Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ta ajiye ledan a d'akinta ta wuce bayi ta d'auro alwala sannan ta wuce kitchen dan ibo abinci. Achan suka had'u da Mami inda take ce da ita "Se yanzu kika ga daman fitowa?" Shiru ta mata bata amsa ba "Ga chan abincin alale na dafa."

"Sannu da aiki."

"D'azu Afzal yazo ai ko baki sani ba?"

"Ban sani ba yaushe?"

"D'azun."

"Allah sarki" tayi maganan tana serving kanta. "Seki kirasa."

"Toh" ta amsa tare da ficewa d'akinta. Instead ta kirasa kaman yadda Mami ta fad'a, bayan da ta idar da sallah taci abincin seta tura masa sak'o as 'Thank you.'

Suna zaune da Nazeefah sak'on ya shigo a farko yaso ya kirata amman sanin idan ya tashi a take Nazeefah na iya gano wani abun se kawai yayi replying nata as 'You're welcome.' Da daren ranan Abdul ya kirata suka sha hira kaman ba gobe tasan ya kamatabace ta canza layinta saboda kar Abdul d'in yana samunta kaman yadda iyayensa suka buk'aceta amman ina baza ta iya ba, son zuciya baze barta ba. Bata son rabuwa da shi, shi kad'ai ne idan tana tare dashi take jin dad'i yake kuma sanyata mancewa da dukkan matsalolinta

Washegari Afzal yayi timing dai-dai break time nasu Amal ya jesa school nasu. A gaban lecture hall nasu yayi parking sannan ya kirata a lokacin wayan na a hannun Maamah tana kallon pictures. "Gashi Ya Afzal na kiranki" ko kallonta batayi ba tace "Bar shi kawai na koma gida zan kirashi."

"Haba Amal rashin mutunci de ba kyau hungo ki amsa."

"Nace zan kiranshi anjima" Maamah bata saurareta ba ta d'aga wayan tare da manna mata a kunne seda Amal ta watsa mata mumunan kallo sannan tayi sallama.

"Wa'alaikumus salam" ya amsa.

"Yaya ina yini?"

"Lafiya Lily, ya kike? Kin fita school ko yau d'inma kina gida?"

"Ina school."

"Toh gani a gaban lecture hall naku.l

"Yaya zan-"

Gano neman excuse take yayi saurin katseta "Please come Lily."

"Wai yaya?"

"Wai yana waje inje in sameshi kinga shiyasa nace ki bari se idan na koma gida in kirasa."

"Amal running away from him won't solve anything, da hak'ura kikayi kika bud'e mishi zuciyarki."

"Maamah it's not that easy, I love Yaya amma ba so na soyayya ba Maamah Ya Abdul kad'ai nakeso."

"Na gane Amal but Ya Abdul ya miki nisa kema kin ba iya kasancewa tare zakuyi ba, beside time heals a hamkali zaki koyi sonsa, yanzu ki fita kije ki samesa kinji?"

"Kefa? Mu je tare."

"Ni meya kaini shiga tsakanin masoya? Barni kurum zan wuce hostel yaso semu had'u achan."

"Maamah please kar kiyi mun haka mu tafi tare."

"Ji min 'ya fa! Ya Afzal d'in bak'o ne? Abeg in zaki tashi ki wuce toh da ya fi miki." Haka tak'i raka Amal, books nata ta tattara ta d'an kimtsa fuskan ta sannan ta fice. "Shine se an shanya ni haka za a fito Lily?" Yayi maganan bayan da ta shiga motan.

"I'm sorry ina copying abu ne da ka kira."

"Alright ya lectures toh?"

"Alhamdulillah ya office?"

"Very good only that I've been missing you haka jiya naje gida kika k'i fitowa."

"Yaya ba haka bane."

"Toh Yaya ne?" Yayi maganan lokacin da ya shiga tuk'i. "Are you still mad at me? Lily I'm sorry bazan gaji da baki hak'uri ba."

"Yaya komai ya riga ya wuce ka dena damun kanka" be sake cewa da ita komai ba har suka isa restaurant da zasu ci abincin. Beso suci a restaurants na cikin school ba gudun kar suci karo da Nazeefah. Sede sa6anin yadda Amal ta saba sakewa da shi tayita masa hira yau jugum tayi ko uffan bata ce da shi ba. Afzal ya rasa meke masa dad'i besan mey zeyi ba Amal ta kuma sakewa da shi kaman da, gashi da zaran ya gwada d'auko mata maganan Abdul se ranta ya soma 6aci. Haka nan da suka gama ya mayar da ita school sam ba walwala tattare da ita.

Haka fa Afzal ya koma tamkar bak'o ga Amal. Sam bata sakewa da shi, kominbyadda yaso su koma yadda suke a da abun ya gagara. Sede kaman yadda Mami tace masa kada ya kariya haka yake danne zuciyansa yana hak'uri. Duk randa he is free yakan d'aukota daga school suje suci abinci a weekends ma idan bashida abunyi ko kuwa idan Nazeefah ta fita unguwa shima se ya shirya ya kawo mata ziyara even though bata ta6a kawo masa hira saidai shine yata zuba ita ko tayi ta basa short short answers.

Tun dawowansa gida yau ya karanchi yanayin Nazeefah ya soya tayi lagwai kaman wanda baida lafiya. "Sannu da zuwa" tace dashi lokacinda ya shiga parlourn.

"Yauwa sannu" ya amsa.

"Your lunch is ready" ta sanar da shi.

"Thank you lafiya? Ya naga ganki haka?" Yayi maganan had'e da zama gefenta akan kujeran data jingina.

"Lafiya nakega stress ne kawai kar ka damu."

"Are you sure?" Ya tambayeta yana ta6a jikinta don jin tempreture'nta.

"Yes karka damu" ta amsa had'e da yi masa murmushi. D'akinsa ya wuce ya watsa ruwa sannan ya fito yaci abinci sede be tarar da ita a parlourn ba, take ya yanke hukuncin ta shiga d'akinta ne. Shi kad'ansa ya zauna a parlour yana kallon sports har izuwa Maghrib. D'akinta yawuce inda ya tarar da ita tana kwance, k'arisawa ciki yayi tare da zama akan side drawer'n sannan ya shiga kiran sunanta. A hankali ta shiga amsawa "Tashi kiyi niyya lokacin sallah yayi."

"Nagode" kad'ai ta iya cewa sannan ya fice. Be dawo gida ba se bayan Isha rashin ganinta da beyi a parlourn ba kawai ya yanke hukuncin jikin nata ne daman tunda ya dawo ya ganta wani iri d'akinta ya wuce ya sameta kwance lamo akan gado. K'arisawa yayi ya zauna gefenta tare da ta6a jikinta sosai tempreture'n nata ya hau.

"Nazeefah you're sick" ya yake hukunci.

"I fear I am" ta amsa murya ciki-ciki.

"Ya kikeji?"

"Zazza6i" ta amsa a takaice.

"Bakiya fleeting d'akinki kwana biyu har sauro suka yita cizonki ko?" Kai ta gyad'a a hankali.

"Yanzu kin huta ai da malaria ya shigeki."

"I'm sorry" ta furta a hankali.

"Ba magani a gida barin fita in siyo miki."

"Ba seka fita cikin daren nan ba kabari ko zuwa gobe."

"So kike in zuba miki ido haka? Ina zuwa kinji?" Kai kad'ai ta gyad'a yayinda ya ja bargo ya rufeta da shi sannan yayi adjusting AC'n d'akin. Dai-dai yazo fita ta kira sunansa "Na'am wani abu ne?"

"Thank you Allah ya kare."

"Ameen don't mention" ya amsa tare da sakar mata da murmushi nan da nan ya d'au key'n motarsa ya fice. A pharmacy'n dake unguwansu ya samu maganin ya sai mata nan da nan ya komo gida ya d'au ruwa ya wuce d'akinta da shi knocking yayi sannan ya shige. Lokacin har tayi bacci zama yayi gefenta ya tada ita had'e da taya ta zama "Sannu ko?"

"Har ka dawo?" Ta tambayesa.

"Eh na samu anan bakin layi kinci abinci?" Kai ta kad'a "Bari in d'ibo miki toh seki sha maganin naki."

"Bari zan sha maganin haka kawai bana son shinkafan."

"Toh an ta6a shan magani akan yunwa ne Nazeefah?"

"Afzal ko naci hararwa zanyi shiyasa."

"Mey kikeso toh?"

"Babu."

"It can't be babu tell me , zaki ci indomie?l" Kai tayi saurin kad'awa "quarker oaths?" Nan ma kai ta kuma kad'awa "What of custards?"

"Dama dama shi ma, bari zuwa anjima idan na d'an samu k'arfi zan had'a thank you so much Afzal."

"Bari zan had'a miki."

"Ka iya girki ne?" Ta tambayesa da mamaki murmusawa yayi "Halan ke kike mun da nake school."

Dariya ta saki kad'an "I'm impressed."

"Kwanta ki huta lemmi get it ready for you." Kwanciyan tayi ya ja mata bargo sannan ya wuce d'akinsa ya rage kayan jikinsa ya wuce kitchen d'in. Nan da nan ya tafasa ruwa a heater ya had'a mata custards d'in ya kai mata. A farko yayi tunanin barinta ta sha da kanta amman tuna yadda tayita masa d'awainiyya sanda yayi targad'e hannunsa yasa ya canza ra'ayinsa. Da kansa ya zauna ya bata custards d'in seda ta shanye tas sannan ya 6allo mata magunan ta ya bata ta had'iye. Bayi ya rakata tayi alwala sannan tayi sallah ta koma ta kwanta. D'akinsa ya koma ya kammala aikin dake gabansa, chan wajajen goma ya watsa ruwa ya sanya shorts nasa ya d'au pillonsa ya zarce d'akin Nazeefah. Ba k'aramin mamaki tasha ba ganinsa da tayi rik'e da pillow. Bade anan yake shirin kwana ba saboda bata da lafiya? Haka kawai ta tsinci kanta cikin farin ciki. Kallon ne yaga ya soma yin yawa yace, "Ko in koma ne?" Cike da wasa.

"Ni yaushe nace haka?" Taya saurin tambaya.

"Toh naga kin k'i matsa min ne ai" yayi maganan sanda yake tsaye akan gadon.

"Gadon ma gabad'aya idan kakeso zan bar maka." Murmushi ya sakar mata sannan ya ajiye pillonsa daga space da tayi masa providing.

"Do you need anything else?" Ya tambayeta kai ta kad'a da haka ya haura gadon ya sameta tare da kashe musu wuta. Jawota yayi a hankali izuwa jikinsa sannan ya furta "Goodnight Nazeefah."

"Goodnight Afzal I love you." Peck yamata placing a hankali da haka har bacci yayi gaba da su duka.



RANA D'AYA!
#RD

Love... King MiemiebeeπŸ‘„βœ¨
[13/08, 02:20] β€ͺ+234 907 483 8352‬: πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€ πŸŽ€πŸŽ€πŸŽ€
πŸŽ€β£πŸŽ€
❣❣

πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
*RANA D'AYA!*
πŸ’¦πŸ’¦ πŸƒπŸƒπŸƒ
July, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by MiemiebeeπŸ‘„_


*PAGE 2⃣1⃣*

_Big sisπŸ—£ (Maman Fadeel) where are you? I just want you to know that I'm devoting this entire page to you. Thank you for always trying to put a smile on my face, for treating me as if I'm one of your true little sis, know that your Lily loves you so much. XX 😘_



Kasancewan jikin Nazeefah a gida Afzal yayi sallah ya jasu tare, bayan sun idar da sallan ne ya shiga shirin office inda tace zata had'a mishi breakfast. Take ya hanata akan ta kwanta ta huta tunda bata da lafiya, he can manage. Haka ya shirya ya had'a breakfast nasa ya ci sannan yayi mata sallama. Kaman yadda ya saba kiran Amal ko wani safiya haka nan ma yayi yau sede har yanzu Amal bata sakewa dashi sama-sama suka gaisa sannan ya katse.

Da yamma bayan Amal ta dawo daga school ta la6e a d'akinta se hira suke a waya da Abdul not knowing Mami na la6e tana sauraronta tun d'azun. Ashe de har yau bata fasa waya da Abdul ba, shin wai meke damun Amal? Ta tambayi kanta, ace mutum an bada shi ma wani amma ya zauna yana hira da wani na daban? Bata yi mata magana ba ta koma ta cigaba da aikin dake gabanta. Bayan dawowan Papi ne ta zaunar dashi take fad'a masa abinda ke faruwa. Amal d'in ya kira bayan ta k'ariso take mai sannu da zuwa.

"Yauwa Mamana ya makaranta?"

"Alhamdulillah."

"Nace yaron nan Abdul ai baku waya yanzu ko? Kuma kin canza sim naki kaman yadda iyayensa suka buk'ata?" Shiru Amal tayi dan ko k'aryan da takeson yi d'inma ta gagara, kum taji bakinta ya kullu.

"Baby?" ya kirata.

"Na'am Papi" ta amsa.

"Baki jini bane? Kode har yanzu kuna waya ne dashi?" Nan ma shiru. "Ba magana ake miki bane Baby?" Mami tasa baki.

"Eh Papi" ta amsa murya chan ciki-ciki.

"Haka kukayi da iyayensa? Ke bakisan cin amana kike ba yanzu Baby? Taya bayan an bada ke ma wani amma ki tsaya kina hira da wani na daban? Kina ganin kin kyauta wa shi Afzal d'in kenan Baby?" Shiru tayi ta kasa cewa komai yayinda take nazarin rabuwa da Ya Abdul.

"Iyye? Kina ganin kin kyauta masa kenan?"

"A'a" ta kad'a kai a hankali.

"Toh kije na baki nan da kwana biyu ki canza sim kuma kar in sakejin kina waya da Abdul d'in kinji?"

"But Papi-"

"Ko baki jini ba? Har yaushe kike son ki cigaba da yaudarar sa? Kefa kikace kin amince zaki auri Afzal kodan ki biyasa alkhairin da yayi miki a baya yanzu kuma kice ba haka ba Baby?"

"Papi bawai dena waya da Ya Abdul d'inne bazan iya ba, naga tunda ba auran Yaya zanyi ba yanzu ai ba laifi idan muna gaisawa da Ya Abdul, Papi dan Allah karkace a'a."

"Kaman ya Baby? Ni da na d'au da jimawa ma kin canza layin naki? Ke bakisan alkhairi ne miki ba idan kika rabu da Abdul d'in tun wuri, kema zaki fi samun kwanciyan haka shima a hankali Allah ze yaye masa son da yake miki kuma gaisuwa ne kad'ai kuke ko hirar masoya?"

"But Papi-"

"Ya isa haka Baby baki cika sa6awa dokokin da nake kafa miki ba, kar kiyi hakan yanzu nan da kwana biyu bana son in sake jin kina waya da Abdul idan kuma ba haka ba zan yima iyayen Afzal magana dama su basu k'i ko a satin nan a d'aura auren ba, se suzo ayi magana asa rana."

"Papi dan Allah kar kayi mun haka."

"Toh kiyi kaman yadda nace." Kai ta gyd'a a hankali tana share hawayenta "Tashi ki fice Allah yayi miki albarka" ko amsawa batayi ba ruga d'akinta a guje ta baje kan katifarta ta shiga aikin kuka. Wayanta ta jawo had'e da shiga photos tana kallon pictures nasu tare da Ya Abdul yayinda kukan yaso yaci k'arfinta. Chan dare kaman yadda ya saba kiranta haka nan ya danna mata kira bata 6ata lokaci ba ta d'aga suka sha firarsu sam bata nun masa wai da akwai matsala a k'asa ba sede ko da yakeson yi mata seda safe tak'i amincewa ya katse wayan ita wai suyita hira kawai. Haka ya biye mata dukda cewan bacci yakeji, wayan suka yita yi har zuwa lokacinda ta zarce bacci se anan yayi mata goodnight yayi hanging call d'in. Washegari bayan ta taso daga school ta wuce Post office ta sai sabon sim sannan ta dawo gida. Video call ta dannawa Ya Abdul shi kansa beyi expecting ba dan tun tafiyansa sau d'aya da sukayi video call basu kuma ba. Haka nan tayita masa hirar shirme har seda kud'inta ya k'are sannan ya kirata suka cigaba har anan bata nuna masa cewan akwai wani abu ba. Da daren ranan ne bayan sun k'are wayan ta karya sim d'in ta sa sabuwa tana kuka haka ta zuba pieces d'in a bola. Ranan ko bacci batayi ba, kuka ta kwana tana yi washegari idanun nan sun kumbura tim ko school ta k'i fita. Dama normally kowani safiya da good morning text messages na Ya Abdul take tashi se gashi yau wayam ba komai. Ba yadda Mami batai da ita ta fito ta karya ba amman tak'i.

Shiko Abdul chan da yamma bayan ya dawo daga office yayi tunanin kiran Amal tunda shiru yau bata kirasa ba sede fa switched off layin nata ke ce masa. Be kawo wani tunanin a ransa ba yace ze gwada anjima, sede har zuwa dare Amal bata kirasa ba gashi ko ya kira switched off da wasa da wasa hankalinsa ya soma tashi. Sak'onni da dama ya tura mata amma ba response yau akeyinta! Danne zuciyarsa yayi yace bari ya bari zuwa gobe. Safe bim ya sake trying layin nata amma still baya shiga, hankalinsa idan yayi dubu be tashi ba shin meke faruwa? Wutansu ne ya 6aci kokuwa wayarta ta aka sace? Tunani de ba wanda beyi ba k'arshe da shirun yayi yawa ya yanke hukuncin kiran Maamah. Tana ganin call nasan tasan Amal ta canza sim ne kenan. Allah sarki Ya Abdul.

Sam bata so d'aga wayan ba amman gudun kar ya fahimci wani abun seta d'auka bayan sun gaisa yake tambayarta ko ta fita school yau. K'arya ta mai tace bata fita ba.

"Toh Amal fa kunyi waya da ita?"

"A'a wallahi tun shekaran jiya rabon mu da muyi waya."

"Ikon Allah I've been trying to reach her but it ain't going through."

"Toh kuma? Kasan wuta ya 6aci gabad'aya gari toh se a hankali nakega bata da chargi ne."

"Nima nayi tunanin hakan gobe zaki fita school ai ko?"

"Ka manta gobe Saturday ne? Besides bani da lecture ma."

"Toh bazaki je gidansu ki duba mun ita ba?"

"Ya Abdul ka kwantar da hankalinka mana ai Amal lafiyarta k'alau wuta ne ya lalace wayan nata ba chargi ka gane?"

"Maamah are you sure?"

"Dagaske amma sunce nan da sati ma zasu gyara."

"Anya kuwa zan iya jure sati banji muryan Amal ba? Ni kawai gobe kije gidansu ki had'amu."

"Allah sarki Ya Abdul zan raka Mama gidan biki fa kabari mana zuwa Monday."

"Mey zakiyi jibi da bazaki je ba?"

"Naji Allah kaimu."

"Yauwa good girl nagode ko?"

"Uhumm you're welcome" hira kad'an suka ta6a sannan sukayi sallama. Wayan ta ajiye had'e da sauk'e nauyayyar ajiyar zuciya gabad'aya ta rasa ya zata 6ullowa al'amarin. Mama taje ta samu ta irga mata halin da ake ciki inda take shawatarta da komin yaya karta kuskura ta basa sabon layin Amal.

Kamar yadda Abdul ya shiga tashin hankali haka Afzal ma, barin ma shi da bashida clue sam gameda rashin samunta a wayan ya rasa dalili, layin Mami ya kira itama unavailable yake cemata. Beso kiran na Papi ba akan zuwa gobe zeje ya duba ta yaji ko lafiya. Sosai Nazeefah ta warware, washegari bayan sallan La'asr Afzal ya zarce gidansu Amal.

Mami da Papi ya tarar a tsakar gidan bayan sun mishi sannu da zuwa ya k'arisa suka gaisa sannan yake tambayar ko lafiya jiya throughout yana neman Amal amma ya kasa samunta.

"Bade bata baka sabon lambar nata ba?" Papi ya furta a hankali sede Afzal ya jiyosa saboda nisan kunnensa.

"Na'am?" Ya tambaya.

"Bata kiraka da sabon layinta ba?"

"A'a" ya kad'a kai cike da rashin fahimta. "Sabon layi kuma?"

"Afzal nasan kana hak'uri amma ka k'ara, kasan Baby yarinya ce tunaninta kad'an ne, bayan nan kuma shi rabuwa da masoyi zafi gare shi, gabad'aya na kasa gane kan yarinyar nan gashi kuma idan akace ta rabu da kai ta koma ga Abdul d'in setace a'a ita bata son abinda ze sake samun lafiyanka ta fita harkan Abdul d'in kuma abun ya gagara. Afzal bazan 6oye maka ba amma idan kasa wasa kana sakaci toh wallahi da k'yar idan zaka iya maye gur6in Abdul a zuciyanta, ban san wani irin makahon so takeyi masa ba. Ka sani yanzu ne kake da daman shiga zuciyarta tunda Allah yayi ta canza layin nata zasu daina waya."

Sosai Afzal yaji wa Amal, ba k'aramin tausayi take basa ba, yasan yadda takeji sarai saboda shima he went through such. Tunanin ya ze iya karkato da hankalinta akansa yake amma gabad'aya ya gagara.

"Papi Amal ta riga ta tsaneni, tsana har a fuska tana nuna mun, wallahi ina iya k'ok'arina don ganin nayi straightening relationship namu but she's not willing to give me a chance I don't know what to do again."

"Abba a gani na idan ba aure akayi ma Baby da Afzal ba, yarinyan nan baza ta ta6a amincewa da cewa Abdul yayi mata nisa ba" Cewan Mami.

lBut Mami makarantar ta fa?l Afzal yayi saurin tambaya kafin Papi yayi magana "Bana son maganan aure ya raba mata hankali."

"Hakane Afzal amma kuma akwai abin dubawa acikin abinda Mamin Baby ta fad'a, idan ba wai har rana taga an sa muku ba bazata ta6a fita daga harkan yaron nan ba tasan yanzu ba ita ba shi."

"Tabbas hakane Papi toh zan gwada yimata maganan inji mey zatace duk abinda akwai zan sanar da ku."

"Toh shikenan hakan ma yayi amma kam kayi sake haka kana ji kana gani 'yar nan zatayi maka nisa."

"Toh zan wuce ko zan iya ganin Amal?"

"Bari inyi mata magana" cewan Mami.

"Toh zan jirata a waje nagode sosai se anjima."

"Ka gaida gida" Papi ya fad'a masa. Da haka ya mik'e ya fice. Koda Mami taje kiran Amal akan cewa Afzal yazo yana nemanta, shareta tayi k'arshe seda Papi ya sa baki. Fuskanta ta fito ta wanke sannan taje ta samesa lokacin har ya gaji da jirarta.

"Yaya ina yini?" Ta gaishesa daga chan nesa yayinda yake zaune kan benchin sa na kullum.

"Fa bazan amsa gaisuwan nan ba sekace wani bak'o Lily? K'ariso nan mu zauna kinji?" Bata mai gardama ba ta k'arisa ta zauna a gefensa.

"Meya faru fuskanki ya kumburo haka?"

"Babu" ta amsa tana tare fuskan nata.

"Dan ance se kin fito shine kike kukan nan Lily?"

"Yaya ba haka bane."

"Lily I'm sorry for making you hate me if you can't love me back please tell me."

"Yaya wani irin magana kuma kake? Har na isa ince bana sonka ne?"

"Gashi kuwa sede a bakin Papi zanji kin soya layinki you had zero intention of notifying me koba haka ba?"

"Jiya fa na canza layin ko Maamah ma ban bata ita ba, ba wanda na kira da ita."

"Toh shikenan dama magana nakeson miki."

"Ina jinka."

"Is it okay with you in turo su Abba for formal introduction?" Wani irin wawan fad'i gabanta yayi bade yanzu Afzal ke shirin auranta ba?

"Lily?"

"Yaya..." se kuma tayi shiru.

"Talk to me kinji? Ki fad'a mun ra'ayinki I'll do only as you wish Lily."

"Yaya Nazeefah fah? Yaya bana son shiga tsakaninka da matarka bana son tashin hankali."

"And who said by agreeing to marrying me zaki shiga tsakani na da Nazeefah? Ke daban ita daban karki damu da ita zata fahimci al'amarin namu in shaa Allah."

"Yaya what of my studies? Kaifa kace baka son abinda ze raba mun hankali dangane da karatu baka tunanin auran nan will be a great distraction to me? Yaya I'm sorry amma ban shirya da yin aure ba yanzu."

"Is this just how much you don't want to be with me Lily? Yanzu inda Abdul ne yace ze turo ai bazaki ce masa haka ba ko? Shikenan ba matsala dama ra'ayinki kawai nakeson ji saboda in sanar dasu Papi. Kina iya komawa ciki" yayi maganan yana sa hannunsa cikin aljihu, wata envelope ya zaro ya sa mata a hannu. Kafin tace zatayi
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment