Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kusan k'arfe goma wanda yake dai-dai da k'arfe sha biyu a k'asar Nigeria Afzal yayi tunanin suyi sallama kodan Amal ta samu tayi bacci, bayan seda safen da tayi masa ya jira tayi hanging sannan ya ajiye wayan a kan side drawer. Daidaita wa Khaleefah dake ta faman bacci blanket yayi sannan ya mik'e ya shiga bayi ya watsa ruwa had'e da d'auro alwalan bacci ya dawo ya kwanta a gefensa.


~•. .•~       ~•. .•~       ~•. .•~      ~•. .•~

   Da dawowansu Afzal da sati biyu kayakin su na Cago suka iso nan yayi sorting out tsaraban da yayi ma mutanen hannun damansa ciki harda na Amal dasu Mami. Na Sultan ya soma kaiwa sannan na colleagues nasa a office. Daga can ya zarce gidansu Amal har ya soma sabawa da 'yan unguwa saboda yawan shiga da fitan da yakeyi. Parking yayi suka gaisa da 'yan bakin shago inda suke tambayarsa ko lafiya kwana biyu shiru yake sanar dasu cewa tafiya yayi.

    Da kansa ya fito da ledojin har zuwa bakin k'ofar gidansu Amal inda ya shiga had'e da yin sallama saidai tun daga bakin k'ofar yake jin hayaniya, kasa kunnen da zeyi ya jiyo muryan Mami da ihun Amal da hanzari ya k'arisa ciki ya tarar dasu se kuje-kuje suke yayinda Mami ke rik'e da tsumagiya tana bin Amal da keta zagaya tsakar gidan. Mami ce ta soma yin tozali da idon Afzal don haka tayi saurin dakatar da abinda takeyi wanda hakan yasa Amal daina ihun da take ta faman yi.

   "Afzal??" Mami ta kira sunansa cike da k'in yarda.

  "Na'am Mami" ya amsa. Amal kam don mamaki da kunya tama kasa magana banda raba idon da takeyi.

  "Wai! Wai! Lale lale mutanen Saudiya sannu da zuwa sannu da zuwa, Baby d'auko tabarma ki shimfid'a masa sannu da zuwa Baba na, sannu da zuwa" Tafiya take wane wanda k'wai ya fashe mata a ciki har ta isa bayan k'ofan d'akin Papi ta d'auko tabaramar.

   "Zo ki shimfid'a a nan" cewar Mami tana mey mata nuni da inda take tsaye. K'arisawa tayi ta shimfid'a ta kai ga d'agowa kenan Mami dake fakonta ta sauk'e mata tsumagiyan zuwat a baya da iya k'arfin ta, wani irin rkicaccen ihu Amal ta saki yayinda ta shiga susa bayan nata take tana kuka.

    "Subhanallahi!" Afzal daya zame shedan yadda tsumagiyar ta sauk'a da k'arfi akan bayan Amal yayi saurin furtawa "Dan Allah Mami kiyi hak'uri" be san lokacin da ya sake ledojin dake hannayensa ba a k'asa tare da shiga tsakanin Mami dake shirin sake kaiwa Amal wani zanan yayinda Amal ke ta faman kuka.

   "Ba zaki rufa ma mutane k'aton bakin nan bako?" Mami ta tambayeta tana neman bin ta gefen Afzal don kuma sauk'e wa Amal wani zanan wanda da sauri Afzal yasa hannu ya k'wace bulalan yana mey bawa Mami hak'uri.

  "Afzal don Allah ka barni da yarinyan nan yau seta fad'amun waya haifi wani tsakani na da ita a gidan nan."

  "Kiyi hak'uri Mami beyi zafi haka ba yi hak'uri."

  "Haba! Wace erin 'ya ce bata jin magana haka? Ba sa'anninki bane suke aure a k'auye amman don an barki anan kina girman jaki kina abinda kika ga dama zaki soma wuce gona da iri? Wancan ma a gefe amman ace kullum sekin k'ona min miya idan nace ki kula da shi? Kinada kud'in sake min wata cafanin ne?" Shiru Amal dake la6e bayan Afzal tayi se faman share hawayen dake ta faman zubo mata take da hannunta.

   "Ba dake nake bane?" Nan Mami tayi kaman zata ture Afzal don ta jawo Amal daga bayansa ta gaggaura mata mari saidai Afzal be bar aukuwan hakan ba as da sauri ya janye Amal sukayi baya yana kareta. "Kice mata tayi hak'uri" ya juyo yana kallon Amal saidai ko d'ago kai ta kallesa batayi ba bale tayi yadda yace se faman kukan zucin da takeyi tana hawaye. "Lily ki bawa Mami hak'uri nace" ya sake fad'a mata.

  "Kiyi hak'uri" ta furta a hankali.

  "Ni da kene a gidan nan ai ba Papinki yayi tafiya ba? Zan koya miki hankali ma tukunna maza jeki ki tattaro duka novels d'innan ki kawo su nan in cinna musu wuta ba shakka suke d'auke miki hankali 'yar iska kawai."

  "Ya isa Mami please kiyi hak'uri bazata sake ba in shaa Allah kiyi hak'uri" Hak'uri Afzal ya cigaba da baiwa Mami yayinda take ta huci, kunde san yadda fad'an itayenmu mata yake idan suka kama basu san suyi shiru ba, da k'yar ya samu ta hak'ura tayi shiru ta janyo hijabi daga kan igiyan shanya tare da d'aukan purse nata akan benchi ta fice don zuwa bus stop ta sake yin wata cafanin. Tana fita Amal ta ruga cikin d'akinta a guje had'e da jan sakata inda ta fad'a kan katifarta tana kuka. Afzal dake tsaye totally out of what to do daga bisani yabi bayanta, k'ofan ya gwada bud'ewa yaji a rufe don haka ya kira sunanta a nitse.

   "Lily?" Shiru tayi bata amsa ba se k'aran shesshek'an da takeyi yake ji.

  "Yi hak'uri ki taso ki bud'e wa Yaya kinji?" Nan ma shiru. "Yaya na miki magana bazaki tashi ba Lily? Yi hak'uri kinji? Ina nan ba inda zani sekin bud'e k'ofar nan" Seda yayi dagaske sannan ya samu ta taso ta bud'e masa, ta kai ga juyawa ta koma ciki kenan ya rik'e k'asan rigarta stopping her. Idanunta da sunka kad'a sukayi ja ta d'ago tana kallonsa a maraice.

"Come with me" ba musu tabi bayansa inda suka zauna akan benchi. K'aramar gelen abayan daya tsinta a k'asa wanda yake da tabbacin a garin guje-gujen da suka ta6a da Mami ne ta yasar ya d'ago had'e da mik'a mata. "Gashi cover your hair" nan ma batayi musu ba ta amsa ta rufe bak'in gashinta me uban shek'i.

   "What happened Lily? Kin manta alk'awarin da kika d'au mun na cewa bazaki sake sa Mami surutu ba? Mey kika mata yau kika fusatar da ita haka har ta ta6amin lafiyar jikinki?" Shiru tayi ta kasa cewa komi gudun kar da ta soma magana ta shiga yin kuka.

  "Talk to me kinji?"

   "Yaya.." ta furta bayan tsawon lokacin data d'auka kafin ta iya furta wata kalman kuka yaci k'arfinta. Tausayi na hak'ik'a ta basa saboda be ta6a ganinta tana kuka me tsuma zuciya kaman na yau ba toh shin meya faru? A kan k'ona girki zalla de Amal baza tayi kuka haka ba kamar yadda itama Mami bazata tayin surutu yadda tayi ba, mey take nufi data kwatanta Amal da 'yar iska? shin meya faru?

  Be sake cewa da ita komi ba saboda yasan how badly she needed to cry, ya sani kukan nan da takeyi ne kad'ai ze iya rage mata k'unar da zuciyarta keyi mata don haka ya zauna yana saurronta tanayi badon yanaso ba sedon ba shida wata mafitar. A hankali ta shiga yin shiru, handkerchief nasa ya ciro daga aljihun wandonsa ya shiga share mata hawayen nata a hankali har ya samu tayi shiru.

   "Yaya-"

  "Shhh" ya katse ta a hankali "Don't speak."

  "Yaya but I need to let you know what's really happening ko Allah zeyi kai zaka yarda da ni kuma bazaka yimin kallon 'yar iskan da Mami keyi min ba."

  "Subhanallah Lily! Meya faru?"

  "Yaya Mami tak'i ta yarda dani dan Allah help me out" ta kuma fashewa da wata kukan. "Wallahi ni ba 'yar iska bace."

   "Shhh it's okay I'm here, yi shiru ki fad'a min meya faru."

  Hanci taja ta share hawayenta sannan ta fara kamar haka; "Ina yaron nan dana ta6a maka hirarsa ranan a office?"

  "Wanne d'aya? Yaron me markad'en bakin hanyan nan?"

  "Shi" ta amsa tana gyad'a kai.

  "Meya faru?"

  Hawayenta ta share da hanky'n da Afzal ya bata ta cigaba "Yaya sharri yayi mun gun Mami wai kullum ba aikina idan ta tura ni markad'e saidai inyi ta mishi hirar banza ina tatta6ashi."

  "Subhanallah!" yayi exclaiming cike da k'in yarda.

  "Yaya ko kai na ta6a shafa koda hannunka ne? Yaya ka yarda zan iya aikata abinda yake tuhumata da shi?" Ta tambayesa cikin kuka sosai.

  "Ko kad'an Amal you'll never do such a thing kibar kukan haka kinji? Your Yaya is here."

  "Thank you Yaya but Mami tak'i yarda dani wai sam ni 'yar iska ce idona a bushe yake ni munafuka ce, bata sanar da Papi ba tukun amman ta rantse se tayi hakan, shekaran jiya data aikeni markad'e ashe yace mata tabi bayana yanada abinda ze nuna mata bayan ya k'arisa markad'en yace in k'arisa in d'auka, dai-dai na kai inda yake tsaye sauran in d'aga roban kenan na zame na fad'a jikinsa ba tare da na sani ba ashe 6awon ayaba yasa mun don in zame. A sanadiyyar ture ni da yayi naji wannan ciwo" nan ta d'aga bakin skirt nata zuwa idon sahu sega wani babban k'warzani, fatan gun gabad'aya ya d'aye don azaba.

  "Subhanallah" Afzal Yayi exclaiming cike da tausayin Lilirsa. "Me kikayi masa ya za6i yayi framing naki haka Amal?"

  "Wallahi Yaya ba abinda nayi masa."

  "Tell me the truth Amal bakiyi masa komi ba?"

  "Wallahi Yaya banda cewa da yayi yana sona na nuna masa ko wuta da aljannah ze bani bazanso mutum irinsa ba bakuma abinda ya sake had'amu shine yace min wai zan gani sena lahira ya fini sukuni." Shiru Afzal yayi ko nazarin me yake se Allah. "Yaya kaima baka yarda dani ba?" Ta tambayesa sabin hawaye na ambaliya a fuskarta "Wallahi ni ban aikata abinda yake tuhumata dashi ba, Yaya please believe me."

   "Shhh!" ya katse ta "I believe you Lily nasan bazaki ta6a aikata abu haka ba, I'm here bazan tsaya ba se inda k'arfi na ya k'are in shaa Allah yaron nan da kansa zaizo har nan gida ya baki hak'uri ya kuma yiwa Mami bayanin gaskiyan al'amarin da bakinsa."

  "Yaya how is that even possible?"

  "Trust me okay?" Kai tayi saurin gyad'awa had'e da yi masa godiya. "Girkin da take cewa kullum kina k'ona mata shi kuma fa, haka ne?"





RANA D'AYA
#RD
Love... king Miemiebee👄✨
[12/08, 22:36] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
April, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 0⃣9⃣*



  "Quite alright nasan ina k'ona mata miya but tun kan alk'awarin dana d'aukan maka wallahi ban sake ba se yau, kawai tana neman huce haushi na da takeji ne taketa nanatawa haka nan" ta fayyace mai hawaye na tsiyaya daga idanunta.

  "Meyasa baki sa hankalinki ba kika bari har girkin ya k'one? Bance idan Mami ta saki aiki ki bar duk abinda kikeyi ba muddin ba sallah bane kisa hankalinki?"

  "Ka fad'a" ta amsa tare da dukar da kanta.

  "Then what happened?"

"Yaya duk hankalina baya jikina, na rasa ina zan sa kaina da abinda Abdul (yaron me markad'e) yayi min kuma wallahi ba wani novel d'in nake karantawa ba hasali ma ina zaune cikin kitchen d'in amman banma san miyan na k'onewa ba seda ta shigo ita kuma ta dage sam wai novel nike karantawa shi ya d'auke min hankali."

  "Shikenan ya isa, bar kukan haka kinji? Am here for you bari Mami ta dawo zan yi mata bayani."

  Bayan isowan Mami Afzal ya sa Amal ta amshi cafanin ta shiga sarrafawa acikin kitchen yayinda shida Mami suka zauna suna tattauna batun Amal da Abdul. Sam Mami tak'i yarda da abinda Afzal ya fad'a mata a cewarta wai kawai Amal ta tsara Afzal d'inne don ya tausaya mata, ita da ta ga abu da idonta Amal ta kwanta jikin Abdul ne kuma za'a tsaya ana mata wasa da hankali? Daga k'arshe ba don tana so ba se don tana jin nauyin Afzal ta nuna masa ta yarda komi ya wuce. Rok'anta sosai Afzal yayi cewa kar ta fad'awa Papi nan ma de tace taji baza ta fad'a mar ba amman dukda haka Afzal be yarda ba seda yasa ta d'au masa alk'awari. Nan ya zazzage tsaraban daya siyo musun, sosai tayi farin ciki da godiya da addu'a har ta buk'ace sa daya tsaya ya jira abinci amman ya nuna daga gida yake don haka a k'oshe yake. Amal ta kira ta nuna mata kayakin inda itama ta nuna farin cikinta sosai dukda cewa chan k'asa hankalinta a tashe yake. Godiya ba adadi tayi masa itama sannan suka rakosa waje, yau zuwa bakin k'ofa Mami ta rakasa tace su k'arisa da Amal kasancewar miyan dake kan wuta. Wajen motansa suka nufa suka shiga ciki suka k'arisa bakin layi gun markad'en su Abdul.

Plan daya shirya yayi ma Amal bayani sannan ya mik'a mata wayarsa bayan ya nuna mata inda zata danna da zaran sun fara magana da shi Abdul d'in. Daga cikin motansa ya zauna yana hangensu yayinda ta k'arasa ta sami Abdul. 

   "Abdul inason magana da kai" tace dashi ba gardama ya mik'e harda d'an guntun murmushinsa ya nufo inda take tsaye. A tunaninsa wai ko tazo ta fayyace mar soyayyan da take masa ne. Nan Amal ta danna button na play had'e da b'oye wayar k'ark'ashin hijabinta gudun kar ya gani sannan ta fara kamar haka;

    "Yanzu Abdul abinda kayi min ka kyauta kenan?"

  "Mene? Ban fad'a miki cewa na lahira seya fiki jin dad'i ba muddin kika k'i bani had'in kai?"

  "Toh Abdul ana soyayyan dole ne? Ka gane mana bana sonka."

  "Ni kuwa sekin soni in ba haka ba ki shirya wa tashin hankalin dayafi wanda kika shiga a baya."

  "Mey kake nufi da hakan?"

  "Ina nufin a shirye nake da inyi komi domin inga na mallakeki."

"Kana nufin zaka iya ta6a lafiyata idan banyi yadda kakeso ba?"

"Sosai ma kuwa har kisan kai zan iyayi a kanki."

  "Lallai kuwa kasani Allah ya fika kuma ma ranan mey kasa min na zame?"

  "Aww ma tambaya kike? 6awon ayaba na ajiye miki bayan nasa Mami ta biyoki ranan don ta tabbatar da abinda na fad'a mata akanki."

  "Dukda cewa kasan k'arya ne ni ban ta6a koda rik'e hannunka ba?"

  "Tabbas sharri na miki mana amman ai na ja miki kunne ko ba haka ba? Kuma na baki nan da sati kije kiyi tunani idan har baki amince da soyayya ta ba ina tabbatar miki da cewa gaba abinda zan miki se 'yan unguwan nan sun k'yamace ki zaman unguwa ya kasa ki ba zaman gidanku kad'ai ba."

  "Nagode se muga yadda Allah ze baka nasara" daga fad'in haka ta juya ta fice. Tana shiga mota ta mik'a wa Afzal wayan inda yayi stopping ya kuma yi saving sannan yayi playing suka saurara.

  "Good job Lily kinga da wannan muna iya kai k'arar sa kotu against the crime of misdemeanor but kafin nan I'll meet him personally to make him go and apologize for you idan har yak'i complying then I'll have to bring police for him."

    "Yaya you're going to do all these for me?" Ta tambayesa a hankali tana mamakin yadda Afzal ke nuna tsananin damuwa duk lokacinda ta shiga matsala.

  "Wanda yafi haka ma zan miki Lily muddin ina raye kuma inada halin" ya jaddada mata.

   "Thank you Yaya sakallahu bil jannah."

  "Ameen don't worry."

   "Toh barin koma gida ka gaishe da Ummi in ka isa."

  "Ki bari in mayar dake."

  "Haba Yaya nan da gidan ne kuma har seka mayar dani dan Allah ka bari."

  "Lily-"

  "Please Yaya karka damu" ta katse sa a nitse.

  "Toh shikenan and please Lily karki sake yin abinda ze fusatar da Mami koda tana miki surutu kiyi mata shiru in har zakiyi magana toh ya zamanto hak'uri zaki bata kinji?"

  "In shaa Allah Yaya nagode."

  "Gobe ko jibi in shaa Allah zan shigo."

  "Toh Allah kaimu se anjima" da haka ta sauk'o daga motar tabi lungun da ze kaita gidansu. Isan Afzal gida keda wuya, bayan an sauk'o daga sallan Maghrib Abba yayi requesting presence nasa a site nasa. Wayansa kawai ya d'aga yabi bayan Micheal suka zarce site na Abba inda ya zauna kan kujera. Bayan d'an tambayoyin da Abba yamasa game da aiki da makamancin haka ya buk'aci Micheal daya mik'a masa bak'ar ledan dake ajiye akan dining table.

  "Ga wannan wedding invitation cards naka ne Prince na d'ibi wanda zan rabar wa jama'a na haka Umminka ma wannan naka ne."

"Duka wannan Abba?" Ya tambaya had'e da zaro idanu waje. Invitation cards sekace wanda za'a rabawa kaf 'yan Maiduguri!

  "Eh Prince nasan iya adadin mutanen da kake dasu fatana de baza su kasa ba ko?"

  "Baza su kasa ba Abba nagode."

  "Yauwa Allah yayi ma albarka."

  "Ameen Abba."

  "Yauwa nace iyayen yarinyan fa suna son fara yi mata jere tunda biki ya matso kusa ga gininka kuma kusan yanzu ma aka fara ina laifin ka yafe neman gidan hayan da kake seka za6i d'aya daga cikin gidaje na dake garin nan? Kowanne ya maka niko zan baka."

  "Ayyah Abba karka damu, I don't want to be a burden to you."

"Nonsense ko ka manta d'a kake na cikina? Kai de karka damu ni da niyyan baka kyautan gidan ma nake as my own gift for you on your wedding."

  "Abba ba abinda zance sede Allah k'ara maka bud'i thank you so much in shaa Allah gobe nida PA'nka zamuje mu duba gidajen zan sanar da kai duk abinda akwai, nagode."

   "Toh hakan yayi sannu kana iya tafiya."

  "Toh Abba seda safe" da haka ya koma site nasa inda ya fad'a kan gadonsa had'e da zaro d'aya daga cikin invitation cards d'in yana galla mar harara. 25th December daya bada d'in shi ke rubuce jikin invitation card d'in ba abinda aka canza. Ji yake kaman ya tattara duka IV d'in gabad'aya ya k'ona don haushi, da k'yar ya samu yayi bacci ranan.

   Washegari kamar yadda yayi promising Abba shida PA'n Abba suka dudduba gidajen Abba dake nan cikin Maiduguri wata bungalow ce a New GRA na layin NUJ yayi masa nan yayi deciding ze d'auka, 6angare biyu ne acikin gidan seda BQ. Na gaban wanda ya kasance master side na da two bedrooms, parlour, kitchen and toilet a ciki se main side d'in kuma wanda ya k'unshi four bedrooms da toilet each, two living rooms, kitchen, dining area da kuma store room. Tun a yinin ranan 'yan uwan Mummy da ita Mummy kanta suka shiga yiwa Nazeefah jere.
   Afzal kuwa ranan be samu zuwa ganin Abdul ba se a washegari, shiga yayi cikin k'ananun kayan da suka mugun amsansa sannan yasa nerdy glasses (fararen tabarau) kafin wajen markad'en ya yi parking sannan ya fito ya tarar da Abdul wanda idan yayi shekaru dayawa a duniya shine ashirin. Ashe ma yaro ne, jiransa yayi bayan ya gama markad'en sannan ya k'arisa yayi masa sallama.

   "Wa'alaikumus salam" Abdul ya amsa yana me zuba ma Afzal ido ko zey iya tuna ina ya wayi fuskan nasa sede ina ya kasa, ba tantama yau ne had'uwansu na farko kokuma halan yana ganin shiga da fitansa cikin unguwan nan.

   "Abdul ko?" Afzal ya tambayesa wanda yasa sa gyad'a kai cike da neman k'arin bayani.

  "Tambaya kake yi ne bawan Allah?" Ya tambayesa.
 
  "A'a magana nakeso muyi."

  "Toh ina jinka."

  "Batun Amal ne" ya fad'a had'e da yin shiru.

"Amal wace Amal kenan?" Abdul ya tambaya yana mey nazari.

  "Baby."

  "Oh! Wani abun ne?"

  "Game da abinda kayi mata ne nakeson jin gaskiyar batun daga bakinka." Dariya Abdul ya k'yalk'yale da ita "A dalilin mey kake tunanin har zaka ji wata abun daga bakina? Mey alak'arku? Ina da yak'inin cewa Baby batada Ya so meya kawo ka nan?"

"To make you go and apologize to her and tell her mother the whole truth" Afzal ya sanar dashi cikin tattausar murya.

  "Turanci kuma zakayi min? Toh dukda cewa ban fahimci duk abinda ka fad'a ba nadeji kanason in sami Mami in fad'a mata gaskiya, ko wani gaskiya kake nufi?"

  "Ka dena pretending kaman bakasan me nake nufi ba, ko ba kai kaje ka samu Mami ka irga mata k'arerayin banza ba akan Amal don ka 6ata mata suna? And also ka ajiye mata 6awon ayaba don ta taka ta zame koba haka ba? Ce maka akayi ana soyayyan dole?"

  "B'awon ayaba? Kai to na ajiye ayimin abinda Allah beyi min ba aikin banza har waye kai zaka tsaya kana gayamun magana iya son ranka wallahi idan ba aikin 'yan tasha kakeson gani ba anan zaka d'ibi k'afafunka ka koma inda ka fito yanzun nan."

  "Zaka je ka bata hak'urin ne kokuwa?"

  "Ba inda zanje ina nan" ya jaddada masa.

  "Good" Afzal yace tare da ciro wayansa yayi playing mar audio da Amal ta d'auka shekaran jiya. Ido wuru-wuru Abdul ya zaro waje yayin da cikinsa ya d'au ruwa. "Taya ka samu wannan magana?"

   "Wancan be shafe ka ba abinda zan jaddada maka shine ka shirya dan kuwa hukuma zata shiga neman ka."

  "A dalilin meh?"

  "Because you've been found guilty of misdemeanor."

  "Ko mey hakan ke nufi?"

  "Laifi ne wanda kotu ke tuhumar duk wanda ta kama yana ma d'an uwansa barazanar yi masa illa kokuwa lahani na jiki ya kuma cimma hakan. Na farko na sanya wa Amal 6awon ayaba da kayi dagangan don ta taka is a battery crime, haka takawan da tayi kuma ta fad'i kakuma sake hankad'eta taji ciwo shima battery crime ne sannan barazanar illata ta da kayi na cewa idan batayi yadda kakeso ba rayuwarta zata iya shiga cikin matsala shi kuma assault crime ne don kuwa yanzu duk wani mumunin abin da ya sameta God forbid ala misali ma ace wani ne yayi mata kisan kai, kaine nan kotu zata tuhuma saboda nauyin kalamunka" Afzal yayi masa bayani.

  "Toh naji nayi dukkanin abubuwan daka k'irga amman waya ganni ina cikin aikatawa?"

  "Smart guy kenan seems like ka mance muryanka ne acikin audio d'innan."

  "Murya kace, murya kuwa sama da mutane goma suna iya yin murya iri d'aya kuma nan yanzu naga dama ina iya sauya murya na in k'aryata duk ewata hujjar da kake tak'ama da ita."

  "Zaka k'aryata fa kace?"

  "Sosai ma kuwa tunda ba fuskata bace murya ne."

  "LOL a gaskiya nayi mamakin yadda ka kasance baho a matsayinka na d'a na miji" Afzal yayi magann had'e da zaro glasses da yake sanye dasu. Wata k'aramar cable yaciro daga aljuhun wandonsa ya had'a da wayansa da glasses d'in sannan ya shiga yin 'yan wasu danne-danne. Shi de har anan Abdul kallonsa yake, zuciyarsa bata tashi tsinkewa ba seda yaga fuskansa live a cikin wayan Afzal tun daga lokacinda yake amsa sallaman da Afzal yayi masa har izuwa k'arshen maganan da yayi. Ashe de glasses me CCTV Afzal ke sanye da wanda ya aro daga gun wani abokinsa lawyer, glass ne me camera ta gefe biyu duka wanda yake baiwa wanda ke sanye da ita daman yin video record na duk abinda yake tsaye gabansa.

  Nan take cikin Abdul ya d'au ruwa gyaran murya Afzal yayi had'e da kashe wayan nasa ya mayar aljihu "Se muga yadda zaka iya kare kanka yanzu a kotu idan na nuna musu wannan don kuwa akasin hakan na iya janyo maka one year inprisonment (shekara d'aya
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment