Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

kuma a kar6e kayan gaisuwa? A'a dan Allah."

"Baka tunanin idan har aka koma da kayakin nan Abdul ze iya fahimtan akwai matsala? Ko ba don wannan bama kaya tunda aka siya da sunanku aka siya idan zakuyi mana adalci ya kamata ku kar6a koda baku so."

"Hakane Alhj amma-"

"Kar kaji komi Mallam Muh'd ai na fahimce ka abu ne Allah ya riga ya k'addara ba yadda muka iya so karka damu dan Allah."

"Toh Alhj amm-"

"Dan Allah fa nace" ya katsesa.

"Toh shikenan Allah saka da alheri" nan suka rakosu waje inda aka nemi almajirai suka sauk'e kayakin daga mota suka jibge aciki. Kayan abinci ne ba abinda babu, shopping kaca-kaca su Baba sukayi. Godiya sosai su Mami sukayi musu har seda motansu ya fice sannan suka dawo ciki.

"Abba wallahi sam banji dad'in wannan abu ba" Mami ta fad'a bayan dawowansu ciki "Baka ga yadda jikin mahaifiyar nasa ya mutu ba wallahi sosai na ji musu ba dad'i barin ma shi Abdul d'in."

"Tasa jarabawar kenan Jamila se muyi masa addu'a Allah ya basa ikon ci."

"Ameen hakane kam itama Baby tana cikin tsaka me wuya rabuwa da masoyi babu dad'i."

"Sosai shiyasa ya kamata mu jata jiki mu nuna mata so sosai don ba k'aramin buk'atanmu take ba yanzu."

"Hakane bari in shiga daga ciki in sameta."

"Toh nima barin d'an fita."

"Toh Abba a dawo lafiya." Da haka ta k'arisa ciki ta samu Amal da keta faman kuka har yanzu hak'uri ta shiga bata tana fad'a mata kalamu masu dad'in da zasu kwantar mata da zuciya akan hakan na daga cikin jarabawanta ne itama idan tayi hak'uri ta kar6a hannu bibbiyu tayi tawakkali komi mey wucewa ne. Da k'yar ta samu kukan Amal d'in ya lafa take sanar da ita yanzun Abdul da iyayensa suka tafi bayan nan kuma sunyi gaggarumin siyayyan kayan abinci sun sauk'e musu dukda cewan Papi beso kar6a ba tunda aure ba yuwuwa zeyi ba amman Baban Abdul d'in ya nuna rashin damuwansa ga hakan ya dage lalle-lalle se sun kar6i kayakin.

"Toh yanzu ya kenan? Kun fad'a wa shi Abdul d'in kenan?" Ta tambayeta a nitse.

"A'a Papinki de ya buk'acesu da su san yadda zasu sanar da shi kaman yadda kika buk'ata so muna fatan zasu san yadda zasu fad'a mishi."

"Mami bana son rabuwa da Ya Abdul."

"Rabuwa ya zama dole Baby kede ki dage da addu'a Allah sa za6in nan shine mafi alkhairi a gareki nima zan tayaki da addu'a kinji?" Kai ta gyad'a a hankali had'e da kwantar da kanta akan cinyan Mami tana share hawayenta.


*****
Tun isansu Mama gida suke tunanin yadda zasu 6ulloma wannan al'amari tabbas Amal masoyiya ta hak'ik'a ce da har tayi tunanin cewa breaking wa Abdul news d'in haka kai tsaye na iya jefa rayuwarsa cikin matsala. Toh yanzu ya zasu 6ullowa al'amarin? Ya zasu fara sanar da shi Amal bazata iya auransa ba?

"Alhj bansan ya zanyi da Abdul ba wallahi ina mugun tausaya masa, bakaga yadda yakeson yarinyar nan ba ko hirarta yake mun jikinsa rawa yake don murna kawai."

"Dama kina da labari?"

"Ai har waya ya ta6a had'ani da yarinyar kuma itama tana sonsa wallahi wannan abu beyi ba."

"Tasa k'addarar kenan akan 'yan matan da yakeso se muyi masa addu'a kaman yadda ya ci na baya ya sake cin wannan d'in."

"Hakane Alhj amman gaskiya Amal nada kaifin tunani da tace kar ayi masa breaking news d'in kai tsaye wallahi nima tsoro nake idan kuma shima ciwon zuciyan ta kamasa fa? What of idan ya samu k'aramar hauka?"

"Subhanallah ya kike magana haka Binta? In shaa Allahu ze fahimce mu."

"Gaskiya a'a Alhj bana son abu ya samu Abdul kasan ya za'ayi kawai amman de kar a sanar dashi kai tsaye haka."

"Ya kikeson ayi toh Binta? A cigaba da zolayarsa kenan? Har izuwa yaushe? I think the earlier the better."

"Yes the earlier the better amman kuma sanar dashi kai tsaye Amal bazata aure shiba ba k'aramin hatsari bane wallahi ni nasan yadda yakeson yarinyan nan I'm very sure news d'innan zeyi devastating nasa ka yarda dani."

"Toh Binta ya zamuyi?"

"Ban sani ba amman we have to think of a way bana son abu ya samu Abdul."

"Toh shikenan zamu tsaya muga me Allah ke ciki ko kafin nan da next week 6ullo mana da wata solution d'in."

"Yauwa toh hakan yafi."

****.
GIDAN ALHJ AMIN (Abban Afzal)

"Assalamu alaikum" Afzal yayi sallama had'e da sa kai cikin parlourn.

"Wa'alaikumus salam" Abba dake zaune a gefen Ummi ya amsa. "Bismillah k'ariso ciki." A nitse ya tako ciki ya nemi gu ya zauna had'e da gaishesu duka.

"Ya jikin naka?" Abba ya tambaya bayan nan.

"Alhamdulillah da sauk'i Monday zan fara fita office in shaa Allah."

"Toh Allah k'ara sauk'i."

"Ameen Abba nagode."

"Dama magana nakeso muyi na turo akira ka."

"Toh Abba ina ji."

"Kafin nan d'ago kanka ka kalleni inason ina kallon cikin idanunka idan ina ma magana" beyi gardama ba ya d'ago kansa.

"Shin wani irin zama kakeyi da matarka Nazeefah a gida?"

"Lafiya k'alau" ya amsa take.

"Kar kayi tunanin yimun k'arya Afzal" ya kirasa da asalin sunansa "Nace wani irin zama kakeyi da Nazeefah? Shin kana kula da ita a matsayinta na wacce take k'ark'ashinka? Shin kana bata hak'k'inta a matsayinta na matarka? Kana kula da tufafin da take sanyawa da kuma kalan mutanen da take mu'amala da su? Shin ka kafa mata dokokin da na miji ya kamata ya kafawa matarsa don kare ma kansa mutunci da ita kanta matar?"

Shiru Afzal yayi don acikin ababen da Abba ya irgo idan akwai d'aya da yakeyi me kyau shine ciyar da Nazeefah da yakeyi se bata tufafi bayan nan ba komai again.

"Da kai nake magana Afzal."

"Abba I'm trying, ina iya k'ok'arina don ganin nayi improving relationship namu I just need some space."

"Lokaci? Lokaci fiye da shekara d'ai Afzal? Koma me de kasani duk abinda kakeyi a gidan Allah na kallonka muddin idan kai kake toye mata hak'k'i to fa Allah baze barka ba dan Allah baya barin a ci mai alhak'in bawa kaji ka sani idan ko ita ke tauye maka hak'k'i itama Allah baze barta ba."

"Na sani Abba."

"Bayan nan tun wuri ka zubar da wannan banzan d'abi'ar taka ta zurfin ciki wallahi banda halaka ba inda zata kai ka. Ace ina matsayin mahaifinka in tambayeka fiye da sau uku meke damunka amman ka bushe mun ido kace kai babu bayan soyayyar yarinya ke neman halaka ka? Toh koma me kake 6oyewa kasani munyo bincike kuma mun gano bakin zaren. Kuma wallahi sa'anka d'aya ne na cewa da likitanka yayi idan har ba a magance maka wannan matsala ba kana iya rasa rayuwanka idan ba don haka ba da na barka kasha d'an banzan wuya k'arshe shi Abdul ya aure Amal d'in a idonka muga ko zaka soma yawo tsirara akan hanya. Kana son mutum amman bazaka iya samunsa ka fad'a masa ba chan kuma ka bugi k'irji kace kai na miji ne? A ina aka ta6a yin hakan? Toh ka bud'e kunnuwan nan naka ka saurareni da kyau tun wuri idan kasan bazaka iya rik'e mata biyu ba ka fad'a min kar kazo kayi mun abin kunya."

Gabad'aya kan Afzal ya d'aure ya rasa inda Abba ya dosa "Mata biyu kuma Abba?"

"Eh matar mutum kabarinsa duk yadda Amal da iyayenta suka so kasancewarta da saurayinta Abdul Allah beso hakan ba ya za6ar mata kai a matsayin mijinta na aure bayan istikharan da takeyi har sau biyu just to tell you how much she loves that Abdul. Afzal ka bamu wuya kasa mun nuna son kai a fili na neman raba wannan masoya biyu. Shine tun wuri idan kasan bazaka iya yin adalci ba tsakanin yaran nan ka fad'a mun kar mu fara abinda baza mu iya k'arasawa ba."

"Abba ban fahimce ka ba, kana nufin kai da Ummi kunje kun samu Amal da iyayenta akaina?"

"Ban sani ba ko ka daina jin hausa da yamma."

"Abba why? Abba ba lallai bane se Amal ta aureni tunda kaima da bakinka ka fad'a ba yadda ta iya ne, ina amfanin tilasta ta against her wish? A gani na hakan ba shida fa'ida. Nagode da d'awainiyan da kai da Ummi kukayi mun amman a gani na is better a bar Amal ta auri wanda takeso."

"Kai kuma se kayi ya da ran naka da kuma son da kakeyi matan?"

"Zan hak'ura Abba, haka Allah ya k'addara kenan amman banason in zame sanadin k'unci da bak'in ciki a rayuwan Amal."

"Na yaushe kuma? Da tun farko da ka gano kana sonta ka tinkareta ka fad'a mata ai da du hakan be faru ba yanzu sede ayi maganan yadda za'ayi ka gyara kuskuren da kayi dan kuskure de kam ka riga kayita saboda haka nakeson gobe ka shirya kaje gidansu ka yima iyayenta da ita kanta godiya ka kuma basu hak'uri musamman ma ita Amal ba k'aramin jarumtaka tayi ba na saudakar da farin cikinta maka kaima ka sani ba sena fad'a maka ba."

"Abba I'm sorry amman bana tunanin I can do this."

Da mamaki both Ummi da Abba suka tsaya suna kallonsa. "Kana nufin duk hidiman da mukayi maka a banza ze tashi kenan?" Ummi ta tambayesa da mamaki shikam Abba yama kasa magana.

"Ummi kuyi hak'uri ba wai zuwa gidansu Amal in basu hak'urin bane bane bazan iya ba."

"Mey toh?" Ta kuma tambayansa yayinda Abba ya kafa masa ido.

"Ummi bazan iya rik'e mata biyu ba Allah ma shaida ne bazan iya ba."

"Kasan da hakan ka kwad'aita wa zuciyarka soyayyan Amal bayan kana da mata a gida?"

"Ummi inda zan iya hana zuciya na son Amal da nayi hakan da jumawa amman ba daga ni bane, I really tried but abun ya gagara."

"Ya zamo dole kenan kaman yadda kowa ma ya hak'ura kaima ka hak'ura ka san ya zaka koyi zama da mata biyu ko a jinka bamu da aikin yine feee se mu d'ibi k'afa mu sake komawa gidansu Amal muce musu gashi kai kace bazaka iya zama da mata biyu ba? Ka sani don lafiyarka muke yin komai Afzal idan ba don haka ba wallahi ko kallonka ma bazanyi ba nide na fad'a maka gobe kaje gidansu Amal ka bata hak'uri da iyayenta tun wuri kuma ka fara koyan zama da mata biyu kana iya tafiya." Abba yace da shi cike tsiwa. Daga yadda yake magana a san ransa ya 6aci. A raunane Afzal ya mik'e ya fice ko hak'uri ya kasa bawa mahaifin nasa. Ummi ce tabi bayansa tare da kiransa, site nata ta jasa suka wuce inda suka zauna akan kujera.

"Prince meyake damunka? Tun da kayi aure ban sake gane kanka ba, ko ka manta ni mahaifiyarka ce da kake gudun gaya mun damuwanka haka?"

"Ummi ba haka bane."

"Toh yaya ne? Kana son Amal ko baka sonta?"

"Ummi it doesn't matter."

"Yes it does kana sonta koko a'a?"

"Ummi kema kin sani, I love her, I love Amal."

"Meya hanaka sanar damu tun wuri toh da muke tambayanka?"

"Saboda bansan ya zan fara zama da mata biyu ba I can't Ummi."

"So kake ka saki Nazeefah kenan seka kawo Amal?"

"Sam ba haka bane Ummi, Nazeefah bata min komai ba idan da adalci be kamata in saketa haka kawai ba don zan auro wata."

"Toh seka had'asu su biyu ai dama tun kafin auran naku ma Abbanka yayi maka alk'awarin cewa kowa ka kawo daga baya kace kanaso za'a aura maka ita."

"Ummi ina sane da hakan."

"Amma abinda kayi ma Abbanka banji dad'insa ba ya kamata ka basa hak'uri."

"Ummi I'm sorry amman bazan 6oye miki ba banji dad'in zuwa gidansu Amal da kukayi ba tare da kun sanar dani ba."

"Ai ba wai haka kawai aka k'i sanar da kai ba Prince kai kanka kasani idan da mun sanar da kai bazaka yarda ba aje gidan nasu, kasani idan fa kai baka damu da halin da kake neman jefa rayuwarka aciki ba mu nan mun damu da kai. Ko ajinka idan ka cigaba da samun attack d'in zaka rayu ne? Wataran zuciyan na iya bugawa kuma tak'i tashi se lahira kenan. Mey kakeson ace damu? Iyayen da suka kasa magance wa d'ansu tilo damuwa? Abu d'aya nake so da kai Afzal ka rage zurfin cikin nan naka duk abinda yake damunka tell me I'm just a call away komin yaya ne zan san yadda zanyi in share maka hawayenka."

"Ummi thank you and I'm sorry."

"Ba komai ya wuce bayan nan kuma ina son ka daidaita tsakanin ka da Nazeefah ka sani idan kana tauye mata hak'k'i Allah baze barka ba, a matsayin matarka take dole ne kana biya mata buk'atunta ka kuma bata lokacinta only then Allah ze sa maka hannu acikin al'amuranka ya shige maka gaba."

"In shaa Allah Ummi thank you."

"Yanzu kaje ka bawa Abbanka hak'uri gobe in Allah ya kaimu seka jeka gidansu Amal d'in kaji?" Kai ya gyad'a a hankali "Very good."
Mik'ewa yayi tare da yimata se anjima ya fice, site na Abba ya nufa ya samesa zaune kaman yadda ya barosa. Durk'usawa yayi ya basa hak'uri se a karo na biyu Abba ya amsa tsabagen yadda ransa ya 6aci. Hak'urin yayita basa amman Abba ya nuna masa ba komai.

Isansa gida keda wuya ya shige d'akinsa had'e da mik'ewa akan gado se tunanin abinda Ummi ta fad'a masa yake. Ya sani sarai Sultan ne ya sanar dasu komai bama amfanin kiransa ya tambayesa. Bayan da ya dawo daga sallan isha ne ya tsinci Nazeefah zaune a parlour tana yin assignment nata. Sannu da zuwa tayi masa bayan ya amsa ya k'arisa inda take zaune akan rug yayi tsaye a kanta. Kai ta d'ago da mamaki tana kallonsa amman bata ce komai ba hannunsa biyu ya mik'a mata da nufin ta kama ya mik'ar da ita sede don mamaki tama kasa koda kyafta ido. "Come" ya buka'aceta biron nata ta ajiye sannan a hankali tasa hannayenta cikin nasa ya mik'ar da ita. Da hannunta cikin nasa yayi gyaran murya sannan ya kira sunanta.

"Na'am" ta amsa. Idanunsa ya d'ago yana kallon cikin nata idon sannan a hankali ya furta "I'm sorry."

Mamaki ne ya rufeta kum tama kasa koda magana da fari ma tayi zaton kode aljanu ne suka shigesa yake bata hak'uri, toh ma hak'urin mey?
"Afzal" ta kira sunansa a hankali.

"I'm sorry kinji? Starting today we'll be living a happily married life in shaa Allah." Dan murna tama kasa cewa komai kawai rungumesa tayi yayinda hawaye ya ciko mata a ido, "Afzal I'm sorry too, forgive me also."

"Shhh!" ya buk'aceta had'e da hugging nata back sun kai kusan minti d'aya a haka sannan ya zame jikinsa had'e da share mata hawaye "Banda kuka kinji?" Kai ta gyad'a a hankali tana mai murmushi "I'm hungry akwai abinci?" Yayi maganan yana lek'an dining space.

"I'm sorry gabad'aya hankali na ya tafi akan assignment d'innan bari yanzu inje in dafa maka macaroni akwai stew na rana senayi heating."

"Ki bari ki gama assignment d'in tukuna kinji?"

"But kace kana jin yunwa."

"I can wait finish up first."

"Are you sure?"

"Yes" ya amsa yana mata murmushi.

"Alright bari inyi sauri saura kad'an dama."

"Okay barin watsa ruwa nima" mik'awa yayi had'e da placing mata light kiss a goshi sannan ya wuce. Mutuwan tsaye Nazeefah tayi gun yayinda farin ciki ya mamaye mata zuciya, ji take tamkar duk duniyan ba wanda ya kaita murna. Nan da nan ta k'arisa assignment natan ta wuce kitchen.

Washegari da yamma Afzal ya shirya tsaf cikin half jamfa maroon color ya feffeshe jikinsa da turare ya janyo k'ofar d'akinsa ya fito.
"Zan fita" yace da Nazeefah dai-dai lokacin da ya k'ariso parlourn. Sosai gabanta ya fad'i mostly idan yayi wanka haka da yamma gun zance yake wucewa ya zatayi yanzu? Gashi bata son da zaran tayi masa magana hakan ya haifar masu da wani fad'an dan haka kawai ta danne zuciyanta tace, "A dawo lafiya kayi kyau."

"Thank you" ya amsa da murmushi sannan ya fice. Gidansu Amal ya wuce direct inda yayi parking ya shige. Mami da Papi ya tarar a tsakar gidan suna zaune. K'arisawa yayi ya tsuguna daga waje-waje had'e da gaishesu.

"Kuma ka tsuguna daga chan ka k'ariso ciki mana" Papi yace dashi ba musu ya k'ariso ya zauna daga bakin tabarman inda suka sake gaisawa da kyau.

"Ya jikin naka? Ka warware ko?"

"Alhamdulillah" ya amsa.

"Shine ka k'i mu kwana biyu ko?" cewan Mami.

"Ba haka bane Mami kuyi hak'uri."

"Gashi ka shigo Amal ta fita bata nan."

"Ayya dama gunku nazo kafin nan."

"Toh toh madallah" Papi ya amsa.

"Papi, Mami kuyi hak'uri nasan ni mey laifi ne amma d'an Adam ajizi ne ku gafirceni."

"Ba komai Afzal komi ya riga ya wuce Allah sa hakan shi yafi alkhairi kawai."

"Ameen nagode, Mami bakice komai ba ko senayi tsallen kwad'o tukuna?"

"Ai ko abinda za'ayi kenan ace yadda muke da kai amman kana son Amal ka kasa furta mana Afzal? Har seda ciwo ya shige ka? Nakega tsallen kwad'on nan zan saka shine punishment naka."

"Yi hak'uri Mami, Papi ka tayani bata hak'uri."

"Wasa take maka ta hak'ura da jimawa itama yauwa nace ya batun matarka ta gida?"

"Lafiyarta k'alau."

"Shin tana sane da abinda ake ciki kuwa?"

"A'a Papi amman idan lokacin yazo zan sanar da ita."

"Kana ganin baza a samu matsala bako? Kasan shi rik'e mata biyu ba abu neba na wasa."

"Tabbas Papi ina fatan Allah ze bani ikon yin adalci a tsakaninsu."

"Toh Allah taimakeka Afzal kasan Amal yarinya ce se anayi ana hak'uri."

"Karka damu Papi zan kula da Amal in rik'eta amana se inda k'arfi na ya k'are."

"Na amince da kai Afzal dan Allah kar ka bani kunya ga Amal nan mun baka ita kaman yadda kake kula da ita da a baya ina fatan zaka k'ara himma yanzu da ta kasance mallakinka."

"In shaa Allah bazan baku kunya ba Papi, you have my word."

"Sekuma abu d'ayan da ya d'aure mun kai."

"Ina jinka."

"Inason jin dalilin daya hana ka sanar damu k'udurinka akan Amal." Shiru yayi be amsa ba "Afzal?"

"Papi banason in zame mata distraction ne having that karatun nata beyi nisa ba, dalili na daman in bari idan tayi nisa da karatun se in fayyace mata koma mey ke tafeni kwatsam kuma sega Abdul abinda ya hanani sanar da ita kenan."

"Kayi gaskiya amma da ko nine seka sameni ka fad'a mun ba lallai se ita Amal d'in ta sani ba."

"Hakane Papi nayi kuskure amman ina sake baku hak'uri, kuyi hak'uri."

"Allah sa mu dace."

"Ameen bari in fita waje in jira Amal."

"Shago ma fa taje bansan meya ajiyeta haka ba" cewan Mami yayinda Afzal ya mik'e. "Toh se anjima."

"Ka gaishe da Abbanka."

"Toh zeji in shaa Allah" da haka ya fice yaje ya tsaya gun motansa inda yake kallace-kallace chan ya hango Amal daga jikin wani shago. K'arisawa yayi ya tsaya daga bakin k'ofar yayinda take ce da me shagon ya bata pad, dai-dai ya mik'a mata ta juya tana shirin sanyawa acikin leda kenan se kawai sukayi ido hud'u da Afzal dake tsaye a bayanta wane wani aljani. Wani irin ruwa cikinta ya d'ura ga kuma kunyan da ya rufe ta duka atake, yasar da ledan kawai tayi abun nata ya fad'i a k'asa. Dukar da kanta tayi cike da kunya. Kafin yace zeyi mata magana har tabi gefensa da hanzari ta wuce murmusawa yayi gano kunyansa taji sannan ya tsuguna ya d'au abinda ta yasar d'in ya sanya cikin ledar ya shiga binta a baya yayinda take ta hanzari ta k'arisa gida. Taku guda biyar yayi masu kyau ya kamato, hijabinta ya rik'e hakan ya sa ta tsaya ba tare da ta juya ba.

"Lily?" Ya kira ta amma tak'i juyawa. Takowa yayi ya k'ariso gabanta tare da tare k'ofar gidan nasu don karta shige, kanta tayi saurin kawarwa.

"Lily taya kikeson in fara baki hak'uri tunda ko kallona bakiya son yi? I'm sorry kinji?" Se shiru tak'i koda kewayowa ta kallesa. "I should go down on my knees? I should?" Ya tambayeta nan ma shiru. "Okay" ya furta yayinda ya shiga sauk'a k'asa.

"Don't Yaya" tayi saurin katsesa kafin ya gama sauk'an.

"Then turn and look at me" sede har anan d'in ta kasa. Sarai kuma yasan kunya takeji har yanzu na ganinta da yayi tana sayan abin chan. Kawai ji tayi ya d'aga hannunta ta cikin hijabin ya sanya mata ledan aciki "Taho kinji?" Ya buk'aceta.

"Ina sauri zan shiga gida" ta furta a hankali.

"Lily nasan ni mey laifi ne amma idan kika cigaba da shareni haka ya kikeson in nemi tubarki? Please come down with me" bata sake yin musu ba tabarsa ya jata zuwa kan benchin dake wajen gidan nasu. Bayan data zauna shima ya zauna a gefenta.

"I'm sorry, I'm so sorry Lily ban san ta ina zan fara baki hak'uri ba I know I've wronged you in so many ways but I'm sorry, I'm sorry for making you pass through all those pains kiyi hak'uri."

"Ba komai ya riga ya wuce" ta amsa ba tare da ta kallesa ba.

"Lily mey zanyi kiyi hak'uri ki kalleni? Yaya is sorry."

"It's really okay" ta amsa had'e da juyowa tana kallonsa.

"Thank you, Lily na san yadda kika tsaneni yanzu and I don't blame you ni na janyo komai, if only I could stop myself from loving you I would have ko dan kar in shiga tsakaninki da Abdul."

"Ka dena kawo maganansa."

"I'm sorry I really am."

"Why didn't you tell me for all these time Yaya?" Ta tambayesa.

"Saboda nasan bazaki amince dani ba" ya amsa take.

"Meyasa kace haka?"

"Saboda kina son Abdul."

"Ina nufin kafin mu had'u da Ya Abdul."

"Nima ban san mey ya hanani ba Lily but maybe kodan kunya nakeji."

"Kunya?" Ta tambayesa da mamaki.

"Yes Lily I'm not your Yaya after all tunda har na bari zuciyata ta koyi sonki, ke kin iya kinyi respecting relationship namu ni kuma na kasa yin hakan har na bari soyayyarki tayi nisa a zuciyana, I felt disgusted at myself na rasa da wani idon zan sake kallonki and now I feel so sorry na shiga tsakaninki da Abdul da nayi, wallahi ban san su Abba sunzo nan ba se jiya yake sanar dani. Amal bana son in kasance sanadin k'unci da rashin walwala a rayuwarki if you know you can't find a place in your heart for me please tell me I can bring back Abdul for you, farin cikinki yafiye mun komai, we marry because of love not pity, ba sekin aure ni ba idan bakiya sona I will understand you."

"Lafiyanka kuma fa Yaya? Ko ka
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment