Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

Ajiyar zuciya Mummy ta sauk'e dama tasan za'ayi haka. Dama tasan Nazeefah ce Afzal ze saka kawai bata so ta nuna mata bane don kar ta tayar mata da hanaki amma tasan haka za'ayi dama kodan ma Allah ya kama Daddy yasa shima yaji zafin da mahaifiyar Amal taji sanda yayi mata fyad'e. Tasani dole ne wannan k'addara ya fad'a akan Nazeefah saboda itama Amal ta samu farin ciki koda sau d'aya ne a rayuwarta. Idan harda ace wannan saki akan Amal ya fad'a da Daddy baze ji zafi kaman yadda ace zeji yanzu da ya fad'a akan Nazeefah. Ta hakan ne kawai Allah ze sanyasa gir6e abinda ya shuk'a, ta hanyar mayar masa da 'ya bazawara kaman yadda ya k'wace wa 'yar mutane budurci.

"Shikenan ka huta ai yanzu Alhj, amma kasani nida 'ya'yana bazamu ta6a yafe maka wannan abun kunya daka aikata ba." Be bari ta shiga takawa ba yayi sauri ya rik'e k'asan hijabinta "Hjy Surayya bazan ma fara tambayan gafararki ba saboda nasan abinda nayi miki da 'ya'yanki is unforgivable but atleast give me a chance to apologize and tell you sorry. I'm gravely sorry for hiding the truth away from you, wallahi bawai don bana sonki bane kokuwa don bana mutuntaki yasa na 6oye miki wannan al'amari, sonki da nakeyi ne ya rufe min ido, bana son abinda ze shiga tsakani na dake Hjy Surayya, bana son in rasa ki. Dan son zuciya irin nawa se naga idan har na sanar dake gaskiya zaki gujeni kik'i aurena shiyasa na rik'e komai wa kaina. I love you so much Hjy Surayya and I'll never stop loving you, I'll wait. Zan jiraki koda kuwa zuwa k'arshen rayuwana ne amma bazan gaji da baki hak'uri ba dan Allah kiyi hak'uri ku dawo gida."

"Babu wani abinda zaka sake fad'amun da zaisa in canza ra'ayina. Idan 'ya'yanka kake so kana iya shiga ciki yanzu ka ebosu amma nikam takarda na nikeso. Kaman yadda ka shiga tsakanin auren yaran nan kasa Afzal ya saki Nazeefah saki ba d'aya ba, ba biyu ba har uku nima haka nake so ka rubuta mun nawa. Idan har 'yata zata shiga k'uncin rayuwa ka tabbata kai m seka shiga ninki ba ninkin nata don haka ka rubuta min takarda na yanzun nan anan. Tunda rayuwan zawarci ka za6a wa 'yarka tayi nima mahaifiyarta shi zanyi."

"Dan Allah kiyi hak'uri Hjy Surayya nasan nayi miki laifi, laifi babba amma dan Allah kiyi hak'uri ki gafirceni. Idan kika tafi kika barni ya kikeson in rayu?"

"Bakayi tunanin hakan ba kafin ka danne 'yar mutane kayi mata fyad'e? Se kaje chan ku k'arasa da ita mahaifiyar Amal d'in that is idan har zata iya yafe ma zaluntar ta da kayi."

"Kema kinsan bazan iya rayuwa da kowa ba bayan ke Hjy Surayya, kinfi kowa sanin yadda nake sonki tun ba yau ba."

"Sam ba haka bane, I was a fool to believe you love me Alhj, yaci ace tun a lokacin chan na gane kud'in mahaifina kawai kake so ba ni ba. Wallahi Allah ne kad'ai ze sak'a mun. Duk kalan halaccin danayi maka na sa mahaifina yayi maka duk baka ga hakan ba you still chose to lie and cheat on me."

"Dan Allah kiyi hak'uri bazan ta6a gajiya da baki hak'uri ba saboda nasan ban kyuata ba amma wallahi I love you Hjy Surayya I really do."

"Shin anya ma kuwa labarin daka tsara min da iyayena na cewa kai maraya ne gaskiya ne kuwa? Shin anya kuwa ba k'arya ka shirya mana ba saboda ka samu kaci arzikin mahaifina Alhj?"

Shiru Daddy yayi gun ya kasa cewa komai. Tabbas yayi mata da mahaifinta daya kasance hanshak'in mai kud'i bahaushe daga Kano k'arya lokacinda yazo aurenta. Saboda gudun da yake kar a nemi iyayensa kowani d'an uwansa a garin hakan asirinsa ya tonu na cewa yayi ma wata fyad'e a k'auye Mummy ta fasa aurensa ko iyayenta su hanata. Tun bayan da abin ya faru ya samu ya dawo makaranta be sake d'aga wayan iyayensa ba, duk lokacinda yaga kiransu baya d'agawa har ta tsinke saboda yasan akan mey zasuyi masa magana shi kuwa bayida abin cewa. Daga k'arshe ma da yaga kiran ya soma isansa se kawai ya sauya lamban wayansa gabad'aya, tun daga nan be kuma sake ji daga garesu ba se...

"K'arya kayi mana ko? Why aren't you saying anything Alhj?"

"Hjy Surayya yes, yes nayi miki da Abba k'arya batun iyayena amma wallahi ba don bana respecting naki bane se don tsoro da nake kar a garin hakan gaskiya ya fito in rasaki."

"Wani gaskiya?" tayi saurin katsesa.

"Batun abinda ya faru tsakani na da mahaifiyar Amal."

"Wane irin mak'aryaci ne kai Alhj? Mey nayi maka a rayuwa da ka za6i ka gina duk wani abinda mukayi accomplishing tare akan k'arya?" Ta tambayesa hawaye na saurin ciko mata a ido. "All I did was to love you Alhj I'm so disappointed in you na tabbata da Abba yana raye a yau da shima baze ta6a yafe maka ba."

"I'm truly sorry Hjy Surayya amma abinda ya faru ya riga ya faru idan da zan iya mayar da lokaci baya da nayi dan in gyara komai amma bazan iya ba please give me a second chance idan kika tafi kika barni taya kikeson in rayu? Tabbas idan ba ke su Nazeefah bazasu amince su dawo gida a gareni ba please kiyi hak'uri."

"Bayan k'aryan nan se kuma wani k'arya ka sakeyi mun?"

"Hjy Surayya a shirye nake da in sanar dake duk wani abinda kike buk'atan ki sani amma zaki galabaita tsaye a nan saboda labarina nada tsawo kiyi hak'uri mu shiga mota kokuwa mu k'arisa cikin reception." Bata ce da shi komai ba kawai ta shiga takawa yayinda yake biye a bayanta, a VIP reception suka zauna sannan Daddy yayi gyaran murya ya soma kaman haka.

"A shekaran da na dawo hutun second year d'ina ne muka had'u da mahaifiyar Amal wato Jameela wacce nake kira da Jamee na. Jameela ta kasance itace mace ta farko da Allah ya fara sanya min soyayyarta a zuciya na, so kuma na aure bana lalata ba. We started off as friends amma cikin k'ank'anin lokaci soyayya mey k'arfi ya shiga tsakaninmu. Jameela was simply everything I could ever ask for, lokacin da muka fara soyayya kwata-kwata shekarunta goma sha shida ne, she was so beautiful, young and innocent. Tsaftacacciyar soyayya muka gudanar nida ita as ko zance naje wajenta iyaka muyi hira ba wani ta6e-ta6e bale makamancin hakan saboda Jameela yarinya ce kamila wacce take san addininta sosai take kuma k'ok'arin bin dokokin da ya kafa mata. Ahaka ne har nazo na koma makaranta wanda bada dad'ewa ba Jameela tayi mun waya cewa mahaifiyarta na shirin had'ata aure da d'an chairman na garinmu idan har ban hanzarta turo magabata na ba ana iya aura mata shi d'an chairman d'in. Hankalina ne ya matuk'an tashi se Allah-Allah nake session d'in ya k'are in dawo gida. Kasancewar a scholarship na samu karatun seya zammana banida gatan dawowa gida kowani hutu se shekara-shekara. Addu'a muka tsayar sosai nida Jameela cikin ikon Allah kuwa se har wata shekarar ta zagayo shi wannan yaro be turo ba. Na dawo bada dad'ewa ba na samu mahaifina nayi mishi maganan Jameela akan ina son a tura tambaya gidansu sede sam Abba yak'i amincewa akan cewa da baki na ne zan ajiye mata idan nayi aure yanzu ina karatu. Duk yadda naso fahimtar dashi cewa Jameela bata da matsala da hakan besides ma ina d'an yin business, makaranta kuma shekara d'aya ne ya rage sedai hakan ya gagara Abba yak'i ya amince ya bani goyin baya. A sanadin haka nida Jameela muka shiga tashin hankali sedai bamu cire rai ba, muka mik'a komai ga ubangiji. Ban san ya akayi ba de amma wataran mahaifiyar Jameela ta jiyota muna waya bayan kuma ita ta riga tayi mata miji a sanadin haka tayi ma Jameela duka tayi seizing wayarta sannan ta horeta da kada ta sake kulani. Kwana biyu na daina ji daga gun Jameela ko na kira layinta baya shiga gashi sun k'are makaranta lokacin bale inje mu had'u a chan d'in. Rana d'aya kawai na jajirce na jeni gidansu dan yadda shirun yayi yawa, dukda cewan ta haneni da taka bakin k'ofan gidnasu saboda yadda ta nuna mun mahaifiyarta bata sona. A farko da naje mahaifiyar ta kar6eni da fara'a kasancewar bata gane waye niba a lokacin da nayi mata bayanin kaina kawai ranta ya 6aci ta sauk'e duk wani haushin da takeji a kaina tayi mun koran kare harda muciyan tuwo ta bini waje. Hakan ba k'aramin 6ata mun rai yayi ba dan dole na hak'ura da Jameelah saboda a rayuwa na washi walak'anci na kuma d'au alwashin sena rama cin mutuncin nan da tayi mun ko ta yaya ne. Rana d'aya ina zaune kawai sega kiran Jameelah ban 6ata lokaci ba na d'aga inda take sanar dani tana son mu had'u. Chan na kaita bayan gari da siyasan cewa abu nake so in nuna mata, ina son Jameelah amma abinda mahaifiyarta tayi mun ya tsaya mun a wuya ko kallonta nayi se na tuna da abin. Haka kawai shaid'an ya soma raya mun in d'au fansa akanta sedai kuma sonta da nake yana rik'eni. Amma haka shaid'an ya rinjayi zuciyana ta hanyan raya mun ai tunda mahaifiyarta tana sonta idan na ta6a lafiyarta kaman na ta6a na mahaifiyar ne don haka idan na lalata mata rayuwa abun seya fi wa mahaifiyar zafi. Ana cikin haka ne sega abokai na guda biyu dana basu labarin abinda mahaifiyar Amal tayi mun nan suka sake k'arfafamun guiwa suka bani had'in kai nayi ma Jameela fyad'e ba tare da d'igon imani ba."

"Koda mahaifinta ya kai k'arana dana mahaifina gurin mey unguwa k'aryata komai nayi na samu abokaina suka rufa mun asiri shima Abba ya goya mun baya saboda baze ta6a kawowa a ransa zan iya aikata abinda nayi ba. Acikin satin ko na gaba na samu na koma makaranta ban sake ji daga garesu ba. A karon chan ne na had'u dake Surayya, kika yi mun erasing duk wani bad memory'n dana bari da a k'auyen Askira. Tunda na sameki komai ya canza Surayya, soyayyar da kika nuna min ta dabance. Banida komai, Baki sanni ba, baki san wani nawa ba amma kika so ni kika kuma amince dani regardless. Ko a mafarki ban ta6a tsammanin cewa wataran zan iya mallakan 'yar babbar gida kamar ki ba mey hankali da tausayi. Lokacin da kika ce mun muyi aure ne nashiga tashin hankali badon bana sonki ba se don banason hakan ya tono mun labarina dana bari a garin Askira. Ban san da wani idon zan sake kallon iyayena da na shafesu a doron k'asa saboda selfish interest d'ina ba na kusan shekara. Rud'ani na matuk'a na shiga yayin da na rasa ya zanyi gashi bana son in rasaki saboda da in rasa ki gara na rasa komi nawa koda kuwa raina ne. Don haka nayi miki da Abba k'aryan cewa ni maraya ne. A tunani na hakan ne kad'ai zaisa Abba ya amince ya aura min ke Surayya. Ba abinda Abba beyi mun ba bayan dana aureki, abinda ya kama kayan da zansa, gidan da zamu zauna, motan da zan hau harta sadakin ki shi ya biya mun, komai da na sani na mallaka a lokacin na Abba ne. Harta aiki shi ya samo mun bayan da ya biya mun kud'i na gama masters d'ina muka dawo gida nan Nigeria idan ban manta ba kina da cikin Khaleefah."

"A lokacin da muka dawo ne bayan na tafi yin service d'ina na koma k'auyen Askira dan d'auko su Abba in nemi tubansu in basu hak'uri ake tabbatar min da cewa sunyi hatsari shekaru biyu da suka wuce a hanyansu na zuwa k'auyen Dambuwa. Shi Abba a take ya cika ita kuwa Umma tayi jinyan wata shida sannan mutuwa yayi halinsa. I felt hopeless and useless Surayya, iyayena sun mutu amma seda shekara biyu nake sani. Ji nayi kaman in soka wuk'a wa kaina in mutu wani irin d'a ne ni? Na sosai nayi nadaman abinda na aikata na d'au alk'awarin yin sadak'atul jariya da sunayensu Allah ya kai musu ladan kabari. Nasan rashin kyautatawan da nayi wa iyayena yasa nima Allah ya jarabce ni da gagararriyar 'ya kaman Nazeefah.l

"Daga gida na wuce gidansu Jameelah inda ake sanar dani suma sun tashi sun k'aura sun bar garin gabad'aya. Ba wanda ya sanar dani cewan rabo ya shiga tsakani na da ita bayan faruwan abun shiyasa ban ta6a sanin Amal 'yata bace se recently. Wallahi ba k'arya nake yi miki ba Surayya please believe me, taya zan so in had'a 'ya'yan cikina kishi Surayya bayan na san yin hakan haramun ne?"

"Yanzu ina ita mahaifiyar Amal d'in take Jameelah?" Mummy data amince da duk wani abinda ya fad'a ta soma da tambayansa.

"Tana cikin garin nan da zama amma bansan inda take ba, rannan Afzal ya taho da ita da mahaifinta gidan Nazeefah inda mukayi magana duka akan yadda za'a 6ullowa al'amarin nan nasu."

"Baka san inda take ba kace?"

"Wallahi ban sani ba Hjy Surayya ai kinsan bazan miki k'arya ba."

"Bawai ina k'aryata ka bane Alhj I just want to be certain, tana da aure?"

"Wallahi banda masaniya akan hakan amma base on abinda Amal ta ta6a fad'amun kaman mahaifiyar nata bata da aure."

"Ka aureta Alhj" ta sanar dashi. Da mamaki ya tsaya yana kallonta yayinda ya kasa amincewa da abinda tace.

"Eh?" Ya tambaya.

"Nace idan har Jameelah bata da aure kuma bata niyyan yin wani auran anan kusa ka aureta."

"Hjy Surayya kin ko san abinda kike cewa?"

"This's the only way zamu iya samu mu had'a kan yaran nan Nazeefah da Amal mu gyara zuri'ar mu. Ka fini sanin halin Nazeefah, yanzu da Afzal ya d'au Amal a kanta ba k'aramin tsanar yarinyar nan zatayi ba dama already ta riga ta tsaneta."

"Toh mey auro Jameelah zeyi ya gyara wannan lamari Hjy Surayya?"

"Tabbas auro Jameelah zaisa Nazeefah ta shiga hankalinta ta nutsu ta sani cewa mu dasu mun riga mun zamo abu d'aya yanzu ta kuma sani cewa shi kishiya na akan kowa ne idan har da tanayin kwatance dani tagani toh yau nima gashi anyi mun kishiya."

"Tabbas kinyi gaskiya Hjy Surayya amma bana son in had'a soyayyarki da kowa ke kad'ai nakeso."

"Karka damu dani kuma ma ai nasan kana son Jameelar taka har yau ko ba haka ba?"

"Amma ba kaman yadda nake sonki ba Hjy Surayya ni tausayin Jameelah kawai nake yanzu."

"Karka damu ai ni nace ka aurota."

"Hjy Surayya nifa banga amfanin yin hakan ba. Ba sena auro Jameelah ba."

"Ka aurota Alhj ni na baka dama karka damu."

"Surayya-" hannunta ta aza akan nasa cutting him off "Don't worry nima ai zama ni d'aya tal d'innan ya isheni ka kawo mun abokiyar zama tana tayani hira na tabbata kaman yadda Amal bata da matsala itama mahaifiyar tata haka ne."

"Wannan ba sekin fad'a ba Hjy Surayya Jameelah sam batada hayaniya."

"Toh kaga komi ya zo mana da sauk'i kenan, ka auro ta kaji?"

Hjy Surayya what can I say? You're the reason behind who I am today and everything I've achieved, banida bakin yi miki da Abba godiya. Allah saka da alkhairi ya cigaba da sanya miki albarka a rayuwarki ya kuma ci gaba da kai rahama kabarin Abba."

"Ameen Alhj tare da iyayenka kai ma."

"Kin hak'ura zaki biyoni gida?"

"Har sena amsa tukuna zaka tabbatar da hakan?"

"Gani nake kaman mafarki nake Hjy Surayya, Allah yabar min ke tabbas irinku acikin mata d'ad'd'aiku ne."




RANA D'AYA!💕
#RD

Love... King Miemiebee👄✨




Miemiebee Novels

Monday, 1 October 2018
RANA D'AYA!
BY MIEMIEBEE
PAGE 45




"Ameen Alhj na."

"Mey hakan ke nufi kenan Hjy Surayya? Kin hak'ura kin yafe mun kenan?"

"We all make mistakes Alhj amma ba dukan mu bane muke gano kuskurenmu har ma mu nemi tuban wanda muka wa laifi, shin meyasa bazan yafe maka ba tunda har kai ka gane kuranka ka kuma nemi tuba? Na yafe maka Alhj Allah kuma ya yafe mana gabaki d'aya" ta k'arashe tana murmushi. Daddy baze iya kwatanta irin farin ciki da murnan da kalamun Mummy suka sanyasa ba. Da murmushi kwance fal a fuskansa ya mik'a hannunsa ya rik'o nata "Thank you so much Hjy Surayya I can say my life has never been better until I met you, Allah ya cigaba da miki albarka ya kuma barmu tare."

"Ameen Alhj you're welcome."

"Kinsan wani abu?"

"Seka fad'a."

"I love you" yana sanar da ita bata san lokacin da ta fashe da dariya ba "Ji Alhj de, yaushe kuma muka fara wasan nan?"

"I'm serious Hjy Surayya saboda bana fad'a miki doesn't mean I don't love you, I love you like the day I just met you Hjy Surayya never forget that."

"Thank you Alhj."

"Thank you kad'ai? Ni bazaki cemin I love you in return ba?"

"Ka ga La'asar ya kusa gara ka tashi ka fice muyi niyya duka."

"Yau kuma? Toh sekin fad'a min zan bar nan."

"Lallai kuwa, nikam ka ga tafiya na" bata kai ga mik'ewa ba ya dakatar da ita ta hanyan kama hannunta. "Alhj ka sakeni mana!"

"Nak'i"

"Zan tara maka jama'a fah."

"Ni d'in Hjy Surayya? Ni d'in naki?"

"Toh ka sakeni."

"On one condition."

"Name it."

"Yaushe zaki dawo gida? Ina matuk'an kewarki."

"Kai da zaka k'aro amarya kode ka manta ne?"

"Amarya daban ke daban so yaushe zaki dawo keda 'yan'yan namu?"

"Zamu dawo karka damu."

"Promise?" Kai zalla ta gyad'a mar sannan ya saketa "Toh se anjima ki gaishe mun da Nazeefah da Khaleefah."

"I'll semun sake magana." Da haka ta fice ciki inda shi kuma ya mik'e ya yi tafiyarsa.
D'akinta da Nazeefah ta wuce direct inda ta tarar da Nazeefah mik'e kan gado kaman maciji ta zurfafa a cikin tunani ko makaranta tak'i fita. "Tashi ki zauna muyi magana" Mummy tace da ita bayan ta zauna a gefenta ta bakin gadon. Ba gardama ta mik'e ta zaune.

"Ina son ki saurareni da kunnen masu hankali a matsayinki na musulma me kar6an k'addara me kyau ko akasin sa." Tun anan gaban Nazeefah ya fara bugun d'ari-d'ari dukda cewan bata fahimci inda Mummy ta dosa ba.

"Ki sani cewa komai na faruwa ne bisa dalili fatan mu kawai Allah ya sa hakan kawai shi ne mafi alkhairi a gareku gabad'aya."

"Mummy ban fahimce kiba shin mey kike fad'i? Meya faru?"

"Ga wannan takardan ki ne Afzal ya kawo wa Daddy jiya yana mey baki hak'uri kuma" ta fad'a had'e da mik'a mata. Jiki na k'yarma Nazeefah ta mik'a hannu ta amsa had'e da bud'ewa sannan ta karance hawaye kawai Mummy taga na gangara daga idanunta ba makawa.

"Nazee-"

"Noooo!" Tasa wani irin d'ankaren ihu "Noo this can't be happening, bani Ya Afzal yayi niyyan saka ba na tabbata munafukan chan ce ta tilasta mai ya rabu dani wallahi bani yayi niyyan saka ba Munmy."

"Nazeefah ya isa" Mummy ta fad'a tana k'ok'arin shawo kanta saidai hakan sake tunzirata yayi. Zabura tayi tana kad'a kai yayinda hawaye ke ambaliya a fuskarta "Mummy wallahi bani Ya Afzal yayi niyyan saka ba ki yarda dani."

"Nazeefah please-"

"Tsaya kiga ina key'n mota na inje in samesa kiji bani bace wannan takardan Amal ne ba nawa ba."

"Wani irin banzan magana kike Nazeefah? Bayan ga sunanki nan boldly rubuce akai? Taya zakice ba naki bane na Amal ne?"

"Wallahi Allah ba nawa bane ina key'n mota na yake?"

"Shin wai ina zakije?" Ta tambayeta. "Zan je in samesa saboda bani yayi niyyan saka ba."

"Nazeefah there is no point kiyi hak'uri ki rungumi k'addarar ki kowa yasan rabuwa da masoyi da zafi amma ba yadda kika iya."

"Hak'uri? Hak'uri Mummy? Wallahi inde akan Ya Afzal ne bazan ta6a hak'ura ba."

"Toh ya zakiyi? K'addara ta riga fata, the earlier kikayi accepting gaskiya the better."

"How Mummy? So kike kice mun shikenan na rasa Ya Afzal a rayuwa na kenan? So kike kice in nad'e hannu in bar Amal ta sace mun miji ina ji ina gani?"

"Kema kinsan Amal baza ta ta6a yin hakan ba, Amal ba ita ta sace miki miji ba Nazeefah, Allah ne ya k'addara rabuwan ku."

"No Mummy kinyi kuskure, idan ba mutuwa ba banga abinda ze rabani da Y Afzal ba" mayafinta ta sanya ta janye key daga gaban dresing mirror da niyan ficewa inda Mummy ta cafke mata hannu.

"Bada yawu na zaki fita ba Nazeefah."

"Just let me go" tace da ita had'e da fisgan hannunta. Kaman a kyaftawan ido Mummy ta isa bakin k'ofa ta kulle da key had'e da zarewa ta rik'e a hannunta.

"Mummy ki matsa mun."

"Ba inda zakije Nazeefah saki ne ya riga ya auku ba abinda kika isa kiyi da zeyi reversing case d'in sede hak'uri kawai, ki d'au komi a matsayin k'addara ki yi tawasalli."

"Na gaya miki Mummy inde akan Ya Afzal ne bazan ta6a hak'ura ba har se sakin nan ya koma kan Amal, bazan rasashi ni kad'ai ba se inde mu biyu duka mu rasa sa so move out."

"Ina nan tsaye anan ba inda zaki." Dube-dube Nazeefah ta shiga yi a d'akin chan ta hango wuk'a a kan bed side drawer nan da nan taje ta d'auka ta saita dai-dai wuyan hannunta (wrist) "Ko ki matsa ko in yanke kaina in mutu" Baki Mummy ta hangame cike da mamaki da k'in yarda tana kallon Nazeefah, batayi tsammanin rashin sanin addinin nata har yakai matakin da za tayi tunanin d'aukan ranta da kanta ba.

"Nazeefah?" Ta kirata da d'umbun mamaki. "Da hankalinki?"

"Mummy banida wata amfani tunda na rasa Ya Afzal gara in mutu in huta kowa ma ya mutu."

"Da hankalinki kike tunanin d'aukan ranki da kanki? Shin baki san hukuncin hakan bane a addinance?"

"I don't care Mummy amma bazan iya rasa Ya Afzal ba I can't because I love him, I love him so very much and Amal stole him away from me, what else can I do?"

"Idan kika hak'ura komi mey wucewa ne Nazeefah wataran se labari."

"No Mummy I can't move on, bazan ta6a iya son wani bayan Ya Afzal ba, I can't do without him dan Allah ku bashi hak'uri ya mayar dani d'akina."

"'Yar uwarki Amal kuma fah? Ya kikeson ayi da ita?"

"Ki daina kwatanta ta da 'yar uwata, idan da ta d'aukeni a matsayin 'yar uwarta da bazata sace mun miji ba so ki matsa ko kuma in yanke kaina."

"It doesn't have to be this way Nazeefah" Mummy ta sanar da ita tana mey matsowa kusa da ita a hankali.

"Mummy stay away."

"Nazeefah dan Allah kiyi hak'uri karki yanke kanki" ko kallon ta Nazeefah batayi ba ta sa wuk'an ta yanke hannunta wani irin ihu Mummy ta k'urma had'e da k'arisawa kan Nazeefah da ta shiga zamewa k'asa. Tarota Mummy tayi suka sauk'a k'asan atare tana mey bubbuga fuskanta yayinda idanunta suka cigaba da kakkafewa. "Nazeefah? Nazeefah? Innalillahi dan Allah ki tashi Khaleefah!" Ba shiri ta saketa ta d'auko wayanta had'e da kiran Daddy. A karo na farko ya d'aga,
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment