Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Allah kibar kukan I take it back." Katse wayar tayi yayinda kukan yaci k'arfinta ta barsa yana ta faman 'hello? Hello?' Sosai kan sa ya d'aure ya rasa mene ya fad'a da ze sanya ta kuka haka kode batun turowan da yace zeyin ne? Shikam wasa yake mata he can wait for as long as it takes inde akan Amal ne har se idan ta amince ya turon. Take ya shiga kiran layin tan sede tana gani amman ta kasa d'agawa don kuka. Gajiya da trying layintan yayi kawai ya kira Maamah a waya da ta zo site nasa yanzun yana jiranta. Bata 6ata lokaci ba ta iso take tambayar sa ko lafiya.

"Ina wayanki?" Ba gardama ta mik'a masa. Numban Amal ya d'ura ya kira nan ma har ya tsinke bata d'aga ba se a karo na biyu.

"Amal I'm sorry" taji muryan Ya Abdul kafin tace zata kashe yayi saurin cewa "Please don't hang up" hak kawai kuma ta fasa. "Amal abinda na fad'a ne ya 6ata miki rai?" Kai ta kad'a wane yana gabanta "Amal I was only joking dan Allah kiyi hak'uri."

"Ya Abdul ba kai bane" ta furta cikin tsananin kuka.

"Toh waye ne?"

"Babu."

"Kina kuka haka kice mun babu Amal? please tell me ko so kike in fito cikin daren nan in samu su Mami?"

"Please don't."

"Then tell me."

"Ya Abdul I'm sorry I'm so sorry."

"Amal please stop."

"Ya Abdul no matter what happens ka sani ina sonka, you're my first love and I shall die with your love here in my heart. I've loved you since day one and I shall continue to love you forever, you'll always remain close here to my heart please don't forget this." Sosai ta sanyasa cikin rud'ani.

"I know Amal but why the sudden confessions? Meya faru? Please talk to me." Ya buk'ata cike da tashin hankali.

"Please forgive me seda safe."

"Amal wait!" Saidai har ta kashe wayan. Hankalinsa ya matuk'ar tashi, ba shi kad'ai ba harta Maamah data kasa fahimtan meke faruwa.

"Ya Abdul meke faruwa?"

"Maamah I don't know d'auko mun key'n mota na."

"Kaje ina?" Ta tambaya da mamaki.

"Gidansu Amal."

"Ya Abdul shin baka san k'arfe nawa bane yanzun? Dubi pass 10 fa."

"I don't care Amal na cikin damuwa get my car key for me."

"Toh iyayenta zaka je ka samu ko wa?"

"I don't care I just want to see her and make her feel okay."

"Ya Abdul dan Allah ka kwantar da hankalinka kayi hak'uri ka bari zuwa gobe ni ma zan raka ka muje muji meke faruwa amman fita cikin daren nan is not a good idea."

"Maamah baki ji yadda take kuka bane?"

"Naji gobe in shaa Allah zamuje mu dubata dan Allah ka kwantar da hankalinka" hak'uri tayita basa da k'yar hankalinsa ya d'an kwanta ya amince se goben zasu je su dubata. Sede kaman yadda Amal tayi kwana zaune tana kuka tana tuna rabuwanta da Ya Abdul, shima haka Ya Abdul d'in yayi kwana zaune yana tunanin halin da Amal tasa take ciki. Ji yake kaman gari baze waye ba.



RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 02:13] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣8⃣*


****
"Alhj?" Ummi dake zaune a kan gado ta kirasa.

"Na'am" ya amsa yana me karkato da kallonsa a gareta.

"Nace ba ina laifin mu fara samun iyayen ita Amal d'in kafin mu nemi Abdul nake ga hakan ze fi fasali."

"Ko meyasa kika ce haka?"

"A tunani na hakan ze fi tunda de ita Amal da bakinta tace mun Prince kaman d'an gida yake a gurinsu and kaga ze fi sauk'i mana ma idan har iyayen nata ne zasu sanar da Abdul d'in halin da ake ciki zefi d'aukan maganan shima da muhimmanci."

"You have a point."

"Thank you so mey kace?"

"We'll do it your way gobe in shaa Allahu se muje gidansu Amal d'in."

"Yauwa toh Allah kaimu."

"Ameen" kammala abinda yake yayi sannan ya k'ariso ya kwanta tare da kashe masu wutan d'akin.

Gari na wayewa wajajen k'arfe goma Abdul yasa Maamah a gaba suka wuce gidan su Amal. Kiranta ya tayi amman tak'i d'aga wayar, haka ma da ya gwada da lamban Maamah still tak'i picking don haka ya buk'aci Maamah da ta shiga ta tabbatar masu meke faruwa. Shigan Maamah taci karo da Mami se suratai take ita kad'ai da ta kasa kunne kuwa seta gano regarding Amal ne tana cewa "yarinya tun jiya ake tambayarki meke damunki amman kink'i kiyi magana se aukin kuka ki tayi"
"Assalamu Alaikum" tayi sallama hakan yasa Mami kewayowa had'e da amsawa.
"Wa'alaikumus salam, a'ah! Maamah?"

"Na'am Mami ina kwana?" Ta tsuguna ta gaisheta "Lafiya k'alau ya kike ya makaranta?"

"Alhamdulillah Amal na gida kuwa?"

"Ga ta chan tana d'akinta tana kuka ki k'arisa ciki halan ke ta gaya miki meke damunta." Ba gardama ta k'arisa ta tsinci Amal nata kuka kaman yadda Mami ta fad'a gabad'aya ta fita daga kamanninta fuskan nan ya kumburo tum idanunta sunyi ja suma sun tara ruwa a k'asa. Hugging nata kawai tayi tsananin tausayin da ta bata, kukan ta cigaba dayi yayinda Maamah ke bata hak'uri da k'yar tasamu kukan nata yad'an lafa sannan ta shiga tambayarta meke faruwa sede Amal tak'i bata amsar komai. Ba yadda Maamah batayi da ita ba amman banda hawaye ba abinda Amal takeyi. Abdul da ya gaji da jiransu a waje ne ya kira Maamah don jin ko lafiya inda take irga mai ai Amal d'in tak'i sanar da ita komai. Abdul be san lokacinda zuciya ta d'aukesa ba ta diresa a cikin gidansu Amal ba shiri. Sallama yayi da wuri Mami taja hijabinta daga kan igiya ta sanya jin muryan na miji sannan ta amsa tana jiran ganin kowa. Bak'on fuskan data gani tsaye bakin k'ofan ne ya sanyata ja da baya kad'an. Se kuma taga tsananin kama tsakaninsa da Maamah to kode wanta ne? Ta tambayi kanta. Tun daga bakin k'ofan ya durk'usa har k'asa ya gaisheta.

"Tashi don Allah tashi kaji?" Amman yak'i seda ta amsa sannan ya mik'e. "K'ariso ciki, wan Maamah kake ko?" Mamakin daya bayyana a fuskansa ne ya sanyata murmushi "Bade mamakin ya na gano kake ba?" Dukda mugun halin da yake ciki hakan be hanasa mayar mata da murmushin ba "Sosai Mami" ya amsa.

"Yo ai kama kuke wane an tsaga kara marabanku de hasken data fika shikenan lale k'ariso ciki barin yi mata magana ta fito."

"Toh nagode amma dama wajen ki nazo" ya sanar da ita. Da mamaki ta tsaya kallonsa "Gu na kuma?" Ta tambaya.

"Eh Mami I'm sorry please."

"Ba komai bismillah k'ariso." Tabarma ta shinfid'a masa ya zauna sannan tayi hakan itama har anan Maamah da Amal dake cikin d'aki basu san meke faruwa ba.

"Toh gashi ban ma san sunan ka ba."

"Abdurrahman" ya sanar da ita.

"Toh Abdurrahman meke tafe da kai?" Gyaran murya yayi tare da dukar da kansa "Mami a farko de ina son in fara da baki hak'uri, dan Allah kiyi hak'uri na shiga gonan ki da Papi da nayi na sace flawanku ba tare da sanar daku ba, I'm sorry." Sosai Mami ta shiga duhu "Baba na kayi hak'uri amman ban fahimce ka ba."
Nauyayyan ajiyan zuciya ya sauk'e sannan yace, "Sama da wata shida kenan muna tare da Amal amman keda Papi ba kuda labari, what's worse is ko izinin nemanta banyi ba daga gareku which I know is very wrong of me amman ku gafarceni. Banida niyyan lalata Amal, ina sonta ne so na tsakani da Allah so na aure idan har zaku bani izini. Sau dayawa nakan gwada rok'an kanta da tabani dama in turo magabatana koda formal introduction ne ayi don asan juna amman hakan ya gagara kullum excuses da take bani daban amman ina da tabbacin tana da k'wak'waran dalilin dake sata hakan. Toh kuma se gashi tun jiya na kasa gane kanta, muna cikin waya kawai ta rushe da kuka tun wannan lokacin bata sake d'aukan kira na ko na Maamah ba. Yau na turo Maamah don ta tabbatar mana da me ke faruwa amman shiru Amal tak'i magana dalilin daya sa nayi wannan zuwan bazata kenan amman kiyi hak'uri sam ban so hakan ba nima da magabata na naso fara tako k'afa na cikin gidan nan, my sincere apologies please."

Shiru Mami tayi tana assimilating kalamunsa wato har na kusan wata shida suna tare amman shine Amal bata ta6a bud'an baki koda wasa tace mata gashi ba? Sau dayawa takan jita a waya amman kota tambayeta da waye ne setace da Afzal ne ashe saurayi tayi a bayan idonsu.

"A gaskiya Abdurrahman bazan 6oye maka ba banji dad'in cewa se yau nakejin wannan batu ba ace na tsawon wata shida kana neman 'yata amman ba tare da ka nemi izini gun d'aya daga cikin iyayenta ba?"

"Nasan ban kyauta maku ba Mami and I'm gravely sorry bana son hakan yasaki tunanin da wata manufan nake neman Amal wallahi my intentions are pure ina son Amal ne tsakani da Allah."

"Kuma da ba don halin da ta fad'a d'inba bakada niyyan bayyana mana kanka yanzu ko ba haka ba?"

"Mami bazan gaji da baki hak'uri ba saboda nasan ni me laifi ne amma kisani wallahi nima ba haka naso abunnan ya kasance ba. My apologies please, and ko a yau kukace in turo magabata na zanyi hakan saboda bana son abinda ze rabani da Amal, inason ta sosai."

"Naji bayanunka Aburrahman kuma na gamsu dasu idan Papinta ya dawo daga tafiya zan mai bayani duk abinda akwai zan sanar da kai."

"Nagode sosai Mami kuma ina sake baki hak'uri."

"Ba damuwa karka damu."

"Se kuma batun Amal ko zan iya sanin meke damunta? Nayi nayi ta sanar dani amman tak'i bazan kuma 6oye miki ba hankali na ya matuk'an tashi banason ganin Amal cikin damuwa."

"Wallahi bazan 6oye maka ba, yadda baka da masaniya akan halin nan da take ciki nima haka ne, tak'i sanar dani matsalarta se kuka kawai. Yanzu haka jiran Papinta kawai nake shi kad'ai take jin maganansa." Ya bud'e baki zeyi magana kenan sega k'ofan d'akin Amal ya bud'u Maamah na fitowa bayanta kuwa Amal ce ta rik'e k'ofan tana shirin rufewa. Idanunsu na had'ewa gabanta yayi mumunan tsinkewa barin ma ganinsa da tayi tare da Maami. Yau shikenan ya gama da ita, tasan she's in a big trouble idan Papi yazo.

"Amal!" Ya kira sunanta da sauri ta mayar da k'ofan kai zallah Mami ta kad'a wai kode aljanu ne suka shigeta? "Kafa kwantar da hankalinka yau Papin nata ze dawo koma mey ke damunta zata sanar dashi ko ta fad'a miki abu ne Maamah?" Ta juyo tana kallon Maamah.

"A'a wallahi tak'i sanar dani komai."

"Toh Mami zamu koma nagode sosai da k'aramcin da kika nuna mun Allah sak'a da gidan aljannah."

"Ameen Abdurrahman ba komai gashi har zaka tafi ko ruwa ban baka ba."

"Haba daga gida nake karki damu mu tafi ko Maamah?" Yayi maganan had'e da mik'ewa har waje Mami ta rakasu sannan ta dawo ta nufi d'akin Amal tare da bankad'e k'ofar. "Ai Papinki ze dawo wai shin a ina kika koyo wannan d'abi'ar iyye? Har kiyi saurayi ba wanda ya sani a gidan nan? Abinda kikeyi a makarantar kenan ko?" Shiru Amal tayi mata don bata jin ma tana da energy'n yi mata bayanin komi.

"Sa'an ki d'aya wallahi yaron nada hankali wato har iyason turo magabatansa amman kike hanasa saboda ke bakison ku gina abinda kuke da shi akan addini ko? Kuma kiji ni kukan nan ya isa haka, ba dukanki akayi ba ba fad'a aka miki ba kawai kibi ki ta da wa mutane hankali haka a banza? Dubi yadda hankalin yaron nan ya tashi da safen nan kika d'agosa duk da hakan kin gansa kin kasa k'arisowa ki gaishesa toh ki cigaba Baby" tana kaiwa nan ta fice. Wani sabon kukan Amal ta rushe dashi a gun haka ta cigaba dayi har izuwa dawowan Papi. Bayan ya d'an huta Mami ta zaunar da shi ta labarta masa ababen da suka faru bayan tafiyansa ta ke kuma yabawa hankalin Abdul. Turata yayi da ta kira Amal bayan sun k'ariso Amal ta tsuguna daga waje-waje tana mey tare fuskarta da hijabinta.

"Mama na?" Ya kirata

"Na'am" ta amsa.

"Daina kukan haka kinji? Ya isa goge hawayenki." Ba musu ta shiga share hawayen nata "Gaya mun meke faruwa?"

"Papi babu."

"Nace ki gaya mun meke faruwa."

"Babu komai."

"Kode se kinji bugu ne?" Fad'in Mami.

"A'a beyi zafi haka ba zata fad'a da kanta gaya mun kinji keda waye ne?Keda Abdul d'inne?" Kai ta kad'a a hankali "Toh waye?"

"Yaya" ta furta chan k'asa-k'asa.

"Afzal??" Papi ya tambaya da mamaki yayinda Mami ta bud'e baki tana kallonta itama cike da mamaki.

"Meya samesa? Wani abun ya miki?"

"Ba shida lafiya, likita yace yana iya rasa ransa."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" both shi da Mami suka sa salati. "A dalilin mey?!" Mami tayi exclaiming cike da tashin hankali Allah sarki ashe shiyasa kwana biyu baya zuwa kuma bayi ko kiranta ita ko Allah be bata ikon kiransa ba dukda cewan yana ranta ashe beji dad'i bane.

"Meya samesa?" Papi ya tambaya finally.

"Ya kamu da ciwon zuciya." Nan ma wani salatin suka kuma sawa. "Allah sarki d'an halak shine baki fad'a mana tun wuri ba Baby? Sede kiyita kuka amman baza kiyi magana muje mu dubasa ba? Haka akeyi ne aka ce miki?" Mami ta kurareta.

"Tun yaushe yake jinyan?"

"Ya d'an kwana biyu Papi" ta amsa tana share hawayenta.

"Ya isa kukan haka in shaa Allah ze samu sauk'i ba wanda ze mutu kinji?" Kai ta gyad'a a hankali "Zamu shirya kuma duka muje mu dubasa kukan ya isa haka."

"Nagode" bata kai ga mik'ewa ba ya dakatar da ita.

"Se kuma batun Abdurrahman ko?" Yayi maganan yana kallon Mami.

"Waye shi?"

"Wan k'awata Maamah ne."

"Mey a tsakaninku?" Shiru tayi ba amsa. "Meyasa baki ta6a sanar dani ko Maminki batu akansa ba? Haka aka ce miki akeyi?"

"Papi I'm sorry kayi hak'uri."

"Baki amsa tambaya na ba meyasa?"

"Papi kuskure ne amman kayi hak'uri."

"Da yakeson turo magabatansa kuma meyasa kike hanasa?"

"Papi ba hanasa nayi ba."

"K'arya Mamin ki take kenan?" Kallon Mamin tayi sannan ta kad'a kai. "Toh meye dalili?"

"Na d'au idan akayi hakan zaku hanasa kula ni ne."

"A ganinki kula shi da kikeyi ba tare da izinin mu ba shine abinda ya kamata?"

"A'a" ta amsa tana kad'a kai.

"Tun yaushe kuke tare?"

"About 6 months now" ta amsa chan k'asa-k'asa.

"D'an gidan waye ne?"

"A Zarma na bakin layin polo."

"A Zarma me masallacin juma'ah?"

"Eh shi."

"Kina sonshi kuma?" Shiru tayi ta kasa amsawa. "Ke fa Baby kina son shi?"

"Eh Papi" ta amsa murya a ciki kallonta Mami tayi had'e da turo baki.

"Idan nace ya turo magabatansa zaki amince ki auresa?"

"Eh Papi."

"Toh shikenan tashi ki fice amman nan gaba karki sake yin wannan rashin hankali duk wanda kuka had'u dashi ya nuna yana sonki kiyi masa kwatancen gidan nan kice yazo ya gana da Papinki kinji? Bawai kuje chan kuna sha'aninku ba bawanda yasani kin ji?"

"Naji Papi nagode kuma ka sake yin hak'uri kema haka Mami."

"Shikenan ta shi ki fice" da haka ta mik'e ta wuce d'akinta.

"Ban yarda wai saboda rashin lafiyan Afzal take wannan kuka ba" fad'in Mami.

"Ko?"

"Sosai ma kuwa Baba kasan tun yaushe take wannan kuka? Da akwai 6oyayyan al'amari a tattare da yarinyar nan."

"Nima nayi zaton hakan amman kinga koda k'arya take anjima idan mukaje asibitin zamu tabbatar da gaskiyar al'amarin."

"Toh shikenan Allah kaimu."

****
Nazeefah ce tayi knocking bisa k'ofan d'akin Afzal sannan ta bud'e ta shiga yana ganin itace ya kawar da kansa. K'arisowa tayi da basket na lunch nasa ta ajiye akan table "How're you feeling? Kana iya d'aga hannun?"

"Tukunna amma da sauk'i" ya amsa.

"I cooked your favorite Rice and stew" ta sanar dashi tana me bud'e hulunan. Bayan tayi serving nasa ta taimaka masa ya zauna sannan ta zauna a gefensa itama da shirin basa abincin.

"Ahhh" ta buk'acesa.

"I can manage karki damu."

"Come on Afzal open up."

"Nace karki damu zan iya ci da kaina."

"I know laifi ne don nayi feeding naka? Besides you're still not fit." Da k'yar ta samu ya amince ta shiga basa abincin har seda ya k'oshi. Godiya yayi mata sannan ta tsiyaye masa ruwa ya had'iye magunansa yake tambayanta Ina Ummi tun jiya be sake ganinta ba.

"Nima tun jiya da na ganta tsaye dasu Sultan da Ummah tace zata masu rakiya ban sake ganinta ba." Haka kawai seyaji gabansa ya tsinke bade wani d'anyen aikin suke shiryawa a bayan idonsa ba ya tambayi kansa.

"Wayyo!" Yasa ihun k'arya.

"Lafiya?" Tayi saurin tambaya.

"Get my Dr! Hurry! Washhh!"

"Keep still ina zuwa" a guje ta fice neman likitansa inda ya ciro wayansa ya kira Sultan. A karo na farko ya d'auka.
"Sultan meke faruwa?"

"Kaman ya? Lafiya?"

"I don't want to believe ka sanar dasu Ummi batu akan Amal ka tuna ka d'au alk'awarin bazaka fad'a musu komi ba."

"Sekuma akace maka na sanar dasu wani abun?" Ya mai k'arya.

"I just have a strange feeling."

"Ka kwantar da hanaklinka ni ban sanar dasu komai ba."

"Yauwa thank you."

"Ya jikin naka?"

"Alhamdulillah zuwa anjima ma zasu sallameni."

"Toh madallah ko kun sake waya da Amal?"

"Nah bata kirani ba nima ban kirata ba."

"Alright sena shigo de."

"Okay you take care." Da haka sukayi sallama. Dawowan Nazeefah da Dr seyace ai daya sha ruwan sanyi yaji sauk'i, dubasa sama-sama likitan yayi sannan ya fice.

Wajajen k'arfe biyu da rabi Ummi da Abba suka isa gidansu Amal. Sallama suka yi a bakin k'ofar seda aka amsa suka shiga, Ummi ce ta soma sa kai.

"Lale sannu da zuwa" cewan Mami lokacin da taga Abba a bayan Ummi ne tayi saurin mayar da hijabinta. "Sannunku da zuwa" dadduma ta shiga ciki ta dau ta shimfid'a musu sannan suka gaisa. "Baki gane ni bako?" Ummi ta tambayeta.

"Eh toh wallahi" ta amsa da fara'a.

"Ummi ce, mahaifiyar Afzal na gefena ko mijina na ne Abban shi."

"Wai wai wai ashe manyan bak'i mukayi lale lale sannunku da zuwa bari in kawo muku ruwa."

"A'a karki damu daga gida muke" cewan Abba.

"Ya jikin Afzal d'in se yau Baby ke sanar damu wai beji dad'i ba."

"Jiki Alhamdulillah da sauk'i" ya amsa.

"Toh Allah k'ara masa lafiya muma muna shirin zuwa dubasa dama da Kakan Baby."

"Ayyah ba komai ko shi kakan nata na gida?" Abba ya tambaya.

"Eh barin yi mishi magana."

"Yauwa toh" da haka ta shiga ciki ta kira shi yayin da ta lek'a d'akin Amal don tazo ta musu sannu da zuwa sede ta ga d'akin nata ba kowa ko yaushe ta fita ba tare da ta sanar da ita ba? Papi na fitowa suka gaisa da Abba sannan Ummi inda Papi keta sawa Afzal albarka yana fad'a masu irin hidiman da yakeyi wa Amal yake kuma godiya. Sosai shi Abba da Ummi suka ji dad'in halin taimako irin na Afzal.

"So Alhj Muh'd ba tare da 6ata lokaci ba bari in sanar da kai meke tafe damu" cewan Abba had'e da yin gyaran murya "Munzo ne batun Afzal."

"Toh ina jinka Alhj."

"Kaman yadda Amal ta fad'a muku be ji dad'i ba, hakan yake likita yayi gwaje-gwajensa an gano ya kamu ne da ciwon zuciya."

"Tabbas haka Baby tace Allah k'ara mai lafiya ya kuma yaye mashi wannan ciwo."

"Ameen ya Allah" duka suka amsa sannan Abba ya cigaba. "Sanadin wannan ciwo daya kama sa se kan kowa ya d'aure mun rasa sababin ciwon, ba irin tunanin da bamuyi ba amman ina mun kasa gano dalilin da ze sanya masa ciwon zuciya a k'arancin shekarun da yake da ita. A fari munyi tunanin ko rashin jituwar dake tsakaninsa da matarsa ne kasancewar auran biyayya duka sukayi amman da bincike yayi bincike se muka gano ba hakan bane ciwon son 'yarku Amal ne da ya kasa furtawa kowa."

"Ciwon son Baby?" Shida Mami suka nanata cike da k'in yarda.

"Tabbas na tsawon lokaci Afzal na son Amal amman ya kasa samunta ko ku ya fad'a muku wanda har izuwa yanzu bamu san meyasa ba, kwatsam kuma kawai sega wannan shi Abdul ko?" Ya juya ya kalli Ummi inda ta gyad'a masa kai "Yauwa shi Abdul ya fito yace yana sonta har ya zamanna sunyi nisa da ita Amal d'in, toh wannan ne sababin rashin lafiyan nasa. Ganin su da yake kullum tare kuma ba yadda ya iya, gashi yana ganin lokaci ya riga ya k'ure masa se ya zammana ba aikinsa kullum se tunani, yana mey tak'ura wa kansa yana bin abun a zuciya har wannan ciwo yayi nasara akansa. Sau biyu kenan yake samun attack gashi likitansa yace muddin ba a magance masa wannan matsala ba yana iya rasa ransa idan ya cigaba da samun attack d'in."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" Mami ta sake sa wani salatin.

"Jiya ina nan ma ai na samu Amal nakeyi mata maganar inda ta tausaya wa halin da Afzal ke ciki ta kuma nuna min zata iya yafe komai saboda ceto ransa dukda cewan bata 6oye mun tsananin soyayyan dake tsakaninta da shi wannan saurayin nata ba amma tace muddin ku iyayenta kun amince ita me iya yafe farin cikinta saboda na Afzal ne. Tabbas mun san Afzal me laifi ne na hadissa duka wannan matsalar, da tun farko ya sanar daku komai da shi Abdul baze ma samu daman shigewa zuciyan Amal ba amma abinda ya faru ya riga ya faru sede ayi tunanin magance ta yanzu haka as we speak Afzal ma ba shida masaniya akan zuwan mu nan. Yanzu haka be ma san mun gano sababin rashin lafiyan nasa ba ma
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment