Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya ajiye a gefen gadon "Dama nace bari in duba ki a hanzarce kafin in wuce sekuma na tarar kina sallah shine nace bari in ajiye miki kawai tunda ba abu bane mey yawa."

"Allah sarki Baba baka gajiya damun d'awainiya haka? Naga kayaki da dama d'azu nagode Allah saka da alkhairi" dukda cewan bey fahimci wani kayakin take nufi ba se kawai ya amsa "Ameen 'yata ba komai Allah k'ara sauk'i ina fatan jikin naki da sauk'i?"

"Alhamdulillah Baba ina samun kulawa sosai."

"Toh madallah barin koma ina da gun zuwa."

"Allah sarki nagode sosai Allah ya saka da alkhairi gashi kazo yau ma iyayena basu nan suna ta son suyi maka godiya."

"Ba komai kice musu kar su damu, toh na wuce se na sake zagayowa." Nan yayi mata sallama ya fito. A gurguje suka bar asibitin gudun kar su had'u da Mami ko Papi. Wani private clinic suka nufa inda ya sanya gashin kan Amal acikin wata farar leda sannan shima ya tsinke kad'an daga cikin na gemunsa ya sanya a leda daban ya mik'a wa driver'nsa tare da yi masa kwatancan likitan da yake son ya kai masa.

"Har ka kai masa?"

"Eh Alhj yace results ze fito nan da kwana uku."

"Toh madallah se mu wuce office ko? Ina da appointment da wasu."

***
Da yamma Daddy ya dawo gida sede har anan beji labarin an sako Nazeefah ba wayan Afzal ya kira inda yaji switched off dama da gan-gan Afzal ya kashe wayan nasa sanin Daddy ze nemesa da misalin k'arfe shida sabon layi ya kira Mummy tana d'agawa taji muryan Nazeefah.

"Mummy dan Allah ku taimaka mun Mummy bana son in sake kwana anan dan Allah kuyi hak'uri."

"Ba daga mu bane Nazeefah Daddy'nki yayi wa Abban Afzal magana shima yace zeyi wa Afzal d'in magana amma shiru har yanzu an kira Afzal d'in ma layinsa a kashe."

"Innalillahi dan Allah ku kira Abbansa please help me out Mummy."

"Naji Nazeefah ki k'ara hak'uri" anan ta katse wayan.

"Alhj ko zaka kira Alhj Amin d'inne kaji daga bakinsa?"

"Kar yaga kaman mun tak'ura masa Hjy Surayya."

"Amma ai ze iya yiwuwa ya mance beyi ma Afzal maganan ba."

"Da wuya mu jira de zuwa gobe."

"Yanzu a cell d'in Nazeefah zata sake kwana kenan?"

"Toh ya muka iya Hjy Surayya?"

"Wallahi Nazeefah ta cuci kanta duk mey hali irin nata yana tattare da asara."

***
Rok'an alfarma Nazeefah ta sakeyi gun securities d'in akan a sake ara mata waya ta kira Afzal sede wayan nasa a kashe, private numbernsa ta kira nan ya shiga a karo na biyu ya d'aga.
"Halo?" Ya soma da cewa.

"Ya Afzal" ta kira sunansa.

"Nazeefah?" Take ya gano muryarta.

"Ya Afzal I'm sorr-" katse wayan yayi nan take ta sake kira haka yana gani yak'i d'agawa daga k'arshe ma kashe wayan yayi gabad'aya. Kwana Nazeefah tayi tana kuka ranan yayinda take nadaman biyewa Rumaysa da tayi. Washegari Afzal yayi resuming office, wajajen k'arfe tara Daddy ya sake gwada layin Afzal se gashi ya shiga, sede har ya tsinke Afzal be d'aga ba instead seya tura masa sak'o akan cewa wai yana meeting ne idan ya fito ze biya police station d'in ayi releasing Amal.

Da misalin k'arfe sha biyu da rabi Afzal ya wuce TH dan duban Amal sede yau ma nurse d'in tak'i barinsa ya shiga, rok'anta yatayi kaman ba gobe har seda ya samu ya shawo kanta.
"Naji zan yi maka hanya ka shiga amma daga yau se yau."

"Thank you so much I couldn't ask for more ita kad'ai ce aciki?"

"Eh d'azun mahaifiyarta ta fice."

"Papi fah?"

"Shi tun safe yazo ya lek'a su ya koma dama shi ba a nan yake kwana ba."

"Okay."

"Muje in kai ka" bayanta yabi ta kaisa d'akin Amal. "Seka yi sauri" kai ya gyad'a mata yayinda ta juya ta fice. A hankali ya bud'e k'ofan yana lek'an ciki, akan gado ya tarar da Amal tana kwance, ciki ya k'arisa ya maida k'ofan inda ya tabbatar da bacci takeyi. Kujera yaja ya zauna a gefenta yayinda hawaye ya ciko masa a ido he can't believe yau kwana uku kenan be sanya ta a ido ba. Hannunta ya d'aga ya sa acikin nasa yana murzawa a hankali "I'm so sorry Amal, I'm terribly sorry" ya shiga bata hak'uri har anan baccinta take ba makawa. Strands na gashin da ya fad'o mata akan fuska ya shiga miyar dasu cikin hulan dake kanta sannan ya soma shafa fuskan nata a hankali yayinda gobaran sonta da tausayi yake ruruwa acikin zuciyarsa. A hankali ya sauk'e hannunsa akan cikinta yana feeling presence na baby'nsa. Gani yake kaman a mafarki, wai Amal na d'auke da cikinsa, oh he can't ask for more.

Ya kai kusan minti goma zaune akanta yana kallonta da hannunsa manne akan cikinta har anan. Cikin bacci Amal ta d'an motsa hannunta dake kan gado ta d'aga dan ajiyewa akan cikinta inda ya sauk'a akan hannun Afzal. Gagam ta rik'e hannunsa yayin da ta cigaba da baccinta minti biyar a gaba Afzal yayi tunanin komawa gudun kar Mami ko Papi suzo su iskesa. Hannun nasa ya shiga janyewa amma ya kasa dan yadda Amal ta k'ank'amesa. Gashi baya son ya tayar da ita, ya zeyi? Hannun nasa ya cigaba da k'ok'arin cirewa amma ya kasa wanda daga k'arshe seda Amal d'in ta farka. A hankali take bud'e idanunta har ta sauk'e su akansa ba k'aramin razana tayi ba ganinsa da tayi akanta. Kad'an ya rage bata sa ihu ba, shin har ya akayi ya shigo ciki? Ta d'au nan restricted area ne se idan an san da zuwan mutum ake barinsa ya shiga how comes toh?

"Amal" ya kira sunanta a hankali cikin wani irin salo hannun nasa ta sake da wuri ta shiga kalle-kalle cikin d'akin tana neman Mami.

"My adorable Kitten" yake sake kiranta lokacin da ta kawar da kanta gabad'aya daga kallonsa. "Amal please turn around and look at me" saidai kaman ba da ita yake ba.
"Amal I'm terribly sorry, please forgive me for doubting on your faithfulness, I've realized the truth nagane Nazeefah da Safiyya ne ke bayan komai dan Allah kiyi hak'uri maganan da nake miki yanzu haka na mik'a su ga hukuma a hukunta munsu, I can never forgive them for what they did to you, yau kwanansu biyu kenan a cell." Mamaki sosai kalamunsa suka sanyata, akanta har ya kaisu police station? Sede tayi shiru bata ce dashi komai ba.

"Amal I felt horrible when I found out Nazeefah ce tasa aka kad'eki however I'm grateful for the fact that you still chose to be alive and didn't leave me all by myself. Bazan iya rayuwa ba ke ba Amal, kinfi kowa sanin hakan, you're my necessity and everything I need to complete my life please don't leave me" hannunsa ya d'au ya ajiye akan cikinta hakan ne kawai yake tunanin ze sata yin magana ai kuwa ba shiri ta cire "Don't you ever touch me Yaya" ta sanar da shi ba tare da ta juyo ta kallesa ba.

"Thank you for speaking to me Kitten, at least yau zan iya bacci tunda na saurari muryanki thank you so much" nan ma shiru tayi masa "Baby why didn't you tell me? Meyasa baki fad'a mun kina da ciki ba?" Mamakin yadda akayi ya gano tana da ciki take, waya sani ko nurses d'in ya tambaya suka sanar da shi.

"Kitten gani kike kaman in kin fad'a mun zanyi denying baby'n ince ba nawa bane? Amal I've never and will never accuse you of cheating on me, I know who you're nasan bazaki ta6a cin amanata ba kuma koda nace miki ban yafe ba idan kika sake shigo mun da maza cikin gida bawai ina nufin wani abu bane course mates naki nake nufi kuma Wallahi ni ban san shirin yaji kikeyi ba da na baki hak'uri na hanaki, senayi tunanin ko so kike ki tare zuwa d'ayan d'akin gabad'aya ban san lokacinda kika tafi ba se washegari dana lek'a d'akinki naga bakiya nan."
So take ta ce masa meyasa be kirata ba toh bayan da yaga bata nan d'in se taga kuma ba amfani tunda ba komawa agaresa zatayi ba.

"I got so mad shiyasa ban kiraki naji daga gareki ba amma bawai hakan na nufin bana sonki bane ko kuwa nayi hakan dan in nuna isa ko dan in walak'antaki ba, Amal sanin kanki ne bazan ta6a yi miki haka ba, I love and respect you alot please come back to me abinda ya faru ya riga ya faru nasan ni mey laifi ne, nasan nayi kuskure, na san ban kyauta miki ba na k'in miki uzuri da nayi da kuma k'in baki dama kiyi bayanin kanki Wallahi duk sharrin Nazeefah ne, she manipulated me please forgive me Amal Yaya is so sorry."





RANA D'AYA!
#RD

Love... King Miemiebee👄✨




Miemiebee Novels

Saturday, 18 August 2018
RANA D'AYA!
BY MIEMIEBEE
PAGE 38




"Amal why aren't you saying anything?" Ya tambayeta a maraice bayan dogon shirun da tayi, shirunta a garesa ba k'aramin tashin hankali bane but he really can't force it ya zama masa dole ya hak'ura ya bata space da take buk'ata har izuwa lokacin da za ta huce.
Tabbas mutum ya guji fushin mey hak'uri koda wasa be ta6a tsammanin Amal zatayi masa fushi haka ba saidai bai ga laifinta ba ko d'aya saboda shi ya turata har bango, idan da wata ce da tun ranan da ya korata daga d'akinsu zatayi mai fushi amma dukda hakan bata fasa yi masa ladabi ba, he's sure with time she'll come by.

Envelope da ya tanadar mata ya zare daga aljihunsa ya ajiye mata a kan gadon daga gefenta sannan ya mik'e "I have to go now, Allah k'ara miki lafiya I can't wait to see you back on your feet I love you so much my adorable Kitten" badan yana so ba ya mik'e ya fice juyawanda Amal zatayi hawaye ya tsiyaya daga d'ayan idonta. Tabbas har yanzu tana son Yaya amma idan ta tuna da abinda yayi mata se taji gabad'aya ya fita mata a rai, she never wished for things to turn out bad between them two like this, amma ya ta iya? She can't change the past only can she make the future better. Gyara kwanciyanta da tace zatayi taji k'aran paper, a hankali ta miyar da idonta wajen nan taga envelope da ya ajiye mata da hannunta d'aya ta d'aga ta zazzage inda ta tarar da kud'i da dama aciki, sabin dubu d'ai-d'ai. Da hannunta d'aya ta irga taga dubu ashirin ne sannan ta miyar ta ajiye a gefe.

***
Koda Afzal ya shiga cikin mota ya kasa kunna engine d'in, be hankara ba kawai yaji hawaye na tsiyaya masa daga ido yau ina ze sa kansa? Ya ze rayu idan ba Amal a kusa da shi? Gani yake idan har bata dawo a garesa ba ze mutu saboda zuciyarsa bazata iya jure rashinta a kusa da shi ba da k'yar ya iya kunna motan ya koma office. Hud'u nayi ya tashi. Gabad'aya ya mance da labarin Hindu se yanzu ta fad'o masa a rai, gidan Nazeefah ya biya inda ya sameta kwance a d'akinta tana bacci, tashinta yayi sannan ya kira driver'n Amal da ya kaita gida bayan sallamarta da yayi. Tana isa gida Ummansu ta rungumeta tana kuka tun jiya take kuka har zuwa d'azu da taje ta duba Safiyya. Dama tun farko ita bata goyi bayan kawosu birni ba dan gudun sharri irin wannan.

Se k'arfe shida Afzal ya wuce police station d'in yayi magana akayi releasing nasu Nazeefah. Da gudu ta fito ta fad'a jikinsa tana kuka "Ya Afzal dan Allah kayi hak'uri ka yafe mun na tuba bazan sake ba" hannunsa yasa ya janyeta "Don't misinterprete my intention, ba wai don ina so nasa akayi setting naki free ba Nazeefah se don Abba ne ya buk'aci hakan, idan da ta ni ne da se kotu ta yanke miki hukuncin da yake dai-dai da laifin da kika aikata sannan zanji dad'i because I want you to change, canji na tsakani da Allah bana muzurun da nake da tabbacin kikayi ba. Bazan 6oye miki ba Nazeefah, da abinda kikayi kinsa na tsaneki kaman yadda Amal ta tsaneni yanzu, ko k'aunan gani na Amal bata so a haka kike cewa kina sona? A tunani na idan kana son mutum har abinda yake so zaka so, kin san ina son Amal but you still went ahead and hurt her I'm still mad at you Nazeefah I might forgive you someday amma bazan ta6a mancewa da abinda kikayi wa Amal d'ita ba let's go home." Driver'n Amal ya kira yazo ya d'auki Safiyya itama kud'in sallamarta yabata sannan ya buk'aceta da idan ta isa gida ta tattare ina-inata tabar masa gida yayinda shi da Nazeefah suka koma nasu gidan suma.

Babban akwatinta ya d'auko mata "Here start packing your clothes ki bar min gida bana k'aunan ganinki anan Nazeefah as long as kika cigaba da zama anan zakina sani tunawa da munanan abubuwan da kika rink'ayi wa Amal d'ita wanda hakan ze sa in sake tsanar kine kawai so its better ki koma gida gun su Mummy." Kuka take sosai ta k'arisa inda yake tsaye had'e da sauk'a k'asa akan guiwarta "Ya Afzal dan Allah karka mun haka, dan Allah don't send me home I'm terribly sorry please forgive me wallahi na tuba bazan k'ara ba dan Allah kar ka sakeni Ya Afzal bazan iya rayuwa ba kai ba please don't divorce me" ta k'arisa cikin tsananin kuka. Hannu yasa ya d'agata "Bazan sake kiba Nazeefah saboda despite everything I still love you and I cherish the moments we spent together, I just need some space and alone time anytime I'm ready zan dawo dake but you really have to go now." Rungumesa tayi tana kukan cire rai "Please don't send me away Ya Afzal I can't live without you dan Allah kayi hak'uri ka yafemun please don't send me home I'm so sorry" kuka ta cigaba dayi ajikinsa na sosai ta basa tausayi shima bawai dan yana so ze korata gida ba dan kawai bayida wani option ne saboda zamanta acikin gidan nan kawai sake sanyasa tsananta zeyi shi kuma baya son hakan saboda idan ya tsani abu ya tsanesa kenan no turbing back, so it's better ta tafi gida kawai. A hankali ya sauk'e hannayensa a bayanta hugging her back sun d'au tsawon lokaci a haka sannan ya janyeta na k'arfi dan yadda ta kankamesa kuka take sosai tana kad'a masa kai "Please don't do this Ya Afzal please don't."

"I'm so sorry Nazeefah I'm really sorry I wish there's something I could do you have the next one hour to pack your belongings zan sa driver'n Amal yayi dropping naki a gida" yana kaiwa nan ya juya. Ihu Nazeefah ta k'urma tana kuka tana kiran sunansa amma ko waiwayawa beyi ba ya fice rushewa tayi a wajen tana kukan tsuma zuciya yau ina zata sa kanta? Ya zatayi da ranta? Ya zatayi da masifaffen son Afzal dake cikin zuciyarta? Bazata iya rayuwa ba shi ba, da ta rasa sa gara ta rasa rayuwarta gabad'aya, soyayyan sa ya riga ya zame mata jinin jiki, idan ba shi baza ta iya rayuwa ba. Tafi minti goma a wajen tana kuka sannan da k'yar ta iya lalla6awa ta k'arisa wajen wardrobe nata yayin da ta shiga tattare kayakin nata, tana yi tana kuka haka har ta samu ta gama tattare kayakin nata ta ja akwatin ta rufe sannan ta fito da akwatin parlour ganin ba Afzal a gurin se ta k'arisa waje nan ma bata gansa ba ashe acikin motansa ya 6oye yana kallonta daga mirror. Waya yayi wa driver'n Amal nan ya k'ariso ya ja mata akwatin nata cikin mota se kewaye take tana nemansa amma ko alamansa babu ga kuma motansa na nan a fake, haka ba don tana so ba ta k'arisa motan ta shiga har driver ya kaita gida tana aikin kuka. Ba k'aramin hamdala su Mummy sukayi ba ganinta ta dawo gida, text Daddy ya turawa Afzal yana yi masa godiya, kwana ranan Nazeefah tayi musu tana kuka, kukan zafin rabuwa da Afzal shima Afzal har hawaye seda ya zubar bayan tafiyan ta, yana sonta amma baze iya cigaba da zama da ita muddin Amal bata dawo a garesa ba toh baze iya dawo da Nazeefah ba, wannan haka take.

****
GIDAN ALHJ AMIN

Seda Ummi ta jira Abba ya gama cin abincinsa sannan tayi gyaran murya. "Alhj?" Ta kira sa.

"Yes My dear?" ya amsa had'e da d'ago kai yana kallonta.

"Dama wata magana nake son yi maka amma sena ga jiya kaman a gaje ka dawo yau kuma throughout baka yini a gida ba."

"I'm sorry schedule d'ina ne kwana biyun nan is so tight se a hankali."

"Ba komai dear Allah taimaka ya k'ara arziki da bud'i."

"Ameen Hjy Mairama ta so what is it you wanted to discuss?"

"Batun Prince ne dama."

"What about him?"

"Amal tayi masa yaji" bata tsaya yin corner-corner ba ta sanar da shi gaskiya kai tsaye.

"What?!"

"Amal tayi masa yaji yau kwana hud'u kenan."

"Kina nufin har mukaje muka gaisheta dama ba a gidansa take ba?"

"I'm sorry but yes."

"Kuma kin sani?"

"Dear I'm sorry."

"Meyasa baki fad'a mun ba?"

"Alhj ina gudun fushin da zakayi masa ne already matsaloli sunyi masa yawa kaga idan kaima ka k'ara da naka abun zeyi masa yawa."

"Wow! Meya faru har tayi masa yajin? Batun abinda Nazeefah tayi ne?" K'arya taso yi masa tace eh amma tuna idan aka je yin sulhu gaskiya na iya fitowa taji kunya se kawai ta fasa ta irga masa gaskiyan al'amarin.

"Afzal d'in?" Ya tambaya da mamaki shi kam da ba a bakin Ummi yake jin labarin ba se yace sharri akeyi wa d'ansa.

"Unfortunately abinda ya faru kenan amma yayi nadama yanzu wallahi Alhj dan kad'an ya rage beyi kuka ba da yake ban labari kayi hak'uri kayi masa uzuri sharrin shaid'an."

"Nadama? Bega komi ba tukuna kuma ki daina kawo zancen sharrin shaid'an wannan ganganci ne da rashin mutunci da kuma rashin tunani da rashin aiki da hankali a fili har 'yar yarinyar nan ne zeyi zarginta? Mey ta sani?"

"Alhj yace shifa ba zarginta yake ba."

"Maganan banza amma ai abinda ya nuna mata kenan kuma abinda zata fad'awa iyayenta kenan."

"Alhj kayi hak'uri tabbas Prince yayi kuskure amma baza mu iya canza hakan ba kayi hak'uri a had'a kai ayi masa bikon yarinyar nan yaso yayi hakan da kansa amma abun ya gagara ko ganin Amal iyayenta sun hanasa yi wallahi yaron nan na cikin tsaka mey wuya ace cikin matansa biyu ba ko d'aya a wajensa."

"Ai daidansa kenan ko nine bazan barsa ya shiga yaga min 'ya ba tunda ya walak'anta ta haka, iyayen Amal sunyi mun dai-dai ko a babu yanzu ze san matsayinta, ma wannan wani irin rashin hankali ne? Wallahi wasu abubuwan in ance min Prince ya aikata se inga kaman sharri ake yi mishi ban ta6a sanin sa da wannan banzan hali da rashin wayo ba."

"Alhj kayi hak'uri ze gyara."

"Kibar 6ata miyan bakinki kina bani hak'uri Hjy Mariam ba dani za'ayi abin kunyan nan ba in kinga na taka k'afa gidansu yarinyar nan toh takardan sakinta na kai mata dan nasan koba jimawa da dad'ewa iyayenta zasu nemi a kai musu takardan 'yarsu bayan nan ba abinda ze kaini gidansu, rashin hankalin Afzal ya isheni haka."

"Alhj dan Allah kar kace haka kafi kowa sanin ciwon Afzal, kafi kowa sanin raunin zuciyarsa da kuma abinda rashin yarinyar nan a kusa dashi ze haifar, ina fatan baka mance da abinda likitansa yace ba."

"Ai idan ma mutuwa yayi shi ya siya mutuwan nasa da kansa kawai dan yarinya na da hak'uri shikenan seya walak'anta ta? A idonsa yarinya ta tattare kayakinta amma dan gadara yak'i koda yi mata magana bale yayi tunanin hanata? A ina aka ta6ayin haka? Saboda yana ganin gidansa yafi gidan iyeyenta gata ko mey? Sannan kuma dan rashin kunya da rainin wayo yace wai bey d'au shirin yaji take ba? Kinga I've had a stressful day I'm very tired in kina da niyyan kwanciya bismillah in kuwa a'a ni seda safe."

"Alhj please kar kayi haka wallahi mune da asara idan muka rasa Afzal kaman yadda Daddy'n Nazeefah yace hannun mutum baya ri6ewa ya yasar toh muma fa hakane komin yaya baza mu k'i Afzal ba kuma kaima fad'a kawai kake wallahi baka gansa kwance akan gadona asibiti bane fighting for his life" ko amsata beyi ba ya k'arisa d'aki abinsa ba tare da ya kewaya ba. Ita kanta bawai taji dad'in abinda Afzal yayi bane kokuwa tana goye masa baya kawai gudun halin da yake iya fad'awa ne idan ba a dawo masa da Amal a garesa ba sanin raunin zuciyarsa. Bazata gaji da basa hak'uri ba tasan zuciyansa yana da saurin fushi amma kuma hak'uri kad'an aka basa ze sauk'o.


***. ****. *****. *****
Kaman yadda likita ya d'au alk'awari bayan kwana uku ya tanadar da results na Daddy. Da yammacin ranan yaje ya amsa da kansa ko da driver be nema ya rakasa ba. Ba k'aramin tsinkewa gabansa yayi ba bayan da ya karance results d'in yaga komi positive yake nunawa, ma'ana Amal 'yarsa ce kad'an ya rage beci tuntu6e ba dan yadda ya razana se hailala yake yana maimaita innalillahi wa inna ilaihi raji'un.

Yanzu Amal 'yarsa ce? Ashe ciki ya shiga jikin Jameensa bayan abinda ya faru a tsakaninsu, yau ina zesa kansa? Ta ina ze fara sanar da mutane wannan badak'ala? Wai wannan a duniya ma kenan Allah yake neman tozarta sa haka ina kuma ace a lahira? Wannan wace irin k'addara ce taya yaransa biyu zasu auri miji d'aya? Shin haka Allah yake kama duk wanda ya d'au alhak'in wani? Shin haka duk wanda ya aikata aikin banza yake fara ganin sakamako tun anan duniya ba ma se anje lahira ba? Shin ashe komin yaya mutum yaso 6oye laifi ko zunubi ta inda baya tsammani Allah ze tozarta sa a idon jama'a? Yau yana cikin wani yanayi ta ina ze fara sanar da Amal shine mahaifinta? Ta ina ze fara sanar da Hjy Surayyarsa yana da shegiya a waje? Ta ina ze fara sanar da Nazeefah Amal 'yar uwarta ce? Da wani ido yaransa zasu sake kallonsa? Da wani ido amininsa da kuma manyan abokansa zasu sake kallonsa harma da 'yan unguwa da masu aiki a k'ark'ashinsa? Shikenan k'wan da ya jima yana gudun fashewansa ya tsage yanzu k'iris ya rage kuma ya fashe ya zube. Kansa ne ya mugun d'aurewa gabad'aya ya rasa mey ke masa dad'i. Allah ne de kawai ya kaisa gida ranan saboda yadda ba hankali a jikinsa yake tuk'i tunda ya isa gida ya rufe kansa a d'aki yayi k'aryan migraine ne ke damunsa baya son a tak'ura mishi, tunanin ta inda ze fara 6ullowa al'amarin nan yake amma ya kasa tabbas acikin yaransa biyu dole se d'aya ta zama bazawara dan bazeyi Afzal ya cigaba da zaman aure da dukansu biyu ba tunda jini d'aya suke. Annabi beyi k'arya ba da yace idan kayi me kyau me kyau ze bika idan kuwa kayi na banza na banzan
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment