Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD



"Nawa kike buk'ata?" Ya tambayeta bayan tsawon lokacin daya d'auka.

"30k ne ankon, sena d'inki 15k san-"

"Nawa ne altogether?" Ya katse ta.

"65k" ta amsa k'asa-k'asa.

"Naji" ya amsa sama-sama. Ganin be kuma yunk'urin cewa wani abu ba ta numfasa, "Afzal yau ne nike buk'atan kud'in."

"Da daren nan kikeso inje ATM? Cash da yake wajena bekai sum da kike buk'ata ba."

"Toh in baka account details d'ina mana seka min transferring" tayi tunani. Kaman wanda baze amsata ba yace, "Write it down for me" ba gardama ta d'ago wayanta dake kan cinyarta "Ko zaka bani number'nka se inyi maka sending?" Nan ma seda ya d'au tsawon lokaci sannan ya irga mata nan take gun ta yi mishi sending, shima ba tare da 6ata lokaci ba yayi mata transferring sum d'in. Baki bud'e cike da mamaki Nazeefah ta bud'e tana kallon cikin wayarta yayinda ta kasa amincewa da abinda idon ta ke gane mata. "Dubu saba'in?" ta furta a hankali.

Kai ta d'ago tana kallonsa yayinda ya mayar da hankalinsa kan Tv'n "Nagode" ta sanar dashi nan ma kaman wanda baze amsata ba yace da ita, "You're welcome" sama-sama. Mik'ewa tayi ta shiga d'akinta tare da fad'awa kan gado cike da jin dad'i. Aminiyarta ta kira dan breaking mata wagga news. "Babe you won't believe this!"

"Ya meya faru?"

"Dubu saba'in mutuminki yamin transferring."

"Like forreal!"

"I'm telling you wallahi ban d'au ze saurareni ba ma."

"Hehe kode so yake kuyi sulhu ne?"

"Lallai kuwa ze 6ata lokacinsa dan kuwa ni ba sa'ar yinsa bane."

"Omo I dey feel my babe anyways congratulations sekiyi maza ki turawa Nana kud'in."

"Ai right away, gobe zaki shigo school?"

"Eh kefa?"

"Also semun had'u."

"Alright ba-bye" da haka sukayi sallama inda tayi wa Nana transferring kud'in.




RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[12/08, 22:45] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣1⃣*


Haka nan de rayuwa ta cigaba da kasance ma wannan ma'aurata ba tare da cigaban komai ba. Nazeefah bata tashi kalmasa kalamunta ga Afzal se idan buk'atan ta ya tashi wanda shi kuma yake biyan mata badon komi ba se don yana ganin nauyinta ya koma kansa yanzu kuma tunda yana da hali. Bayan nan ba abinda yake sake had'asu, girki ma idan ta tashi yi ba dashi takeyi ba kaman yadda ko ta kan kulolinta bayyayi shima. Ana nan watan bikin Nana ya tashi, wanda akayi events duka a nan garin Maiduguri banda dinner wanda dangin ango sukayi organizing a Abuja. A daren tafiyan (bayan d'aurin aure) Nazeefah ta shirya akwatinta tsaf amman ko sanar da Afzal zatayi tafiya batayi ba shide kawai ganinta yayi washegari tana jan akwati amman ko k'ala be ce da ita ba.

Kamar yadda ango da abokansa zasu bi jirgi haka itama amarya da k'awayenta suka bi, cikin d'an k'ank'anin lokaci suka isa Abuja, da yammacin ranan suka shiga shirin dinner sede tun abun be damun Nazeefah har ya soma yi a hankali. Kusan kowacce daga cikin k'awayenta seda samarinsu suka kirasu suka yi masu sun sauk'a lafiya amman banda ita da take da miji, ko text message bata gani ba balle kira har d'aya daga cikin k'awartan ke tambayarta ko lafiya taji Afzal shiru itako tayi mata k'arya cewa shima Afzal d'in yayi tafiya bai ma k'asar kwata-kwata.

Haka nan suka je dinner suka dawo still Afzal be kirata ba yo taya za ayi ya kirata daman bayan bata sanar dashi inda zata ba. Ta fannin Afzal kuwa koda da yamma yayi har dare ya shiga amman Nazeefah bata dawo ba, be damu ya kirata ba kamar yadda be damu ya kira gidansu ba don jin ko lafiya. K'ofansa yayi locking yayi kwanciyansa.

**Washegari da kowa ke juyowa gida ita Nazeefah tak'i akan ita se washegari, haka seda ta k'ara kwana sannan ta juyo. Lafiya k'alau Allah ya dawo da ita gida, koda ta iso ciki a kulle ta tarar da k'ofa, da ta gwada tambayan me gadi key kuwa yake cemata Afzal be ajiye masa ba da ze fita haka nan ta zauna bakin k'ofa tana jiran zuwansa. Ba da dad'ewa ba ya iso inda ya tarar da ita zaune kan kujera a varenda, k'arisawa yayi ya bud'e k'ofar ya shiga ba tare da yace da ita komai ba, itama ko k'ala bata ce masa ba iyaka bin bayansa da tayi ta nufi d'akinta.

Gaba dai gaba dai, har Allah ya kawo su Nazeefah k'arshen semester Alhamdulillah ta samu tayi clearing duka courses nata. Tunda akayi hutu mutumiyar ku ta samu saran fita yawo tun safe se yamma take dawowa gida ba wai kuma tana tambayan izini bane fitanta kawai take tamkar zaman kanta take a gidan, ta d'ayan 6angaren kuwa Afzal ya riga ya rantse kan cewa duk uban rashin hankalin da zata tafka a gidan ba zeyi mata magana ba tunda Allah yayi tana da hankali bawai bata da shi ba, sarai tasan what's right and wrong.

Ana cikin tafiyan ne k'awar Nazeefah wato Nana wacce akayi auranta bada dad'ewa ba tayi mata waya take sanar da ita k'aruwan da suka samu ita da mijinta. Lis jikin Nazeefah ya mutu tuna yaushe ne akayi bikin nasu har gashi sun samu k'aruwa, ita da auranta ke neman wata shida ko bakwai amman shiru. Zama ita kad'ai tayi bayan wayan tana nazari, gashi de ta fad'i hali d'aya na Afzal da ke k'untata mata ta kasa har rana me kaman na yau bata ta6a jinsa yana waya da budurwa ba, kud'i idan ta tambaya yana bata, girki se ta ga dama takeyi kuma ko uffan bai ce mata, ta rasa dalilin daya sa basu jituwa. Samarukan nata ma da take ganin suna sonta tana da tabbas a kansu suma gashi yanzu da zama yayi zama suma sun soma watsewa suna ja da baya, shin me takeyi wa kanta? Tunani ta fara kode ta sauya halayenta ne ta bawa Afzal dama? Wala Allah zasu daidaita tsakaninsu suma su soma zaman lafiya kaman yadda kowani ma'aurata keyi saidai inaa jiji da kanta baze barta ba. Se ce mata wani ra'ayin yake ai ma idan neman sulhu ne na miji ne ya kamata ya fara ba mace ba don haka zata zuba wa Afzal ido taga iya gudun ruwansa bi izinillahi shi ze soma nemanta. Haka nan ta cigaba da tafka rashin hankalinta amman mey bata ga cigaban komi ba, sam ba canji ta fannin Afzal, tamkar bata gidan haka yake rayuwansa ko kallonta bayayi harkan gabansa kawai yake. Da kad'an-kad'an abun ya soma damun mutumiyarku har ya zammana ita kad'an ta seta had'a tagumi a d'aki tana tunani, ita bawai son sa take ba, ta rantse baza ta ta6a sonsa ba kawai de ita zama haka ba kulawa daga gun miji ne ya soma isanta, duk buro-uban da zata tada a gidan akan lallai-lallai se Afzal ya saketa shi ko be ta6a biye mata ba, hasali ma idan ta fara haukan nata d'akinsa yake shiga ya rufe k'ofa bai fitowa kuwa se ya tabbata tayi shiru kokuwa ya fita ya bar mata gidan ma gabad'aya.

Ganin ba mahalicci se Allah kawai ta d'au wayarta ta buga wa Aminiyarta Rumaysa kira don tuntu6arta shawara inda zancen nasu ya k'aye haka;
"Hmm Babe kenan ai ni da jimawa nasan Afzal nakin nan na son ku daidaita tsakaninku kece de baki gane ba" cewar Rumaysa.

"Kaman ya kenan K'awa?" Nazeefah ta tambaya take.

"Kiga mana bayi fa miki magana bale fad'a ko kin neme sa da magana ma baya biye miki gashi kud'i ko nawa kika tambaya ze baki, ai duk neman ki sauk'o ku shirya ne" tayi mata bayani.

"Toh meke hana sa sakewa dani? Kiji fa d'azu Nana ta kirani wai she's pregnant."

"Kai don Allah!" Tayi exclaiming "Allah inganta."

"Ameen fah wallahi jikina ya mutu haka ranan ma Mummy ta kirani tana min wani irin magana, bata de fito fili tace gashi ba amman na fahimci inda ta dosa."

"Ke yanzu kina son Afzal d'inne?"

"Allah wadai inso Afzal wallahi yayi kad'an."

"Toh na me kike tada hankalinki akanshi?"

"Rayuwa hakan ne ni ya isheni tunda baze iya bani kulawar da ya kamata ba a matsayin matarsa ya sakeni in je in auri wanda zamuyi zaman aure mana."

"Kema kinsan Afzal kam baze sake ki ba."

"Toh ya kikeson inyi?"

"Ki sauya d'abi'un ki na banzan nan kawai, ku daidaita tsakaninku shikenan, shi Afzal bashi da matsala."

"Babe wai nufi kike in soma yi masa ladabi da biyayya?"

"Sosai ma kuwa" ta amsa ta take.

"Shamawai! Wallahi bazata saku ba wai bindiga a ruwa think of a better solution kawai."

"That's the only option you have left Nazeefah ki duba kiga da auran ki beyi wata shida ko bakwai ba? Me kika tsinana wa kanki banda kondon-kondon zunubi?"

"Yanzu K'awa nice kike gayawa magana haka? Ba laifinki bane ni na kiraki har nike tambayar ki shawara ai se anjima."

"Nazeef-" bata bata daman k'arisa abinda tayi niyya ba ta katse wayar abinta tare da wulla sa kan gado yayinda ta shiga tunani. Tafi sati tana nazari akan abinda Rumaysa ta fad'a mata daga k'arshe de taga fa idan ba wai ta sauya halayan nan nata bane al'amura bazasu ta6a dai-daita tsakaninta da Afzal ba don haka tayi fad'a wa kanta ta d'an rage yawon banzan da take, da safe zata tashi tayi wanka tsaf tasha kwalya ta fito parlour ta zauna tana kallo sede ko Afzal ya fito bata iya gaishesa, dukda cewan tana son ta gaishesan amman ina tak'ama da jiji da kai irin nata baze barta ba. Shi de Afzal ko da yaga canji kwana biyu beyi magana ba, da farko kan ma yayi tunani ko motarta ce ta 6aci amman jin bata yi masa magana a kai ba se shima ya basar kawai ya zuba mata ido don ganin iya gudun ruwarta. Abinsa ze fita office daga chan idan ya tashi ya wuce gidansu Amal atimes kuma in batada abinyi a gida tazo ta tayasa da abokinsa Sultan hira a office nasa. Shak'uwa na hak'ik'a ne ya shiga tsakaninsu wanda a rana idan basu ga juna ba ko kuwa basu ji muryan juna ba se suji kaman zasu shiga cikin matsala.

A haka ne har new session ya gabato wato watan d'iban sabon admission wanda Afzal ya tsaya akai sosai don ganin Amal ta samu wannan course da take da buri akai, admission na fitowa bim sunan Amal na cikin first batch wayyo dad'i tunda Afzal ya fad'a mata ta samu admission take ta tsalle-tsalle a gidan ta hana kowa sakat. Chan anjima ta d'au wayan Mami ta kira shi ita yaushe ne zasu fara lectures ita bata ma tunanin registration da sauransu damuwarta kawai lectures ne. Ana fara registration Afzal ya sata a gaba haka ze karb'i excuse a office sujesu Unimaid su bi wa Amal layi inda sanin ido yayi magana ayi mata nata da wuri su gama su koma gida har Allah ya kawo su k'arshen registration d'in, kuma da ikon Allah basu ta6a had'uwa da Nazeefah ba se aranar k'arshe ne layin final clearance wata classmate na Nazeefah back then a secondary school wanda bata samu admission ba se this year ta ga Afzal da Amal. Binsu ta rink'ayi har seda taga sun shige mota sannan ta kira Nazeefah ta labarta mata komai wato Nazeefah bata ta6a sanin tana kishin Afzal ba se a wannan lokaci wani irin wawan kishi ne ya tokareta wanda alokacin takeji inda zata ga wannan yarinya seta soketa har lahira. A farko kan ma taso k'aryata batun k'awar nata har take cemata ai office Afzal d'in ya fita yau don tun 7am ya fita kaman yadda ya saba not knowing daga office d'in ya zarce gidansu Amal ne. Hankalinta de ya kasa kwanciya yayinda ta shiga sintiri a parlourn tana jiran isowan Afzal tayi confronting na shi. Ba shi ya tashi dawowa gida ba se chan yamma. Bata ce masa komi ba dukda cewan a tak'ure take ta mai magana sede wani abun nata rik'eta shin ma me zata ce masa bayan rabonsu da suyi magana wa juna kusan sati kenan yau tun ran da ta tambayesa kud'in wasu handouts da textbooks. Kuma ma ai idan ta mai maganan yanzu ze ga kaman ta fara sonsa ne har take kishi akansa kode ta share maganar ne? Kash sede tana ganin idan har batayi confronting nashi ba tana iya mutuwa don haka bayan sallan Isha ta tabbata ya dawo gida ta fito tayi kansa a lokacin yana zaune a parlour yana ta faman aiki akan laptop nasa. Kujeran dake kusa da nasa taje ta zauna akai, shi a tunaninsa ma gabad'aya kud'i take buk'ata dan kuwa bata tashi zama cikin kamala haka se idan damuwanta ya tashi, duk maganan da zata yi masa tana tsaye a kansa takeyi. Bata kaiga mar magana ba ya katseta "Nawa kike buk'ata?" Ya tambayeta ba tare da ya kalleta ba.

Har ga Allah ranta ya 6aci wato irin gata karuwan nan ba ta inda tafi kauri seta fannin kud'i but even still she has no one to blame but herself itace se idan tana neman abu take mar magana ko gaisuwa bai had'asu. Danne zuciyarta tayi tace, "Ni ba kud'i nake buk'ata ba." D'ago kai yayi yana kallonta da nufin idan ba shi ba toh me? Numfasa tayi sannan da k'yar ta furta kalaman "Ina kaje yau da ka fita?" Shi dariya ma ta basa, murmusawa ya shiga yi sosai ta gefe wanda hakan ya bawa one sided dimple nasa daman lotsewa ciki wanda hakan ya mugun fito da kyansa. Shi don dariyan data basa ma ko iya tanka ta ya kasa, don haka kawai ya miyar da kansa kan laptop nasa yana me cigaba da aikin gabansa. Nazeefah da ta ciko dam ji take kaman ta waske latptop d'in ta buga a k'asa wato ma mahaukaciya ya miyar da ita tana mishi magana sede ya kalleta yayi murmushi ya cigaba da harkan gabansa da kyau.

"Afzal magana nake maka" ta fad'a cikin tattausar murya.

"Sorry regarding?" Ya tambayeta had'e da kafa mata lumsassun idanunsa.

"Where did you branch to after work today?"

"I think that's none of your business" ya mayar mata tare da kawar da kansa.

"Ban gane it's none of my business ba, matarka ce ni and I demand to know your whereabouts."

"Really?" Ya tambayeta yana me sauk'ar da laptop nasan zuwa kan center table had'e da kewayo da kallonsa gabad'aya a kanta. "Duk yawon da kikeyi a gidan nan did I ever questioned you ina kike zuwa? Tafiya kikayi gabad'aya kin sanar dani ne? And is like you seem to be forgetting wa ke zaman wani a gidan nan, remember that, kece kike k'ark'ashina and not the other way round."

"Ai da sauk'i tunda ni yawo nakeyi ba'a ta6a buga maka waya ance an ganni ina yawo da wani k'ato akan layi ba kamar yadda kake yi da karuwanka-"

"Kul!" Yayi saurin katseta "Ko da wasa kar ki sake kwatanta baiwar Allahn chan da karuwa."

"Idan na sake fa?" Ta tare shi. "Ai ba k'arya nayi ba idan ba karuwa ba tasan kanada aure amman take janka kuna yawo a titi kowa na kallonku, wannan abun kunya dame yayi kama sede a kirani ace min ga miji na akan layi da wata?"

"Tun yaushe kika fara regarding d'ina as mijinki? That aside koma wanene ya kawo miki wannan rahoto tell that person ba komai tsakani na da yarinyar nan da suka ganmu tare, ta samu admission ne na kuma taimaka mata ta kammala registration nata that's all."

"That's all? Amman kana da mata a gida baka iya ka mata hakan ba? Kana ganin kayi adalci kenan?"

"Lmao, har kina da bakin furta kalman adalci?? See I've had a very busy day and as you can see I'm still working idan ke baki da abinda yafi k'wak'wulo suratai please allow me work I'm not ready for this."

"Toh wallahi ka cigaba muddin ni zan mutuntaka in dena biyewa samarukan da nikeso suke kuma sona don kare maka mutunci I see no reason why da bazaka min haka ba kaima ka dena biyewa karuwanka, ko ka dena ko in d'au mataki da kaina trust me you won't like the details nide na fad'a maka" tana kaiwa nan ta mik'e ta fice. Shi de Afzal bin ta kawai yayi da kallo sannan ya cigaba da harkan gabansa.

Washegari...
Gidan wata k'awar Ummi dake sayar da zannuwa, laces da ready made hijabs Afzal ya wuce inda ya d'iba wa Amal kaloli da dama, koda k'awar Ummi ke neman tsokanansa take tambayarsa duka wannan wa amaryar mu ne shiru yamata yana murmushi. Daga chan ya wuce 3G ya sai mata shoes and bags na dad'in fita lectures sannan ya biya gidansu. Kasancewar anyi musu kwalta yanzu har gaban gidansu mota na iya kaiwa, yayi parking dab gaban k'ofar nasun inda ya saba kullum sannan ya mata waya yace ta fito. Ba tare da 6ata lokaci ba ta fito sanye da hijabinta kamar kullum se fara'a takeyi ta k'arasa ta shige suka gaisa bayan nan take tambayarsa dalilin daya hanasa k'arisawa ciki yau.

"Haka kawai nace yau bazan shiga ba."

"Kai Yaya kode wani laifin akayi maka ne inyi gaggawan bada hak'uri."

"Ai Lily bata laifi."

"Toh ya kake ya office?"

"Alhamdulillah yau ba islamiyya ne?"

"Akwai fa amman bazan samu daman zuwa ba Mami tace zan rakata suna."

"Ohh! Ina fatan kin soma shirin school, kinsan in a week time zaku fara lectures."

"Haka nagani a jikin time table d'in, Allah kai mu."

"Ameen mu fita in sauk'e miki kayakin naki ina da meeting by 3" yayi maganan yana duban babban agogon dake d'aure a hannunsa.

"Wasu kayaki kuma Yaya?" Shiru yayi bece komi ba har seda ya bud'e booth d'in motan ya sauk'e kayakin tukuna. "Kinga jami'a zaki shiga yanzu dole kiyi sabin kayaki in bahaka ba wataran seki nemi na sawa ki fita lectures ma ki rasa."

"Yaya kana nufin duka ledojin nan kayaki ne aciki?" Tayi maganan cike da k'in yarda yayin da take k'ok'arin lek'a cikin "Haba Yaya ina zan kai wannan kayaki haka? Gaskiya kayi hak'uri amman bazan iya amsa ba."

"Kinde san bana wasa dake ko? Kai zo!" Ya kira wani almajirin dake wucewa, "Zo ka k'arisa da kayakin nan ciki" yana gama kaiwa ciki Afzal ya sallameshi. Ba yadda Amal batayi da Afzal ba yashiga ciki su Papi su mai godiya amman yak'i ya jirata ta shiga ciki ta musu magana ma yak'i haka nan ya tafi sannan ta shigo ciki tana kallon kayakin, ninke acikin d'aya daga cikin atamfofin ta tsinci kud'in d'inki. Ita kam sau dayawa takan zauna tayi tunanin mene tayi wa Allah daya shigo da Afzal cikin rayuwarta, damuwarta tun kan ta furta ze yaye mata shi, d'azun take tunanin yadda zata na fita lectures har ta fifftito da kayakinta tana ware sababbin wanda basu sha ruwa sosai ba. Koda ta kira sa anjima, chan bayan sallan Isha dan su Mami suyi masa godiya kashe wayan yayi wai shi baya so. Washegari ita da Mami suka kai mata d'inki.

A satin daya zagayo ta amshi d'inkunan nata da tailor tasamu ta gama don fara fita lectures dasu, tomorrow being her first day at school, tun Asuba da Mami ta tada ta sallah bata sake komawa bacci ba ta fad'a bayi tayi wanka, tana cikin shafa mai sega wayan Mami na ruri kasancewar wayan a gunta ya kwana jiya. Ba tare da 6ata lokaci ba ta d'aga suka gaisa yake sanar da ita by 6:30am zezo ya d'auketa he'll be the one to drop her off today, duk yadda taso hanasa yak'i ya amince ita a ganinta d'awainiyan ze yi masa yawa. Shirin ta kammala nan da nan ta karya tashiga jiransa, ana cikin haka ne Papi ya fito ya tarar da ita, kud'in mota dana abinci ya bata inda take sanar dashi halin da ake ciki na cewa Afzal yace ze zo ya kaita. Fad'a sosai Papi yayi mata kan meyasa zata amince masa da hakan maza ta kirasa tace masa zata tafi da kanta.

Yana cikin karyawa wayan nasa na dake gefensa akan table ya shiga ruri dai-dai lokacin Nazeefah ke k'arisowa dining d'in zata d'au condensed milk daga cikin fridge da alama itama makarantar zata wuce kaman an aiketa ta lek'a screen na wayansa inda taga 'Lily' na flashing akai. Tunani ta soma don a iya saninta Afzal bai da k'anwa kowacece wannan d'in? Fridge d'in ta bud'e ta shiga neme-neme don ta samu daman sauraron wayan nasa. Goge bakinsa yayi da wata mini towel sannan yayi picking call d'in freely, "Halo Lily?"

"Na'am Yaya nace ka bari kawai zan tafi da kai na."

"Meyasa?" Ya tambayeta take.

"Kamar yadda na fad'a maka haka ma Papi yace babu amfani kawai zaka sa kanka wahala ne."

"Ai ni nace zan kaiki ki jirani ina zuwa." Baki wangalau Nazeefah ta bud'e tana kallonsa daga baya kode wannan d'in itace wacce k'awarta Aisha ke fad'a mata ranan? Amman lallai Afzal ya cika wato ita be ta6a cewa ko hanya ze rage mata ba amman idan karuwarsa ce har nema-nema yake tana hanasa da kyau. Duk yadda taso sauraron abinda Amal ke fad'a ta wayan ta kasa. Daga k'arshe de taji Afzal ya kammala wayan da yana fitowa yanzu. Yana juyawa ya bud'e wallet ya ajiye wa Nazeefah kud'in makarantarta bekai da taka k'afa ba ta kira sunansa wanda hakan ya sanya sa tsayawa chak. "Yes?" Ya juya yana kallonta.

"Nace mota na ya lalace jiya shi kad'ansa yake hayak'i kuma gashi ina da lectures 7:30 you'll have to be the one to drop me off to school" ta shirya k'aryar nan take. Iska ya fisga yana me sosa kansa cike da rashin sanin abun yi "Why didn't you inform me tun jiya mey gyara yazo ya duba miki?"

"Na mance se yanzu na tuna."

"Inada muhimmin gun zuwa yanzu let me talk to Ummi's driver yazo ya kaiki" be bata daman magana ba ya fice. Tun kan ya fita ya kira driver'n Ummi ya sanar dashi buk'atan shi. Haushi ne ya cika Nazeefah dam daba don ta makara ba data bi sahunsa taga gidan wannan 'yar dake raba masa hankali.

Isan Afzal gidansu Amal keda wuya yayi parking ya shiga ciki, tana ganinsa ta mik'e tare da yi masa sannu da zuwa sannan ta shiga ta ma Papi magana. Bayan gaisuwa Papi ke masa fad'a kan mey nan da makaranta da baze bar Amal taje da kanta
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment