Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ki bata wayanta ni bana son matsala."

"Mstw" wayan Amal taja ta bud'e ta latsa numban Nazeefah had'e da zubawa cikin wayan Safiyya sede da mamaki taga babu numban a wayan Safiyya how can it be possible? Ta tambayi kanta.

"Babu ba?" Amal ta tambayeta kai zalla ta gyad'a "Ai na fad'a miki ba su bane dan Allah ki bata wayarta amshi Safiyya kiyi hak'uri."

Amsa tayi tace "Ba komai Aunty Allah k'ara miki lafiya" da haka ta fice.

"This can't be possible wallahi ina ji a jikina 'yar nan munafuka ce."

"Maamah please enough gashi de kin gani ko lamban Nazeefah bata dashi kuma bataje boko ba bale kice ta haddace lamban ne akanta ranan lamban ta na tambayeta amma bata sani ba, babu yadda za'ayi kuma ace ta haddace na Nazeefah, na gaya miki ba had'in Safiyya da Nazeefah."

"Hmm toh mey gadin kine? Wallahi dole akwai wanda yake fad'awa Ya Afzal abubuwan nan ko kina tsammanin shi yake zama yake shirya zancen?"

"I will not be surprised idan shi yake shirya komi Maamah saboda a fili yake nuna mun na fita a kansa baya sona ban ta6a tsammanin Yaya zemin haka ba watarana wallahi yanzu nake nadaman auransa da nayi nasan ko da wasa Ya Abdul baze ta6a yimun haka ba."

"Kar ki ce haka Amal Ya Afzal mijinki ne har yanzu."

"Maamah I miss Ya Abdul I miss him so much" hugging nata Maamah tayi yayinda ta cigaba da bata hak'uri.

"Amal be kamata mu nad'e hannu mu zubawa koma wa yake miki wannan aika-aika ido ba we have to do something."

"Mey zamuyi toh Maamah? Ba muda hujja bamuda komai."

"Ido ya kamata ki sawa mey aikin kin nan wallahi ina ji ajikina itace munafukar lamarin nan."

"Nace miki ki cire Safiyya daga lamarin nan."

"Hmm toh ke yanzu haka zaki cigaba da zama a gidan nan Ya Afzal na cusa miki bak'in ciki yana miki walak'anci har seya kasheki tukuna? Da wanne zakiji? Da laulayi ko kuwa da masifan miji?"

"Maamah tunda nasan ni banyi masa komai ba ya cigaba da koma mey yakeyi tabbas wataran Allah ze wanke ni kuma shi zeji kunya, zan cigaba da kai kuka na wa Allah ai shi ba azzalimin bawa bane."

"Haka wannan yake amma ki kira Mami ki sanar da ita wannan k'aruwan da kika samu."

"I'll amma ba yanzu ba saboda nasan one way or the other magana ze kai kunnen Yaya idan har na sanar da Mami abinda bana so kuma kenan bana son Yaya yasan ina da ciki."

"Amma ai ya kamata ya riga kowa sani tunda shine mahaifin abinda ke cikin naki, Amal you can't do this on your own."

"Ki yarda dani idan nace miki Yaya yana iya denying baby'n nan yace ba nashi bane tunda har ya iya bud'an baki yace mun ina kawo masa maza gida."

"Wallahi Ya Afzal na tattare da babban asara tunda de kome aka gaya mishi hawa yake ya zauna akai ba tare da yayi bincike ba, sannu kinji?"

****
Yini ranan Maamah tayi mata se wajajen biyar da rabi ta tafi. Seda Safiyya ta tabbata Amal tayi bacci ta dannawa Nazeefah kira lokacinda tasan Afzal bai gida ya fita masallaci.

"Hello Aunty?"

"Ya zaki kirani warhaka idan da Ya Afzal na gida fa?"

"Aunty naga kaman lokacin isha yayi ya fita sallah ne."

"Idan da kuma bai fita ba fah? Ba nace se ya fita office zaki na kirana ba?"

"Aunty kiran gaggawa ne."

"Meya faru?"

"Wallahi Aunty ciki take dashi."

"Ci mey!" Nazeefah tasa wani d'ankaren ihu.

"Wallahi ciki take dashi."

"Innalila..inna..innalila" dan rikicewa tama kasa k'arisa salatin yayinda cikinta ya d'au ruwa. Yau ga ranan da ta jima tana gudu. "Amal nada ciki kikace?"

"Eh Aunty."

"Wayyo na shiga uku na lalace ya kika gane? Kinsan ba a wasa da zancen ciki ko?"

"Wallahi ba wasa ba Aunty, tun rananda Uncle ya tafi ta ke zazza6i da amai d'azu wata k'awarta tazo sena ji suna tattauna wallahi ciki ne da ita."

"Yau na mutu na lalace taya Amal zatayi ciki gabani na? Wallahi baze yuwu ba koda sama da k'asa ne zasu had'u se na san yadda zanyi na zubar da cikin nan wallahi bazata haifesa ba."

"Aunty gashin be isa haka ba? Wallahi Aunty ta fara zargi na kokuma ince k'awarta, k'awarta ta fara zargi na d'azu harda amsan wayana ta zuba lamban ki aciki da ace nayi saving da shikenan sun kama mu."

"Wata mak'irar k'awarce take neman rusa mun plan bayan na kusan cimma burina?"

"Wata wai Maamah."

"Safiyya aikin mu ya koma baya be kamata ace Amal nada ciki ba nashiga uku amma Ya Afzal be sani bako?"

"Gaskiya da wuya kinsan basu magana."

"This's the only opportunity I have ya zama mun dole in zubar da cikin nan kafin su shirya dan muddin suka shirya shikenan nawa ya k'are ya zamuyi? Be kamata mu bari Ya Afzal ya gano Amal na d'auke da cikinsa ba."

"Toh ya zamuyi Aunty ni Wallahi tsoro nakeji kar a kama ni, ko a haka muka bar Aunty ta sha wuya, ya isa haka please."

"Wawiya ki saurareni gobe Afzal ze dawo mata inason ki taho mu had'u dake inda muka saba an gama rubutun zan baki seki je ki sa mun cikin wardrobe nasa ta k'ark'ashin kayakinsa kina jina?"

"Eh Aunty."

"In shaa Allahu daga gobe zaman Amal a gidan ya k'are na tabbata idan Ya Afzal ya karance rubutun nan se ciwon zuciyansa ya kusan tashi daga nan seya buga mata saki ta tattara tabar gidan mu samu mu zubar da cikin kowa ya huta."

***
Ba k'aramin rama Amal tayi ba acikin wannan kwana biyu sosai cikin yake bata wuya d'an kumatun da take da shi ma tuni suka zube ta kuma yi duhu. Yau da yamma ana neman shida Afzal ya dawo gida sannu da zuwa Safiyya tayi masa sannan ya wuce d'aki ya rage kayan jikinsa ya bud'e wardrobe nasa ya sanya wasu files aciki ya sake kullewa sannan ya fito parlour.

"Amal na gida ne?" Ya tambayi Safiyya.

"Eh tana d'akinta."

"Batun maganan da kikayi mun ranan shin dagaske ne Amal ta shigo da wani gidan nan?" Har yau zuciyarsa ta kasa aminta masa da hakan.

"Uncle meyasa zan fad'a maka abinda idanu na basu gane mun ba? Ni tasa na kawo masa drink da snacks wallahi ka yarda dani."

"In tambayi mey gadi? Kisani idan har sharri kikayi mata ina iya 6a6alla ki a gidan nan." Sosai cikin Safiyya ya d'au ruwa yadda Afzal yake maganan sam ba wasa tattare da shi.

"Kasan Malam Ahmad da zama a majalisa kuna fita shima yake fita se lokacin dawowanku ya ke shigowa da k'yar idan yana nan Aunty ta shigo in kuma baka yarda dani ba muje a gabanta ka tambayeni a idonta in shaa Allahu amsan dana baka zan sake nanatawa saboda ba k'arya nake yi maka ba."

Sajen fuskansa ya shafe cike da mamaki da kuma rashin sanin abunyi gabad'aya kansa ya d'aure. "Shikenan mey kuka girka?"

"Babu Aunty bata ji dad'i ba kwana biyu so bata girka komi ba nima batace in girka komi ba kuma."

"Bata da lafiya?"

"Eh."

"Meyake damunta?"

"Toh nima ban sani ba gaskiya."

"Ina take?"

"Tana kwance a d'akinta tana bacci nakega."

"Jeki ce mata ta shirya driver ya kaita asibiti."

"Toh" ta amsa ta fice sallama tayi bakin k'ofan Amal sannan ta shiga ta k'arisa ciki had'e da durk'usawa daga gefen gadon.

"Wani abu ne?" Amal ta tambaya.

"Uncle ne ya dawo."

"In yunwa yake ji seki dafa masa abinci kinsan banida lafiya ban iya nayi girki ba."

"Eh na sanar dashi."

"Rashin lafiyan nawa?"

"Eh."

"Meya kaiki? Ni na aike ki?"

"Kiyi hak'uri Aunty yanzu de yace ince miki ki shirya wai driver ya kaiki asibiti."

"Kice mishi nagode bana buk'ata."
Sak abinda Amal ta fad'a mata taje ta fad'awa Afzal a fusace yace, "Ki ce mata ta shirya ba wasa nake ba." Haka ta dawo ta fad'awa Amal inda Amal ta sake turata kice mishi "Nace bazan je ba."

"Uncle wai bazata je ba" a fusace ya k'arisa d'akin had'e da bankad'e k'ofan na sosai Amal ta tsorata.

"Ki tashi a kaiki asibiti nace."

"Nace bazan je ba nagode."

"In ta halin ki za a bi a jinki ko kallon ki zanyi ne a gidan nan? Karki 6ata mun rai Amal ki tashi driver ya kaiki asibiti."

"Nace bazan jeba Yaya ana dole ne?"

"Rashin kunya kuma zakiyi mun? Ki cigaba Amal zamuga inda wannan banzan d'abi'ar zata kaiki" bata sake ce masa komai ba har yaja k'ofan ya fice. Wani irin masifaffen kuka ta rushe da, maghrib nayi ta mik'e tayi niyya bayan sallan Isha ta sanya hijabi ta fito waje takawa take wane wacce k'wai ya fashewa aciki har ta wuce Afzal dake zaune a parlour yana aiki akan laptop nasa, be ce mata komi ba itama bata ce da shi ko k'ala ba. Chan bada dad'ewa ba yana zaune kawai ya fara jin sautin amai daga kitchen besan lokacinda yayi wulli da laptop nasa ba ya nufi kitchen d'in inda ya tarar da Amal tsugune jikin sink tana ta kwararo amai. Na matuk'a ta basa tausayi kad'an ya rage beje ya rungumeta ba amma ya dakatar da kansa. Kallonta ya cigaba dayi har tagama ta d'auraye bakinta zamewa k'asa tayi don yadda bata da k'arfin ko sisi sosai Afzal yake ji ajikinsa duk yadda yaso shareta hakan ya gagara besan a lokacinda ya k'arisa ciki ya shiga d'agata ba.

"Ka sauke'eni bana so I can take care of myself" ta fad'a a galabaice sede be saurareta ba ya d'agata sama chak be sauk'eta a ko ina ba se akan kujera a parlour "Safiyya!"

"Na'am Uncle" ta amsa had'e da fitowa daga d'akinta.

"Wuce ki d'auko mun key'n mota na."

"Ki dawo Safiyya nace maka bazan je asibiti ba" Amal ta fad'a a kasalance "Zo ki tayani in mik'e Safiyya" ta buka'ceta har Safiyya ta shiga takowa gun Amal Afzal ya dakatar da ita "Nace kije ki d'auko mun key'n mota na ko?"

"Uncl-"

"Bakiya ji ne?" Har ta shiga takawa zuwa d'akin nasu Amal ta tsayar da ita "Nace kizo ki tayani in mik'e baki jini bane?"

"Uncle dan Allah ka bari in taimaka mata kayi hak'uri" ta fad'a tana kakkarwa.

"Kije idan kika kashe kanki seki huta kowa ma ya huta" yace da Amal ko kallonsa batayi ba ta jira Safiyya ta taho ta taimaka mata ta kaita d'aki.

"Sannu ko Aunty?"

"Ki had'a mun black tea please."

"Toh Aunty" da haka ta fice nan da nan ta had'o mata tean tazo wucewa d'akinta Afzal ya kirata chak ta tsaya had'e da tsugunawa.

"Na'am Uncle?"

"Meyake damun Amal? Karki yi mun k'arya."

"Uncle wallahi ban sani ba zazza6i tace mun."

"Kin ganta taje asibiti?"

"Gaskiya a'a tunda ka tafi ko makaranta bata sake fita ba" ta mai k'arya gudun kar ya gano gaskiyan al'amarin.

"Ya jikin nata?"

"Tace in had'a mata tea."

"Shikenan kina iya tafiya." Yana kammala abinda yakeyi ya rufe laptop d'in ya koma d'akinsa towel yaja ya shiga bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa yana neman shorts da ze sa k'ark'ashin wani wandon da yakeda niyyan sanyawa da fari Safiyya ta ajiye takardan da Nazeefah ta bata har ze janye wandon seya fasa ya hango wani a sama, zara yayi ya sanya sannan ya kwanta sede ya kasa yin bacci se tunanin Amal kawai yake tuna yadda take amai d'azu kaman wacce ke neman harar da hanjin cikinta. Shin meyake damunta? Ko da wasa k'wak'walwarsa be kawo masa ciki ne da ita ba.

Washegari Amal ta d'an samu sauk'i don haka ta shiga shirin makaranta koda ta fito ta tarar da Afzal zaune kan dining yana karyawa bata yimai magana ba harkan gabanta kawai ta cigaba da yi. Sosai ya sha mamakin yadda ya ganta back on her feet contrary to yadda take jiya kaman wacce zata mutu. Sosai yake son tambayarta ya jiki amma ya kasa har yanzun haushinta yake ji na abubuwan data ringa yi masa tana gama abinda zatayi tayi ma Safiyya sallama yana jiran ko zata tambayesa kud'in makarantar ta yaga kawai ta fice.

K'arfe biyu Afzal ya dawo daga office lokacin Amal ma har ta dawo tana zaune a d'akinta tana karatu, d'akinsa ya wuce bayan Safiyya tayi masa sannu da zuwa. Kayan jikinsa ya rage ya fad'a bayi ya watsa ruwa fitowansa ya nufi wardrobe nasa dan neman kayan da zaisa a garin haka takardan da Safiyya ta sanya a tsakankanin wandunansa ya fad'i hannu yasa ya d'aga tare da bud'ewa in da ya soma karancewa kaman haka;

_To my most beloved soul on earth (Ya Abdul) I write this with a very heavy heart. Darling words cannot describe how much I miss you, I miss you terribly I wish I hadn't sacrificed your love for Ya Afzal cause it's true he doesn't deserve my love, I regret the day I chose him over you, Ya Abdul I wish you were here to cry along with me and take my sorrows away, I wish you were here to fight for me and set me free from this miserable torture. If I were to be given another chance, I would choose you a thousand times over Ya Afzal. Ya Afzal is such a heartless demon now that I've thought of it I just realized it was never love he really felt for me but rather lust. All these while he's been after my body and now that he's gotten what he's wanted he treats me more like a maid than his wife, Ya Abdul you're the one I truly love and not Ya Afzal I'll never love a heartless demon like him, I so hate him and I hate destiny even the more for separating me from you. My love for you will never die Habibi it's still fresh like an open wound and I shall continue to hold onto it, I believe that one day you'll come back to me, I will forever love you Ya Abdul. Life without you is so dull and colourless I need you to brighten up my world and wake me up from this horrible nightmare-_

Afzal be k'arisa karancewa ba ya fad'i a k'asa bisa ga wani irin k'una da ciwon da zuciyansa ya shiga yi masa birgima ya shiga yi wajen yana rik'e dai-dai saitin zuciyansa yayinda idanunsa suka kad'a sukayi ja zir cike da wahala ya d'age carpet ya 6oye takardan aciki. Wayansa ya shiga lalima amman yayi masa nisa haka ya cigaba da birgima a wajen har seda ya sume chan Safiyya da ta gama had'a masa abincinsa tayi sallama bakin k'ofan.

"Uncle na gama" takai minti biyu tana magana bakin k'ofar amma shiru dan haka taje ta samu Amal.

"Lafiya?"

"Aunty uncle ne yace in dafa masa farar spaghetti ya taho da sauce gashi na gama naje kiransa ina ta sallama bakin k'ofar d'akinsa amman shiru."

"Hala wanka yake ki jira idan ya fito."

"Toh" da haka ta fice bayan minti kusan biyar amma bata ji hayaniyan Afzal ba ta koma bakin k'ofan inda ta cigaba da yin sallama amma ba response d'akin Amal ta koma ta sanar da ita shiru fa har yanzu.

"Safiyya kina damuna kije mana ki lek'a d'akin halan bacci yake." Da haka ta koma d'akin ta bud'e k'ofan wani irin rikicaccen ihu ta k'urma bisa ga sumammiyar jikin Afzal da ta tarar a k'asa.

"Auntyy!!!" ta k'urma wa Amal kira ba shiri Amal dake kwance ta zabura tana tambayan ko lafiya har ta iso bakin k'ofan inda Safiyya keyi mata nuni da cikin d'akin a rikice. Lek'a d'akin da Amal tace zatayi itama ta k'urma wani d'ankaren ihu had'e da k'arisasa da salati a guje tayi kan Afzal had'e da aza kansa akan cinyarta tana bubbuga fuskansa "Yaya? Yaya? Yaya please wake up" ba shiri ta shiga yin kuka "Yaya I'm terribly sorry dan Allah kayi hak'uri ka tashi na shiga uku Safiyya kije ki kirawo driver" a guje Safiyya ta fice Amal se kuka take a wajen yayinda take kakkarwa "Yaya dan Allah karka tafi ka barni I'm so sorry please don't go." Mik'ewa tayi ta janyo kayansa ta sanya masa sannan driver ya k'arisa ya cicci6esa sukayi mota duka har da Safiyya. Tunda aka shige da Afzal emergency room Amal keta safa da marwah bakin corridon gabad'aya ta rasa nutsuwarta tsabaragen yadda ta tsule ko Mami ta kasa kira bale su Ummi. Safiyya ce ta kira Nazefah ta sanar da ita, ita kanta Nazeefah bata d'au hakan ze tayar wa Afzal ciwonsa ba sosai ta rikice yanzu idan hakan kuma ya zame sanadiyan mutuwansa? Da ko itace da babban asara. Sarai tasan Afzal bayi so idan ciwonsa ya tashi iyayensa su sani amma da gan-gan dan aga laifin Amal ta kira Ummi ta sanar da ita akan Afzal ya samu attack ba shiri Ummi ta kira Abba ta sanar da shi.

Kaman daga sama kawai Amal taga Nazeefah na shigowa bada dad'ewa ba sega Ummi har ma da Abba. Yau nata ya k'are 'hasbunallahu wa ni'imal wakeel' kawai take ta nanatawa. Kanta suka yo duka suna tambayarta meya faru Amal ta kasa magana se hawaye kawai daga k'arshe suka koma kan Safiyya.

"Wallahi ban sani ba ya shigo gida yace in dafa masa spaghetti bayan da na gama naje nayi mai sallama amman shiru se nida Aunty mukayi zaton ko wanka yakeyi chan da shirun yayi yawa na sake duba shi bud'e k'ofan da zanyi kawai na tarar da sumemmiyar jikinsa a k'asa."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" Ummi ta furta cike da tashin hankali.

"Dole akwai abinda akayi masa" cewan Nazeefah dake ta faman kukan munafirci "Sanin mune nan duka ciwon Ya Afzal bai ta6a tashi kazai haka dole saida sanadi" Nan ta kewayo kan Amal da gaban hijabinta ya jik'e jak'ab da hawaye. "Amal mey kikayi wa Ya Afzal? Sanin kowa ne kece sanadin ciwon sannan mey kikayi masa?"

"Nazeefah wani irin magana kike haka? Har kina tunanin zanyi wa Yaya abinda ze tayar masa da ciwonsa da gan-gan? Wallahi banyi wa Yaya komai ba wallahi ban mishi komai ba Ummi" ta sanar dasu cikin tsan-tsan kuka.

"Taya zakice baki yi masa komai ba Amal bayan kinsan kece sanadin ciwon nasa? Bayan sarai kinsan da zaran kinyi masa abinda zuciyar bata so ciwon na iya tashi yet you still went ahead kika k'untata masa. Idan ban manta ba jiya kafin Ya Afzal yabar gidana seda yace kina yi masa abubuwan da baya jin dad'insu amma baze yi miki magana ba saboda yana gudun 6acin ranki meyasa ke bazaki mishi haka ba ki nisanci duk abinda ze 6ata masa rai?"

"Nazeefah ki yarda da ni Ummi, Abba wallahi ban yi wa Yaya komai ba."

"Ummi wallahi ita ce ita ta janyo komi koda rasa ransa Ya Afzal yayi kisani kece sanadi Amal kuma bazan ta6a yafe miki ba idan wani abun ya samesa" nan ta fad'a jikin Ummi tana kuka.

"Amal me kikayi wa d'ana? Mey kikayi wa Prince? A tunani na kece mace ta k'arshe da zata guji yi masa abinda zuciyarsa bata so meya faru Amal?"

"Hajiya Mariam ya isa haka please mu jira likitan su fito tukuna" da haka Abba ya samu ya toshe wa Nazeefah da Ummi baki koda kowa ya nemi waje ya zauna Amal ta kasa zama se safa da marwah take a wajen chan globe na bakin k'ofan da akeyi wa Afzal aiki aciki ya mutu nan suka duk'ufa suna jiran fitowan Dr. Kusan a tare duk suka jefa masa tambaya.

"Humm!" Dr'n ya sauk'e nauyayyan numfashi "Bazan 6oye muku ba ku sani by each attack da yake samu hakan na weakening rate and efficiency na heartbeat nasa ku magance masa matsala tun ba yau ba kun kasa kun zuba masa ido ranan da zuciyan ta buga gabad'aya shikenan se ku huta muma mu huta."

"Yanzu ya jikin nasa?" Abba ya tambaya.

"Munyi masa abinda zamu iya sauran ku jira ya farfad'o d'ayan ku ya biyoni ya amshi list na drugs da za'a sai mishi." Abba ne yabi bayansa ya rage su Ummi.

"Ummi dan Allah kibar kukan haka" cewan Nazeefah tana share mata hawaye. "Amal kin de ji abinda Dr'n Ya Afzal yace ko? Rayuwan Afzal yayi depending akan ki ne dan Allah ki kiyaye k'untata masa idan baki damu da shi ba mu nan we love and care about him."

"Nazeefah-"

Katse ta tayi da wuri "Ummi wallahi tun ba yau ba Ya Afzal yake mun complaining akanta gashi yanzu seda ta kwantar mana da shi."

"Nazeefah wallahi bani bace dan Allah ki yarda dani."

"Toh wa kikeso a zarga idan ba ke ba Amal? Ummi dan Allah ki sa baki."

"Amal dan Allah ba dan ni ba dan Allah nace kiyi hak'uri ki rufa mun asiri ki na yima Afzal abinda yakeso kin fi kowa sanin halin da yake ciki" Ummi ta rok'eta cikin kuka. "Na sani ba koda yaushe Afzal yake da dad'i ba amma dan Allah kina hak'uri da shi kina yi mishi abinda yakeso please Amal I can't afford to lose him shi kad'ai Allah ya bani."

"Ummi dan Allah kiyi hak'uri I'm so sorry, please forgive me."

"Shikenan bari in shiga in duba sa" ta kai kusan minti goma aciki sannan ta fito har anan Afzal be tashi ba tana fitowa sega Abba nan shima ya dawo da magunan Afzal wanda ya mik'a wa Ummi. Bayanta ya bi ya shiga ya duba Afzal shima bayan ya fito ya buk'aci Nazeefah next da ta shiga, k'arshe Amal ta shiga. A hankali ta k'arisa cikin d'akin ta zauna daga gefensa tare da sa hannunta cikin gashin kansa tana shafawa a hankali.

"Yaya I'm so sorry dan Allah ka tashi ka fad'a musu bani bace" kuka ta shiga yi sosai a wajen a hankaki ta kwantar da kanta a k'irjinsa yayinda kukan nata ya tsananta "Yaya please wake up wallahi ban aikata ko abu d'aya daga cikin ababen da kake tokari na dasu ba wallahi wasu ne suke neman shiga tsakanin mu Yaya bazan ta6a aikata abinda nasan ze 6ata maka rai ko zubar maka da mutunci ba you have to believe me and stop bothering yourself I beg of you please" a hankali ta d'ago da kanta tare da had'a hannunsu gu d'aya "I love you so much and no matter what I'll never leave your side" a hankali ta sauk'e light kiss akai. Har ta kai ga mik'ewa taga ya motsa yatsansa zamanta ta gyara ta shiga kiran sunansa har seda ya bud'e idonsa.

"Yaya you're back!" Tayi exclaiming ba shiri tayi hugging nasa sede ko ta6a jikinta beyi ba gabad'aya ji yayi ta haramta masa tunda har yanzu Abdul ne a zuciyarta. A hankali ta d'ago daga jikinsa "Yaya what happened?" ta tambayesa had'e da zira hannunta cikin gashin kansa. Kan nasa ya shiga girgizawa da nufin baya so a hankali ta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment