi mun? In ba haka ba a ina ne kika ta6a ganin inda uwar gida tazo nema wa mai gidanta aure?"

"Gaskiya ba a ta6a yin hakan ba amma kuma I trust Mummy na tabbata Mummy baza ta ta6a aikata abinda ze cutar dake ba Mami."

"Wai meyasa kike biye wa Mahaifin naki ne haka?"

"Because he loves you Mami and he's sorry mey aciki idan kin yafe masa kunyi reconciling? Duk mun san abinda Daddy ya miki da ciwo da zafi amma yayi nadama Mami please kiyi hak'uri ki yafe masa ki sauraresa."

"Baby-"

"Please Mami do this for me" rok'an kanta Amal ta rik'a yi amma ina Mami fa sam babu a ranta ta auri Daddy. Suna gama wayan Amal ta kira Papi ta irga masa komai mamaki yasha yadda har abu haka ze faru amma Mami bata sanar da shi ba. Chan dare bayan sun k'are cin abinci yayi gyaran murya had'e da kiran sunanta.

"Na'am Abba wani abu ne?"

"Tun shekaran jiya kika ce Khaleefah be sake shigowa ba?" Dum taji zuciyanta ya tsinke amma sam bata kawo a ranta har Amal zata kirasa ta sanar da shi komai ba dan haka se tayi masa k'arya "A'a wani abu ne?"

"Meyasa kike yi mun k'arya Jameela? Yaushe kika fara haka?"


DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment