Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

har yanzu yak'i tafiya. Wucesa Papi yayi niyyan yi amma Afzal ya dakatar da shi ta hanyan shan gabansa cikin hawaye yace, "Papi dan Allah kayi hak'uri nasan nayi kuskure, nasan ban kyauta maku ba, na sani na ci amanar rik'on amanar da na d'au alk'awarin zanyi amma wallahi sharrin shaid'an ne Papi kafi kowa sanin yadda nake son Amal dan Allah kar ku rabani da ita I beg your pardon."

"Kana son Amal? Meyasa bakayi tunanin hakan ba kafin ka ci mata mutunci ka walak'anta ta haka? Ka sani Afzal Amal tafi k'arfin a walak'anta ta, Amal tafi k'arfin kace zakaci mata mutunci" ransa ne ya mugun 6aci ya shiga d'aga murya se tunawa yayi a asibiti suke "Kaga a asibiti muke bazan so in d'aga murya in shiga hak'k'in wasu ba so tun wuri kafin ka 6ata mun rai ka fice anan."

"Papi dan Allah kayi hak'uri, Papi I'm not asking for too much nasani abunda nayi muku will take much time to heal all I'm asking is ku barni inga Amal, dan Allah kar ku hanani ganinta please Papi."

"Baza ka ganta ba Afzal, ganin Amal ne nace baza kayi ba maza ka kama hanya kabar nan tun kafin insa a koreka."

"Bazan gaji da baka hak'uri ba Papi kuma koda kasheni za'ayi bazan fasa zuwa duban Amal ina baku hak'uri ba har se idan Allah ya huci zuciyanku" Papi be sake cewa da shi komai ba ya fice haka nan har Papi yaje ya siyo abincin wa Amal ya dawo Afzal be tafi ba. Se chan wajajen k'arfu hud'u da rabi ya mik'e yaje yayi alwala yayi sallah ganin ba mahalicci se Allah kuma ko min yaya ba barinsa su Papi zasuyi yaga Amal ba kawai ya d'ibi kansa ya fice. Police station ya wuce inda ya tattaro 'yan sanda sannan yayi gida dasu inda aka d'au Safiyya aka sata a mota se kuka take tana had'a Afzal da Allah amma ina idan shima ze sha wuya toh se ya tabbata ita da uwar d'akinta sun d'ana wuyan da ze sha. Daga gidan Amal suka wuce na Nazeefah inda ya tarar da ita zaune akan carpet na parlour ta had'a taguni tana ganinsa ta mik'e tsaye yayinda jikinta ya hau 6ari. Kallonta yayi sau d'aya ya kawar da kansa dan yadda yayi mata jina-jina da jiki ko ina a jikinta ya kumbura yayi pink dan azaba ga shatin belt kaca-kaca.

Takawa yayi yaje ya sameta cikin rud'ani tace, "Dan Allah Ya Afzal kayi hak'uri na tuba dan Allah kar ka sake ta6ani."

"I'm so sorry Nazeefah, I'm terribly sorry" ya bata hak'uri cike da d'aurewan kai tace, "Ya Afzal ni ya kamata in baka hak'uri please forgive me."

"A rayuwa ba abinda na tsana kaman inga na miji yana dukan mance, musamman ma inga magidanci yana dukan matarsa, tun da nake ban ta6a sha'awan d'aga hannu in mari 'ya mace ba bale har in d'au abun zana in zaneta hasali duk mijin da naga yana dukan matarsa tsanansa nake sega yau kinsa na aikata abunda nafi tsana a rayuwata Nazeefah. It pains me alot ace yau na d'aga hannu na mari matata ban tsaya anan kad'ai ba har seda na zaneta ta tayar maga da jiki haka" yayi maganan had'e da d'aga hannunta yana shafa kan shatin belt d'in a hankali cike da tausayi "Kinsa na tsani kaina yau Nazee I so much hate myself for hurting you like I did amma kuma babban abinda kikayi yau shine na sanya ni tsanarki. I hate you right now Nazeefah, I hate the fact that I'm married to you, looking at you disgusts me right now. Na so ki Nazeefah, na so ki har cikin zuciyata son da bana tsammanin wani d'a na miji ze iya yi maki irinsa, akwai gur6in da ke kad'ai kika mamaye shi acikin zuciyata, gur6in da ko Amal bata isa tace zata mamaye sa ba amma se mey? Se keda kanki kika 6ata rawarki da tsalle kika sa na tsaneki tsanan da bana jin zan iya sassauta shi. Zaman ki a gidan nan ya k'are Nazeefah yadda kika rabani da Amal kema dole ne in rabu dake idan har zanyi ma Amal adalci, yadda kika fiddata daga gidan nan be kamata ace ke kin cigaba da zama ba."

"Ya Afzal dan Allah kar kace haka I beg of you dan Allah kar ka sakeni idan ka rabu dani ban san ina zansa kaina ba bazan iya rayuwa ba kai ba, Ya Afzal I love you, I love you so very much" ta sanar da shi cikin kuka.

"Nima bazan iya rayuwa bake ba Nazeefah, batin duk abinda kikayi mun, batin yadda nakejin na tsaneki yanzu know that I still love you, kin riga kin zame ga6a a jikina Nazeefah amma bazan iya cigaba da zama dake a cikin gidan nan ba looking at you everyday remembering what you did to my innocent Amal, I can't Nazeefah."

"Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri I'm terribly sorry wallahi na tuba dan Allah ka yafe mun."

"No Nazeefah, you're never sorry, you're never sorry na sani tuban muzuru kikayi ba dan wai kinyi nadaman abinda kika aikata ba, hungo" yayi maganan had'e da janyo hijabinta dake kan couch "Amsa kisa" ba gardama ta amsa tasa "Na taho da 'yan sanda sunzo su d'aukeki."

'"Yan sanda?!" Ta nanata yayin da gabanta yayi wani irin mumunan tsinkewa '"Yan sanda fa kace Ya Afzal? Dan Allah ka rufa mun asiri Ya Afzal dan Allah kar kayi mun haka" jikinsa ta fad'a had'e da zagaye hannayenta a bayansa tana kukan tsuma zuciya "Ya Afzal dan Allah kar ka bari su tafi dani bazan iya kwanan cell ba Ya Afzal I beg of you please don't do this idan tuban Amal kakeso in nema na amince zanyi hakan amma dan Allah kar ka bari 'yan sanda su tafi dani" shi kansa seda idanunsa suka cika da hawaye dan yadda ta rik'esa gam take kuka take kuma had'asa da Allah. Na sosai ta basa tausayi shima har cikin ransa beso hakan ba amma hakan ne kad'ai hanyan da ze iya sak'awa wa Amal abubuwan da Nazeefah sukayi mata. Hannu ya sa na k'arfi da yaji ya raba ta daga jikinsa "Securities!" Ya kira su Nazeefah bata tashi rikicewa ba seda taga matan polisawa suna dosan inda take wani irin rikicaccen ihu tasa had'e da fashwwa cikin wani irin kuka mey tsuma zuciya "Ya Afzal dan Allah kar ka bari su tafi dani Ya Afzal I'm deeply sorry please don't let them take me wayyo Allah Mummy na dan Allah kizo ki taimakeni Ya Afzal please don't let them take me wayyo Allah na."

"Take her away" yace da polisawan hawaye na tsiyaya daga idanunsa hannu yasa ya share da wuri. Ihu da bori Nazeefah ta cigaba da yi bata kuma fasa kiran sunansa ba tana da had'a sa da Allah sede he's mind is already made up, ko juyawa ya kalleta beyi ba se hawaye yake ta zubarwa shima kaman ba na miji ba haka yana ji yana gani aka janyeta waje aka sata mota d'aya da Safiyya sukayi police station.
Ga shi nan yau ba Nazeefah ba Amal daga kansa se kansa sauk'a yayi a wajen ya zauna kan kujera sannan ya shiga yin kuka tsakaninsa da Allah, kukan da ya rasa akan wa yake yi, akan Nazeefah ne ko akan Amal ne. Daga k'arshe ya gane kuka akan dukansu biyu yake. Kuka yake akan zafin rabuwa da Amal da kuma abinda yayi wa Nazeefah a matsayinta na matarsa. Be ta6a tsammanin Allah ze k'addaro masa da ranan da zeyi wa matarsa jina-jina kaman yadda yayi ma Nazeefah ba har yanzu zafin hakan yakeji, sannan kuma har ya sake turata kwana a cell tabbas yau rana ne da baze ta6a mancewa da shi ba a rayuwansa.

Yunwa yake ji amma baya jin ze iya sanya komi a bakinsa tuna Amal nasa na kwance a asibiti rai a hannun Allah, ruwan zafi kad'ai ya iya sha ya watsa ruwa sannan ya kwanta. Da ya rufe idonsa se ya tuna da abinda mey shagon d'azu ya fad'a masa akan cewa kan Amal ne ya fashe acikin jini aka d'auketa aka sanyata cikin motan da ya yi agaji. Wayansa ya d'auko ya lalimo lamban Amal sannan ya shiga kiranta.

***
Tana rigingine jikin gadonta Mami na bata abinci wayanta ya shiga ruri a hankali take juya kanta ta kai kan wayan gani tayi Habib Albi🌹💍🔐 na flashing akan screen d'in da hotonsa wanda tayi saving contact d'in da shi. Silencing wayan tayi ta bar shi ya cigaba da ruri, be dad'e ba Afzal ya shiga kira again kafin tayi silencing Mami ta tambayeta "Wa ke kira? Afzal ne?"" Kai zalla ta gyad'a.

"Amma baida kunya shin mey ze kira ya fad'a miki?" Wayan na tsinkewa Afzal ya shiga kira again kashe wayan Amal tayi gabad'aya yanzu. "Kin san kuwa d'azu yana nan? Tun kafin mu shigo yake nan amma nurses suka hanasa shiga saboda restricted area ne nan d'in, haka har seda Papinki yaje d'ibo mana kayakin mu sannan ya tafi."

"Mami dan Allah kibar yi mun maganansa I'm not interested."

"Shikenan Baby yi hak'uri yi sauri ki cinye mu kwanta ki huta." Wajajen goma da rabi ta d'au wayanta ta kunna da sak'on Afzal ta fara cin karo ko bud'ewa batayi ba ta goge baza ta ta6a mancewa da kalan walak'ancin da yayi mata ba, in shaa Allahu ba abinda ze sake had'ata da shi idan ta samu sauk'i zatayi ma Papi magana a amso mata takardanta dan muddin Nazeefah na cikin gidan chan bazata ta6a komawa ba.

*****
GIDAN ALHJ ABDALLAH.

"Khaleefah d'auko mun glasses d'ina a d'aki" fad'in Daddy lokacinda suke zaune duka a kan dining suna shirin karyawa. Mik'ewa yayi ya wuce d'akinsa ya d'auko masa sannan ya dawo yana zama wayan Mummy dake kan dispenser.

"My phone Khaleefah" ta sanar da shi kaman wanda zeyi kuka ya mik'e a rayuwa ba abinda ya tsana kaman aike. "Wa ke kira?" Ta tambaya.

"Number ne" ya amsa yana mik'a mata, swiping tayi ta d'aga "Halo Mummy?"

"Nazeefah?"

"Na'am Mummy."

"Ina kika ajiye wayanki? Tun jiya ina trying numban ki switched off."

"Mummy dan Allah ki taimaka mun."

"Meya faru?"

"Mummy a cell na kwana."

"A cell! Innalillahi wa inna ilaihi raji'un!" chak Daddy dake karanta newspaper ya tsaya haka Khaleefah ma dake shan tea.

"A cell? Meya faru? Ina Afzal?"

"Mummy shi ya kawo ni."

"Innalillahi mey ke faruwa me kikayi?"

"Mummy dan Allah kizo police station na Damboa road muke."

"Toh gamu zuwa" tana sauk'e wayan Daddy yayi saurin tambayarta "Ya meke faruwa?"

"Nazeefah ce wai Afzal ya kaita police station a chan ma ta kwana."

"Police station?" Daddy Yayi exclaiming "Dalili?"

"Nima bata fad'a mun ba kawai cewa tayi muje mu sameta achan Damboa road take." Breakfast da basuyi ba kenan duk suka mik'e suka duk'ufa cikin mota se police station.

Suna isa akayi dasu 6angaren da su Nazeefah suke kuka tasa lokacin da ta gansu haka Mummy ma. "Nazeefah meya faru? Meyasa Afzal ya kawo ki nan? Mey kikayi masa."

"Mummy dan Allah kuyi hak'uri Mummy I'm so sorry."

"Meya faru Nazeefah?" Daddy ya tambaya.

"Ya Nazeefah?" Khaleefah da har yanzu ya kasa amincewa da abinda idanunsa ke gane masa kirata.

"Daddy laifi nayi masa, laifin da ni kaina ina jin kunyan sanar daku please help me out Daddy dan Allah kar ka barni in sake kwana acikin nan." Waya Daddy ya zaro ya kira Afzal bada dad'ewa ba ya d'aga.

"Ka taho inda ka kawo Nazeefah yanzun ina jiranka." Bacci yakeyi lokacin da Daddy ya kirasa yana sauk'e wayan ya koma baccinsa seda ya k'ara baccin kusan minti talatin sannan ya mik'e ya d'aga wayan nasa sak'o ya tura wa Amal ya miyar da wayan ya zarce bayi yayi wanka ya fito ya karya da corn flakes ya koma d'aki ya shirya tsaf sannan ya fito. Isansa police station d'in ya tarar da su Abba da Ummi har su Daddy sun kira su. Saidai ko alamun tashin hankali babu tattare da Afzal dalili kuwa yasan shine da gaskiya. Binsu yayi duka da gaisuwa sannan yasa aka fito da Nazeefah daga cikin cell d'in jikin Mummy ta fad'a tana kuka sosai yayinda Safiyya ta la6e a lungu tana kuka itama. Breakfast da ya siyo musu ya mik'a aka basu nan da nan suka karya a wajen sannan Abba ya tambayeshi meya faru.

"Baki fad'a musu abinda kikayi bane?" Ya tambayi Nazeefah da jikinta keta k'yarma har yanzu. "Magana nake miki Nazeefah confess your crime, crimes if possible" sede ta kasa magana gyaran murya yayi "Tunda bazaki fad'a ba ni zanyi hakan. Mutane tayi hiring tasa aka kad'e Amal yanzu haka Amal na kwance a gadon asibiti rai a hanun Allah duk wai a sunan kishi."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" salati kawai kukeji yake tashi a wajen. "Nazeefah?" Mummy ta kewayo tana kallonta "Da hankalinki? Yaushe kika fara kisan kai?"

"Mummy dan Allah kiyi hak'uri wallahi sharrin shaid'an ne."

"Sharrin shaid'an? Sharrin shaid'an?" Mari me kyau Mummy ta zabga mata cike da 6acin rai, wannan wani irin haihuwa ne? Taya zaka haifi d'a amma d'a ya gagareka? Ashe duk kalan nasihar da takeyi wa Nazeefah a wajen take ajiye mata abinta? take Ummi ta shiga tsakaninsu tana bata hak'uri.

"Tarbiyyan da na baki kenan? Da abinda zaki sak'a mun kenan nida Daddy'ki? Wannan wace irin rayuwa ce?" Tuni ta shiga yin kuka yayinda Ummi ta cigaba da bata hak'uri.

"Afzal kayi hak'uri" cewan Daddy "Dan Allah kayi hak'uri."

"Hak'uri nayi Daddy amma Nazeefah must pay for what she did" har a nan Abba bece komi ba yana bayan d'ansa d'ari-bisa-d'ari saboda akan gaskiyansa yake.
Wayan Nazeefah Afzal ya zaro daga aljihunsa ya kunna "Gashi da hannunki zaki kira mutanen da kika sa suka bige Amal kice musu suzo su sameki dai-dai bakin junction d'innan justice must be served for Amal." Amsa Khaleefah yayi ya mik'a mata nan ta lalumo lamban d'aya daga cikinsu tayi kaman yadda Afzal ya umarceta se kakkarwa take. Har anan mamakin ta Mummy take, sam ba irin tarbiyyan data bata ba kenan, kunya take ace ita ta tsuguna ta haifi gagararriyar 'ya kaman Nazeefah idan a d'an shekarunta zata iya sa a bige mutum gaba mey zatayi kenan?

Yaran suna isowa bakin junction d'in sukayi mata waya nan Afzal ya d'au 'yan sanda uku a motansa suka fice tare da ita Nazeefar a gaban mota suna isa wajen ya umarceta da ta sauk'a tayi musu magana achan aka kamasu aka k'ariso dasu cikin police station d'in. Mummy se kuka take Ummi da Khaleefah suna bata hak'uri.

"Officers ku hukunta mun su hukuncin dake dai-dai da attempt nayin kisan kai" Afzal yace da polisawan yana nuni da yaran da Nazeefah tayi hiring samari guda biyu. "Wad'an nan biyu kuma" yayi nuni da Nazeefah da Safiyya "Ka miyar dasu cikin cell ka kulle mun su I'll speak with my lawyer in shaa Allah justice must he served for Amal nan gaba ko akan mey bazasu sake yin ganganci ta6a lafiyar wani ba bama Amal kad'ai ba."

Yana kaiwa nan ya juya ya fice kiransa Daddy yake amma ko ya juya bale ya sauraresa motansa ya shiga ya basa wuta.

Kaf wajen ba wanda kansa ya mugun d'aure yake kuma cikin tsananin tashin hankali kaman Daddy da yaji Afzal ya ambaci sunan Amal a matsayin wanda Nazeefah tasa aka kad'e. Shin wata Amal ce wannan? Amal da ya tsince ta a bakin makaranta jiya ya kai asibiti ne? Shin Amal Abdallah ce kishiyar Nazeefah Abdallah 'yarsa? yau wani irin k'addara ne wannan? Wani irin fallasa ne yake shirin afkuwa masa? Wani irin badak'ala ne wannan? Ta inda Allah ze kamasa alhak'in Jamee da ya d'auka kenan? Fatansa d'aya ne Allah yasa Amal Abdallah ta asibiti ba 'yarsa bace idan kuwa har hakan ya tabbata 'yarsa ce nasa ya k'are that mean 'ya'yansa biyu suna auran miji d'aya kenan. Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un.





RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨



Miemiebee Novels

Friday, 17 August 2018
RABA D'AYA!
BY MIEMIEBEE
PAGE 37




"Ina securities?" Daddy ya tambaya "Nawa ne kud'in bailing nata?"

"Ranka shi dad'e ai baze yiwu kayi bailing nata ba saboda 'yarka is accused of an imprisonable offense wanda hukuma take tsoron saketa gudun kar ta sake tafka wannan laifi dan haka kotu ya nemi a ajiyeta under close supervision idan har ba wai wanda yayi filing case akantan bane ya buk'aci a saketa that is idan yaja baya da case d'in" d'aya daga cikin securities d'in yayi masa bayani.

"Alhj Amin dan Allah kayi wa Afzal magana yayi hak'uri duk nan mun san Nazeefah bata kyauta ba amma yayi hak'uri yaja baya da filing case d'innan hannun mutum baya ri6ewa ya yasar komin munin halin Nazeefah bazan so ta k'are a gidan yari ba kuma tabbas idan Afzal ya kai k'aranta kotu tunda tana da laifi chan zasu kaita, ni bazanyi fighting against Afzal ba saboda shike kan gaskiya. Amma dan Allah ba dan ni ko ita ba kayi wa Afzal magana yayi hak'uri, kai kad'ai keda ikon hanasa aikata hakan please." Hannu Abba ya dafe a kafad'ansa "Karka damu Alhj Abdallah zanyi masa magana in shaa Allahu za a sake Nazeefah."

"Nagode nagode sosai."

"Toh bari mu wuce Hjy Mariam mu tafi ko?" nan sukayi sallama suka fice. Har anan kuka Mummy keyi.

"Yanzu mey riban wannan abin kunyan da kikayi mana kika kuma yi wa kanki Nazeefah? Ki gaya mun mey riban hakan? Kiga yadda Daddy'nki ke rok'an Abban Afzal kaman mey maula yanzu hakan ya miki kyau?"

"Mummy dan Allah kiyi hak'uri, Daddy I'm sorry" ta amsa cikin sautin kuka.

"Wace wacan?" Mummy ta tambayeta tana nuni da Safiyya.

'"Yar aikin Amal ce."

"Mey tayi ita kuma?"

"Mummy please forgive me."

"Ki bud'e bakinki kiyi magana ana tambayanki!" Daddy ya tsawata mata.

"Daddy dan Allah kayi hak'uri wallahi sharrin shaid'an ne."

"Am asking you for the last time idan har baki amsa tambayan da Mummy'nki tayi miki ba wallahi tallahi kin deji rantsuwa ba kaffara ko? Zame hannu na zanyi acikin wannan al'amari Afzal yayi duk abinda yaga dama da ke tunda ke kince bakida hankali."

"Daddy wannan itace 'yar aikin Amal Safiyya wacce nayi amfani da ita na fidda Amal daga d'akinta."

"Kika fidda Amal daga d'akinta?" Mummy ta tambaya da d'umbun mamaki. "Kina nufin kinsa Afzal ya saki Amal?"

"Be saketa ba yaji tayi."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Nazeefah! Is this how evil you've become? A iya shekarunki kike wannan mak'irci? har kinsan ki raba aure ki shiga tsakanin miji da mata? Wallahi ba tarbiyyan dana baki ba kenan Allah ma shaidana ne" ta k'are maganan tana neman fara sabon kuka. "Duk kalan wa'azi da nasihan da nake yi miki ashe shiga kunneki kawai yake ta dama yana fita ta hagu ashe a wajen kike ajiye mun magana na, wallahi ba abun in ja miki Allah ya isa ba."

"A'a Hjy Surayya kiyi hak'uri duk bey kai ga haka ba" Daddy yace da ita yayin da Khaleefah ya cigaba da bata hak'uri yana shafa bayanta a hankali. Shi kansa mamakin halin 'yar uwarsa yake.

"Mey da mey kika rink'a sanya yarinyar nan yi haka har kika sa Amal tayi yaji iyyeh?" Tisata Mummy tayi a gaba seda ta irga dukkan abubuwan da ta aikata "Wallahi Alhj idan har baka bari an hukunta taba an yanka mata watanni ko shekaru a gidan yari ba uba kage ga 'yar nan ba, ni da kaina zan kira Afzal in k'arfafa masa guiwa in shaa Allah sekin biya abinda kikayi wa baiwar Allahn nan, har kisa mijinta ya zargeta? Zargui fa Nazeefah! Innalillahi wa inna ilaihi raji'un."

"Mummy dan Allah kar kiyi mun haka Daddy na tuba dan Allah karka saurari Mummy."

"Kin bani kunya Nazeefah, na d'au kinyi hankali dagaske har nake alfahari da hakan ashe halin nan naki na nan har yanzu, yaudara na da Mummynki kawai kikayi kika nuna mana kin shiryu, wallahi ban ta6a tsammanin hakan daga gareki amma bazan biye miki ba, Hajiya Surayya kiyi hak'uri hanun mutum baya ri6ewa ya yasar komin mey Nazeefah tayi har yanzu a matsayin 'yarmu take hakan baze ta6a canzuwa ba. Kuma ko kema fad'a kawai kike baza kiso ace an kai 'yarki gidan yari ba hak'uri ya zama dole dama acikin 'ya'yanka dole akwai wanda ze gagareka saidai mu a matsayin mu na iyaye muyi hak'uri mu cigaba da yi musu fatan shiriya."

"Hakane Alhj" ta amsa tana kewayowa kan Safiyya "Ke kuma Safiyya kike ko wa kinga abinda kwad'ayi ya janyo miki ai ko? Shin a ina ma kika samota tun farko?" Ta tambayi Nazeefah.

'"Yar mey aikin Su Rumaysa ce k'awata wallahi tun farko ita ta fara bani shawaran nan."

"Ke kuma dake dabbace Allah beyi miki hankali ba kika biye mata ko? Ai kinga ni da idonki kinga yadda ta kaiki ta baroki."

"Mummy dan Allah kiyi hak'uri wallahi na tuba."

"Tashi mu tafi Khaleefah."

"Mummy please don't go Mummy I'm sorry Daddy dan Allah ka bata hak'uri." Ko sauraronta Mummy batayi ba ta fice "Alhj muna jiranka." Juyowa yayi ya kalli Nazeefah ba shida bakin yi mata horo saboda abun kunyan da ta aikata kad'an ne a ganga da nasa, tausayi ta basa sanin duk abinda takeyi shi ya janyo komai, ko dan alhak'in Jameela daya d'auka yaci ace Allah ya basa gagararriyar 'ya kaman Nazeefah.

"Nazeefah kiyi hak'uri in shaa Allahu zan nemi Afzal inyi masa magana bazaki sake kwana cikin nan ba."

"Daddy kaima tafiya zaka yi? Dan Allah kar ku tafi ku barni."

"Mummy'nki na jira na a waje se anjima idan na dawo" kuka take sosai tana kiran sunansa amma haka ba waiwaya ya fice shima, nan aka sake miyar dasu cell ita da Safiyya, ba abinda take nadama kaman fara bin shawaran Rumaysa da tayi. Gashi yanzu tana chan tana morar rayuwarta a k'ark'ashin AC ita tana nan tana shan wuya. Tabbas duk duniya bakada abokiyar shawarar da ta fi mahaifiyarka, itace kad'ai zata baka shawarar da bazata cutar da kai ba amma idan ka biye wa k'awaye musamman na banza irin su Rumaysa da Suwy da ta so sata aikata shirka toh tabbas kana tattare da k'alubale. Yau ta gane bin shawaran k'awa bala'i ne musamman irin nasu Rumaysa. Tayi nadama, tayi nadama matuk'a.

Mummy ta kasa hak'ura suna isa gida takira maman Rumaysa bayan da suka gaisa take irga mata halin da Rumaysa ta jefa Nazeefah aciki. Atafir maman Rumaysa tace ita sharri ake yi wa 'yarta, 'yarta baza ta ta6a aikata haka ba. Itama Rumaysan munafukar kanta bayan da Mamanta ta kirata tayi mata maganar bushe ido tayi tace ita bata ma san da wannan zance ba iyaka abinda ta sani Nazeefah tace ta nemo mata yaran aiki guda biyu d'aya nata d'aya na kishiyarta.

***

Afzal kam yana fita daga police station d'in ya kama hanyan TH dan duban lafiyar Amal tasa, saidai kaman jiya yau ma nurse dake bakin k'ofan ta hanasa shiga. Ba irin rok'an duniyan da beyi mata ba amma ta hanasa shiga acewarta bashida appointment da kowa. Ana cikin haka sega Mami ta fito be 6ata lokaci ba yaje ya tareta. "Mami ina kwana?" Kaman wacce bazata amsa
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment