Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

***
Kasancewar Nazeefah ta cika masa ciki da abinci koda ya isa gidan Amal be buk'aci abinci ba se chan wajajen tara, serving nasa tayi ta zauna a gefe kasancewar macaronin be gameta ba yau. Cokali d'aya ya kai baki ya harar take.

"Subhanallah Habib Albi!" Tayi exclaiming a rud'e. Goran ruwan dake gefensa kawai ya bud'e ya shiga kwankwad'a seda ya kusan shanye duka ya cire. "Habib Albi lafiya?"

"Kitten mey kikasa a abincin nan haka?"

"Kaman ya mey nasa kuma Habib Albi? Wani abu ne?"

"Kinji gishiri da barkonon da yake ciki? Baki san bana son yaji bane?"

"Barkono da gishiri kuma Habib Albi?" Ta tambayesa da mamaki a iya saninta attarugu biyu tasa gishiri kuwa kad'an maggi ma tafi bawa k'arfi a girkin, mey Afzal yake cewa toh?

"Yes" ya jaddada mata tare da k'arar da ruwan goran plate d'in taja don d'anawa sede be barta ba yayi sauri yaja "Don't mind bazaki iya tasting ba."

"Wallahi attarugu biyu kacal nasa."

"Maybe yana da zafi ne."

"Toh gishirin fah? Har dana kusan sauk'ewa ma fa na d'ana kuma banji yayi rad'au ba please ka bani in ta6a inji." Plate d'in ya tura mata spoon d'aya takai itama ta harar gora ya mik'a mata da wuri nan ta kur6e itama. "Kinji?"

Mamaki ne ya cikata shin ya akayi haka? Abincin se kace an d'ibo ledan gishiri ne aka juye a ciki ga wani d'an banzan borkono "Habib Albi I'm so sorry wallahi ban san ya hakan ya faru ba believe me har dana kusan sauk'ewa ma na d'ana and everything was okay ka kira Safiyya ka tambayeta kaji."

"Haba Kitten me yayi zafi harda tambayan Safiyya? It's okay kinji? Karki damu ina Safiyya kirata tazo ta zubar da abincin don ko almajirai ban jin ya dace a basu abincan."

"Habib Albi dan Allah kayi hak'uri I'm very sorry."

"Ohh Kitten" yayi maganan had'e da dafe hannunta dake ajiye kan table d'in "It's really okay just be careful next time okay?" Kai ta gyad'a hankali har cikin ranta bata ji dad'in hakan ba, sam ta rasa ya akayi hakan ya faru koda wasa kuma bata kawo a ranta wai Safiya zata iya zuba mata borkono da gishiri cikin girki ba.

"In dafa maka indomie toh?"

"Karki damu."

"Habib Albi kayi fushi dani ne?" Ta tambayesa tamkar zatayi kuka.

"Meyasa zanyi fushi dake Kitten kinsan mey?" Kai zalla ta kad'a mar. "Sanya hijabinki muje muci abinci a waje."

"Hab-"

"Shhh not a word" da kansa ya kira Safiyya ta zubar da abincin sannan ya sanar da ita zasu fita. Suna fita ta d'au wayanta ta kira Nazeefah a karo na farko ta d'aga. "Aunty ina yini?"

"Lafiya ya kike?"

"Lafiya k'alau Aunty yau baki san meya faru ba."

"Meneh?"

"Hmmm abinci Aunty ta ke girkawa da ta shiga d'aki na saci idonta na shiga kitchen d'in na barbad'a borkono da gishiri akai gashi yanzu Uncle ya dawo ya kasa cin abincin k'arshe ma cemin yayi in zubar."

"Kai Safiyya!" Tayi exclaiming cike da jin dad'i.

"Wallahi Aunty."

"Wow kinci kyauta, aikinki yayi kyau yanzu ina suke?"

"Naga sun fita amma de kam beji dad'i ba da be tarar da girki mey kyau ba har a fuskansa naga hakan."

"Haka nakeso ki cigaba da gashi Sofin gaye niko na miki alk'awain sabon atamfa harda d'inki."

"Godiya nake Aunty."

"Yauwa se anjima aikinki na kyau" da haka sukayi sallama.

*****
Haka tun daga ranan sede Amal batayi girki ba se Safiyya ta zagaya ta zabga mata gishiri ko yaji aciki gashi koda wasa Amal bata ta6a zarginta ba saboda yadda ta amince da Safiyya ta rik'eta da zuciya d'aya bayan nan ga yadda it Safiyyan da kanta take nuna mata girmamawa da k'auna. Gashi kaman dagaske duk sanda girkin ya 6aci ta rink'a nuna damuwa. Abun daya sake d'aurewa Amal kai shine se idan Afzal ze zo mata ne girkin yake tashi 6aci idan ba haka ba girkinta me kyau takeyi idan baya nan amma da zaran ya dawo se gishiri da borkono su fara zarcewa. Abu kaman wasa seda Afzal ya ya tattare borkono da gishirin ya kulle a storeroom, attarugu kuwa ya kyautar don kar girkin nata yana 6aci sede aikin banza yayi. Muddin Amal tayi mai girki toh se gishiri da borkono yayi yawa. Sosai abun ya d'aure masa kai. Amal kam har kaman ta fara samun ta6in hankali ne tsan-tsan tashin hankali. Ba aikinta se kuka a gidan, ace wai yanzu Afzal nata baze iya cin girkinta ba? Hakan ba k'aramin k'ona mata rai yake ba. Gabad'aya ta fita daga hayyacinta barin ma yanzu da Afzal ya fara zancen hanata yin girki kwata-kwata don tun baya nuna damuwa abun ya fara damunsa. Ya rasa gane meke faruwa. Tunani ya fara kode iskokai ne suke mata wasa da hankali? Sede be san ta ina ze fara sanar da ita hakan ba, shi kansa ba wai ya amince da hakan bane, be ta6a ganin mace mey son addini kaman Amal tasa ba har taya iskokai zasu ci nasara akanta? Kullum suka fita seta tuna masa yayi addu'an barin gida haka idan suka dawo, na shiga bayin nan bata wasa da shi ko ruwan d'umi zata zubar setayi istihaza toh tayaya aljanu zasuyi nasara akanta? Sede kuma ba wanda yafi k'arfin jarawaba.

Kuka take sosai tana rantse mishi akan cewa lallai-lallai bata sa gishiri da attarugu ko d'igo ba cikin girkin amma ga abincin nan rad'au da uban borkono. Yau kusan sati biyu kenan suna abu d'aya.

"Kitten it's okay kibar kukan haka."

"Habib Albi please believe me."

"I do believe you Kitten I do" ya amsa yana share mata hawayenta amma ina se zuba sabi suke.

"Wallahi ban bud'e storeroom d'in na ciro gishirin ba kana iya zuwa muje ka gani ko kuwa ka tambayi Safiyya, a kulle d'akin yake wallahi ban bud'e ba" hannunsa ta kama da niyyan jansa storeroom d'in akan yaje ya gani sede yayi saurin tsayar da ita ta hanyan rik'e ta.

"Shhhh it's okay it's okay" ya fad'a yana k'ok'arin calming nata. "Calm down okay? I believe you, I do believe you Kitten nasan baki bud'e d'akin ba amma ai kinji amount na gishirin da yake cikin abincin ko?"

"Wallahi ban sa gishiri ba Yaya."

"I know Kitten and I do believe you, kinsan mey nake so da ke? Ki huta na kwana biyun nan kar ki sakeyin girki duk abinda kikeso zan siya miki ko kuwa Safiyya ta girka miki amma ke karki sake aza tukunya a gidan nan hala stress na school ne yake damunki you need to rest."

"Har zuwa yaushe Habib Albi? I don't need to rest ba hauka nake da shi ba wallahi ban sa gishiri cikin girkin nan ba you have to believe me tunda ka tattare gishirin ka rufe a store ban sake yin girki da shi ba, taya zakace kar in sake aza tukunya a gidan nan Habib Albi?"

"It's just for some time Kitten please stop crying" Ya amsa yana share mata rushing tears nata had'e da rungumarta "Kiyi hak'uri kibar girkin na kwana biyu until everything is okay kinji?" Jikinta ta janye daga nasa "Kai kuma fa Yaya? Wa ze na maka girki? Wa ze na dafa maka abinci? Shikenan bazaka sake cin girki na ba?"

"Wayace bazan sake cin girkin ki ba Kitten? It's just for the mean time okay? Zan na ci a restaurant kafin nan kin huta kema I'm sure stress ne ya miki yawa."

"Yaya wani irin stress? Wallahi ba wani stress dan Allah kar ka hanani yi maka girki I beg you please Yaya" kuka take sosai tana rok'ansa. Hannayensa ya kama acikin nata.

"Kitten dan Allah kibar kukan nan haka bawai hanaki yi mun girki nake shirin yi ba its just for the meantime."

"Yaya please I beg you, I promise daga yanzu zanna sa hankali maggi baze sake zarce mun ba please kar ka hanani yi maka girki."
Kuka take sosai shi kansa ya rasa mey yake ciki shin ya kira malami a yi mata ruk'iya ne? Kokuwa likitan mahaukata ze nema? Shin meyake damun Kitten tasa? He don't want to believe ta6in hankali ne ke shirin kamata, he can't afford to lose her. Taya zata na rantsuwa bata sa gishiri da barkono a girki ba amma kuma ga abinci rad'au? Meke faruwa? Hugging nata yayi gam a jikinsa yana shafa bayanta har suka sauk'a k'asa akan gado. Be saketa ba seda ya tabbata bacci ya d'auketa. A hankali ya shimfid'ar da ita akan gadon ya rufeta da bargo sannan ya fito. D'akin Safiyya ya nufa yayi knocking bisa k'ofan take ta amsa ta fito.

"Sannu Uncle."

"Safiyya?" Ya kirata "Na'am?" ta amsa tana kallon k'asa. "Meyake faruwa idan na tafi office?"

"Kaman ya Uncle?"

"Meyake samun Auntin ki? Meyasa girkinta kullum gishiri yake zarcewa bayan na tattare gishirin na kullesu a d'aki ke kike d'auko mata?"

"Wallahi ba ni bace Uncle kuma kaman yadda baka sani ba wallahi nima banida masaniya game da abinda yake faruwa ni kaina mamaki abun yake bani a ido na tayi girkin d'azun nan maggi da tattasai zalla tasa kuma har da ta kusan sauk'ewa seda muka d'ana mata amma da zaran ansa a flask se abincin ya 6aci."

"Are you sure?"

"Na'am?"

"Nace kin tabbata?"

"Eh Uncle."

"Bake kike yin gwaninta ki k'ara mata a bayan idonta ba?"

"Meyasa zanyi hakan Uncle? Allah ma shaidana ne."

"Huhhh" nauyayyan ajiyan zuciya ya sauk'e.

"Ban so inyi maganan ba d'azu a gabanta sede ranan naga Aunty tana wani abin al'ajabi."

"Abin al'ajabi?" Ya tambayeta cike da rashin fahimta.

"Eh uncle a kitchen ranan naganta tana magana da kanta haka jiya ma."

"Tana magana da kanta kuma?"

"Eh Uncle ita kad'ai sekaga tana suratai dama Aunty tana da aljanu ne?"

"Aljanu kuma? Kina ganin aljanu ne suke mata wasa da hankali?"

"Toh ban sani ba amma da abun tambaya dan akwai wata k'anwar mamar mu a k'auye da aljanu suka tak'ura mata. Itama amarya take kaman Aunty amma sai dai bata d'aura girki ba baya nuna. Ko kwana kwanon zeyi akan murhu baze ta6a nuna ba daga k'arshe seda aka kaita gun Malami akayi mata ruk'iya sannan ta samu sauk'i."

"Subhanallah" ya furta yana shafa sajensa "I'll figure out what to do dan ko ni na fara zaton aljanun ne nima gashi de kema kince bata sa gishiri toh taya abincin yakeyin rad'au haka?"

"A gwada nemo malami yayi mata ruk'iyan ni kaina tausayi Aunty take bani wallahi se kaga kukan da takeyi d'azu."

"Kiga koda wasa kar ki nuna mata munyi maganan nan kinji ai ko? Bana son kowa yaji maganan daga ni sai ke, kin gane?"

"In shaa Allah Uncle Allah ya bata lafiya."

"Ameen" da haka ya koma d'akin nasu ya zauna a gefenta hannunta ya rik'o cikin nasa a hankali yana murzawa "Kitten what's really going on? Meyake faruwa? Why is this happening to you?" Sosai ya tausaya mata he can't believe aljanu na son haukatar masa da ita.

Kuka sosai Amal ta sha washegari da Afzal ya hanata yi masa breakfast yasa Safiyya. Ko makaranta tak'i fita ranan tun fitan Afzal ta rufe kanta a d'aki tana kuka, se hak'uri Safiyya ke bata kaman dagaske chan tace zata shiga bayi tana ficewa taje ta kulle kanta a d'aki ta d'au paper'n da Nazeefah ta rubuta mata lambarta ta zuba tare da danna mata kira.




RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:37] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
August, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 3⃣2⃣*


"Assalamu Alaikum Aunty ina kwana?"

"Sofin gaye ya kike?"

"Lafiya k'alau Aunty ya Hindu?"

"Hindu tana gida ni na fita school ya uwar d'akinki?"

"Hmmm Aunty ina da labari mey dad'i miki."

"Kai Sofin gaye har ta gama haukacewan ne?"

"Gashi Uncle jiya yazo d'akina yana tambayata ko meke faruwa na tsara mishi labari kaman yadda kikace inyi yanzu haka yace ze nemo malami ayi mata ruk'iya don shima ya fara zargin ko aljanun ne."

"Kin min dau-dai shin ta sake yi masa girki?"

"Ai hanata yayi yau gata chan a d'akinta se kuka take."

"Bravo alaiki Sofin gaye tsaraban ki na nan na tanadar miki."

"Toh amma Aunty yanzu idan aka kira Malamin ya duba ta yace lafiya fah? Za a iya gano ni ke k'ara mata gishirin fah."

"Inji wa? Taya za a gane ki bayan duk malaman ruk'iyan nan kud'i kawai suke so? Da mutum nada ciwo da bashida shi muddin an kaisa gun su se sun bada magani dan abasu kud'i in return saboda haka ki kwantar da hankalinki in shaa Allah baza a kama ki ba kede ki cigaba da gashi."

"Toh Aunty."

"Mission number one complete muddin akayi mata maganin kar ki sake 6ata mata girki mu barta nan haka se idan an kwana biyu se mu fara mission number two."

"Ohh kar in sake sa mata gishirin?"

"Eh mana baya riga ya hanata yi mai girki ba yanzu?"

"Eh."

"Toh kinga idan akayi mata maganin seya zammana kaman dama akwai matsalar amma an samu an magance yanzu."

"Nagane."

"Yauwa jeki sameta kiyita bata hak'uri idan Ya Afzal ya dawo kice d'azu ma kin ganta ita kad'ai tana suratai."

"Toh Aunty" da haka sukayi sallama. Wani irin dad'i maras misaltuwa Nazeefah taji burinta ya cika ta haukatar da Amal ta sa Afzal ya daina cin girkinta, ita taso ace ta6in hankali ma Afzal ya soma zarginta da shi bama aljanu ba yadda za a d'auketa akaita chaan asibitin mahaukata ta fara rayuwarta ta bar mata Afzal nata amma hakan ma be 6aci ba.

****
Da Azahar Afzal ya wuce restaurant yaci abinci daga chan ya biya gida gun Ummi kallo d'aya tayi masa ta gano akwai matsala.

"Prince?"

"Ummi" ya amsa a ksalance.

"Meke faruwa?" ta tambayesa.

"Ummi it's Amal."

"Subhanallah lafiya dai ko?"

"Ummi I don't know na rasa gane ta6in hankali ne yake neman kamata ko kuwa aljanu ne suke mata wasa da hankali."

"Subhanallahi meya faru? Wani abun tayi ne?" Labarin komi ya kwashe ya bata batare da ya skipping komai ba.

"Shine baka ta6a bud'an baki ka fad'a mun ba Prince? Allah sarki Amal gata mahadacciyar Qur'ani oh! kowa da tasa jarabawan amma anya kuwa aljanu ne? Ba ta6in hankali ba?"

"Ummi I don't know I'm totally clueless kuka take yau seta yimun breakfast amma na hanata saboda ko tayi ba iya chi zan ba banda gishiri da borkono ba abinda yake cikin girkinta yanzu."

"Kuma ba ita take sawa ba?"

"Gashi na tambayi Safiyya tace a gabanta Amal tayi girkin bata sa gishiri ba shiyasa nake zaton ko aljanu ne."

"Kuma gashi yarinyan tace tana ganinta tana magana ita d'ai?"

"Har sau biyu ma tace."

"Ikon Allah kode aljanun ne toh?"

"Shine nima ban sani ba mu fara kaita psychiatric hospital (asibitin mahaukata) ne su duba ta ko mu fara dana gargajiyan?"

"Toh nide gani nake kaman aljanu ne amma a fara kaita asibitin idan sun kasa gane kan abun se mu dawo na gargajiyan, akwai sanannen malamin dana sani yana ruk'iya sosai zan nemesa."

"Toh yanzu ya zan fara sanar da ita zan kaita asibitin mahaukata Ummi? Wallahi bazata amince ba bayan nan kuma gani zatayi kaman naci amanarta ne ina danganta mata ciwon hauka kuma bana son su Mami suji maganan nan se idan abu ya gagara tukun zamu sanar dasu ko ba haka ba?"

"Tabbas kayi tunani Prince tunda de yanzu Amal responsibility'n muce."

"Toh kinga..."

"Ka san yadda zaka sanar da ita Prince ai matarka ce zata fahimce ka in shaa Allahu."

"Toh Ummi I'll try, please karki manta kiyi wa Malamin magana."

"In shaa Allah Prince kuma duk abinda akwai ka kira ka sanar dani Allah ya bata lafiya."

"Ameen bari zan koma" rakiya tayi masa sannan ta dawo ciki. Yana isa gida Safiyya tayi mishi sannu da zuwa sannan ya k'arisa d'aki inda Amal ke mik'e akan gado amma ba bacci take ba ko da taji shigowansa bata juya ta kallesa ba Sallama yayi ta amsa ciki-ciki ba tare da ta kewayo ba. Kayan jikinsa ya rage sannan ya k'arisa gefen gadon ya zauna a gefenta.

"Kitten?" Ya kirata sede bata amsa ba. "I called you twice baki d'aga ba why?"

"Ban san inda na jefar da wayan ba" ta amsa ba tare da ta kallesa ba. Hannu ya mik'a ya mik'ar da ita zaune "How're you feeling?" Ya tambayeta.

"Kaci abinci?" Ta mayar masa tunanin da take tayi tun d'azu kenan, shin yaci abinci, mey yaci? Ya k'oshi? It pains her alot idan ta tuna Afzal baze sake cin girkinta ba yanzu, sosai zuciyarta keyi mata k'ona.
Allah sarki sosai ta basa tausayi, bata ma damu da lafiyarta ba, ita burinta kawai taji yaci abinci ne, "Kefa kin ci?" Ya tambayeta.

"Yaya I really want to cook for you koda sau d'aya ne ka barni in sake yi maka girki please Yaya I miss feeding you" ta rok'esa yayin da idanunta suka shiga cikowa da hawaye.

"Kitten please cut it out, kibar kukan haka."

"Then allow me cook for you and feed you one last time."

"Baby" ya ambaci sunanta had'e da rik'o hannunta cikin nasa yana murzawa a hankali "Ba kida lafiya ki bari se in kin samu sauk'i kinji? I myself miss your cooking kinsan kece best cook d'ina ko?"

"Yaya can't you see? I'm perfectly okay wallahi lafiyata k'alau ba abinda yake damu na" kwantar da ita yayi a jikinsa yana shafa bayanta a hankali "Zamu kaiki asibiti gobe su duba ki in shaa Allah idan kika samu sauk'i se kiyi resuming normal duties naki ki cigaba da yimun girki kinji?" cike da rashin fahimta ta d'ago kanta tana kallonsa "Asibiti Habib Albi?"

"Kitten I'm so sorry-"

"No" ta furta cike da tashin hankali tare da janye jikinta daga nasa.

"Kitten please understand me-"

"No Yaya" da sauri ta janye hannunta da yake k'ok'arin rik'ewa "Mey kake nufi da hakan? Ina da hauka?" Ta tambayesa cike da d'umbun mamaki.

"No Kitten ba haka nake nufi ba" ya amsa a rud'e shima, a rayuwa ba abinda yafi tayar masa da hankali kaman yaga Amal tana kuka, da zaran yace ze rik'e hannunta se ta ja da baya.

"Ni Mahaukaciya?" Ta ambata da mamaki yayinda hawaye ke bin k'uncinta.
"Kallon mahaukaciya kake mun Yaya?"

"Kitten please-"

"Yaya.." kasa cewa komi tayi kawai ta rushe da wani irin masifaffen kuka yayinda ta mik'e da hanzari dan bar mai d'akin. Hannunta ya cafko ya kwantar da ita a jikinsa had'e da matse ta gagam wane wani na shirin k'watar masa ita. Kokowa take sosai ya saketa amma yak'i hak'uri ya ta bata yana shafa bayanta a hankali har seda ya sauk'ar da temper'nta. A hankali ya d'agota yana share mata hawayen nata "Kitten please understand me bawai cewa nayi kina da hauka ba, bazan ta6a kwatanta ki da mahaukaciya ba but contrary to abubuwan da suke faruwa bakiya tunanin ko akwai wata matsala?"

"Yaya ashe Allah ze kawo ranan da zaka yi mun kallon mahaukaciya?" Ta tambayesa hawaye na bin k'uncinta.

"Kitten I will never refer to you as that kema kin sani I love you and I only want the best for you, dan za ki ga psychiatrist doctor (likitan mahaukata) bawai hakan na nufin kinada hauka bane, ze iya yuwuwa wani matsalan ne daban yake damun ki psychologically ko stress ko makamancin hakan."

"There is no stress Yaya and I'm not losing my mind ni ba mahaukaciya bace kana tsammanin zansa gishiri acikin girki ba tare da na san nayi hakan bane? I told you ni bani kesa gishiri da attarugu ba, ba ni bace!" Sosai ranta ya 6aci taya upon all people Afzal baze yarda da ita ba? Taya za'a ce mijinta tilo yana yi mata kallon mak'aryaciya kuma mahaukaciya? Cikin tsananin kuka tace, "I thought you love me Yaya, I thought you trust and believe in me."

"Of course I do Darling, I love you with every burning fiber in my soul and I do trust and believe in you than I do myself."

"No Yaya inda har kana nufin abinda ka fad'a da baza ka fara tunanin kaini gun likitan mahaukata ba, da zaka yarda dani idan nace maka bani kesa gishiri da borkono cikin girkin ka ba."

"I know Kitten nasan ba ke kike sawa ba shiyasa na fara zargin ko aljanu ne suke miki wasa da hankali."

"Aljanu? Yanzu kuma mey kallon iskokai kake mun Yaya? Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" juyawa tayi da niyyan bar mai d'akin bata ma jin zata iya yi masa magana. Da sauri ya sha gabanta "Kitten please ki fahimceni ki sani lafiya nake nema miki wallahi na gaji da ganinki haka cikin k'unci da kuka kullum, kiyi hak'uri ki bari a magance miki wannan matsala please."

"Ni bana tattare da aljanu I know how I feel saboda haka ba wanda zeyi mun ruk'iya, nasan kaina kuma na dogara da addu'o'in da nakeyi."

"Kitten bawai ina jayayya da hakan bane ni kaina sheda ne game da yadda bakiya wasa da addu'o'in kariyan nan I'm aware of everything."

"Toh mey kake nufi Yaya? Kallon mey iskokai da ta6in hankali fa kake mun how do you expect me to feel and react?"

"Darling I'm sorry but I'm just worried, ke da bakinki kika ce bake ke sa gishiri da borkonon nan ba kuma na amince da hakan I trust you Kitten amma toh wa yake sawa? Bakiya tunanin akwai wata 6oyayyan al'amari? Kuma baza mu ta6a iya gano inda matsalar take ba bale a magance miki se har idan kin amince kin bada had'in kai Kitten. I promise no harm will come to you, I've got you Baby, ba wanda yace kina da ta6in hankali I just need to find out what's really going on. Please calm down everything is going to be alright in shaa Allah okay?" Ya k'are yana matso da ita kusa da shi. Cike da dabara ya kwantar da kanta a k'irjinsa yana shafa kanta "I love you
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment