Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ya kasa 6oye farin cikin da ya tsinci kansa aciki, se kallon ckin wayan nasa yake yana cize la66e. Da murmushi kwance fal a fuskansa ya haura sama d'akinsu inda ya tarar da Nazeefah zaune akan towel tana shafa mai.

"Ya rouhi (my soul, sunan da take kiransa da shi) ina kaje?" Ta soma da tambayarsa.

"Wani friend d'ina ne yazo na sauk'a muka gaisa" ya had'a mata k'aryar nan take.

"Ai na d'au tafiya kayi ka barni."

"Har na isa in fita ba tare da Rabba'atul bait d'ina ba? Ko de so kike hukuma ta kamani?"

"Har kana tunanin zan bari hukuma ta kamaka?"

"Toh gashi na d'au kafin in dawo har kin gama shiri sede gashi mai ma kike kan shafawa."

"Toh Ya Rouhi ai bazaka had'a tsawon wanka na da naka ba kaifa cikin minti biyu shaa ka yi wanka ka fito."

"Ke kuma har sama da minti talatin ba."

"Eh mana" ta amsa tana murmusawa.

"Toh shirya dai ina jiranki." Zama yayi akan gado yana kallonta yayinda take ta shafa manta a hankali. A garin mik'ewa bayan da ta gama shafa man towel nata ya kusa sincewa da hanzari ta tattare sekace wacce aka ce mata idan ta bari towel d'in ya fad'i toh wuta za a kaita. Yadda ta kid'ime ne ya sanya Afzal dariya, ba shiri ya shiga dariya har yana neman k'warewa. Har akwai abinda be gani bane a jikin nata da take wannan rawar jikin? Shi bata ma ishesa da kallo ba.

"Ya rouhi wallahi mugunta ba kyau" ta sanar dashi tana turo baki. Dariyar yake har yanzu da k'yar ya iya ya tsagaitar sanan ya mik'e ya k'arisa inda take tsayen had'e ca janyota jikinsa yana mey zagaye hannayensa a 'yar k'ugunta yayinda da ta zagaye nata a wuyansa.

"Toh koda towel d'inma ya kunce mene ban gani ba anan d'in Rabba'atul bait?" Ya tambayeta yana yi mata nuni da ido.

"Kai Ya Rouhi dan Allah ka dena" ta fad'a cike da kunya, kafin tace zata sauk'e hannayen nata daga wuyan sa yayi sauri ya miyar dasu. A lokaci guda wani zuciyan ya raya masa da ya sanar da ita cewan ya kusa k'ara aure saboda this is the right time da zata yima kanta addu'a ko Allah ze sassauta mata zafin kishinta yayinda wani zuciyan kuma ya hanasa yin hakan yana rinjayansa cewan ai akwai sauran lokaci.

"Tunanin mey kake haka Ya Rouhi?" Ta tambayesa a hankali bayan tsawon lokacin data d'auka tana kallonsa.

Kai yayi saurin kad'awa yana me sake matso da ita kusa da shi, har nishinsu na had'ewa sannan ya murmusa yana mey kallon cikin dara-daran idanunta. "Was I thinking of something?" Ya tambayeta.

"Gashi gabad'aya hankalinka baya jikin ka."

"Well I'm just happy that you're happy being with me."

"Awwn Ya Rouhi being with you is my absolute pleasure. I love you so much, so much that bazan ma iya kwatantawa ba."

"Allah?"

"Sosai fa wallahi k'awaye na har cemun suke wai nafi sonka fiye da yadda kakeso na kuma Allah na yarda da hakan."

"Ko meyasa?"

"Saboda baka ta6a cemun kana so na ba koda kuwa ni na fad'a maka" ta fad'a sincerely. Sosai ya tausaya mata saboda yasan how she must be feeling anytime yayi mata hakan, shima duk lokacin da yace wa Amal yana sonta amman tayi shiru tak'i mayar masa da amsa ba k'aramin damunsa hakan yake ba, wai a hakan ma shi na miji ina ga Nazeefah ita mace kuma? Murmusawa yayi "Then stop feeling sad about it."

"But I can't."

"You have to because I love you too my rabba'atul bait" ya sanar da ita. Har cikin ranta taji dad'in kalamun nasa yayinda suka kwanta a birnin k'irjinta .
"Ze iya yuwu wa ban ta6a furta miki ba amman ba wai hakan na nufin bana sonki bane I love you so much."

"Dagaske Ya Rouhi? You really love me?" Ta tambayesa yayinda ta kasa 6oye farin cikin da ta tsinci kanta aciki.

"Wai tayaya ne ma bazan fara son wannan kyakkyawar yarinyar da bata da burin da ya fi taga ta farinta mun ba? Mace mey ladabi da biyayya, da iya soyayya da kuma sanin ya kamata, macen da ta gwammace ranta ya 6aci da nawa ya 6aci, wacce ta tsani ganin fushi na. Macen da kowani na miji zeyi alfaharin samunta a matsayin uwar gidansa taya ya kike tsammanin bazan so ki ba my rabba'atul bait? Amsa da kanki you think it's possible?" Kai ta kad'a a hankali cike da kunyan jin dad'i. "I love you kinji? I love you so much my rabba'atul bait."

Bata san lokacinda ta soma zubar da hawayen jin dad'i ba "I love you much more Ya Rouhi, my husband, my heartbeat and everything, Allah ya bar min kai ya kare min kai wallahi banjin zan iya rayuwa idan ba soyayyarka."

"Shhh!" Ya katse ta yana mey share mata hawayen nata "I'm never leaving your side till eternity bar kukan haka."

"Thank you Ya Rouhi" a hankali ya mik'a had'e da sauk'e lips nasa akan nata yayin da ya shiga yi mata wani irin kiss yana kashe duk wani sassa a jikinta. Tuni yasa ta mance da inda take, basu hankara ba kawai suka jisu akan gado. Cike da daraba ya janye towel da take ta faman tare jikin nata da shi ya wullar a k'asa sannan ya shiga sarrafa ta yadda yakeso. Unguwan da basu zo suka fita ba kenan!



RANA D'AYA!
#RD

Love... King MiemiebeeπŸ‘„βœ¨
[13/08, 09:33] β€ͺ+234 907 483 8352‬: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
πŸŽ€β£πŸŽ€
❣❣

πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
*RANA D'AYA!*
πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by MiemiebeeπŸ‘„_


*PAGE 2⃣5⃣*


Shirye-shiryen biki kuma aka shiga yi na sosai, kaman yadda akayi bad'ad'in bad'a haka aka kuma. Kyautan gida Abba ya sake yiwa Afzal a matsayin gudumawan da ya bayar. Sosai Ummi take taimaka wa Afzal, kusan komi ita takeyi, duk wani abinda yake buk'ata fa toh tun kafin ya furta zata tambaya masa gun Abba. Akwatuna har guda ashirin da d'aya aka had'a wa Amal sannan na Nazeefah kuma set mey k'waya shida na fad'an kishiya. Kusan duk zannuwan da suke cikin na Amal akwai su a na Nazeefah babancin kawai na Amal sunfi yawa ne. Abinda ya kama daga kan kayan kitchen, gadaje, kujeru, show glasses, rugs, da komai Ummi ne suka siya, ba yadda Mami batayi da ita ba akan ta bari ko wani abu k'adan ne su kawo yaso se a had'a kud'in ayi siyayyan amman Ummi tak'i kasancewar Afzal ya rok'eta da komin yaya karta yadda ta amsa koda kobo ne daga gun su. Sude kawai suyi focusing akan abincin da za'a dafa.

Mutum na iya rantsewa 'yar Ummi ce zatayi aure don kalan kayakin d'aki masu tsada da alfarman da ta sai wa Amal. Gida yayi kyau sosai se wanda ya gani. Yau ana saura sati uku d'aurin aure kenan.

***
"Halo Yaya?" Tace bayan ta d'aga wayan.

"Na'am Baby" ya amsa.

"Yaya wai yaushe ka fara kirana da Baby?" Yau kam ta kasa hak'ura seda ta tambayesa. Kusan sati kenan yana kiranta da hakan, kuma da gan-gan yake gano bata so.

"Jimin 'ya da ba sunanki bane?"

"Ni Amal ne suna na."

"Baby'n fah?"

"Sunan gida ne."

"Ni d'in ba d'an gida bane?"

"Ni ba haka nake nufi ba kawai na gwammaci kana kira na da Amal ne."

"Toh nak'i ni Baby nafi so."

"Toh Allah taimake ka, ina yini?" ta gaishesa.

"Lafiya d'an fito waje kinji?"

"Yaya ka fa san an fara yimun gyaran jikin."

"Se akace baki sake tako waje?"

"Toh ai Yaya idan na rink'a fita muna had'uwa bazaka ga effect na gyaran jikin ba."

"Nide fito ina jiranki." Nan da nan ta janyo hijabinta tasa ta fita taje ta samesa.

"Tabarakallah gaskiya Allah yayi halitta anan" ya ce da ita lokacinda ta shiga motan "Masha Allah, Abba yayi gaskiya da yace na iya za6i kin ganki kuwa?"

"Kai Yaya kadena zolayata mana."

"I'm damn serious wai ma yaushe ne auren? I can't wait any longer."

Wani irin ruwa cikinta ya d'auka, ba shiri ta had'iye miyau had'e da tambayansa,
"Uhm so what brought you here?" Don canza topic d'in.

"Is it a crime idan ango ya zo ganin amaryarsa sati uku kafin aurensu?"

"Ba wai haka nake nufi ba I mean akwai matsala ne?"

"Ohh wato ma haka kika miyar dani se idan akwai matsala nake tahowa ko?"

"Goodness! Nifa ba haka nake nufi ba."

"Toh yaya ne?"

"Babu nayi shiru."

"Yauwa da yafi kam so jiya kika gama bada haddanki duka wai ko?"

"Eh."

"Congratulations then, Allah sanya albarka aciki yasa idan kika tashi haifo mun yara ki haifa mun hafizai kaman ki Lily I'm so proud of you."

"Ameen Yaya thank you" ta amsa tana mey jin kunyansa.

"Yauwa wai inji Ummi tunda aka shiga yi maki jere baki je kinga gidan naki ba?"

"Gida na kuma? Gidan mu de." Ba k'aramin dad'i lafazin nata yayi masa ba.

"Toh gidanmu" ya gyara kaman yadda ta buk'ata.

"Eh amma Mami tace cikin satin nan zamuje."

"Toh ni nazo in kaiki ne yanzun."

"Toh ai ya kamata in sanar da ita kafin nan."

"I've already done that so don't worry."

"Toh shikenan."

"Kafin nan ina fatan kuna waya da tailor'n naki? Idan fa baki tak'ura mata da kira kad'an ne daga cikin aikinta tayi disappointing naki se ranar dinner'n yazo ki rasa kayan sawa."

"Yaya ni dole ne se anyi wannan dinner?"

"Wannan kuma seki tambayi Ummi tunda ita tace zatayi, da kud'in d'inkin ki dana komai ita tace zatayi handling ni karki sani cikin shirgin ku."

"Toh ai laifinka ne da kace mata baka buk'ata tunda de Allah yayi wannan ba shine auren ka na farko ba ai zata ji."

"Kefa kike gani kaman ba wannan ne aurena na farko ba tamkar sabon saurayin da ze angwance nake jin kaina so be calling the tailor on frequent basis kina mey tuna mata kayan naki, okay?"

"Toh shikenan."

"Sekuma batun wushe-wushe da kamu ko? Lokacin aurenmu da Nazeefah naga su Mummy sunyi mata and I can say I absolutely loved everything about the event inason a naki ma ayi."

"Yaya dan Allah kayi hak'uri nifa ban ga amfanin tarukucen nan ba wallahi hanyan kashe kud'i ne kawai, kayan dinner kad'ai kusan dubu d'ari biyu wannan kuma nawa zasu ce? Ni gaskiya banason kashe kashen kud'in haka ya isa."

"Toh banda ke da abunki wushe-wushe kam ba al'adanku bane ku shuwa? Ai ya zamo dole kiyi."

"Bawani dole d'innan ni kashe kud'i ne bana so."

"Laffaya nefa kawai zakisa."

"Shi d'in bada kud'i za a siya bane?"

"Lily wai ni ke miki magana kina jayayya dani?"

"Ni ba jayayya da kai nake ba Yaya, a matsayina na wacce zaka aura ne nake yi maka gyara."

"Toh banaso se anyi wushe-wushen da kamun ga wannan" yayi maganan yana d'auko wata bak'ar leda daga backseat. "Gashi" ya mik'a mata. Amsa tayi ba musu ta bud'e sabon laffaya ta gani me uban kyan k'arshe irin na 'yan Sudan masu d'ankaren tsadan nan. Yaya!" Tayi exclaiming.

"Yayi miki?"

"Fisabillahi nawa ka kashe a nan?"

"So kike in fad'a miki kud'in saboda kice baza ki sa ba? Ki kwantar da hankalinki ba tsada."

"Mey k'arya..." se tayi shiru

"Naji mey k'arya d'an wuta bade hakan ze sa in fad'a miki kud'in ba, so yanzu an gama da maganan wushe-wushe se kuma na Kamu."

"Ni wallahi 6arna da kud'i ne banaso ga walima ga wushe-wushe ga dinner mey na wani kamu kuma? Kai baka tausaya wa kanka dasu Abba ne kam Yaya? Ni gaskiya ba wani kamun da za'ayi."

"Allah baki isa ba."

"Har Allah fa kace Yaya?"

"Eh baza kiyi auren nan dry ba mey sekace auren dole za ayi miki? Ai ko na Nazeefah da na dolen ne ma anyi celebrating se naki ne zaki wani ce a'a? Ko so kike ki nuna mun auren dole ake shirin miki Lily?"

"Yaya ba haka bane kashe kud'in ne ya isheni dubi ko tsinke fa ka hana su Papi siya."

"Ai ni na d'auke muku ba ku kukace nayi hakan ba kuma ko a addinance ma ya halatta idan miji nada k'arfi ya d'auke wa matar da ze aura da iyayenta nauyin komai so ki daina bothering kanki kinji? Ni naso in d'auke muku kuma ko a ina ma yin hakan ba laifi bane."

"Thank you so much Yaya Allah k'ara bud'i, I really like this laffaya, wallahi yayi kyau sosai."

"Ameen glad you like it, so kin amince ayi kamun? I'll just talk to our wedding planner."

"Nikam a'a wushe-wushen ya wadatar."

"Mey laifin in anyi duka toh Lily?"

"A'a gaskiya nikam guda d'aya za'ayi."

"Toh wa ze hak'ura cikin mu?"

"Yaya kai babba bazaka hak'ura ba?"

"Nak'i hak'uran."

"Toh shikenan ni k'arama zanci girma."

"Nak'i yarda da hakan."

"Toh kuma?"

"Duka biyu za'ayi."

"Wai kam cire kud'i ba amfanin nan baya damunka ne? Wallahi haramun ne ko sena ja maka aya tukun?"

"Ko ki yarda ko in samu Papi ince mishi gashi tun kafin ayi aurem kina mun rashin kunya ina miki magana sam bakiya ji."

"Ni yaushe na yi maka rashin kunya? Sharri zaka soma min tun kafin in shiga gidan naka?"

"Toh ki amince kai karma ki amincen da kin k'i da kinso se anyi duka hungo wannan" yayi maganan yana d'auko wata bak'ar leda dake ajiye gun k'afansa. "Mey wannan d'in?" Ta tambaya tana warware ledar. Invitation card na programme of events na auren nasu ta tarar aciki, ashe duk surutun nan da yakeyi har ya riga ya sa an buga komai ciki harda kamu da wushe-wushen kawai neman sata surutu yake.

"Ashe har ka sa an buga."

"Dama in fad'a miki ne kayan da zakisa a kamun already na gun tailorna bada measurement naki."

"Ni wallahi har kunyarka nakeji Yaya komai kai kakeyi."

"Ba wani abin kunya dama al'adan yarabawa ango shi keyin komai ko cokali mace bata kaiwa gidanta so stop bothering yourself."

"I know thank you won't compensate but thank you so much Allah k'ara bud'i."

"Ameen don't mention so mu tafi?"

"Eh muje ba kace ka riga ka sanar da Mami ba?" Da haka ya jasu suka wuce gidan nasu wanda yake unguwan Old GRA. Amal seji take kaman komi a mafarki yake faruwa, koda wasa bata ta6awa kawowa a ranta cewan wataran zatayi aure acikin fankacecen gida irin wannan ba, itama 4 bedroom flat ne da parlour biyu se kitchen da store d'aya da kuma guest toilet d'aya. Ita ba abinda yafi burgeta ma kaman yadda aka k'aya kitchen natan, yadda komi yake in purple and white gaskiya ba k'aramin kud'i su Ummi suka kashe ba. Addu'a tayita yiwa Afzal da Ummi dan idan ba addu'ar ba bata tsammanin akwai abinda zata iya yi da ze iya biyansu kalan d'imbum alkhairin da sukayi mata. Gida sekace mutum na aljannar duniya. Bayan ya sauk'eta a gida sukayi sallama sannan ya biya gida gun Ummi.

"Kayakin Nazeefan kazo d'auka ko?"

"Eh Ummi are they ready?"

"In a moment, amma Prince kace akwati shida be isheta ba se har an yi mata goma? Sekace itace amaryar?"

"Ummi kinsan halin Nazeefah yanzu haka idan taji na Amal 21 nata shida wallahi ba k'aramin tada mun hankali zata yi ba."

"Lallai kam kai kaso amma ban ta6a jin inda akayi kayan fad'an kishiya set goma ba shidan nan da muka had'a mata a farko yayi."

"Ayi mata goman kawai kowa ya huta."

"Toh shikenan kayaki suna hanya sun kusa isowa."

"Alright toh thank you so much Ummi Jazakillahu khair."

"Ameen wa iyyaka, ya amaryar tamu? Munyi waya da Mami d'azu tace wai ka d'auki Amal ka kaita duban gidan nata."

"Eh wallahi lafiyarta k'alau tana gashe ki ma."

"Ayya ina amsawa, yaya gidan tace wai? Komi yayi mata ko?"

"Sosai ma, bakiga kalan godiya da addu'an da tayita yi maki ba wallahi."

"Allah sarki 'yar albarka kace mata kar ta damu."

"Ai ko na fad'a mata, wai ayi kamu da wushe-wushen da yake kaman al'adansu wai sam baza ayi ba walima ya wadatar ita bata son kashe kud'i dinner'n ma ta amince ne saboda tana jin kunyarki" ya sanar da ita. Dariya sosai Ummi tasa. "Ai ustazancin Amal takan nan kam se a hankali, kuma fa ba komai yake hanata amincewan ba tuna yadda zata fita ba mayafin kirki a idon jama'a ne yake damunta."

"Ai kaman kin sani da fari ma cemun tayi wai abaya zata sa zuwa gun dinner'n" Nan ma wani dariyan Ummi ta kuma sawa "Kai!! Amal takan nan drama queen ce, ai nace da tailor'n nata tayi mata decent d'inki, kayan da baze bayyana jikinta ba."

"Hakan yayi sosai."

"Toh Allah bada zaman lafiya ya nuna mana ranar auren nan."

"Ameen Ummi thank you for all that you've been through for me wallahi bansan ta ina zan fara biyanki ba."

"Ba komai Prince karka damu bayan kai fa ba kowa idan ban yi maka abinda kakeso na lalata ka ba wa zan lalata toh?"

"Your boy loves you so much."

"I love him even more."

"So mey Daddy'n Nazeefah yace bayan da Abba ya sanar dashi zan k'ara aure?"

"Me kuwa zece? Ya taya ka murna mana ai har ya sanar da mahifiyar nata ma don jiya ta kirani take cewa in tayaka murna."

"Ayyah Alhamdulillah toh."

"Yanzu dey matsalar d'aya ce Nazeefah Allah sa tayi maka kyakkyawan fahimta duk da cewan ka makara, yaci ace ka sanar da ita da jimawa."

"Ameen fah wallahi ni har tsoro ma nakeji kinsan kalan zafin kishinta kuwa? Akwai lokacin da Amal ta ta6a kawo mun aldeb sena zuba flasks d'in acikin fridge bakiga yadda hankalin yarinyan nan ya tashi ba da ta ci karo da flasks d'in."

"Aikam daga yadda take magana ma mutum ze san tana da zazzafar kishi Allah de sa ta yayyafawa zuciyar tata ruwan sanyi tayi maka kyakkyawar fahimta."

"Ameen Ummi" bada dad'ewa ba akwatunan da yasa a k'ara d'in suka iso nan ya had'a dana farkon ya cika goma cus aka sanya masa a booth. Sallama sukayi da Ummi sannan ya fice, se hasbunallai wa ni'imal wakeel yake ta nanata cikin motan yau yasan se gobara ya kusa tashi masa a gida.

A cikin motan ya baro kayakin ya k'arisa ciki. Mik'ewa tayi tamai sannu da zuwa had'e ba sa light kiss on the lips.
"Ya Rouhi ina kaje haka tun d'azu ina jiranka?"

"Akwai wasu ababen da na kula dasu ne I'm sorry for keeping you waiting."

"Ayyah ba komai muje in had'a maka ruwa kayi wanka food is ready." D'akin nasa suka k'arisa nan da nan ta had'a masa warm water sannan ya shiga. Tana cikin ninke kayakin sa da ya cire dan kaisu laundry room wayan sa dake kan gado ya shiga ruri bata damu ta duba wa ke kira ba ta cigaba da harkar gabanta. Call d'in na tsinkewa meshi ya sake kira se anan ne tayi tunanin bari ta lek'a taga ko waye ne, idan Ummi ce tace mata yana wanka.

'Lilyβ€πŸ’•' taga yana flashing akan screen d'in bayan nan ga picture'n Amal da yayi saving contact d'in dashi. Wani irin mumunan fad'i gabanta yayi bata san lokacinda ta shiga yin kakkarwa ba. Tabbas ta wayi fuskan nan amma ta rasa a ina, kode a makaranta ne? Kai da wuya toh a ina ta waye ta? Da hanzari tayi picking kafin call d'in ya tsinke had'e da yin shiru.

"Halo Yaya?" Amal ta soma da cewa.

"Kina neman waye?" Nazeefah ta tambayeta, Amal na jin muryan tasan na Nazeefah ne bata sake cewa komai ba kawai ta katse wayar. Nazeefah bata kai ga ajiye wayan ba Afzal ya fito daga bayin d'aure da towel a iya kunkuminsa. Kallo d'aya yayi mata yasan ba lafiya ba, idanunsa na sauk'a akan hannunta da ke rik'e da wayan nasa kuwa ya gama tabbatar da abinda ke faruwa. Tabbas Amal ce ta kira Nazeefah kuma ta d'auka. Innalillahi! Meya hanasa shiga da wayan nasa bayi kaman yadda ya saba? Sam ba haka yaso ba, yafi son ya sanar da ita komai da bakinsa ba wai ta gano hakan da kanta ba. Nauyayyan numfashi ya sauk'e sannan ya k'arisa inda take tsayen har yanzu.

"Nazeefah-"

"Da abinda zaka sak'a mun kenan Ya Rouhi?" Ta katse sa.

"Meya faru? Mey wayana keyi a hannunki kuma if I may ask?"

"Kiranka akayi na d'aga" ta amsa.

"Kawo muga" ba gardama ta mik'a masa kaman yadda ya k'udura a ransa kuwa Amal d'in ce ta kira.

"Wacece ita? Meyasa take ce maka Yaya? Mey ma'anan wannan hearts da suke gaban sunanta?" Ta jero mai tambayiyo a lokaci guda.

"Nazeefah calm down."

"I can't calm down Ya Rouhi I can't! You mean to tell me for all this while dama kana da wata a waje? Wow!" Ta numfasa cike da d'umbun mamaki se ganin al'amarin take kaman raha.

"Nazeefah I'm sorry but wallahi inada niyyan sanar dake komai."

"Sanar dani mey? Akan kana da budurwa? Seriously Ya Rouhi? Meney bana yi maka a gidan nan da zaka za6i ka k'untata mun haka? Why do you have to flirt behind my back?" By now har idanunta sun soma cikowa da hawaye.

"Nazeefah please don't cry" ya fad'a a kid'ime. Hannun sa tayi saurin cirewa kafin ya samu ya rik'e ta. "I'm not flirting behind your back kema kinsan ba hali na bane hakan, I respect you a lot to hurt you like this."

"Then explain mey contact na yarinyan nan keyi a cikin wayanka da kuma dalilin da zaisa tana kiranka Yayanta."

"Sunanta Amal and am willing to marry her." Wani irin mumunan fad'i gabanta yayi aure de?
"Aure?" Ta nanata cike da k'in yarda. "Aure Ya Rouhi? Aure kake shirin yi?"

"Yes Nazeefah ina son in k'ara aure kuma Amal nike son in aura, kiyi hak'uri na rashin sanar dake da wuri da banyi ba but kar kiyi tunanin nayi hakan ne don inci zarafin ki. Not at all, I do have a reason for not informing you, nafi son
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment