Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

a gidan yari)."

   "Shekara de?" Abdul ya nanata cike da k'in yarda lallai kuwa ya yayyafa wa kansa ruwan sanyi. Ai kafin yasan Baby ma ya rayu se akayi yaya don tace bata son sa? Yaga de soyayya bata kisa. Yanzu bama wannan ba waze na taya mahaifiyarsa yin markad'ai da kula da kuma saiwa k'annensa 'yan biyu magani idan aka turasa gidan yari? Amman wannan mutumi baze gama da duniya lafiya ba yanzu akan d'an k'ank'anin abinda ya aikata wanda be d'aukesa a bakin komi ne ba har yake neman jefa masa rayuwa cikin had'ari haka? Hmm!

  "Ka shirya gobe polisawa zasu zo nemanka don kaika kotu muddin kayi tunanin guduwa kuma that will be a double offense and kasani cewa duk inda ka shiga a fad'in garin nan me sauk'i ne a kama ka, a word is enough for the wise" Afzal na kaiwa nan ya juya ya shiga tafiya. Daga bisani Abdul da yayi shiru tun d'azu ya rasa na cewa bLe nayi ya k'wala wa Afzal kira had'e da bin bayansa.

  "Bawan Allan ka tsaya, don Allah ka tsaya kayi hak'uri" ko ta kansa Afzal beyi ba se faman tafiyansa yake.

  "Dan Allah ka tsaya" Abdul ya fad'a a lokacin da ya iya yasha gaban Afzal causing him to stop. "Dan Allah karka kaini kotu kayi hak'uri, k'annena biyu suna iya rasa rayukansu idan kayi hakan please."

  "Ashe de bakada kunya? Kasan da hakan amma kai baka tsaya kayi tunanin cewa da abinda kayi wa Amal ka sa ta rasa martabarta da darajarta a idon iyayenta ba?"

  "Na tuba officer don Allah ka rufa min asiri."

   "Bana magana biyu bana kuma ja da baya, tun wuri ka nemo lawyer'n da ze iya tsaya maka a kotu dukda cewa nasan mey wuya ne yin hakan saboda evidences da nake dasu a kanka are strong."

  "Wallahi ko kud'in d'aukan lawyer ma banida kuma koda ina dashi ma ni bazanyi fad'a da kai a kotu ba amman kayi hak'uri don Allah."

  "Matsa min a gaba in wuce."

  "Naji na amince zan bawa Baby hak'uri in kuma fad'awa mahaifiyarta asalin gaskiyan al'amarin amman don Allah ka ja baya da kai k'arana kotun nan."

  "Come again kace zaka yi mey?" Sake nanata abinda ya fad'a yayi a rud'e "Wallahi idan kana so yanzun nan ma ina iya zuwa in bata hak'urin ni de kawai ka ja da baya da zancen nan."

  "Ni kakeson raina wa hankali? In ba wai ka kurmance bane I said to get out of my face ka kuma shirya gobe za'a zo a d'auke ka."

  "Officer dan Allah kayi min rai ka tausaya min." Bayan d'an tsawon lokacin da Afzal ya d'auka daga bisani yace, "Shige cikin motar nan."

  "Dan Allah kayi hak'uri."

  "Ba wani gun zan kaika ba a idanu na nakeson ka bawa Amal hak'uri saboda in zame sheda."

  "Ba kotun zaka kaini ba ko?"

"Kaga alamun wasa a tattare da ni ne?" Da sauri Abdul daya gama rud'ewa ya kad'a kai tare da zagayawa ta passenger's side ya bud'e murfin motar ya shiga. Dai-dai inda Afzal ya saba parking yayi ma yau suka fito da Abdul dake biye dashi a baya suka k'arisa cikin gidansu Amal. Da mamaki Mami ta kar6esu ta shimfid'a musu tabarma sannan Afzal ya buk'aci ganin Amal.

   "Tana Sallah" Mami ta amsa sa a takaice "Lafiya dai ko?" Ta tambaya duk ta kid'ime.

  "Lafiya k'alau Mami ki kwantar da hankalinki" zaman jiran Amal suka shiga yi, bayan ta kammala azkhar nata ta fito sanye da d'aya daga cikin hijaban da Afzal ya d'inka mata chan daga gefen Mami ta zauna ta gaishesa bayan ya amsa ya ta6a Abdul da yayi tsit tun shigowansu ko gaishe da Mami ya kasa da nufin yayi magana.

  "Bazaka yi maganan bane?" Afzal yace dashi cikin tattausar murya.

  "Zanyi zanyi, Baby kiyi hak'uri" ya furta yana kallon k'asa.

  "Ka d'ago kanka tana kallonka kana kallonta ka bata hak'uri don't make me change my mind." Kan nasa ya d'ago ya kuma bata hak'urin kamar yadda Afzal ya buk'ata, ita de Mami sosai ta tsinci kanta cikin duhu ko hak'urin mey?

  "Saura Mami."

  Gyaran murya Abdul yayi sannan ya nesanta yace, "Mami kema kiyi hak'uri ki yafe min wallahi sharri nayi wa Amal bata ta6a aikata koda rabin abinda na fad'a miki tanayi ba duk sanda kika turo ta markad'e, k'azafi nayi mata saboda tun ba yau ba nike cewa ina sonta amman tak'i bani had'in kai senayi tunanin hakan kadai ce mafitar da zeysa ta soni idan nasata na dole amman don Allah kiyi hak'uri."

  "Abdul? Da hankalinka kuwa? Kasan me kake fad'i?" Mami dake jin al'amarin kamar wata raha ta jero wa Abdul wannan tambayoyi cike da rashin yarda.

  "Tabbas na sani Mami amman kiyi hak'uri."

  "Kai d'ago kai ka kalleni ka kuma sake nanata min abinda ka fad'a" ta buk'ata.  Ba gardama ya kuma yi, mamaki ne sosai ya rufe Mami akan kunyan da ta jiyo. Shin yanzu da wani idon zata sake kallon Amal? Amman kam Abdul be kyauta mata ba, take gun ta soma nadamar duk abunuwan da tayi ma Amal barin ma zaneta da tayi gaban Afzal da kuma kiranta 'yar iska da tayi shi yafi komi ci mata rai. Ita ta tarbiyyarta da Amal be kamata tayi kokonto akan hakan ba koda mey aka fad'a mata akanta face ta tara hujjoji da dama, amman kuma ai itama ba laifinta bane duk mahaifiyar data ga 'yarta na rungumar wani dole ranta ya 6aci but even still kamata yayi tayi bincike tabi diddigin komi ba wai tayi jumping into conclussion ba.

   _Gareku iyaye bawai duk abinda aka zo aka fad'a akan 'ya'yanku zaku d'auka ku zauna akai ba saboda muna zamani ne yanzu wanda munafukai sukayi yawa wanda burinsu bai fi su 6ata wa yara suna a idanun iyayensu ba, mutum ya tabbata  yayi bincike sosai tukunnah saboda kamar yadda yara keda hak'k'i akan iyayensu to suma fa yaran nan haka suke da hak'ki akan iyayensu kuma duk wani iyayen da ya d'au hak'k'in d'ansa toh fa Allah ze tsayar dashi akan hakan, Allah is the best of all Allah kare mana zuri'ah, ameen._

   "Amman Abdul tsakani na da kai sede Allah ya isa wallahi."

  "A'a Mami dan Allah kar kice haka" fad'in Afzal.

  "Toh mey zance Afzal? Ka dubi yadda na rik'a d'aukan alhak'in Baby mana Baby?" Ta kirata tare da kewayo da kallonta akan Amal datayi lamo jikin garu tana was da k'asan hijbinta. "Baby ki yafeni nasan nayi miki laifi Baby kiyi hak'uri."

   "Mami ya wuce Allah yafemu gabaki d'aya."

  "Baby nima ki yafeni don Allah" fad'in Abdul.

  "Da Allah chan malam rufa man baki kuma maza ka tashi ka bar min gida kuma in shaa Allahu sena sanar da mahaifiyarka abinda kayi mana da 'yata tasan cewa bakada hankalin ko kobo."

  "Mami please calm down tunda har Allah yayi shi Abdul ya sauk'e girman kai ya gane kuransa ya kuma zo ya bada hak'uri kamata yayi ki yi hak'uri ki yafe masa mu kanmu munayi wa Allah laifi amman kuma yake yafe mana so please kiyi hak'uri" Afzal yayi bayani a hankali.

  "Wallahi darajan Afzal kad'ai kaci in ba haka ba Allah ne kad'ai zai mana hisabi kuma dukda hakan ma se mahaifiyarka taji wannan zance." Hak'uri da wa'azi akan yafiya Afzal ya tayi wa Mami cewa duk wanda ya rufa wa d'an uwansa asiri toh shima Allah zeyi masa ranan gobe k'iyama, hakan ne kad'ai yasa Mami ta hak'ura daga k'arshe ta ja baya daga alwashin data d'aukan ta kuma jaddada masa cewa ya fita harkan Amal idan har ya sake yi mata wani abun ko ya tinkareta da kalman so toh se inda k'arfinta dana Papi ya k'are.

   Da yazo tafiya ne ya mik'a wa Mami invitation card na d'aurin aurensa cewa a baiwa Papi. Sosai Mami ta tayasa da murna tare da yi mai fatan alkhairi. Ko bayan tafiyan Afzal kuwa hak'uri Mami tayita bawa Amal amman Amal ta nuna mata ba komai ya riga ya wuce. Alhamdulillah tunda Afzal ya cika mata burinta ya wanke ta daga cikin daud'an da Abdul ya aza mata. Bata san da wata bakin zatayi masa godiya ba. Da daren ranan ne bayan sallan Isha ta ari wayan Mami ta tura masa saqo tana mey masa godiya na sosai tare da yimasa addu'o'i da dama.
 
~•. .•~                 ~•. .•~                 ~•. .•~

   Preparations na biki ne ya sha gaba sosai ta fannin Ango da Amarya gabad'aya as auren na faruwa ne acikin sati na uku me gabatowa.
      Afzal yadda kuka san ba ango ba, ba abinda ya d'agashi bale ya nana shi a k'asa d'an shirye-shiryen angoncewan nan ba abinda ya ta6a. Muddin baya tare da Amal ko Sultan toh su uku suna tare ne, sosai yake taimaka mata da karatun jamb nata irin past questions d'innan duk ya sai mata tana bin exercises d'in on her own tana solving. Gashi Allah yayi kuwa Amal is a very fast learner, aya bata k'arya dama malamai sunce duk meh haddan Qur'ani a ka toh karatun boko baya basa wuya, Alhamdulillah Amal na ja sosai ta fannin boko.

   Ta fannin Nazeefah kuwa dukda cewa ba son auren take ba amman don ta k'ure k'awayenta 'yan k'aryan nan ta bawa Mummy had'in kai sosai. Sam kuma bata nuna wa k'awayenta cewa auren had'i bane za ayi mata da Afzal, hasali ce musu take ita da Afzal sun jima suna soyayya kawai sun yi deciding to keep it private ne, gyaran jikin nan tun dawowansu daga Saudi wata mata daga Nijar keyi mata. Shirye-shirye de ba inda ba'a ta6o ba.

Ana saura sati biyu d'aurin aure Mummy da kanta ta kawo wa Ummi invitation na programmes of events da za'ayi wanda suke nan kusan guda biyar. Ita kanta Ummi shakkan sanar da Afzal take sanin halinsa, tasan sarai yau d'inma se sun haura sama kafin ya amince gashi ko Abba baze tilasta masa cewa lalle-lalle se yayi attending ba tunda ba abun addini bane saidai da mamaki data nuna mishi invitation d'in ko complaining beyi ba illa ma cewa da yayi Allah ya nuna mana. A satin gaba aka soma events wanda duk wanda ake buk'atan halattar Afzal ya samu yaje illa bridal shower da Walima wanda k'awayen amarya ne zallah da family. Bawanda ze ga Afzal da Nazeefah yayi tunanin wai auren dole aka sanya su saboda walwala da farin cikin da suke portraying. A haka ne har Allah ya kawo ranarda aka d'aura auren Afzal da Nazeefah akan sadaki dubu d'ari biyu da sisin gold guda hamsin wanda daren ranan Ummi tayi organizing gaggarumin dinner to welcome Nazeefah into the family. Budiri sosai aka sha gun dinner, ba yadda Afzal beyi ba da Amal cewa tayi attending event d'in amman tak'i a cewarta wai dinner ne bazeyi tasa hijabi ba se gyale ita kuma a rayuwa idan akwai abinda bata so shine ta fita da jikinta a bud'e.

   Bayan abokan ango sun sallami k'awayen amarya suma bada dad'ewa ba suka tafi ya rage Afzal da amaryarsa kad'ai. Bayan rakiyan da yayi musu ya dawo ciki inda ya zarce kitchen ya d'au goran ruwa yana sha yana tafiya, har ya kaiga bud'e k'ofan d'akin seyaji Nazeefah na magana. Sa hankalin da zeyi ya gano a waya take maganar don haka ya kasa kunne yana mey saurararonta.

"Haba Bestie a dalilin mey zan had'a shimfid'a dashi? Ai da in bashi kyautan budurcina na gwammaci wasu 'yan iskan chan sunyi min fyad'e a kan layi... Hm ai kede bari tunda aka tauye min hak'k'i aka aura min shi I'll make sure shima na tattauye masa hak'k'i a gidan nan zamuga iya gudun ruwansa, sooner or later ze rubuta min takardan saki na se muga ko shima Daddy d'in ze sake bin gida by gida yana rok'on yaran mutane da su taimaka su aure masa yarinya."

Murmushi Afzal ya saki tare da kad'a kai sannan daga bisani ya bud'e k'ofan yasa kai ciki. Nan take Nazeefah ta katse wayar tare da cusawa k'ark'ashin pillon dake gefen hannunta. Ko k'ala be ce mata ba ya nemi waje ya zauna ya kwankad'e ruwan daya d'auko daga kitchen, kazan amarcin da su Sultan suka sanya sa siyan na dole ne ya d'ago daga side drawer'n dake gefensa ledoji biyu ne ciki da alama kowanne da kaza d'ai aciki. D'aya ya d'auka ya tura mata d'ayan side nata.

Lek'a cikin tayi ta tabbatar kazan ne a ciki sannan tace, "Kana iya d'aga gabbage d'innan daga gaba na dan kuwa ba a yunwa ka d'auko ni daga gidan ubana ba" ta sanar dashi cike da rashin kunya bako tsoron ido, sede yadda kuka san bada Afzal take ba ko kallonta beyi ba bale yasan da shi take, ledan kazan ya gama bud'ewa ya shiga ci seda ya ci kusan rabi sannan ya kora da juice dake gefe se a nan ne ya dawo da kallonsa a gareta yaga de har yanzu bata ta6a kazan nata ba.

"Kina iya bar min d'aki I suppose this is my room and I want to sleep" yace da ita cikin deep voice nasa. Da mamaki ta tsaya tana kallonsa. "D'akinka fa kace? Wallahi idan har kaga nabar d'akin nan to gawa na akazo fita dashi idan kaga you can't cope with me the earlier the better tun wuri ka rubuta min takardan saki na ba d'akin kad'ai zan bar maka ba gidan in whole" Ba tare da yace komi ba ya zaro d'aya daga cikin ninkakkun kayakin baccinsa had'e da ragowan kazansa da drink nasa ya fice mata daga d'akin. Se yanzu Nazeefah ke bin d'akin da kallo tabbas tasan wannan gado baya d'aya daga cikin wanda ita da Mummy suka siyo daga Dubai bade Afzal bane ya taho da abinsa? Oho! Koma meye anan zata na kwana sede shi ya bar mata d'akin. Rage kayan jikinta tayi ta janyo kazan taci fiye da rabi, tun wayewan garin Allah yau banda tea da tasha seda maltina d'aya bata sake cin komi ba. Bayan tayi nak ta tsiyaye ruwa daga dispenser tasha sannan ta shiga bayi ta watsa ruwa tayi alwala tayi sallah daga k'arshe ta kwanta. Tun kwanciyanta ba abinda taji wane gawa se bayan dawowan Afzal daga massalaci ne yayi tunanin dubata don tabbatar da ko tayi sallah ko batayi ba. Knocking bisa k'ofar yayi sannan ya bud'e ya kunna wuta inda ya tarar da ita kwance se bacci take tayi. Wutan d'akin gabad'aya ya kunna wanda hakan ya sata bud'e idon dole.

"Kina iya tashi kiyi sallah" daga fad'in haka ya mai mata da k'ofan ya fita. Wayewan garin Allah keda wuya Afzal ya bud'e wayansa don going through feeds, mails da messages nasa gabad'aya ma ya mance yau birthday nasa ne seda ya soma cin karo da message na Amal wanda take wishing nasa happy birthday sena Ummi da Abba da sauran mutanensa. Kiransu yayi one by one yana musu godiya, kasancewar Amal ce ya kira k'arshe bayan sun k'are wayan take tambayarsa in ze iya shigowa yau she has a surprise for him. Bayan sun gama wayan ya katse ya fad'a bayi yayi brushing sannan ya zira d'aya daga cikin jallabiyansa ya fice siyo musu breakfast bayan yaci nasa ya zauna a parlour yana replying birthday wishes from followers and friends nasa na social media accounts nasa.

   Yana cikin hakan ne chan sega Nazeefah ta fito daga d'akinta da alama banda brushing da tayi ko wanka bata d'aura akai ba dan kuwa da sleeping dress nata na jiya ta fito sanye da, kanta kuwa a bud'e yake ta kama sa sakwa-sakwa a tsakan kanta. Dining direct ta nufa tana hamma yayin da ta janye takeaway'n da Afzal ya ajiye mata ta soma ci ba gaisuwa bale godiya. A nitse ya mik'e ya bar mata dining d'in ya shiga d'akin data kwanan, kayanta na jiya, wayanta, charger, ragowar kazanta da wata k'aramar akwatin da yake da tabbacin ba nasa bane ya fito dasu bakin k'ofan ya ajiye sannan ya tattaro kayakinsa daga d'ayan d'akin daya kwanan ya maida su asalin d'akinsa had'e da locking k'ofar ya sa key d'in a aljihunsa dai-dai nan Nazeefah ke shigowa corridor d'in.

"Ya haka Mallam?" Tayi saurin tambaya ita da take da aniyyar shiga d'akin ta koma bacci. Yi yayi tamkar be jita ba, ta gefenta yaso bi seta tare sa "Wannan wani irin childishness ne? Taya zaka watso min kayaki na waje? Wallahi tun wuri ka bud'e kokuma a kunnen Ummi."

"Ummi kad'ai? I thought Abba zaki kira, I told you this is not your room why're you so dumb to realize that? Zan fita idan na dawo na tarar da kayakin nan anan don't be surprised idan na wulla su waje" Daga fad'in haka ya bud'e d'akin ya shiga tare da locking again. Bayi ya shiga yayi wanka tsaf ya shirya cikin k'ananun kayan da suke bala'in amsan figure'nsa ya fice gidansu Amal. Nazeefah dake tsaye har yanzu bakin k'ofan ta rasa nayi se binsa da kallo take a ranta tana tunanin abinda zatayi masa ta rama wannan rashin mutunci. Haka ba yadda ta iya ta tsuguna ta tattara kayakinta, sauran d'akunan ta dudduba sannan ta d'au d'aya aciki. Akwatunanta wanda muhimman kayakinta ke ciki ta jawo ta kaisu d'akin da ta tare sannan ta jejjerasu cikin wardrobe d'in. Bayan da ta gama ta fad'a bayi tayi wanka ta shiga bin gidan tana zagayawa har anan Afzal be dawo ba. Da azahar Nazeefah ta soma jin yunwa, tayi girki ne? Ta tambayi kanta. Amman ai amarya bata girki a ranar farkon kaita gidan miji kamata yayi har na wata Afzal yana siyo musu abinci ko ba haka ba? Zama tayi a parlour ta shiga duban channels na DSTV in search of abin kallo.

   Afzal kuwa fitansa ya wuce gun Sultan daga chan ya zarce gidnsu Amal. Gani yayi an shimfid'a babbar dadduma a tsakar hidan gashi ko ina fefes kake gani fiye dana kullum. Kan daddumar ne aka jera kuloli na abinci daban-daban ga silver flasks kusan kala hud'u da yake da tabbacin Aldeb da su ginger ne aciki. Da murmushi kwance a fuskansa ya k'arisa ya zauna daga gefe chan sega Amal ta fito sanye da purple jallabiyar data sha stone work koba a tambaya ba ansan kaya ne me tsada kuma ba shakka yana d'aya ne daga cikin tsaraban da Afzal ya kawo mata. D'aurin kai me kyau tayi irin na zamanin nan da ake kira Zahra Buhari wanda k'awarta ta koya mata.

   Cike da kunya da girmamawa ta k'ariso ta zauna daga d'ayan 6angaren da Afzal ke zauna had'e da gaishe sa.

  "Yaya?" Ta kirasa for the second time jin be amsa gaisuwan ba da tayi mar banda kallonta da yake ko kyafta ido babu. "Yaya?" Ta kuma kiransa se anan ya kad'a kai yana me dawo da kansa asalin rayuwa daga duniyan tunanin daya fad'a.

  "Lily?" Ya kirata yana me kasa d'auke idonsa a kanta har yanzun. Ba wai wani kwalyan azo a gani tayi ba kwalli zalla da powder ta shafa se lip gloss amman wani kyan da tayi sekace wacce a ka yima bridal makeover.

  "Yaya lafiya?" Ta tambaya yayinda kallon da Afzal keyi mata ya soma sanya ta tsoro.

  "I'm sorry" ya furta tare da kawar da kansa.

  "Wani abu ne Yaya?"

  "Nothing Lily illa kyan da kikayi, kinyi kyau sosai" ya sanar da ita wani murmushi cike da jin kunya ta sakar masa. "Kai Yaya har kasa naji kunya" ta amsa tana kare fuskarta.

   "Masha Allah ina Mami?"

  "Tana ciki tana fitowa."

  "Lily wannan kuma fah?" Ya tambayeta yana nuni da kulolin.

  "Har ka mance yau birthday naka ne? This is my birthday treat for you."

  "Lily you didn't have to do all these for me, I'll appreciate even the little things from you."

  "Haba Yaya ai you deserve even more, nifa raine kawai zance baka d'auka ka bani ba so kabar damuwa don Allah, Happy birthday."

  "Thank you Lily, I do appreciate but next time please karki kashe kud'inki a kaina haka save it you'll need it more yanzu nawa kika kashe anan?"

   "Yaya ba wan-" katse ta yayi gano tana shirin yi mai k'arya "Remember kin d'au alk'awari cewa baza ki sake yimin k'arya ba."

  "Toh Yaya kabar tambaya na nasan zaka min fad'a."

  "I promise bazan yi ba."

  "Ba kud'i na ni kad'ai bane harda na Mami da Papi."

  "Lily!"

  "Yaya please stop complaining kai nawa ne baka kashe ba akan mu a gidan nan? Ina de fata Amarya bata cika maka ciki ba" da wayo ta canza topic d'in.

  "Ai ko a k'oshe ma nake I must create room for Lily's cooking." Murmushi cike da jin dad'i ta sakar masa sannan ta shiga bud'e kulolin sede duka favorites na Afzal ne aciki, d'ayan flask d'in pepper soup na kifi ne aciki se kuma d'ayan garnished spaghetti wanda yasha sardines kaca-kaca aciki. A rayuwa ba abinda Afzal keso kaman kifi yafi sonsa fiye da kowani irin form of protein. Bayan n ga su spring rolls da samosa abinde ba'a cewa komi.

Amal na cikin serving nasa kenan sega Mami ta fito itama tayi wankanta fes cikin wata atamfa d'inkin riga da zani.

   "Bak'on namu ya iso kenan" ta fad'i tana nufan inda suke tare da zama gefen Amal. "Ina yini Mami?" Afzal ya gaisheta cike da girmamawa, bayan nan tayi masa fatan alkhairi na shiga sabon shekara da addu'o'i da dama.

"Thank you Mami da wahala haka kuma."

"Haba Afzal ai ka zamo na gida yanzu ina ce de abincin gishiri beyi yawa ba ka de san girkin Baby kullum da k'urak'uri."

"Kai Mami! Lily fa ta iya girki ai daba don boko ba se a bud'e mata restaurant." Gwalo Amal ta juya tanayiwa Mami harda kama kunnenta.

"Kade hura mata kunne d'an girkin data iyan ma ta shiga kofsa sa."

"Ai sede ta k'ara himma ko Lily?"

"Sosai ma Yaya kodan wasu suji kunya" Amal tayi maganan tana nufi da Mami.

"Aw taron dangi kuma za'ayi mun? Toh barin baku waje ina d'aki idan kuna buk'atan wani abun."

"Toh Mami" Afzal ya amsa, da haka ta shige ciki yayainsa Amal ta rink'a jan Afzal da hira yana cin abincin har seda yayi nak sannan ya kora da zo6onsa me sanyi ta kawo masa ruwa da sabulu ya wanke hannunsa.

"Yaya are you free today?"

"Sure Lily wani abu ne?"

"Yaya saura sati biyu exams na mun gashi ban gama covering syllables d'in ba ko zaka taimaka min?"

"Why not Lily? Jeki d'auko books nakin." Cike da jin d'adi ta shiga ta d'ibo books natan nan ya fara tutoring mata ababen da bata gane ba, mamaki ne sosai ya cika Amal sosai yadda Afzal ke solving questions d'in da ko ita da take fresh gradute ma baza ta iya ba. Sa hankali sosai tayi tana mey d'aukan duk abinda yake koyar mata ahaka har Papi ya dawo ya tarar dasu. Bayan sun gaisa yayi ma Afzal fatan alkhairi na shiga sabon shekaran da yayi shima sannan ya k'arisa ciki ya samu Mami.

Se La'asr Afzal ya musu sallama bayan tattara mishi ragowan birthday treats da Amal tayi cikin robobin takeaway daga k'arshe ta rakasa. Masallaci ya zarce yayi sallah inda ya wuce restaurant ya sai wa Nazeefah abinci shikam na Lilirsa zeci zuwa anjima. Isansa gida keda wuya ya tarar da Nazeefah da yunwa ya gama cin k'aniyanta se shar6an bacci take ta bar Tv na aiki da alama ko sallah ma batayi ba. Sauk'e ledojin dake hannunsan yayi akan centre table sannan ya d'au
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment