Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

masa godiya har ya k'arisa cikin motansa yana k'ok'arin tada ita. Seda taga ficewansa sannan ta k'arisa ciki. Ko mutum be tambaya ha yasan ransa ya 6aci, daga yadda yayi magana ma.

Kud'in ta mik'awa Mami akan gashi Afzal ya bata. Zaunar da ita Mami tayi "Baby?"

"Na'am?" Ta amsa.

"Yanzu kina ganin kina kyautawa Afzal kenan?"

"Mami ni kuma mey nayi?"

"Kisani wallahi koda ba don istikharan nan da kikayi ba, bawanda ya cancanci soyayyarki sama da Afzal ki tuna da kalan hidiman da yaron nan ya miki ba ke kad'ai ba harta ni da Papinki. Be sanmu ba, besan daga ina muke ba amma ya d'au nauyin karatunki, kud'in takardu da handouts tun kafin ki tambaya yana baki amma ace kike wulak'antasa haka Baby? Wallahi samun mutum kaman Afzal a zamanin yanzu se an tone. An sani rabuwa da masoyi da zafi amma yaci ace kin yayyafawa zuciyarki ruwan sanyi be kamata ace har ki bari Afzal ya fahimci cewa bakiya sonsa ba."

"Mami ni yaushe nace bana son Yaya? Wallahi ban ta6a furta hakan wa kowa ba."

"Amma haka halayyanki suke nunawa abinda nake fad'a kenan. Kuka ne kawai be min ba ranan gabad'aya kin tada masa hankali har yake cewa shi ze hak'ura kawai a dawo maki da Abdul d'in haba mana Baby ki sani fa ba duk abinda mutum keso yake samu ba a duniyan nan. Yanzu gashi duk da kalan rashin mutuncin da kike masa hakan be hanasa baki kud'in k'arshen watan ki ba harda k'arin dubu ashirin akai."

"Zan kirasa inyi masa godiya."

"Da kin kyauta dan babu dad'i hakan kiyi hak'uri ki sani Abdul ya riga ya miki nisa ki bud'ewa Afzal zuciyarki sanin kanki ne Afzal baze ta6a cutar dake ba."

"Mami na sani."

"Toh kina iya tafiya Allah yayi maki albarka."

"Ameen" da haka ta wuce d'akinta. Wayarta ta d'auka ta kira Maamah se a karo na biyu ta d'aga kasancewar bata san layin ba.

"Halo Maamah? Amal ce."

"Amal? Ya kike."

"Lafiya k'alau ya kwana biyu?"

"K'alau ai na d'au nima baza a nemeni da sabon layin bane."

"Haba Maamah ya gida?"

"Lafiya k'alau jiya Ya Abdul ya kirani wai baya samun line naki."

"Allah sarki Ya Abdul I miss him already please komin ya za'ayi karki basa sabon layi na bana son in cigaba da zolayansa Maamah, ina tausayawa kaina but I pity Ya Abdul the most."

"Haka ma Mama tace."

"Maamah I'm so sorry for hurting your brother."

"Ba komai Amal ai yin Allah ne ba naki ba."

"Thank you so much for everything."

"You're welcome."

"Toh sekiyi saving numban nawa se mun had'u a school ran monday."

"Alright I'll" da haka sukayi sallama bata kaiga ajiye wayan ba sega call na Ya Abdul. Ko gaisawa be bari sunyi ba ya hau kurareta akan tabar duk abinda takeyi taje gidansu Amal taji ko lafiya haka kawai yana ji a jikinsa ba k'alau ba. Corner-corner tayita masa akan yau bazeyi ta fita ba seko gobe haka nan ma washegarin daya kirata tace ai taje gidan su Amal d'in Mami tace bata gida amma lafiyarta k'alau. Matuk'a hankalinsa ya d'an kwanta na jin lafiyanta k'alau amma rashin jin muryarta hankalinsa ya kasa kwanciya gabad'aya.

Amal ko sosai take kewansa sede gabad'aya ta rasa me take ciki, sosai maganan da Mami tayi mata keta yawo mata a kai tun jiya se tunanin magann take gashi har yau bata kira Afzal d'in ba seta d'au wayan zata kirasa se ta fasa. Haka tayita yi har tazo ta kirasa k'arshe. A lokacin suna tare da Nazeefah suna kallo, ya tashi ya amsa yana gudun kar ta fahimci wani abun, yayi rejecting call d'in kuma baze iya ba haka kawai ya rufe ido ya d'auka.

"Assalamu Alaikum" ta soma da cewa.

"Wa'alaikumus salam" ya amsa sa6anin yadda ya saba kiranta da Lily yau sallamar kad'ai ya amsa ita ko se ta d'au kodan abin da tayi masa ne yake fushi.

"Yaya I'm sorry" ta furta chan ciki-ciki.

"Ba komai karki damu."

"Dama na kira ne inyi maka godiya tun jiya ina trying numbanka baya shiga" tayi mai k'arya.

"Ayya bakomai."

"Wannan ne new line nawan se kayi saving."

"Alright I'll se anjima" nan ya katse, da mamaki Amal ta tsaya kallon wayanta yau har Yaya ne ya katse waya a kanta? Hmm

Nazeefah kuwa kallon sa ta tsaya yi tana nazari kode da budurwansa yayi wayan ne? Kud'i ya bata ne take godiya har yake cewa ba komai? Amma kuma ai idan budurwarsa ce baze bari ma ya amsa wayan a gabanta ba, toh ko business colleague tasa ce?

Kwana hud'u Maamah ta jera tana raina wa Ya Abdul wayo tun be d'auki abun da zafi ba har ya fara zaton wani abun daban. K'arshe da abun ya ishesa Mama ya kira yake ce mata gashi kwana biyu baya samun Amal yayi da Maamah da ta had'asu amma abun ya gagara inda hali please ko ma waye ne asamu a tura gidansu Amal d'in aji ko tana lafiya, Mama bata nuna masa komai ba tace washegari zata tura ayo bincike se anan hankalinsa ya d'an kwanta sede har gari ya waye rana ya sauk'a Mama bata kirasa ba duk yadda ya k'osa haka ya hak'ura ya bari se a jibi sannan ya sake kiranta itama wani hujjan ta nema ta sake basa. Haka suka yita waina sa, suna masa wasa da hankali ba wanda ya iya fitowa fili ya sanar dashi zahirin abinda ake ciki, ta fannin Amal kuwa duk yadda take missing d'insa hakan besa ta d'au waya ta kirasa ba dukda cewan bata k'i hakan ba. So dayawa takan zuba numbansa da niyyan zata kirasa amma idan ta tuna da fad'an Mami na ranan seta fasa. Sosai fad'an ya shigeta haka ko tana kewansa sede ta rufe kanta a d'aki ta sha kukanta amman bade ta kirasa ba. Hotunansu kuwa har yau ta kasa gogewa haka zata zauna tana kalla tana kuka.

Ta fannin Afzal kuma tun kan amsan da Amal ta basa ranan akan cewa ita bata shirya auransa ba gabad'aya ya rasa walwalansa ko kiranta be sakeyi ba, a gida kuwa ba yadda Nazeefah batayi da shi ba amman yak'i sanar da ita halin da yake ciki haka ya bari abin yayita chin sa har seda wani attack d'in yaso kamasa. Daga fitan Nazeefah d'auko masa ruwa dawowan da zatayi kawai ta tarar da shi zube a k'asa se birgima yake yayinda ya rik'e saitin zuciyansa inda yake masa k'una sosai, se wani sama-sama numfashinsa ke masa. Salati tasa yayin da yasar da goran ruwan a k'asa ta nufi kansa da gudu tana k'walla masa kira.

Kafin ta tashi tace zata nemi mai gadi dan yazo ya d'aukesa su kaisa asibiti ya rik'e hannunta. "Don't call Ummi.." ya furta da k'yar yayin da ya shiga yin tari.

"Afzal so kake ka mutu ne? Barin kira D'an ladi stay calm kaji?" Ta buk'acesa a rud'e "Don't call Abba too please" ya rok'eta kai tayi saurin gyad'a mai sannan ta kira D'anladi nan da nan ya cicci6esa suka yi mota. Akan cinyarta ta ajiye kansa yayinda take ta kuka ganin yadda yake wasu irin abubuwan wane wanda ake cire ma rai.

Sintiri ta rink'ayi bakin k'ofan nasa gabad'aya ta rasa me take ciki gashi yace mata karta kira su Ummi shin ta biye masa ne ko ta kira sun? Amma kuma tasan halinsa sarai ba k'aramin aikinsa bane idan ya farfad'o ya gansu akansa yayi mata fushi. Haka nan ta rasa me take ciki chan da likitan nasa ya fito ta nufi kansa tana tambayansa ya jikin nasa.
Ya buk'aceta ne da ta kwantar da hankalinta Allah yaso an samu an kawosa asibitin da wuri tun kafin heart d'in yayi failing, an kuma basa immediate treatment yanzu sauran a jira farfad'owansa nan da kaman minti ashirin haka. Hamdala ta saki yayin da ta shiga yi masa godiya. Bayan sa tabi ta shige d'akin Afzal inda ta tsince sa kwance kan gadon, wane wanda k'wai ya fashewa a ciki haka sid'ak-sid'ak ta k'arisa ta zauna kan kujerar dake gefen gadon nasa yayinda hawaye ya ciko mata dam a ido. Sunansa da tace zata kira kawai se hawaye. Kuka sosai ta sha wajen ta rasa me ke janyo masa bugawan zuciyan, komi da ta sani baya so tana iya k'ok'arin dainawa amma ace ciwo yak'i ci yak'i cijewa? Ita abu d'aya take gudu ranan da zuciyar nasa zata buga gabad'aya tak'i aiki tasan ko sama da k'asa zata had'a ba wanda ze ta6a amincewa akan ba ita ce sanadin ciwon nasa ba. Tana cikin kuka ba makawan ne Afzal ya shiga kyafta idanunsa har ya bud'e su gabad'aya. Da mamaki ya tsaya yana kallon yadda take kuka gabad'aya se ta basa tausayi.

"Afzal" ta kira sunansa a hankali ko amsata ya kasa. "Dan Allah idan wani abun nake maka wanda ka kasa furta mun please tell me I'm tired of seeing you collapsing everyday like this idan wani abun nakeyi maka wanda baka jin dad'insa please tell me."

"Nazeefah" ya kira sunanta cikin dashasshiyar murya.

"Please tell me Afzal I promise zan yi iya k'ok'ari na inga na kiyaye."

"Bar kukan haka kinji?" Yayi maganan yn neman share mata hawayen nata. Fuskan nata taja baya "Not until you tell me mey ke jawo maka attck haka please tell me idan nice."

"Bake bace bar kukan haka."

"How can I? Bazan iya ba Afzal so kake se idan ka mutu kowa yace nice na kashe ka? Dan Allah ka tausaya mun ka fad'a mun matsalar."

"Nazeefah nima han sani ba all I want is ki kwantar da hankalinki baki da alak'a da rashin lafiya na kuma ko a gaban waye me zanyi defending naki kinji? Stop bothering yourself like this."

"Then mey ke jawo maka?"

"Nazeefah I'm sorry but I can't tell you."

"Afzal nasan ba wani jituwan kirki bane a tsakaninku nasan nayi maka laifuka da dama I know I'm not the perfect girl for you, amma matarka nake kodan wannan matsayin please tell me."

"I can't Nazeefah" ya sanar da ita.

"Saboda ban kai inji damuwanka ba?"

"Sam, saboda nima ban san meke damuna ba, I have no idea why."

"Ban yarda da hakan ba Afzal tun ba yau ba nasan kana 6oye mun damuwanka zan cigaba da addu' har izuwa rananda zaka fara fad'amun damuwanka I believe mey hak'uri shi kan dafa dutse ya sha romo, I love you Afzal I'll do everything to stay by your side this's how much I love you."

"Thank you Nazeefah, come here" hannunsa ya bud'e mata a kasalance, a hankali ta shige jikinta dai-dai saitin k'irjinsa ta aza kanta yayinda ya rufeta da hannayensa yana mey shafa bayanta a hankali. "Forgive me for hurting you this much? I'm so sorry." Kai ta gyad'a masa a hankali yayinda ta sake shigewa jikinsa tana mey cigaba da kukan da takeyi. A nitse ya d'agota had'e da share mata hawayen ta "Kin kira su Ummi?"

Kai ta kad'a "Kace kar na kirasu."

"Very good thank you so much Nazeefah Allah miki albarka."

"Ameen" kafin tayi wani k'wak'k'waran motsi wayanta ya shiga ruri dubawan da azatayi taga Mummy ke kira. "Waye ne?" yayi saurin tambayarta.

"Mummy" ta amsa cike da fargaba.

"Ki d'auka."

"What if tana gida taje duba mu ne fah?"

"D'auka kice mata mun fita." Hakan ta d'aga Mummy take ce mata gata da Khhaleefah bakin gate sunata honk amma ba kowa. Kaman yadda Afzal ya buk'ata haka tayi tace mata sun fita ne D'anladi kuma yaje duban gida.

"Can I use your phone to call Sultan?" Ya tambayeta bayan da ta kammala wayan.

"Sure" tayi maganan tana mik'a masa "Amma banida numbansa."

"Don't worry I have it off hand." Numban Sultan d'in ya zuba ya kirasa.
"Halo Sultan?"

"Triple A?"

"Yes Sultan kana ina?"

"Office ina ka ajiye wayanka inata kiranka baka d'auka."

"Kazo TH please."

"Subhanallah bade jikin naka bane?"

"Yes but da sauk'i and please don't tell Umma banason su Ummi suji ina asibiti nima yanzu zance suyi discharging d'ina come quickly."

"Alright I'm on my way."
Be 6ata lokaci ba ya kar6i excuse a office ya kama hanyan TH saidai kafin nan ya kira Amal yasan sarai itace sanadin komai. Tana d'agawa yake sanar da ita ai Afzal ya sake samun wani attack d'in yanzu haka ma yana TH an rik'e shi. Sosai gabanta ya fad'i salati kawai ta shiga yi har Sultan ya ajiye wayan. Yanzu mey zatace wa su Ummi? A banza tana neman kashe musu d'a. Bata jira lectures d'in ya k'are ba ta tattara jakarta ta fice kasancewar university da TH ba nisa kusan a tare ita da Sultan suka isa tana sauk'a a napep se gashi yana k'ok'arin shiga shima. K'arisawa tayi cikin motan nasa suka shiga tare. A waiting room yace ta jirasa gudun kar kuma suna shiga suci karo da Nazeefah. Bayan ya k'arisa d'akin Afzal suka gaisa da Nazeefah sannan ta basu waje.

"Amal ce har yanzun?" Sultan ya soma da tambayansa.

"Sultan haka so yake?" Ya tambayesa a raunane. "Tunda nake ban ta6a son wani mahaluk'i sama da iyayena a duniyan nan ba, ban san haka so yake da sharri ba da nayi duk abinda zan iya na hana son Amal shigewa zuciyana."

"Triple A..."

"Sultan I'm tripping" ya katsesa, "Ban san ya zanyi da son Amal ba, ina sonta amma kona second d'aya bata sona, bata da niyyan bani daman in kasance masoyinta. she disperses me Sultan help me out please, ina jin idan ban samu Amal ba ina iya rasa rayuwana."

"Calm down Afzal, meya faru?"

"Komai ma ya faru ni yanzu nakega kawai zan hak'ura ne zan nemi transfer in d'au Nazeefah mu bar nan kawai maybe by doing so Allah ze rage mun sonta a zuciya, gar da gar ta nuna mun she can't marry me ya kake tsammanin zanji? I've tried my best to forget it but I can't, da kalamunta kullum nake tashi nake yini, I'm mad over her. And to be frank, I'm tired of seeing Nazeefah like this, gabad'aya ta d'au laifin komai ta d'aura wa kanta, na gaji I don't know what to do again."

"Mun taho tare da Amal" ya sanar dashi.

"You what?" Ya tambayesa cike da d'umbun mamaki.

"Yes tana waiting room, kana kirana itama na kirata se muka k'ariso tare."

"Why? Meyasa ka kirata? So kake su had'u da Nazeefah? Maza why?"

"Saboda tasani idan ta cigaba da abinda take yi maka tana iya jefa rayuwarka cikin matsala."

"And? Ba wai kaman ta sona bane bale idan rayuwan nawa ya shiga matsala hakan ya dameta."

"Taya zakace Amal bata sonka Triple A? Ai zuciya bata ta6a k'in me kyautata mata ya kamata ka gane cewa Amal na duk abinda takeyi ne saboda haushinka da takeji na shiga tsakaninta da Abdul amma bayan nan wallahi ko ita bata isa ta buga k'irji tace bata sonka ba."

"Wai kam bakaji me ta fad'a mun bane? Amal bata sona."

"Amal na sonka Afzal she's just too broken to realize that, gabad'aya soyayyar Abdul ne ya rufe mata ido aikinka ne ka maye gur6insa a zuciyarta idan ko kayi sakaci kana iya rasata har abada amma so kam akwai shi achan k'ark'ashin zuciyarta."

"Ko meyasa kace haka?"

"Da bata sonka da baza tabar duk abinda takeyi ta iso nan atake da na kirata ba, and you know the funniest part? Ta jirani a waiting room d'inma tak'i wai sam semun k'ariso tare, kallo d'aya mutum zeyi mata yasan tana cikin tashin hankali. Gabad'aya ta rasa natsuwarta a haka zaka ce bata sonka? Yanzu that aside, ya za'ayi in shigo da ita?"

"I don't know nide bana son su had'u da Nazeefah ban shirya ma wani masifan ba."

"Kasan ya za'ayi? I'll call Nazeefah se kace mata kana jin yunwa taje tayi maka girki kafin ta dawo de nasan Amal harta tafi."

"Sultan nifa bana son su had'u."

"Trust me" yana fad'in haka ya fice ya kira Nazeefah akan Afzal na nemanta.

K'arisowa tayi ta tsaya a kansa tana shafa kansa a hankali "Kana buk'atan wani abu ne?" Ta tambayeshi a maraice.

"I'm hungry" ya sanar da ita.

"Mey kakeson ci?" A farko yayi niyyan cewa stew tuna akwai stew a gida seyace spaghetti.

"Toh bari D'anladi ya zo ya kaini gida inyi sauri in had'a maka, shikenan ko kana buk'atan wani abu?"

"Shikenan."

"Alright I'll be right back."

"Thank you."

"Don't mention" murmushi kad'an ta sakar masa sannan tayi sallama da Sultan ta fice. Nan suka samu suka shigo da Amal.

Tana shiga ciki tayi kan gadon nasa a guje had'e da rushewa a gabansa tana kuka sosai sede ko kallonta Afzal beyi ba. Kukan tayita yi chan ta d'ago kanta ta shiga basa hak'uri. "Yaya I'm so sorry please kar ka mutu."

"Bakiya son ya mutu kuma kike wulak'antasa haka Amal? Afzal d'in? Bari in kira su Mami in sanar dasu halin da kika jefasa daga nan se asan nayi idan ma rabaku za'ayi toh don da shi zefi alkhairi ma because bazan iya jure ganinki kina destroying min life na amini ba, Amal baki san idan kika cigaba da hakan ba kija iya zamewa sanadin mutuwansa ba?"

Kuka take sosai tace, "Ya Sultan please don't call Mami wallahi tana iya kasheni da duka kuma ya kake magana haka? Sanin kanka ne Yaya yafi k'arfin in wulak'antasa."

"Kuma shine kike wulak'antasa hakan?"

"Ni ban wulak'anta Yaya ba, sanin kanka ne ina son Yaya, Yaya please say something." Sede ko kallonta Afzal be juya yayi ba.

"Toh ai ba haka ake so ba Amal kowa ya sani rabuwa da masoyi da ciwo amma ya zamo dole ki hak'ura tunda an riga an bada ke wa Afzal ko ba haka ba?" Kai ta gyad'a a hankali.

"Yanzu haka iyayensa basu da labarin yana asibiti saboda baya son ya had'a kanku amma still kina wulak'antasa haka? Sanin kanki ne Afzal na sonki I don't have to tell you."

"Ya Sultan I'm sorry dan Allah kayi hak'uri."

"Ni baki yi mun komai ba Amal, Afzal zaki bawa hak'uri let me excuse you two" daga fad'in haka ya mik'e ya fice tare da ja musu k'ofan. Shiru ne ya rufesu a d'akin Afzal yak'i yayi magana itama Amal tayi shiru bata sake cewa komai ba. Chan ta numfasa had'e da kiran sunansa.

"Yaya please ka juya ka kalleni kaji? Yaya I'm sorry please look at me" ganin har yanzu be juya yako kalleta ba ai seta rushe da kuka wajen. Kuka sosai take tun Afzal na iya jure sautin kukan nata har abun ya gagara, be san a lokacinda ya juyo yana kallonta ba don kukan Amal ba k'aramin tada masa hankali yake ba.

"Yaya I'm so sorry dan Allah kayi hak'uri please don't go and leave me, I'm here please don't go."

"You're not here Lily, you're never here. You don't love me, you don't even care about me baki damu dacna rayu ko na mutu ba. Lily nasan ni mey laifi ne but I'm sorry, bazan kuma gaji da baki hak'uri ba but please ki amince ki aureni, Lily bazan iya rayuwa ba ke ba you've become a part of who I am that I can't do without, you complete me, I feel so incomplete and lost without you. Lily idan baki kasance mallaki na ba ina iya rasa rayuwa na. I'm sorry but I love you, I love you morethan life itself, your love runs in my veins duk yadda naso 6oye soyayyarki hakan ya gagara, duk yadda na so cireki daga zuciyana nakasa, Lily I was created for you. Nazeefah might be my wife but you're my home, my soul, my happiness and life, please don't let me go astray."

By now kuka Amal take sosai. A hankali kalamun Afzal suke shigewa jikinta suke kuma tasiri, tabbas ba k'arya ko d'aya acikin kalamunsa tasani batada masoyi sama da shi abu d'aya yake hanata sakewa da shi idan ta tuna yadda ya rabata da Abdul sede kuma da ta zauna tayi tunani, seta gano komi na faruwa ne saboda dalili. Allah nada dalilin daya ya turo Abdul rayuwarta ya kuma ciresa a lokaci guda, dalilin kuwa itace ta sani cewa ba duk abinda mutum yakeso yake samu ba a rayuwa. Hawayenta ta shiga sharewa a hankali ta soma da cewa;

"Rana d'aya Allah ya kawo ka cikin rayuwana Yaya, acikin k'azanta da yarinta ka ganni ka kuma ce kana sona, baka sanni ba, baka san daga ina na fito ba, bakasan suwaye dangi na ba ka nuna min so da k'auna ka kuma ja ni jiki tamkar k'anwar ka ta jini ka k'ara bani daman kiranka Yayana. Rana d'aya bayan na cira ran zan sake komawa boko ka dawo mun da mafarki na ka nuna min everything is possible with you and God, ban ta6a neman abu na rasa a k'ark'ashinka ba Yaya. Damuwa na tun kafin in furta kake yaye minsu, baka wasa da sha'ani na komai nakeso shi kake mun taya bazan so ka ba Yaya? Idan nace bana sonka wallahi na zama mak'aryaciya but I love Ya Abdul too, ina sonshi amma bawai hakan na nufin ina shirin rasaka bane. Ina iya sadaukar da raina maka Yaya, batun maganan mu na ranan kuma ina sake neman gafararka kayi hak'uri na baka amsa bisa rashin tunani da shawara da nayi. Yaya idan har aurena ne ze farinta maka rai then I'm ready to be your wife, ko a yau kakeson in kasance matarka na amince zan aureka but please ka dena tada hankalinka a kaina haka bana son abinda ze ta6a lafiyanka bana son a sanadi na ka rasa rauwanka, dan Allah ka yayyafawa zuciyarka ruwan sanyi ka sani I'm only yours and no one else's."




RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 09:28] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 2⃣2⃣*


Har cikin ransa yaji dad'in kalamunta dukda cewan ya san ta fad'i komai ne don kawai yaji dad'i bawai don har cikin zuciyanta tana nufin hakan ba, yasani tausayinsa kawai takeji bawai sonsa take ba.
"Yaya why are you not saying anything?" Ta tambayesa a sanadin shirun da yayi. "Dan Allah kayi hak'uri."


DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment