Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

yasamu heart attack ne."

  "Ciwon zuciya??" Ta nanata had'e da zaro idanunta waje. "Me ya had'a Yaya da ciwon zuciya Ya Sultan dan Allah kace wasa kake."

  "Ba wannan a tsakanin mu Amal and bazan 6oye miki ba kece nan sanadin wannan rashin lafiya nasa."

  "Inna lillahi wa inna ilaihi raji'un ni kuma Ya Sultan? Dan mey zaka ce nice sanadin rashin lafiyan Yaya bayan kasan nafi kowa damuwa da lafiyarsa da kuma farin cikinsa, dan Allah ka rufa mun asiri" kuka ta shiga yi sosai.

  "Na k'aryata hakan Amal so kike kice har yanzu baki fahimce komai ba?"

  "Komai game da me fa?"

  "Taya zakice har yanzun baki gane cewa Afzal na son ki ba? Tayaya Amal?" Wani irin sara kanta yayi mata yayinda jiri ya d'ibeta daba don Sultan da yayi saurin tareta ba da tuni ta sha k'asa, k'aryata zancensa ta shiga yi tana kad'a kai yayinda take kuka na hak'ik'a.

  "Ya Sultan baka gane bane, baka gane ba Yaya ba sona yake ba. Yaya baze ta6a sona da wata manufan ba, dan Allah kabar fad'in haka."

  "Dalili? Kibani k'wak'k'warar dalilin da ze hana Afzal sonki Amal, kin d'au duk hidimar nan da yake miki a banza ce? Ko mey yakeyi muddin ke kika kira bari yake and be at your service you think it shall go in vein just like that?"

  "No amma kuma idan har dagaske ne Yaya yana sona da ya sanar dani idan beyi hakan ba kuwa ko Papi ne ze samu ya fad'a mishi baku gane bane Yaya ba sona yake ba."

  "Sosai yana da niyyan yin hakan sede baya son ya raba miki hankali ne daga karatu Amal, so yake se idan lokacin yayi ya sanar dake kwatsam se gashi kin samu wani har kun daidaita taya kike tsammanin zeji? Taya ciwon zuciya baze kama shi ba?"

  Salati kawai Amal ke ta nanatawa bayan nan ta kasa furta koda uffan. Meyasa bata gane cewa sonta Yaya yake ba?
 
  "Nide na fad'a miki kuma ina sa ran zaki d'au mataki ki ceto mana ran Afzal ke kad'ai keda ikon hakan."

   Taya ya Ya Sultan? Ta tambayesa cikin kuka sosai "Ya za'ayi nayi hakan? So kake in je in samesa a matsayina na mace in ce masa ina sonsa bayan banji daga bakinsa shi yana sona ba?"

    "I've said my own amman duk abinda ya samu abokina bazan yafe miki ba."

  "Ya Sultan ya kake magana haka? So kake in haukace in rasa raina? Kafi kowa sanin yadda farin cikin Yaya yake da matuk'ar muhimmancin a rayuwata. I'm willing to sacrifice everything for Yaya amma Ya Abdul fah? Meyasa Yaya be sanar dani tun wuri ba har ya bari soyayyan wani ya shiga zuciyana?"

  "Ban sani ba nima Amal, Afzal nada wani irin hali ko abu na damunsa bai son nunawa ko ni nan da nake miki wannan magana bawai shi Afzal d'in ya sameni ya fad'a min hakan bane, ni na karance sa har na gano hakan. Afzal na sonki Amal, idan har da zakiyi adalci kuma kema kin sani ba wanda ya kamanci soyayyar ki kaman shi. Rai ne kawai Afzal be d'auka ya baki ba, is about time kiyi repaying all the kind gestures da ya miki, nasan da ciwo amma ya zama dole ki rabu da Abdul naki kibawa Afzal soyayyar ki it is the only thing that can save his life." Shiru tayi tana share hawayenta, "Shin bazan iya zuwa in duba sa ba? I want to see him, I want to see him so badly."

  "Hakan zeyi wuya amma zanyi iya k'ok'ari na inga kin samu ganinsa."

  "Are you free yanzu? Zaka iya kaini?"

  "Sure let's go." Asibitin suka koma inda ya barota acikin mota ya fito ya samu Ummi yake ce mata taje gida ta huta ze cigaba da kula da Afzal zuwa lokacinda zata dawo bata masa musu ba ta kira driver ya kaita gida. Dama ba Nazeefah ba Mummy don haka ya shigo da Amal ya tsaya daga bakin k'ofa yana guarding nasu. Rawa jikinta yake sosai yayinda ta k'arasa cikin d'akin nasa ta zauna kan kujerar dake gefen gadon nasa. Wani irin mumunar tausayinsa ne ya kamata, ina ma ace zata iya kar6e rashin lafiyan nasa ita tasha wahala a maimakonsa. Sam wannan rashin lafiya be kamace sa ba, "Yaya?" Ta kira sunansa a hankali.

  "Yaya dagaske ne? Dan Allah ka tashi kace musu k'arya ne. Yaya in har abinda suke fad'a gaskiya ne meyasa baka sanar dani ba? Yaya kafi sanin kowa yadda nake sonka, I'll sacrifice everything for your happiness mesa baka sanar dani da jimawa cewa wannan ne k'udurinka akaina ba har kabari na shigo da Ya Abdul cikin rayuwata? Kana tunanin da kaina zan gano hakan ne? Tabbas yaci ace na gane hakan amma banyi ba, I'm so sorry for every pain Yaya please forgive your Lily" tasa k'asan hijabinta tana share hawayenta. Tafi minti biyar zaune a gun tana aikin kuka akansa kawai taga alaman yayi blinking idonsa.

  "Ya Sultan!" Ta k'wala masa kira ba shiri ya shigo ciki yana tambayarta ko lafiya. "Yaya ne yayi motsi get his doctor" a guje ya fice dan nemo likitan. "Yaya please open your eyes it's me your Lily, I'm right here kaji? You can do this" kalamun kwantar da hankali tayita furta masa a hanakli ya shiga bud'e idon nasa har ya bud'esu duka had'e da sauk'esu akanta.

  "Yaya you're alive! You're alive" tasa ihu tana share hawayen farin cikin dake sauk'o mata. Kallonta kawai yake amman ya kasa cewa komi ahaka ne har Sultan ya dawo da Dr'n Afzal inda ya masa wasu gwajin ya tabbatar da cewa condition nasa is stable sannan ya fice.

   "Yaya baka gane ni bane? It's me your Lily." Maida kallonsa akan Sultan yayi idonsa suna d'auke da d'imbun tambayoyi gano hakan Sultan yayi saurin cewa "bari in kira Ummi ina zuwa" nan ya fice ya barsu su biyu a d'akin.

  "Yaya?" Ta kirasa sede ina yak'i koda juyawa ya kalleta. "Yaya I'm sorry, I'm so sorry dan Allah ka juyo ka kalleni" nan ma shiru. "Yaya I'm so sorry dan Allah ka dena fushi dani kayi hak'uri" sede fa duk had'asa da Allahn da tayita yi yak'i koda kallonta. Haka ba yadda ta iya ta mik'e tabar masa d'akin.

  "Ya haka?" Sultan daya ga yadda take kuka yayi saurin tambaya.

  "Yaya yak'i ya kalleni balle ma yamin magana, Ya Sultan ban san ya zanyi ba dan Allah ka basa hak'uri."

  "Yak'i ya miki magana kaman ya?"

  "I told you Yaya ba sona yake ba kune baku gane ba, I can't do this anymore ni zan tafi kawai."

  "Ah'ah ki tsaya tukuna" d'akin Afzal ya shiga ya zauna gefensa.

  "Ya jikin naka?" Ya tambayesa.

"Meyasa ka kawo ta nan? Ina su Ummi?" Abinda ya soma cewa kenan.

  "Abinda kad'ai zaka iya cewa kenan?Ka lek'a lahira ma bazaka zubar da wannan halin naka bako?"

  "Ba abinda na tambaya ba kenan ina Ummi? So kake su ganta? Mesa kake abu baka tunani ne kam Sultan? So kake se sun ganta sunyi zargin wani abun?"

  "Ai ko basuyi zargeta bama ni zan sanar dasu komai."

  "Komai kaman ya?"
 
"A tunaninka baki na zeyi shiru ne? Na riga na sanar da Amal gaskiyan al'amarin cewa kana sonta sauran idan su Ummi sun iso suma in fad'a musu haka kawai ina ji ina gani bazaka cigaba da punishing Nazeefah ba bayan ita batayi komai ba."

  "Kayi meh kace?" Afzal ya tambayesa cike da tashin hankali yayinda zuciyansa ya tsinke da sauri ya rik'e wajen daya fara yi masa zafi. "Gara ka kwantar da hankalinka kabi komi a hankali dan idan wani attack d'in ya sake kamaka se lahira yanzu."

   "Amma me na fad'a maka? Ni na fad'a maka ba son Amal nake ba don mey zaka sameta kace mata ina sonta? What is the meaning of this Sultan?"

  "Aww har yanzu bazaka yi admitting son da kake yi wa yarinyar nan ba?"

  "Sultan just get out idan har kasan suratan banza zaka cigaba dayi ka tashi ka bar min d'aki."

  "Yanzu kai fisabilillahi baka tausayawa kanka da ita Nazeefah harda Amal d'inma? Wallahi girman kan nan ba inda ze kaika illa halaka Nazeefah bata san hawa ba bata san sauk'a ba aka d'aura mata laifin komai, Amal na da wanda takeso amman ya zama mata dole yanzu ta rabu dashi saboda kai duk hakan be isheka ba bazaka hak'ura ka amince da komai ba?"

  "Ni ban rok'eta tabar wanda take so ba Nazeefah kuwa ni bani na fad'awa su Ummi suyi blaming nata ba saboda haka nima kadena blaming d'ina."

  "Da kyau" yace dashi had'e da mik'ewa yabar masa d'akin kafin ya fita har Amal ta tafi nemanta ya shiga yi chan sega Nazeefah shigowa.

  "Ina yini?" ta gaishesa.

  "Lafiya Nazeefah ya hidima?"

  "Alhamdulillah wai Afzal ya farfad'o?"

  "Eh yana ciki kije ki samesa."

  "Toh ya naga kaman kana neman abu? Lafiya?"

  "Ko kinga wata yarinya da farin hijabi a hanya?"

  "Wata doguwa hakan nan?"

  "Eh ita."

  "Ina shigowa naga tana tsaran napep."

  "Toh shikenan thank you." Da haka ta wuce d'akin Afzal knocking tayi sannan ta shige. Basket na abincin ta ajiye akan table sannan ta k'arasa ta zauna a gefensa.

  "Afzal ya jikin naka?"

  "Da sauk'i" ya amsa k'asa-k'asa.

  "Thank you for staying alive, Allah k'ara maka lafiya."

  "Ameen thank you" ya amsa.

  "In sa maka abinci?"

  "I'm not hungry."

  "Afzal kaman ya baka jin yunwa? Rabonka da abinci tun yaushe? Dan Allah kayi hak'uri in sa maka koda kad'an ne kaji?"

  "Nace bana jin yunwa" bata sauraresa ba ta d'iba ta d'au ruwa tazo ta zauna gefensa. "Tashi ka zauna kaji? Please don't say no."

  "Afzal magana fa nake maka dan Allah kayi hak'uri ka tashi" kaman wanda baze motsa ba ya shiga mik'ewa sede hakan ma ya gagara k'arshe seda ta taimaka masa. Abincin ta d'aga ta mik'a masa "Zaka iya ci ko in baka?" Beko kalleta ba ya amshe plate d'in bayan da ya k'are wa abincin kallo ya maido da kallonsa a gareta.

"Afzal lafiya?" Ta tambayesa saidai still kallonta yake. "Afzal tunanin ko wani abun na sa maka aciki kake? Dan mey zan cutar da kai? Wallahi ba komai aciki ina iya d'ibawa inci a gaban ka idan baka yarda dani ba" ganin ta mik'e yayi saurin cewa "Don't bother ki zauna" komowa tayi ta zauna yayin da ya shiga ci a hankali.

Murna kenan zan so kuga farin cikin daya bayyana a fuskan Nazeefah rabonta da tayi farin ciki irin na yau a rayuwarta har ta manta. Finally Afzal ya d'and'ana girkinta yau. Zama tayi tana kallonsa yayinda yake ci a hankali dududu beci ya kai rabi ba yace ya k'oshi. Ita a hakan ma ta gode.

  "In had'a maka ruwa kayi alwala ko?" Nan ma kai zalla ya gyad'a mata bata kai da mik'ewa ba sega Ummi ta shigo. Da gudu tayi kansa had'e da rungumosa yayinda hawaye ya ciko mata a ido.

  "Prince you're back! Alhamdulillah! Alhamdulillah!" A hankali ta sakesa ta shiga shafa fuskansa "Prince na d'au zaka tafi ka barni."

  "Come on Ummi, I'm here."

  "I missed you."

  "I missed you too bari inyi sallah."

  "Haka fa kafin nan kaci abinci? Barin aika driver yaje ya siya maka don miyan kuka akayi a gida."

  "Karki damu Nazeefah ta taho da abinci." Ita bata ma lura da presence na Nazeefah ba seda ya ambaci sunanta.

  "Nazeefah?" Ta juyo da mamaki tana kallonta.

  "Na'am Ummi?"

  "Prince?" Ta juya tana kallonsa shima.

  "Yes?" Ya amsa.

  "Kana lafiya? Ko a kira ma likitan ka?"

  "Why wani abu ne?"

  "Prince mun d'au ai idan kaga Nazeefah ciwon naka ze tashi ke Nazeefah ba ance ki kiyayi shigowa d'akin nasa ba kar wani abu ya samesa" Shiru Nazeefah tayi dan ko bata san me zata ce ba, tsana k'iri-k'iri both mahaifiyarta da surikarta suke nuna mata. Idanunta ta d'ago a raunane tana kallon Afzal tana jiran jin ko zeyi magana dan shi kad'ai yake da ikon wanketa daga wannan daud'a da su Ummi suke ganinta da.

  "Meyasa?" Ya tambayi Ummi a k'arshe.

  "Prince meye silar ciwon nan naka? Ba Nazeefah bace?"

  "Waya ce muku itace?"

  "Prince mey kake fad'i wai kam?" Ta tsaya kallonsa da mamaki.

"Nazeefah batayi komai ba I'll ask you to keep her away from this." Tirk'ashi wai meke faruwa ne? Ummi ta tambayi kanta "Kaje kayi alwalan zamuyi magana idan Abbanka ya iso munyi waya dashi d'azu jirginsu ya tashi." A nitse ya mik'e ya k'arisa bayin ya d'auro alwala kamin ya fito har Nazeefah ta shinfid'a masa sallaya. Sallolin daya rasa ya shiga ramawa. Ana cikin haka Mummy ta shigo itama suka gaisa bayan da ya idar d'in take sanar dashi abinda ke tafe da ita na cewa Daddy ya turota ne akan idan har ya ga baze iya ba da rashin hankalin Nazeefah ya sawwak'e mata kawai su koma gida yanzu tunda de tace ita bazatayi hankali ba. Kafin Afzal yayi magana Ummi ta rigasa.

"A'a shiko Alhaji ai ba haka akeyi ba, zama yakamata shi da Abban Afzal suyi da shi Afzal d'in kansa a dai-daita koma menene koba haka ba?"

  "Dan Allah kibar maganan nan Hajiya Mariam banason ganin ranan da za'ace ga 'yata nan ta kashe d'an wani kuma idan aka cigaba da tafiya haka tabbas wataran Nazeefah zata aikata hakan tunda gashi ta d'au hanya har ta sanya masa ciwon zuciya." Shiru Afzal da suke tsammanin zeyi magana yayi. "Afzal?" Ta kira sunansa yayinda da ya d'ago kai yana kallonta "Mey kace kai?"

   "Mummy ni Nazeefah bata yimun komai ba don haka bazan saketa ba kuma ina rok'anku da kudena blaming nata akan laifin da ba ita ta aikata ba" Wani irin sanyi Nazeefah ta jiyo a ranta bata tsamman Afzal ze kareta haka ba.

  "Wani irin magana kake ne wai Prince? Idan ba Nazeefah ba toh waye?"

  "Ni ba wanda ya d'aura mun ciwo banda Allah, kuma na rungumi k'addara."

  "Ya kake neman raina mana hankali ne kam Prince? Dama ansan ai lafiya da rashinsa daga Allah ne ko ka ta6a jin jinin mutum ya hau ciwon zuciya ya kamasa ba tare da tashin hankali ba? Wallahi to kar kayi magana Abbanka na nan tafe idan yazo se muga ko wannan silly answers d'in zaka basa Hajiya Fatsuma tashi in raka ki Afzal is not willing to talk."

****
  Amal ce kwance akan katifarta se aikin kuka take, gabad'aya ta rasa meke mata dad'i tun dawowanta gida bata sake lek'a waje ba. Ba yadda Mami batayi da ita ba amman tak'i fad'a mata ainihin meke faruwa. Toh ma ta ina zata fara? Ta ina zata fara sanar da Ya Abdul wannan zance? Wayanta ta jawo ta shiga viewing pictures nasa da kuma nasu da suka d'auka tare, tana son shi tana son shi na sosai bata jin zata iya rabuwa dashi aman kuma ta d'ayan 6angaren bata son Sultan da shi kansa Afzal d'in da kuma duk wanda wannan labari ya iskesa suyi mata kallon butulu. Sedai har yanzu takasa amincewa da maganganun da Sultan ya sanar da ita, gashi abin haushi sun kasa dena yawo akanta.


***
   Ba yadda Ummi batayi da Afzal ba akan cewa ya taho gida da ita amman yayi insisting yace shi fa Nazeefah ze bi. Haka nan suka komo gida tare ta tambayesa ko me yakeson ci. A karo na farko kam babu ya sanar da ita. Seda tayita had'a sa da Allah sannan yace indomie ma yayi. Ba tare da 6ata lokaci ba ta wuce kitchen ta shiga girka masa. Nan ya d'auko wayansa dake cikin wardrobe, gabad'aya gani yayi battery d'in yayi draining. Had'awa yayi bayan ya kawo wuta ya soma cin karo da sak'on Amal da sauri ya bud'e ya karanta kaman haka. 

  'Get well soon Yaya, my prayers are with you.'

  Duba lokacin da sak'on ya shigo yayi yaga wajajen k'arfe shida ta turo. Maida wayan yayi yayinda ya fad'a duniyan tunani. Yanzu da wannan shirmen da Sultan ya tafka masa da wani idon ze sake kallon Amal?

Washegari Abba ya turo driver akan ya taho da Afzal idan kuma jikin nasa baze iya barinsa ba shi da kansa yana iya tahowa su tattauna komai. Wanka yayi ya karya sannan suka fice. Suna is ya zarce parlourn Abba inda yaci karo da Sultan, take gabansa ya fad'i don mey za'a kira Sultan? Yana da tabbacin cewa aikin Ummi ne wannan. A nitse ya k'arisa d'akin ya zauna se kallon Sultan yake ko idonsu ze had'u yayi masa ido komin mey kar ya fad'i komai amman yadda kukasan gunki tun zaman Sultan ko kewaye-kewaye yak'i yi. Gaisawa sukayi da Abban yake tambayansa ya jiki sannan da Ummi bayan nan Abba yayi gyaran murya.

"Ina jinka Prince meya faru?"

"Abba babu" ya amsa kansa a duke.

"Idan kun kasa jituwa da ita Nazeefan ne ai seka taho gida kamun bayani amfanin idan iyayenka suna raye kenan bawai ka tsaya kana bin abu a zuciya ba."

"Abba ni Nazeefah bata yimun komai ba."

"Sorry ban fahimce ka ba."

"Nazeefah has nothing to do with this Abba" ya sake nanatawa Ummi dake gefensa ji tayi wane ta hankad'esa don haushi ita ta rasa dalilin da yasa yake rufa mata asiri.

"Toh wanene?"

"Babu."

"Nace wanene?" Abba ya sake tambayansa cikin tattausar murya.

"Abba matsala muka samu a office wanda nayita bi da zuciya shikenan."

"Prince d'ago kai ka kalleni" ba gardama yayi hakan "Yanzu ni zaka kalli cikin idanu na kayi mun k'arya wallahi sam wannan ba d'abi'ar ka bace I'm very disappointed in you."

"Abba kayi hak'uri."

"Sultan?"

"Na'am Abba" ya amsa.

"Tabbas nasan kana sane da duk wani abinda ke faruwa tunda Afzal ba shida amini sama da kai I'll ask you to tell me what is really going on idan ko kayi mun k'arya Allah na kallonka." Shiru Sultan yayi yana nazarin sanar da Abba gaskiyan batun ne koko a'a. Amma ai dan abokinsa besan ciwon kansa ba doesn't mean shima ya biye masa.

"Sultan magana nake maka."

"Abba a gaskiya ni ban san mey zahirin maganan ba don ko ni nan Afzal be ajiye ni ya sanar dani abinda ke damunsa ba sede in baka amsa base on yadda na karanci yanayin sa."

"Bismillah ina jinka."

"Akwai wannan yarinyar da Afzal keyi ma hidima wanda da zama yayi zama na soma ganin alamun son yarinyar a tattare da shi koda na gwada masa magananta akan cewa is about time ya sanar da ita k'udirinsa kuwa se abin ya koma fad'a ransa ya 6aci. Toh kwatsam kawai se mukaji yarinyan ta samu wanin da har sun dai-daita dashi sunyi nisa. A tunani na wannan ne dalilin daya jefa Afzal cikin wannan hali dan tun daga lokacin ban sake gane kansa ba ko office nasu naje acikin tunani nake tsintansa kullum." Tunda Sultan ya soma bayanin Afzal ya dukar da kansa k'asa amman baze ta6a yafe masa wannan d'anyen aikin daya masa ba.

"Ko kasan yarinyar da kuma iyayenta?" Shiru Sultan yayi yana nazarin sanar dasu gaskiya koko a'a sarai ya sani idan yayi hakan Afzal na iya fushi dashi har abada don haka ya kad'a kai "Ban san komi akanta ba Abba banda hotunan ta da nake gani da a wayansa kafin ya goge."

"Shikenan Sultan nagode Allah sak'a maka da alheri kana iya tafiya."

"Ameen Abba, Ummi ni zan wuce."

"Mungode sosai Sultan ka gaida gida" yana ficewa Ummi ta maido da kallonta akan Afzal "Ai dama na sani nasan za ayi haka kai baka san ciwon kanka bane kake neman kai kanka ga halaka akan mace iyye? Macen da kana da tabbacin zata amince da k'udirinka muddin idan ka sanar da ita amman kak'i har wani can ya sace maka ita? Meye amfanin mu Afzal da bazaka zo ka sanar damu damuwanka ba?" Shiru yayi bece komai ba.

"Afzal?" Abba ya kirasa.

"Na'am" ya amsa.

"Wacece wannan yarinya?"

"Abba ni fa ba wata yarinya ni kaina ban san a ina Sultan ya had'o wannan labari ba ya baku kaman yadda na fad'a maka matsala muka samu a office na kusan rasa aiki na shine nabi a zuciya."

"Nace wacece yarinyar?"

"Abba I'm sorry amman kaman yadda na fad'a maka ba wata yarinya."

"Afzal wai meke damunka ne? Kai bakasan zurfin ciki na kai mutum ga halaka ba?"

"Ya isa Hajiya Mariam bar shi tashi ka tafi Allah k'ara ma lafiya."

"Ameen nagode" yana kaiwa nan ya mik'e Ummi ce tabi bayansa tare da k'wala masa kira.

"Prince meke faruwa ne? Meya sameka? Prince idan baka sanar dani damuwanka ba mawa zakayi hakan? Wallahi koma wacece wannan yarinya da kakeso kasa zuciyanka a ruwan sanyi dan ka riga ka sameta just tell me wacece ka kuma bani address nata."

"Ummi nagode amman ya kamata ki gane cewa ba wata yarinya."

"Da kyau Prince yau ka nuna min matsayina dake ba ni na tsuguna na haifeka ba dole ina tambayanka abu kana 6oye mun."

"Ummi please wani irin magana kuma kike?"

"No ka tafi nagode" nan ta juya ta shiga tafiya duk kiran da Afzal keyi mata tak'i juyawa har ta k'arasa site nata.
Tunanin had'uwansa da Sultan kawai yake a dalilin mey ze fad'awasu Abba gaskiyan al'amarin?



RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 00:40] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣7⃣*



Yadda yak'i kiran Amal ita ma haka bata sake kiransa ba iyaka sak'on da ta sake masa sending take tambayarsa ya jiki Allah k'ara lafiya. Anan d'inma k'in replying yayi. Kan Ummi ya samu shawo bayan wuyan da ya sha dan sosai tayi fushi da shi amman dukda hakan yak'i sanar da ita batun Amal se musantawa yake sam fa shi ba wata yarinya. Bayan tafiyansa Ummi ta kira Sultan take rok'ansa cewa idan har ya san gidansu yarinyar nan karya 6ata lokaci ya fad'a mata kar ya biye wa abokin sa amman sanin abinda hakan ke iya haifar wa tsakaninsa da amininsa ya busar da ido yace wa Ummi shi sam be sani ba ai idan da ya sani ko basu tambaya ba ze sanar da su a haka ya samu sukayi sallama.

Abba kuwa be sake yi takan Afzal ba tunda kusan sau uku yana tambayansa abu d'aya amman yak'i sanar dashi idan tayi tsami shi da kansa ze bud'a bakinsa ba se an rok'esa ba. Sau dayawa Ummi na bawa Abba hak'uri akan ya sake kiran Afzal yayi masa magana k'ila ya amince ya fad'a musu damuwansa amman ina shifa Abba yace ba ruwansa again.

Kwana biyu Afzal ya d'auka sannan ya warware ya soma fita office, da safe Nazeefah ta tashi ta had'a mishi breakfast harda coffeen sa a flask da ze tafi da shi, yau
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment