Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

"Abba-"

"Ashe har matarsa ya turo da ta baki hak'uri amma kika k'i sauraronsu?"

"Abba ba haka bane."

"Dakata tukuna, shi fa d'an Adam ajizi ne kuma dukan mu nan ba wanda zece baya yi wa Allah sa6o amma kuma mey? Da zaran muka tuba kuma muka nemi yafiyarsa yana yafe mana ba wanda yace Khaleefah ya kyauta abinda yayi miki amma tunda ya gane kuransa yana son ya dai-daita komai meyasa bazaki basa had'in kai ba?"

"Abba ba haka bane."

"Jameelah har yanzu ke yarinya ce shekarunki dududu nawa ne? Kin kai arba'in ne?"

"A'a Abba"

"Toh haka kikeson ki k'are rayuwarki ba aure? Bakiya son ki bar yaran da zasu yi miki addu'a bayan kin rasu? Ko gani kike Amal ita d'ai ta isheki? Kisani fa dan ba na nuna miki bawai hakan na nufin ina jin dad'in zamanki a haka bane, kiyi wa kanki fad'a ki dubi tuban mutumin nan ku rufa wa junanku asiri." Shiru tayi batace ko k'ala ba "Ko baki ji ba?"

"Naji Abba."

"Toh tashi ki tafi."

"Toh seda safe." Ko bacci Mami ta kasa yi ranan se tuna abunda Amal da Papi suka fad'a mata take gabad'aya ta rasa mey take ciki ita har ga Allah bata k'aunan abinda ze sake had'ata da Daddy saboda kasa mancewa da abinda yayi mata da take. Duk sanda ta kallesa se ta tuna da wancan mumunar ranan taji ta tsanesa. Amma ya ta iya yanzu tunda har Papi yasa baki? Bayan nan kuma kaman yadda Mummy ta fad'a ko ba dan tana so ba kamata yayi ta amince saboda su gyara zuri'a su had'a kan yaransu. Daga k'arshe de kawai ta yanke hukuncin yin Istikhara duk abinda Allah ya za6an mata shi zata bi.

_One week later..._

Cikin satin nan da aka shiga su Amal da Nazeefah suka fara exams har yau Mummy bata sake ji daga Mami ba shima Papi be sake yi mata magana ba as ya zuba mata ido yaga iya gudun ruwanta. Amal da Afzal suna zaune a parlour se faman kallo yake a laptop nasa yasa earpiece a kunne ita kuwa se karatu take kasancewar tana da paper k'arfe d'aya gobe. Wayanta dake gefenta ne ya shiga ringing dubawanda zatayi taga new number, without hesitation ta d'aga tare da yin shiru.

"Assalamu Alaikum" akayi sallama daga d'ayan 6angaren.

"Mummy?"

"Ashe 'yar tawa zata gane muryan uwarta."

"Mummy ina yini?"

"Lafiya k'alau ya kike ya gida ya Afzal kuma?"

"Alhamdulillah dukan mu lafiya."

"Ya exams toh?"

"Alhamdulillah Mummy ya Nazeefah? Jiya ma Khaleefah ya kirani muka gaisa."

"Allah sarki ya Mami?"

"Lafiyarta k'alau."

"Kwana biyu shiru banji daga gareta ba nace ko zaki iya mun texting number'nta."

"Sure Mummy bari in miki texting yanzu."

"Yauwa 'yata thank you Allah ya bada sa'an jarabawa."

"Ameen Mummy seda safe" nan tayi hanging take tayi mata sending numban Mami, itama Mumny tana gani tayi replying nata da 'Thanks.'

"Lafiya dai ko?" Afzal da ya zare kunnen earpiece nasa d'aya ya tambaya.

"Lafiya kawai tana son su gaisa ne."

"Oh Rania I'm hungry."

"Toh Ya Omri baga kitchen ba."

"Aww ma ni zanyi girkin da kaina?"

"Toh Ya Omri karatu fa nakeyi" ta fad'a cike da shagwa6a.

"Ni o'o" ya fad'a harda doke kafad'a wanda hakan yasa Amal dariya. "Toh mey kakeso kaci?"

"Na fasa chin abincin ma I just want to sleep."

"Tun yanzu?" Ta tambaya had'e da duban agogo "it's just 9 O'clock."

"Yes Rania na gaji kallon ma na fasa."

"Toh sekaje ka kwanta ai seda safe."

"Ni kad'ai?"

"Toh Ya Omri baka ga karatu nakeyi ba?"

"Nasani anan nake nufi" kafin ta karanci abinda yake shirin yi kawai taji ya sauk'e kansa a k'irjinta ita ta rasa damuwansa, ga gado amma yace shi se a jikinta ze kwanta adjusting kansa yayi ya kwanta da kyau a jikinta "Toh goodnight" tace da shi.

"Goodnight Rania I love you."

"I love you too Ya Omri" ta amsa had'e da placing peck a cikin gashin kansa. Handout nata ta d'auka ta cigaba da karatunta haka har bacci ya d'auketa itama. Se chan wajajen k'arfe biyu Afzal ya farka se jin numfashin mutum yake a kansa shafawa da yayi ya gano Amal ce. Murmushi ya saki sannan ya rik'e kanta ya janye nasa a hankali. Handout na hannunta ya cire ya d'agata ya kaita d'aki suka kwanta.

Washegari Mummy da Daddy suka jesu gidansu Papi kaman yadda Munmy ta sanar da ita cewan zasu shigo sede bata ce da Daddy ba sam Mami batayi farin cikin zuwansu tare ba amma ya ta iya? Sannu da zuwa tayi musu ta shimfid'a musu tabarma sannan ta kira Papi inda duk suka gaisa.

"Toh ga Jameelah nan sama da sati kenan yau ina jiran ji daga wajenta amma shiru se jiya da daddare bayan da Surayya ta kira take fayyace mun cewa tayi Istikhara kwanaki hud'u da suka wuce za6i kuma Allah yayi mata" se kuma yayi shiru.

"Muna jinka Abba" Daddy da ya kasa hak'uri ya tambaya.

"Khaleefah zan d'auki amanar 'yata in baka ba wai dan ka cancanta ba se don yin hakan ne ya kamata kodan mu samu mu had'a kawunan yaran nan. Kai ba yaro bane ka riga kasan komai ba sena sake nanata maka ba seka taimaki kanka kayi abinda ya dace wannan duka matanka ne ka kwatanta yin adalci a tsakaninsu Allah ya baku zaman lafiya gabaki d'aya batun yafiya kuma duka mun yafe maka Allah yafe mana gabaki d'aya."

"Ameen Abba nagode sosai in shaa Alalhu zaka sameni mey rik'on amana Jameelah nagode Allah sak'a da alkhairi."

"Ameen" duka suka amsa.

"Abba in ba matsala bana so a jinkirta auren."

"Toh Khaleefah gaskiya seka d'an bamu lokaci mu shirya."

"Wani shiri Abba? Ba shirin da zakuyi zan d'au nauyin komai da komai ni kawai kar mu jinkirta."

"Toh madallah zamuyi magana duk abinda tace haka za'ayi."

"Toh nagode, nagode sosai zamu koma."

"Toh Surayya kekuma Allah ya sak'a miki da alkhairi ya baki riban hak'uri tabbas irinku acikin mata d'ad'd'aiku ne Allah ya baku zaman lafiya mai d'aurewa."

"Ameen Abba nagode" ta amsa.

"Toh zamu koma ga wannan" Daddy yayi maganan had'e da zaro wani bak'in leda daga aljihunsa wanda yake d'auke da kud'i.

"Na mey kuma? Kaga kar mu fara haka da kai."

"Abba dan Allah kar kayi rejecting mu tafi Hjy Surayya." Duk yadda Papi beso kar6an kud'in ba seda ya kar6a saboda yadda Daddy yayita insisting.

Da Maghrib bayan Daddy ya dawo daga masallaci Nazeefah tayi sallama ta shiga d'akinsa inda ta tarar da Mummy aciki. "Ya Nazeefah lafiya?"

"Daddy ina son bayan graduation namu inyi proceeding masters program d'ina."

"Toh masha Allah anan Unimaid zakiyi?"

"A'a a UK."

"K'asar waje?" Mummy tayi sayrin tambaya.

"Eh Mummy."

"Ko meyasa?"

"Achan nafi so inyi yafi sauk'i."

"Toh shikenan se ayi making arrangements amma ai sekin jira results naku sun fito."

"Zan tafi tun yanzu in results d'in ya fito seku amsa min a tura mun achan, Nagode" tana kaiwa nan ta mik'e ta fice. Bayanta Mummy ta biyo "Why the sudden decision Nazeefah? I thought ke kikace bakiyason fita k'asar waje karatu?"

"I changed my mind Mummy."

"Saboda mey?"

"Babu."

"Saboda kiyi nesa da Amal yeah???"

"Mummy Amal ba matsala ta bace bani da damuwa da ita I'm doing this for myself."

"Ke Nazeefah bakiya tunanin mutuwa ne? Rayuwan ma nawa take da har kike neman gujewa 'yar uwarki haka?"

"Amal ba 'yar uwata bace stop referring to her as one."

"Da kin k'i da kin so Amal 'yar uwarki ce yanzu maganan da muke da Daddy'nku ma shirin auro mahaifiyarta yake Jameelah."

"What? Wa d'in?"

"Mahaifiyar Amal, Jameelah."

"Wannan wani irin abin kunya ne? Kuma kika amince?"

"Hasali ni na kawo masa shawaran ma saboda mun riga mun zama abu d'aya yanzu."

"What? Mummy are you okay? Taya zaki amince Daddy ya k'ara aure, auren ma wai mahaifiyar Amal of all people? Wallahi baza ayi abun kunyan nan da ni ba."

"Ya kika iya? The earlier the better Nazeefah just accept it mu da su mun zamo abu d'aya."

"No Mummy bazan ta6a accepting su Amal as one of my own ba duk abinda kuke shirin yi count me out cause I'll never welcome their kind into my family."

"Yayi miki kyau."

****
Acikin wata d'aya Daddy yagama had'a d'akin Mami, an sa rana nan da sati uku. Da ikon Allah kuma su Amal suka k'are exams nasu results yafito alhamdulillah duk sunyi passing. Ba yadda Mummy batayi da Nazeefah ba da tabari se bayan d'aurin auren tayi tafiyan nata amma tak'i. Ana saura sati d'aurin aure tabar Nigeria.

****
"Rania lafiya?" Afzal daya kasa hak'ura dan jin meke faruwa ya tambaya.

"Ya Omri" kawai seta rushe da kuka.

"Subhanllahi!" da sauri yayo kanta hugging her in his arms yana bata hak'uri. "Ya Omri ta tafi" ta amsa at last.

"Ita wa?"

"Nazeefah" ta sanar dashi yana share mata hawayenta.

"Ta tafi ina?"

"UK tabar Nigeria tace bazata sake dawowa."

"What? Meyasa?"

"Ya Omri har yau Nazeefah takasa acepting d'ina da Mami tun kafin ma taji Daddy ze auri Mami tace ita zata wuce Uk tayi proceeding masters nata yanzu kuma dataji gaskiyan al'amarin jiya bayan sunyi landing ta kira Mummy ta jaddada mata cewa bazata sake dawowa ba."

"Shhh it's okay sooner ot later zata gano gaskiya in shaa Allah kuma da k'afarta zata dawo."

"I really do hope so Ya Omri bana son Nazeefah tayi nesa da gida the more she stays away from us the more lost she'll be."

"I know but don't lose hope okay? Nasan Nazeefah she'll soon come around."

"Thank you Ya Omri."

"Anytime, still zamu fita d'in ko?"

"Yes."

"Alright toh."

***

Mami ce zaune a d'akinta ta baje zannuwa da dama a gabanta tana za6an wanda zata kai d'inki. Tana cikin haka sega wayanta dake gefenta ya shiga ruri dubawan da zatayi taga Daddy ke kira. 'Yar murmushi ta saki sannan ta d'aga.

"Amarya bakiya laifi koda kin kashe d'an masu gida ne."

"Haka de kace" ta amsa tana murmusawa.

"Toh ya kike?"

"Lafiya k'alau ya 'yar uwata?"

"Lafiyanta k'alau yanzun tace tasan kanki yayi zafi k'ila ma kina jin yunwa amma ba hankalinki."

"Ai kuwa wallahi ina ta sorting kayakin nawa."

"Toh mey kikeso ayi miki ordering wai?"

"Laaa kace mata kar ta damu zan dafa taliya in ci."

"A'a nikam kinga aikana tayi fad'a mun."

"Toh inde haka ne kace mata duk abinda ya sawwak'a."

"Toh shikenan ki gaishe min da Abba."

"Zeji se anjima."

"Yauwa" da haka sukayi sallama.

"Mey tace wai?" Mummy dake gefensa ta tambaya. "Cewa tayi akai mata duk abinda ya sauwak'a."

"Toh se a sai mata fried rice and chicken ai ko ya kace? Ita da Abba."

"Se abinda uwar gida tace."

"Kai Alhj bana son zolaya fa."

"Ai gaskiya ce."

"Nifa har yau fushi nake da kai."

"Afuwan in uwar gida na fushi dani a ina zan sa kaina?"

"Eh mana kak'i had'ani da 'yar uwata a gida d'aya."

"Ba wai nak'i bane Hjy Surayya."

"Kak'i ne mana tun yaushe nake binka ayi a had'a ginin nan kak'i."

"Ai kinga har yau aikin ake kan yi in shaa Allahu ana kammalawa zan dawo da ita nan chan d'in temporary ne."

"Promise?"

"I cross my heart."

"Toh Allah nuna mana ."

"Ameen Hjy Surayya nawa na kaina, bari in je in siyo ma 'yar uwar taki abinci."

"Gaskiya kam kar mu bar amarya da yunwa."

"Toh a dawo lafiya."

***
Ranar Asabar aka d'aura auren Alhj Abdallah da Jameela Muh'd akan sadaki dubu d'ari da sisin gwal arba'in. D'aurin aure kawai akayi da yammacin ranan aka kai amarya d'akinta. Se wani tattalinta Daddy yake, bayan sunci kajin amarcinsu Daddy yasa su sukayi raka'a biyu dan yima Allah godiya.




RANA D'AYA!
#RD

King miemiebeeđź‘„




Miemiebee Novels

Saturday, 6 October 2018
RANA D'AYA!
BY MIEMIEBEE
PAGE 46




Washegari...
Hayaniyan da Daddy ya jiyo a kitchen ne ya sanyasa fitowa daga d'aki inda yake kwance. Mami ya tarar tsaye gun sink ko mey takeyi oho.

"Jamee na mey kuma kike yi?" Ya tambayeta tsaye daga bakin k'ofan.

"Oh Alhj!" Ta juyo a d'an razane "Har ka tashi ne?"

"K'aran kwanukanki suka tadani" ya sanar da ita.

"Ayya yi hak'uri inzo in mayar da kai baccin ne ko zaka koma da kanka?"

"Ko d'aya tambaya nake mey kikeyi?"

"Oh! Doya nake ferewa Abba kasan bey karya ba."

"Inji wa? Ai da kin tambaya, tare aka siyo mana breakfast d'in nasa mey gadi ya kai masa nasa se inde zaki site nasa ku gaisa."

"Allah sarki nagode."

"Jimin matan nan fa godiyan mey kuma kike mun? Dan na ciyar da Abban mu? Taho mu koma d'aki" ya k'are had'e da mik'a mata hannunsa murmushi cike da kunya ta saki sannan ta mayar da kayan aikin ta k'ariso ta mik'a hannunta ta sanya acikin nasa, janta yayi izuwa d'akinsu had'e da zaunar da ita kan gado. Cikin wardrobe nasu ya nufa ya d'auko wani package sannan ya dawo ya zauna a gefenta.

"Hungo" ya mik'a mata.

"Mey wannan?" Tayi saurin tambaya.

"Kede bud'e ki ga" ba tare da yin gardama ba ta amsa ta bud'e d'an kunne ta tarar aciki k'waya d'aya. "Ko na waye wannan Alhj?"

"Bazaki iya tunawa ba?"

"A'a gaskiya" ta amsa tana kad'a kai amsa yayi daga hannunta yace, "Kin tuna rana na uku dana fara d'auko ki daga makaranta muna tsaye a k'ark'ashin makeken bishiyan chan muna hira muna shan rakke chan kika ta6a kunnenki kikaji ba d'an kunne? Muka ta nema amma muka rasa?"

Murmushi take sosai cike da mamakin yadda akayi har yau Daddy be mance da wannan rana ba bayan ita da ba don ya tuna mata yanzu ba ta riga ta mance da shi shaf. "Toh ai bayan dana raka ki gida na dawo na cigaba da nema ashe ma ba a wajen ya fad'i ba tun a bakin makarantar ku ya fad'i."

"Shine ka adana har yau Alhj?"

"Kamar yadda na adana soyayyarki a cikin zuciyata na tsawon shekaru ashirin da biyu." Ya amsa nan take.

Mamaki ne ya mamaye Mami gabd'aya ta rasa na cewa chan ta kira sunansa inda ya amsa a take "Alhj idan har kana so na haka toh meyasa ka gujeni? Na fahimci kayi mun abinda kayi ne saboda ka rama abinda Umma tayi maka amma meyasa ka kujeni? Meyasa ka daina d'aukan wayana?"

"Duk da hakan ma be kamata inyi miki abinda nayi miki ba Jamee amma a lokacin shaid'an ya riga ya rinjayeni I'm terribly sorry."

"Komai ya riga ya wuce Alhj ka daina neman tuba na."

"Nagode Allah yayi miki albarka."

"Ameen Alhj baka amsa min tambayan danayi maka ba."

"Kinsan wani sa'in mutum baya sanin muhimmancin abinda yake da shi se idan ya rasa, da fari nak'i in amince da cikin Amal nawa ne saboda tsoro da nake kar in 6ata wa mahaifina suna acikin gari, kowa ya sani mahaifina sanannen malami ne ba k'aramin zubar masa da mutunci zanyi ba idan har na amince da cikin cewa nawa ne. Tsoro ne yasa na gujeki Jamee, na d'au bayan da nayi nesa daga gareki zan iya mancewa dake, na d'au yin hakan ne ze fiye mun kwanciyan hankali ashe sam ba haka bane. Tun bayan da nayi cutting off conact dake da duk wani nawa rayuwata ta dame, acikin k'unci nake kwanciya in tashi har seda Allah ya shigo mun da Surayya cikin rayuwata, wacce ta yaye mun duk wani bak'in ciki nawa take kuma bala'in tuna mun da ke ta kowani 6angare. Duk da hakan saide idan ban kwanta ba Jamee senayi mafarkin ki, lokacin da na fara neman layinki kuma se yayita cemun switched off."

"Ba shakka nakega lokacin da muka bar Askira ne Abba ya buk'aceni da in yasar da sim card d'ina ze sai min sabo."

"Tabbas ma hakanne, saide duk da hakan ban kariya ba kullum se na gwada layinki amma baya shiga, a wannan lokacin ne na tabbata da cewa guje miki da nayi shine babban kuskuren dana tafka a rayuwa na, a wannan lokacin na tabbatar da cewa akwai gur6in da kika mamaye a zuciya na, gur6in da se ke ne zaki iya cike mun shi. Lokacin da muka dawo Nigeria na koma Askira don nemanki inda ake tabbatar mun da cewa Allah yayi wa Abba da Umma rasuwa."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un Allah ya jik'an su da rahama a tunani na gabad'aya wanda ka kaini gunsu sune iyayenka."

"A'a wan Abba ne da matarsa."

"Allah sarki."

"Daga chan se na wuce gidanku inda ake cemin kun bar garin Askira da dad'ewa kuma ba wanda yasan inda kuka dosa nayi cigiyarku har na gaji amma rana baya ta6a wucewa ban yi tunanin wani hali da yanayi kike ciki ba. Please forgive me Jamee."

Hannunsa ta d'au ta had'a da nata tana murzawa a hankali "Alhj komai ya riga ya wuce wannan d'an kunne kuma zan cigaba da adana shi as a symbol of my love for you" Murmushi ya sakar yana mey jin dad'in abinda ta fad'a sannan ya janyo wayanshi "Bari in kira Hjy Surayya muji daga gareta."

"Gaskiya ya kamata." A karo na farko Mummy ta d'aga wayan inda suka gaisa. "Kun jini shiru ban kawo muku breakfast ba ko? Wallahi Khaleefah ne yamun tsiya na sa Alarm a wayana kawai ya saci ido na ya d'auke wayan sena makara."

"Barka, dama waya aikeki? Karki damu mun riga mun karya."

"Kai ina ruwanka? Idan na kawo se kar ka ci so ka fad'awa 'yar uwata kar tayi wahalan yin girkin rana I'll make it up to you guys."

"A'a Hjy Surayya dan Allah karki sa kanki wahala."

"Nikam ka had'ani da 'yar uwata mu gaisa" yana murmushi ya mik'awa Mami wayar "Assalamu Alaikum" ta soma da cewa. "Amaryar mu" Mummy ta amsa.

"Kai 'yar uwa bazaki bar zolaya bade ya kike toh ya Khaleefah?"

"Gashi se shiri yake ya kusan komawa school."

"Allar sarki Allah kiyaye ya bada sa'a."

"Ameen sena shigo anjima sauran kice zakiyi girki kuma."

"Oh 'yar uwa kar ki sakaltani dayawa fah."

"Ba ga Alhj ba yasan yadda zeyi dake ai."

"Kai 'yar uwa."

""Ahtoh barin bar ku haka se na shigo anjima."

"Toh muna godiya Allah kaimu."

"Yauwa se anjima."

Kaman yadda Mummy ta d'au alk'awari bayan sallan Azahar ta shigo da abinci kala-kala se sauk'e kuloli kawai ake tayi daga mota. Yini Mummy tayima Mami se kusan Maghrib da Daddy ya kusa dawowa ta koma gidanta. Zaman lafiya maras misaltuwa Mummy da Mami sukeyi sekace ba kishiyoyi ba wane wasu 'yan uwan jini, dai-dai da rana d'aya Daddy be ta6a jin kansu ba. Hasali har had'a kansu suke su biyu su waresa. Bayan ya k'are wa Mami kwana bakwai na amarchi ya soma yi musu kwana bibbiyu duka.

***
Haka kwanaki suka cigaba da shud'ewa yayinda zama yake k'ara yima wad'annan abokan zama dad'i. Labarin Nazeefah kuwa duk sanda ta bugi iska takan d'au waya ta kira Mummy amma dai-dai da rana d'aya bata ta6an d'aukan waya ta kira Daddy ba ko da shi ya kirata ma se ta ga dama take d'agawa.

9 months later...

Abubuwa da dama sun gudana, Amal hutu ya k'are sun koma makaranta har sun k'are first semester suna second semester yanzu. Maamah kuma an kai goron tambayan auranta, labarin dawowan Ya Abdul kuwa shiru har yanzu ko su Mama sunyi mishi magana se yace shi ba yanzu ba. Sultan ko har yau labarin aure shiru ya tsaya rawan ido. Labarin k'awar Amal Falmata kuwa tayi aure abunta tabar Maiduguri ta koma a Azare take da zama inda mijin ke aiki. Har Azare su Amal suka kaita suka dawo. Tun tafiyan Amal wane akan allura Afzal yake zaune, minti-minti yake yi mata waya yaushe zata dawo. Sam baya iya jure rashin ta a kusa da shi.

***
Amal ce zaune a d'akinsu da Afzal se faman karatu take gefenta kuwa plate ne cike da kayan k'walama ba abinda babu daga abinda ya kama kan tuwon madara, calanda, gullisuwa, tsamiyan biri, ba abinda babu ta d'au wannan ta d'au wancan. Haka kawai ta ke wani irin wawan kwad'ayi kwana biyu duk abinda tagani setaji tana so. Ba da dad'ewa ba wayanta dake ajiye a gefenta ya shiga ruri dubawanda tayi taga Afzal ke kira k'aramar tsuka taja ta cigaba da yin abinda ke gabanta. Yana tsinkewa ya shiga kira again nan ma tak'i d'agawa be dad'e ba sega sak'on sa.

_Please pick up Rania I'm sorry._
Tana cikin shawaran ta d'aga ne kokuwa sega call nasa again nan ma seda ya kusa tsinkewa ta d'aga had'e da yin shiru.
''Baby yi hak'uri mana."

"Nifa ban ce kayi mun laifi ba."

"Toh meyasa in na kiraki bakiya d'agawa?"

"Karatu nake bana son distraction."

"Baby Ya Omrin na kine kuma yau distraction? Yi hak'uri kinji Yaya is sorry."

"Shikenan ni kayi ta mun wasa da hankali kenan kullum, yau kace gobe, jibi kace gata dan kawai kaga ina missing naka."

"Haba baby yi hak'uri wallahi sune suka k'i sakemu saura mana trips biyu amma de yanzu."

"Toh nikam se yaushe zaka dawo?"

''Zuwa next week in shaa Allah.''

''Har next week Ya Omri?''

''I'm sorry.''

''Promise?''

''I promise Baby.''

''Toh Allah ya kaimu.''

''Ameen kin daina fushin?''

''Ba dole na ba."

"That's my Rania so ya kike? Should I FaceTime you?"

"Okay." Nan ya katse wayayn ya yi mata video call inda ta d'auka suka cigaba da gaisawa. "Baby?"

"Na'am'' ta amsa.

''Mey kikeci haka ba ni?''

''Oh tuwon madara ne.''

''Da kuma mey? Mey wancan bak'in abun?'' Plate d'in ta d'aga ta matso da shi kusa ''Tsamiyan biri ne.''

''Rania yaushe kika fara wannan ciye-ciye?''

''Ba ka nan ma ban tsira ba ko?''

''Toh ya Mami? Sun dawo?''

''A'a wai daga chan zasu wuce Dubai."

"Oh ayyah Papi fa? Yana nan k'alau?"

"Eh Mummy tana kula da shi."

"Allah sarki toh yayi kyau."

"Toh se anjima ko? Kaga karatu nake" tayi maganan tana nuna masa handouts nata.

"Wait Rania d'an tsaya."

"Yaya wai yau kai kake hana ni karatu?"

"Not at all, Idona ne kokuma k'iba kika k'ara bayan tafiya na?"

"K'iba?" Ta nanata tana duban jikinta

"Eh mana kinga yadda kumatunki suka ciko."

"Kai Ya Omri ka fa san bana son inyi k'iba."

"Ai kuwa se kin fara slimming dan kin riga kin d'au hanya."

"Omg! Dan Allah dagaske kake na k'ara k'iba?"

"Kije ki duba mirror kiga" katse video call d'in tayi ta ruga gun madubi tana matse kumatunta. Kuma fa hakanne da gaske ta k'ara k'iba toh kode? Kai da k'yar
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment