Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kam har da godiya Afzal yayi mata sannan ya fice. Ba k'aramin dad'in hakan taji ba bayan tafiyansa itama ta shirya ta wuce school. A makaranta ne Ummi ta kirata bayan sun gaisa take bata hak'uri game da abinda tayi mata, sosai Nazeefah ta nuna mata komai ya riga ya wuce saboda ko itace a shoes na Ummi abinda zata aikata kenan kawai abinda bata ji dad'insa ba shine damar da ita da Mummy suka k'i bata tayi bayanin kanta.

Afzal ne zaune a office gabad'aya hankalinsa ya duk'ufa akan waya yana kallon hoton Amal Sultan yayi knocking bisa k'ofan, kafin yace ze kimtsa har shi Sultan d'in ya sa kai. Da wuri Afzal ya tura wayan nasa k'ark'ashin drawer sede Sultan ya riga ya gansa, kai kawai ya kad'a ya k'arisa ciki. Afzal kam ya sha mamakin ganin Sultan. Zama yayi akan kujera tare da mik'a wa Afzal hannu da ikon Allah Afzal ya kar6a suka gaisa.

"Ya jikin naka?" Ya tambayesa.

"Da sauk'i I'm fit."

"Ma shaa Allah Amal ce ta turoni dama."

"Da mey?" Yayi saurin tambaya. Ledan dake ajiye a gefen k'afansa ya d'ago tare da turawa Afzal ta 6angarensa "She's wishing you a speedy recovery." Amsa yayi ba musu ya sa a fridge bayan daya lek'a ciki yaga Aldeb ne kaca-kaca da zo60. "I'll call her up."

"Alright ni zan wuce." Shiru Afzal yayi masa har ya kai ga bakin k'ofa sannan ya kira sunansa, hakan ya sanya sa tsayawa chak.

"Thank you" ya furta.

"You're welcome" ya amsa sannan ya fice had'e da ja masa k'ofar. Wayansa ya zaro yayi scrolling kan contact na Amal tare da dialing bada dad'ewa ba se gashi ta d'aga sede sa6anin yadda ta saba kiran sunansa anytime ya kirata yau d'in batayi ba ko sallama ma tak'iyi shi da kansa yayi gyaran murya yace, "Assalamu alaikum" da shirun yayi yawa.

"Wa'alaikumus salam Yaya ina kwana?"

"Lafiya k'alau ya kike?"

"I'm good ya jiki?"

"Alhamdulillah yanzu Sultan ya iso min da sak'onki nagode ko?"

"Ba komai Yaya Allah k'ara sauk'i." Sede daga yadda take mar magana sama-sama yasan tana fushi dashi kuma yes ya sani she has every single right to act this way.

"Ya school yau baki fita bane?"

"Se anjima banida early morning lectures."

"Alright toh."

"Toh se anjima" wow ya numfasa a hankali yau har Amal ce ke neman kashe waya a kansa? "Wait" yayi saurin cewa.

"Yes wani abu ne?"

"I'm sorry kinji?"

"Ni baka mun komai ba Yaya."

"Na sani Lily you don't deserve any of the attitude I've been giving you and I'm sorry."

"Ba komai Yaya ya wuce."

"Ki gaida su Mami toh."

"Zasuji" da haka ta katse wayar. Tunani ya shiga yi shi kad'ansa.

*****
Haka nan tafiyar ta cigaba ba laifi Afzal ya soma sakewa da Nazeefah sukan zauna a parlour suyi kallon sports ko film tare har abinci ma sun soma ci tare akan dining table. Nazeefah can't ask for more a duk lokacin da suke tare da Afzal ji take like she's the most happiest girl on earth, tana son shi, tana sonshi sosai ba tantama akan hakan. Da kansa yau Asabar bayan sallan La'asr yayi tunanin zuwa gun Amal dan gabad'aya ta fita harkansa ko kiransa bata sake ba har yau, abinda ya mata a asibitin ba k'ramin 6ata mata rai yayi ba tace ta yafe amman bazata iya mancewa da shi ba. Shiri yayi tsaf ya wuce gidansu wanda baze iya tuna rabonsa da yin hakan ba, sosai yayi missing nata baze ma iya kwatantawa ba sede isansa ya tarar da exactly motan ranan wanda yake da tabbacin motan Ya Abdul ne. Daga bakin corner'n ya tsaya yayinda gabansa yayi wani irin mumunan fad'i lokacin da ya hango kan Amal cikin motan be 6ata lokaci ba ya juya. Tuk'i yake amman gabad'aya hankalinsa bai kan hanyan shi kansa besan inda ya dosa ba. Zuciyarsa ce ta soma yi masa k'ona yayinda idanunsa suka shiga kakkafewa dan azaba kafin ya hankara kawai ya jisa jikin pole. Da sauri mutanen kusa suka afka kansa akayi saurin kaisa asibiti sannan aka shiga neman 'yan uwansa. Abba aka samu aka kira ko daya ji beyi mamaki ba dama yasani nan kusa se abu makamancin hakan ya sake faruwa. Kafin ace mey labari ya iske 'yan uwa gabad'aya nan da nan shi da Ummi suka yo asibitin itama Nazeefah bata 6ata lokaci ba ta wuce a chan sukaje suka had'e. Bayan likita ya fito suka duk'ufa sukayi kansa suna tambayansa ya jikin Afzal d'in.

"Idan ban manta ba this was the patient I treated some weeks ago right?" Ya tambayesu. Ummi ce tayi saurin gyad'a kai "Yes Dr."

"Haba Hajiya haba! Taya kuke neman halaka d'anku? Shin baku san idan ya cigaba da samun arrest d'innan wataran zuciyar tana iya mutuwa tak'i tashi gabad'aya ba? Yaci ace kun gano inda matsalar take kun magance ta tun wuri don bazan 6oye maku ba rayuwan d'anku na cikin hatsari" ya fayyace masu. Sosai Nazeefah ta shiga duhu toh meke jawo masa tsinkewan zuciyan ne? Gashi nan de a gida bazaka ta6a ganinsa cikin damuwa ba. Kode shida mutanen sa ne na office? Ta tambayi kanta sede bata da amsa.

"Yanzu ya jikin nasa?" Abba ya tambaya.

"Mude munyi abinda zamu iya sauran mun bar wa Allah."

"Dr dan Allah do what you can to save him."

"In shaa Allahu excuse me." Ummi da Nazeefah ne suka shiga ganinsa yayin da Abba ya ke6e a waje yana mamakin halin da Afzal ke neman jefa kansa. Wajajen k'arfe tara na dare Sultan yazo dubansa shi kad'ai ne a lokacin yana mik'e kan gadon nasa da hannunsa a d'aure inda ya samu targad'e sanadin accident da yayi encountering d'azu.

"Ya jikin?" Kai zallah ya gyad'a masa nufin da sauk'i.

"Afzal me kake shirin yima kanka? It has to stop idan kai baka valuing life naka mu munayi dan Allah ka yayyafa wa zuciyarka ruwan sanyi ka sauk'e girman kan nan ka sanar da Amal kana sonta. Don kayi hakan doesn't mean zaka mutu amman rik'ewan da kakeyin shine ze iya kashe ka."

"So be it idan na mutu Sultan but gaskiya d'aya ce it's too late for everything."

"It's not Afzal it's never too late." Kai ya kad'a da nufin a'a "Amal ta riga tayi mun nisa bazan iya samunta ba."

"Ka bani go ahead kawai in sanar da Abba address nata ina da tabbacin su Abba bazasu hak'ura ba har se idan sun shawo kanta da iyayenta ta kasance taka."

"Ban tsamman hakan is possible there's no point of telling Abba and Ummi about her, tana son Abdul bazata iya rabuwa dashi saboda ni ba."

"Haka kake gani?"

"Haka yake I went to visit her d'azu ne ko jiya ne bazan iya tunawa ba achan na gansu tare a motanshi, tana son shi Sultan, da k'yar zata iya yafe sonsa ma wani koda kuwa mutumin ya kasance ni ne."

"Toh yanzu ya kenan? Kana nufin ba matakin da zaka iya d'auka?"

"Babu tunda bata sona I can't force her into loving me."

"Ya kake magana kaman ka sameta kace mata kana sonta tak'i ka ne? Fa Amal bata ma san kana sonta ba wallahi bata sani ba."

"Toh what difference will it make koda ta sanin?"

"What if I tell you itama Amal d'in tana sonka?"

"Da kace ka sanar da ita ranan, dagaske kake?"

"Yes Afzal bazan iya juran ganinka a haka ba so I told her you love her."

"Mey tace?"

"Ta kasa yarda amman bata bud'i baki kuma tace bazata iya sonka ba."

"Just let her be there's nothing more I can do."

"Kai ke da abunyi Afzal kuma har yanzu ina fad'a maka kana da daman mallakar Amal saboda ba wanda ya cancanci soyayyarta kaman ka."

"How?? Dan ina mata hidima shikenan se ya zamanto dole ta soni?"

"Ba haka nake nufi ba Triple A ina nufin a tsakaninka da Abdul yake kowaye, kai ka dubi k'aranchin shekarunta ne dakuma karatunta dalilin da yasa kaja baya kenan kak'i furta mata k'udirinka ko ba haka ba? Kafi son se karatun nata yayi nisa right?" Kai ya gyad'a a hankali yana mey sauraronsa. "Toh shikuma Abdul d'in be damu da ta cigaba da karatun nata ba koko a'a shi burinsa kawai ya mallaketa ne ko anan aka zauna aka duba ansan wa yafi wani kaifin tunani da kuma wanda ya cancani soyayyarta. Ka riga Abdul saninta, ka riga Abdul fata sonta saboda haka Amal taka ce ba tasa ba, ka sameta ka fad'a mata k'udrinka Afzal ina da tabbacin cewa Amal bazata yi turning naka down ba."

"Ka mance da ita kawai Sultan."

"Idan nayi kai bazaka iya ba Afzal, Amal ta riga ta zama jinin jikinka bazaka iya rayuwa ba ita ba."

"Don't tell Abba anything about her please Sultan."

"Afzal-"

"Dan Allah nace maka komin yaya ne kar ka sanar da shi komai."

"Haka kakeso ka cigaba da zama da wannan ciwo har seta kasheka tukun?"

"Yafiye mun da inyi forcing Amal lallai-lallai seta soni."

"Shikenan Allah k'ara ma lafiya."

"Ameen thank you."

"Toh ni zan wuce" yayi maganan had'e da mik'ewa. "Sena dawo gobe Ummah ma gobe zata shigo tace."

"Allah ya kaimu kace ina gaisheta" da haka ya fice ya ja mishi k'ofan. Sallama yayi wasu Abba sannan yayi tafiyarsa.

Washegari shi da Ummansa suka dawo kaman yadda ya fad'a. Bayan sun duba Afzal sun fito Abba ya buk'aci Sultan da ya tsaya don haka Ummah ma ta tsaya jiransa.

"Hajiya Aisha?" Ya kirata.

"Na'am Alhj" ta amsa "Zamu wuce."

"Mungode sosai Allah ya biya amman kafin nan I want to have a word with you."

"Toh Alhj ina jinka."

"Bismillah kizo ki zauna" ba gardama ta k'arisa gefen Ummi ta zauna. Gyaran murya Abba yayi sannan yace, "Ko ban tambaya ba Sultan nasan kasan gidansu yarinyar nan da take bawa Afzal wuya, ka dubi girman Allah da halin da yaron nan ke neman jefa kansa ka kaini gidansu in samu iyayenta asan nayi. Idan shi baida wayo besan ciwon kansa ba ai kai a matsayinka na abokinsa kasan hakan ko ba haka ba?"

"Wai Alhj kana nufin Sultan yana sane da komi yak'i yin magana?"

"Haka nake zato Hajiya shiyasa nakeson a matsayinki na mahaifiyarsa ki rok'esa kisa baki ya bamu had'in kai mu ceto ran d'an nan baza mu biye masa ba."

"Sultan?"

"Na'am Ummah."

"Yanzu kana sane da komai amman ka gwammace kayi shiru saboda rashin lafiyan abokin naka be dame ka ba?"

"Wallahi Ummah ba haka bane Abba kayi hak'uri nake ganin nafi kowa damuwa da halin da Afzal ke ciki musamman ni dana san kalan hidiman da yake yima yarinyar nan, nauyin makarantarta gabad'aya ya d'auke wa iyayenta. Duk abinda ya dace ayi Afzal nayi mata amman ya furta mata k'udirinsa ya kasa wai sede ita ta gano hakan da kanta ita kuma ta kasa, nayi-nayi dashi abun ya gagara kuma ya had'ani da Allah kar in sanar daku komai akanta komin yaya ne."

"Toh kuma seka biye masa ne Sultan? Bakaji me likitansa yace ba? The more yake samun attack d'in wataran zuciyan na bugawa gabad'aya ta daina aiki shikenan kuma k'arshensa kenan ai kamata yayi tun kan maganan yayi nisa haka kazo ka sameni ka fad'a mun abinde ake ciki wallahi banida labari se yau" cewar Ummi. "Meye sunan yarinyar?"

"Amal" ya amsa.

"Amal?" Ta nanata, "Bade Amal da na ke ji a bakinsa ba? Yo Alhj ai nasan yarinyar mun sha gaisawa da ita ta wayan Prince."

"Kinsanta fa kikace?" Abba ya tambaya da mamaki.

"Ban ta6a ganinta ba amman muna waya itace me kawo mana Aldeb me dad'in nan amman Afzal anyi bahon d'a wallahi yanzu yarinyar nan dake sonsa d'inne ya kasa tunkararta ya fad'a mata yana sonta har abun yayi nisa haka?"

"Wallahi Ummi bakiga fad'an dana rink'a yi masa ba amman yak'i jina shine kawai na hak'ura na barsa in ga iya gudun ruwansa."

"Ita yanzu yarinyar tasan yana sonta ne?" Abba ya tambaya.

"Bata sani ba Abba nine nayi gwanintan gaya mata."

"Mey tace?"

"Tak'i yarda sam har kuka tayi mun da hawaye wai sharri nakeyi wa shi Afzal d'in take cewa idan da har dagaske ne ai da ze sameta ya fad'a mata kokuwa iyayenta."

"Tabbas tayi gaskiya" Ummah tace.

"Yanzu tashi ka kaini gidan nasu" cewar Ummi "Kai Alhj ba seka je ba tunda na riga nasan yarinyar zanyi mata magana in shaa Allahu za'a dace dan idan har itace Amal d'in kaman yadda Sultan ya fad'a toh yarinyar bata da matsala."

"Toh Allah kare" basu kai ga mik'ewa ba sega Nazeefah ta shigo da basket na abinci rik'e a hannunta, binsu duka tayi da gaisuwa sannan take tambayarsu ina zasu bayan ga abinci nan ta kawo.

"Ermm.." Ummi ta shiga neman dalili "Zan rakasu ne nan in wuce gida in watsa ruwa kiyi sauri ki kai wa Afzal d'in kar yaji yunwa."

"Toh Allah ya kare" nan ta zarce d'akin Afzal yayinda su kuma suka fice. Sauk'e Umma Sultan yayi sannan shida Ummi suka k'arisa gidansu Amal. Waya yayi mata akan cewa ta fito bayan ta fito ya sauk'o daga motan ya sameta inda suka gaisa.

"Ya Yaya yake? Ya jikin nasa?"

"Jiki ya sake tashi ai yanzu haka ma yana asibiti."

"Innalillahi wallahi banida labari, tun yaushe?"

"Jiya bayan da yabar nan."

"Nan kuma?" Ta tambayesa cike da rashin fahimta "Yaya bezo nan bafa jiya."

"Yazo kede baki gansa ba amman shi ya ganki."

"Anya kuwa Ya Sultan? Da yaushe?"

"Sosai kuwa lokacin da kuke tare da Abdul se be k'arisa ba ya juya. Bisa yadda ciwonsa ya tashi yayi hatsari a hanya amman da sauk'i targad'e kad'ai ya samu." Mutuwa sosai jikin Amal yayi gun ta ma kasa cewa komai se chan muryarta ta dawo mata.

"Ya Sultan-"

"Ga Umminsa nan acikin mota tazo kuyi magana." Wani irin har6awa zuciyarta tayi, yanzu take gaskata zancen Falmata, Ya Abdul, Maamah da kuma shi kansa Ya Sultan d'in. Sede kanta ya d'aure, meyasa Yaya ya kasa sanar da ita k'udurinsa akanta? Meyasa yay ta wahalar da kansa akanta? Ko dan bata kai ya furta mata kalaman so bane? Well tasani Yaya ba tsarinta bane amman ai da ko Papi ne ya samu ya sanar da shi, da duk hakan be faru ba. Yanzu ba wannan ba, shin ina yake son tasa soyayyar Ya Abdul nata?

"Bismillah ki shiga motar" kai ta shiga kad'a masa da nufin a'a.

"Ya Sultan dan Allah ka rufa mun asiri wallahi ni ba nice sanadin halin da Yaya ke ciki, ban san Yaya so na yake ba wallahi da na gano hakan bazan ma fara kula Ya Abdul ba koda kuwa ace be furta yana so na ba please karka had'ani da Ummi."

"Calm down Amal tazo ne ta nemi alfarma gunki ba da niyyan tashin hankali ba ki k'arisa ciki tana jirarki" sede ina Amal ta kasa gabad'aya ta rud'e k'arshe seda Ummin ce ta fito da kanta. Bakinta na rawa ta tsuguna ta gaishe da Ummi sannan ta d'agata ta share mata hawyenta ta jata izuwa wani benchi suka zauna.

"Baki gane ko ni wace ba ko 'yata?"

"Ummin Afzal?" Kai Ummi ta gyad'a mata. "Ya jikin nasa?" Ta tambaya a hankali.

"Da sauk'i Alhamdulillah nasan kina mamakin gani na aban haka ba notice ko?" Nan ma kai ta gyad'a a nitse. "Taimako nake nema koma ince alfarma don shi yafi dacewa da k'udurin da nake tattare da shi. Zan iya samu?" Shirun da tayi ya bawa Ummi go ahead.

"Amal ran Afzal na cikin hatsari, likitansa yace idan ya cigaba da samun attack wataran yana iya rasa ransa gabad'aya kuma ke kad'ai keda ikon ceto mana ransa."

"Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un" ta furta yayinda idanunta keta kan cikowa da hawaye.

"Kinji Mama na? Nasan da wuya da ciwo da kuma zafi amman dan Allah ki amince ki auri Afzal ki cetosa daga cikin wannan halin da ya fad'a" wani irin mumunan fad'i gaban Amal yayi. Aure gabad'aya? What if she's not ready? What of Ya Abdul? Shi anyi masa adalci kenan?

"Amal baki ce komai ba" Ummi tayi magana bayan shirun da Amal tayi. Baki na kakkarwa tace, "Ummi ban san me zance ba, ina son Yaya, banida kaman shi ban ta6a neman abu gunsa na rasa ba, komi nakeso yana mun, baya wasa da sha'ani na, na d'aukesa a matsayin wa na babba wanda nake da burin zama big aunty ga yaransa not that ni in kasance matarsa, bazan iya auran Yaya ba."

"I know how it feels Amal ko ni nan da kike gani banso aure na da Abban Afzal ba, ba nice mahaifiyarsa ba. Ya ta ce mahaifiyarsa, ya ta na k'ut-k'ut mutuwa tayi mana k'atutuwa gashi lokacin Afzal na d'an jariri ko wata be kai ba. Dole aka sani rabuwa da masoyina aka aura min mijin ya ta imagine how difficult it must be for me amman hakan na hak'ura na rungumi k'addara look at where I am today, Abban Afzal shine sanyin idanu na bana jin zan iya rayuwa ba shi. Kema idan kika hak'ura komi me wucewa ne kinsan halin Afzal ba sena irga miki ba muddin yana son abu yana iya k'ok'arinsa yaga ya adana abun ya kuma kula dashi, Afzal will never disrespect or take you for granted dan Allah kiyi la'akari da halin nan da yake ciki ki amince Amal."

"Ummi ni idan ta nine bani da matsala, I can sacrifice the entire world for Yaya, zan iya yafe farin cikina saboda na Yaya because he deserves it and kamar yadda kika fad'a nasan Yaya baze ta6a walak'anta ni ba matsalar ba daga ni bace."

"Daga ina ne toh Mama na?"

"Ya Abdul" ta numfasa.

"Waye shi?""

"Shine wanda muke tare da shi, wanda yake da burin mallakata kaman yadda nima nake da burin kasancewa da shi. Ya zanyi? Ta ya kukeson in fara sanar da shi wannan labari? Bazan iya ba his last girlfriend cheated on him nima bazan iya masa hakan ba, Allah ma seya tambayeni" tasa kuka.

"Shhh!" Ummi ta rungumota tana bata hak'uri "This is not called cheating my dear, ba da son ranki zaki rabu da shi ba and I know, na sani Afzal yayi kuskure amma bazamu iya maida hannun agogo baya ba all we can do now is to make things right. In har Abdul nakin na da tausayi ze fahimci halin da Afzal ke ciki ya yafe son da yake miki masa, Amal bana son in rasa d'ana."

"In shaa Allah ba zaki rasa sa ba Ummi."

"Toh ki amince ki aure sa."

"Ummi I'm not the one to decide like I told you zan iya yafe farin cikina saboda na Yaya idan Ya Abdul ze iya hak'ura nasan iyaye na ma basu da matsala dan Yaya kaman d'an gida yake problem d'in kawai Ya Abdul ne."

"A'ina ne gidansu ni da Abban Afzal muje muyi musu bayanin halin da ake ciki."

"Yana nan Polo."

"Zan iya samun layin wayanshi?" Kai ta gyad'a ta d'ago wayanta takai kan contact d'in sannan ta mik'a mata nan take ta kofe a wayarta. "Nagode sosai Amal, thank you so much." Nan ma kai zalla ta gyad'a "Zan iya komawa ciki?"

"Sosai mamana ki gaishe Umminki idan kin shiga ina sauri ne da na tsaya mun gaisa."

"Bakomai zataji" sallama tayi wa Sultan sannan ta wuce ciki direct se d'akinta. Kuka kawai ta shiga yi a tunaninta shi ze iya magance mata wannan musiba. Wannan wace irin k'addara ce da se an rabaka da masoyinka? Taya zata fara kallon idanun Yaya da wani manufa? Taya zata fara zaman aure da mutumin da ta d'aukesa a matsayin wanta na jini? This's so wrong bazata iya ba. Meyasa Yaya ya jata jiki haka bayan yasan da wannan manufan a zuciyansa? Oh Allah ga ni gareka.


**** A gida Sultan ya sauk'e Ummi nan da nan ta samu Abba ta sanar da shi yadda sukayi da Amal. Amsan numban Abdul d'in yayi akan shi zeyi masa magana ko gobe se suje gidan nasu. Har a nan Afzal dake asibiti be san meke faruwa ba, shi de se duba wayansa yake ko zega sak'on Amal tunda daman ta daina kiransa yanzu amman sak'on ma yau babu. Amal nata kanta ko tunawa da shi batayi ba. Wajajen k'arfe goma Ya Abdul ya kirata. Share hawayenta tayi ta gyara muryarta gudun wai kar ya gane kuka take sannan ta d'aga.

"My Baby" ya soma da cewa.

"My Ya Abdul" ta amsa "Ina yini?"

"Lafiya ya kike? Ya school?"

"Alhamdulillah ya office? I missed you."

"Alhamdulillah I missed you more my baby."

"Shine baka zo ba?"

"Aiki ne ya rik'eni Baby har ranan sunday ma ban tsira ba."

"Ya suke wahalar min da Baby na hakane kam?"

"Karki damu wahalan is worth it, atleast it comes with money kinga se nayita tarawa in auran mu yazo muyi gaggaruman celebration me hashtag irin na Instagram" dariya sosai ya sata dukda cewan bata mood d'in.

"Ko ba haka ba?"

"Hakane" ta ce dashi duk da cewan tasan idan ba wani ikon Allahn ba bazata iya kasancewa da Ya Abdul ba.

"Ya naji muryan ki k'asa-k'asa haka Baby lafiya?"

"Lafiya Ya Abdul mura nakeyi."

"Shine baki fad'amun ba ni da nace ko cizo sauro ya miki you should call and tell me." Nan ma bata da niyyan yin dariya amma seda ya sanya ta yi. "I'm sorry forgive your Baby."

"Baby ta shirya shan pepper soup gobe se muran ya sauk'a gabad'aya."

"There's no need for that ina shan magani."

"Nifa na fad'a miki sauran inzo kik'i fitowa har cikin d'akinki zan shigo in fito dake."

"D'ankaren nauyi ne da ni fa bazaka iya ba."

"Niko d'ankaren k'arfi ne dani ba abinda bana iya d'agawa."

"Toh shikenan da-" se kuma tayi shiru. Haka kawai taji kar tayi saurin sanar dashi abinda ke faruwa tana sa ran wani mu'ujizan ze faru ya zamanto Afzal ya warke ba se an raba ta da masoyinta ba.

"Ya kikayi shiru?" Yayi saurin tambaya.

"Babu."

"A'a fad'i de."

"Allah babu."

"Baby so kike in taho da bulala gobe ko?"

"Kuma seka zaneni?" Ta wani zum6uro baki.

"Toh tell me menene?"

"Dagaske babu."

"Kinga irin taurin kan naki da nakeso ba? Amal I can't wait to own you, ki bani go ahead amma kink'i kullum kice ke a'a it's almost getting to a year."

"Kai Babe kai kuma harda zugau 5 months ne fa."

"6 ne and it still makes no difference ni ko formal gaisuwa ne azo ayi su Mami de su san sunyi in law."

"Ya Abdul I'm sorry" kawai seta rushe da kuka.

"Subhanallahi wani abun ne na fad'a? Dan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment