Join Our WhatsApp Group

Idan ku ka ga kun taba wani wuri ya fitar daku a shafinmu, sai ku danna back kuyo baya, ku sani yanzu muna amfani da tallan Popunder a shafin, so karatu zai muku dan wahala, amma ta hakanne kadai zamu iya cigaba da rike shafinnan. idan har bakwa son talla sai kuje ku yi subscription na shafinnan akan karamin kudi ku runga downloading kawai. SUBSCRIBE


DOWNLOAD

You Cannot Download this book untill you login but you can read it .


Login Register
DOWNLOAD

ba, se yake ce masa ai dan yau ranar zuwanta na farko ne shiyasa dukda kuwa shi bek'i kullum shi zena kaita ba muddin yana da hali. Da haka Papi ya musu Allah ya kare suka fito.

"Lily?" Ya kirata chak ta tsaya tare da juyawa tana kallonsa, camera kawai ya haskata dashi. "Bade hoto kamin ba Yaya?" Ta tambaya tana kare fuskarta. "Yaya dan Allah ka goge ai ba a yiwa mutum hoton bazata haka."

"Village girl waya fad'a miki? Ke bakisan unexpected pictures sunfi kyau ba?"

"Toh ai yau banyi kyau ba fuska na du yabi ya kumbura."

"Inji waye? Ai dan kyan da kikayi yasa na d'aukeki hoton and today is your first day at school too."

"Wai nayi kyau kaide kasan kan zagin mutum Yaya."

"On a serious note kinyi kyau Lily, kyau sosai tabarakallahu feek."

"Thank you Yaya" ta amsa cike da kunya, haka take duk lokacin da Afzal yace tayi kyau setaji kunya ya ziyarceta, ta kuma rasa dalili. K'arisawa cikin motan sukayi ya jasu, har gaban lecture room nasu ya sauk'eta sannan ya sallameta nan ma seda suka kusan fad'a sannan ta amince ta amshi kud'in, Allah bada sa'a ya mata ta fice seda yaga shigewanta ciki ya ja motansa ya wuce office.

Ta fannin Nazeefah kuwa koda driver'n Ummi yazo d'aukanta ko ta kansa batayi ba, motarta taja don bak'in ciki ta wuce school. Throughout the lectures kuwa hankalinta bai jikinta se tunani take haka har suka fita cin abinci ma daga k'arshe seda Rumaysa taja ta gefe take tambayarta ko lafiya, abinku da shagwa6a66iya ba seta 6arke da kuka ba kawai da k'yar Rumaysa tasamu ta sata tayi shiru, ta fad'i meke damunta kuma tak'i, k'arshe gida kawai ta dawo ta watsa ruwa ta kwanta ta hau tunani.

Bata son ta tabbatar da abinda zuciyar ta ke raya mata, taya ma zata fara son Afzal?? Is it even possible?? Taya zuciyarta zatayi mata haka bayan ta d'au alwashin bazata ta6a sonsa ba, a farko taso yaudarar kanta da cewa kishinsa kawai take ba sonsa ba amman kuma ai se idan kanason abu ne har zakayi kishi akansa yanzu shikenan ta fad'a kogin son Afzal kenan? Sai dai sam bata bawa kanta laifi ba dalili kuwa shine ta tabbata ko wace macece aka kawota gidan tabbas itama seta fad'a tarkon son Afzal batare da tasani ba, da irin abubuwan da yake yi komin taurin zuciyan mutum dole ne zuciyar tayi laushi ta soma sonsa. Na farko bai ta6a k'untata mata ba a gidan se har idan ita ta tsokolosa, na biyu se abinda takeso takeyi ko k'ala baya ce mata, ga kud'i ko nawa ta tambaya bata yake, wannan a gefe babban tashin hankalinta shine ta gansa zaune ba kaya gashi yadda kukasan al'ada haka ya camfa zama shirtless a gida. Muddin yana gida toh befi yasanya d'an three quarter wando ba idan yayi mutunci shine ya sanya singlet dake bayyana well defined chest nasa, taya idanunta bazasu kwad'aita wa zuciyarta wannan kyakkyawan halitta ba? Ita yanzu damuwanta d'aya ne yadda za'ayi ta cire soyayyan Afzal daga zuciyarta tun wuri kafin tayi mata illa, sede ya zatayi hakan? A tunaninta idan auran nasu ya mutu soyayyar ma zata mutu don haka yau tayi making up mind nata, Afzal na dawowa gida zata tisa sa a gaba yadda ko ya so ko ya k'i seya rubuta mata takardan sakinta tun wuri tasan inda gari ya waye mata.



RANA D'AYA
#RD

Love... King Miemiebee👄✨
[13/08, 00:29] ‪+234 907 483 8352‬: 🎀🎀🎀 🎀🎀🎀
🎀❣🎀
❣❣

💦💦 🍃🍃🍃
*RANA D'AYA!*
💦💦 🍃🍃🍃
June, 2018
beeenovels.blogspot.com

_Written by Miemiebee👄_


*PAGE 1⃣2⃣*


Tun dawowan Afzal gida ta soma yi masa k'orafi ita ya saketa zaman ya isheta, be kaiga sa key a k'ofan d'akinsa ba ta hankad'e k'ofan tana masa ihu haka yadda ya dawo a gajiye da ciwon kai ya sake ficewa abun tausayi yabar mata gidan gabad'aya ko tanka ta beyi ba. Gida kawai ya nufa ya wuce site nasa inda ya watsa ruwa ya mik'e kan gado se bacci chan kaman a mafarki yaji ana yi masa knocking tamkar wanda baze tashi ba ya lalla6a ya bud'e segani Ummi yayi tsaye bakin k'ofan.

"Ashe de dagaske ne ka shigo" ta soma da fad'i tana binsa da kallo na sosai, jin be amsa ba ta k'arisa ciki "Prince?"

"Uhmm" ya amsa yana kakkafe lumsassun idanunsa wane wanda ya sha abu ya bugu.

"Lafiya dai ko? Mey haka sekace wanda yasha wani abu?"

"Ummi please we'll talk later, a gaje nake yanzu, kaina ciwo allow me to rest."

"A gidanka ba wajen hutu ne da seka zo nan zaka kwanta? Ba za ayi wannan rashin hankalin dani ba. Meye dalilin ka? Chan d'in meya samesa?"

"Ummi please kiyi hak'uri kaina ciwo yake I'll explain everything to you later."

"Fad'a min meke faruwa tukun ko sena kira Abbanka?"

"Gidana ba lafiya and I need to rest right now please kiyi hak'uri" ganin yadda idanunsa ke kakkafewa kawai yasa ta fice ta ja mar k'ofar. Komawa yayi ya kwanta bashi ya tashi ba se bayan Maghrib, ya na idar da sallah ya nufi site na Ummi inda ya zauna a gefenta suka gaisa take tambayarsa meke faruwa.

"Babu kawai mun samu misunerstanding ne da Nazeefah" yayi mata k'arya, har ga Allah beyi niyyan fasawa Nazeefah tyre ba saboda there's no point ma, k'arshenta kawai ze had'a kanta da iyayenta ne ya kuma zubar mata da mutunci da girma a idon Ummi.

"Prince kalleni" ta buk'acesa. "K'arya kakeyi."

"Kamar ya kuma k'arya Ummi? Wallahi matsala muka samu amman na tabbata yanzu ta sauk'o zan koma gida muyi negotiating komi idan Abba ya dawo ki gaishe shi."

"Toh shikenan ka gaishe da Nazeefan kuma ka k'ara hak'uri kaji? Ko zaka tsaya kaci abinci? An kusa sauk'ewa."

"A'a bana jin yunwa tea kawai zansha idan na isa gida."

"Toh Babana bari in raka ka se hak'uri zama da mace kaji?" har gun motansa ta rakasa tana yi masa nasiha sannan ta dawo ciki. Da ikon Allah har ya isa gida ya shige d'akinsa Nazeefah dake bayi tana wanka bataji dawowansa ba se chan kusan k'arfe goma da ya fito d'aukan soda daga fridge suka had'u, ba wanda yace ga d'an uwansa ko k'ala kowa harkan gabansa ya cigaba dayi.

Kusan sati Afzal ya jera yana kai Amal makaranta sannan ya samu wani me napep suka daidaita wanda ze na kai Amal makaranta yana d'aukota a k'arshen wata se a biya sa. Sosai Amal ta miyar da hankalinta ga karatu, daga bokon har islamiyyan bata bar ko d'aya ba.

Ta fannin Afzal kuwa ababen sun soma canzawa suna ca6e masa wanda kuma ya rasa dalilin hakan, haka kawai yake tsintar kansa cikin wani irin nishad'i duk lokacinda yake kallon hotunan Amal kokuwa yake sauraron muryarta baya manta sati d'ayan daya jera yana kaita makaranta, a kullum tana sanye da three quarter hijabanta da side bag nata a gefe kokuwa ta rataya backpack nata a baya. Komin bak'in cikin da Nazeefah ta cusa masa muddin ya shiga kallon hotunan Amal toh seya nemi wannan bak'in ciki ya rasa. Yau ma kaman kullum yana zaune a office nasa gabad'aya ya zurfafa yana kallon wani hoton Amal da take sanye da wani navy blue hijab me hannu, yatsunta ta k'ayatasu da jan lalle wanda ta rik'e fuskarta dasu ta gefe yayinda hankalinta ya duk'ufa kan wani abu, da alama bata ma san an d'auketa hoton ba. Har Sultan ya bud'e k'ofa ya k'ariso cikin office d'in ya zauna Afzal besan ya shigo ba se ji kawai yayi an fisge wayan daga hannunsa kafin yace ze amshe har Sultan ya k'are wa hoton kallo.

"Iyye! Ka fad'a kace" ya fad'a mishi cike da meman tsokana. "Kace ta sace maka zuciya."

"Mtsw! bani waya na" Afzal daya had'e rai kaman hadari ya fad'a cike da tsiwa. Ba gardama Sultan ya mik'a masa wayan amsa yayi ya rufe had'e da cusawa cikin aljihunsa.

"Hope I'm not interrupting something?" Sultan ya sake tambayansa mockingly.

"Kaga bana son suratan banza, if you've nothing better to say just shut up."

"Yau kuma? So tell me ka sanar da ita kokuwa kana jira muje ne tare?"

"What're you even saying?" Ya tambayesa tamkar be fahimci inda ya doso ba.

"Don't pretend you don't know, maganan Amal nake."

"What about her?"

"C'mon maza yau kuma ni zaka 6oye ma abu? Kana son Amal ko ba haka ba?"

"So fa kace? How is that even possible?"

"I've been observing you lately, duk abinda ya shafi Amal baka wasa da lamarinsa, the way you smile anytime ta shigo office d'innan shima is not normal ba haka kake ba da gashi typical example yanzu har na bud'e k'ofan ka na shigo na zauna baka san da shigowa na ba gabad'aya hankalinka ya duk'ufa akan kallon hotonta."

"Shikenan kuma se akace don ka k'irga wannan ababe ya zame ina sonta? Kokuma haramun ne in kalli hotunan dake cikin waya na?"

"Ai ba kallon tsakani da Allah kake ba."

"Lmao, da tsakani da tsuntsu ne?" ya tambayeshi sarcastically.

"Kallon soyayya kakeyi mata do you deny that?"

"Shima son yana da kallo ashe ban sani ba."

"Maza jokes apart daman ni nasan za'ayi haka jiran ranan kawai nake, so ka sanar da ita ne kokuwa kana jiran muje tare?"

"Nifa suratan banza ne banaso shikenan ban isa in kalli hoto a waya na ba se kace ina son mutumin?"

"Baka amsani ba zamu je tare ne kokuwa ni in je a madadin ka?"

"Wallahi da kuwa me hanani yanka ka se Allah."

"Lol ka yarda kana sonta kenan."

"Dan Allah drop this topic ni ban ce maka ina son Amal ba, taya ma zan fara sonta bayan kasan yadda take mutuntani ta kuma d'aukeni a matsayin yayanta data amince da shi, that aside ko ka manta ma ni ina da mace a gida."

"Toh kuna jituwa da matar naka ne kokuwa ance kai mijin mace d'aya ne?"

"Ba a ce ba amman ni banida ra'ayin rik'e mata biyu."

"Kana nufin da ba don igiyan auren Nazeefah dake a kanka ba kenan da zaka auri Amal?"

"Eh I mean no! Subhanallah I mean please shut the fvck up!" Ya k'arisa a fusace.

"Woahhh! Lallai kayi nisa maza Amal ta gama da kai."

"Tashi ka bar min office tashi ka fita."

"Hab-"

"Sultan am serious ka tashi ka fita min daga office idan har kasan suratan banza zaka cigaba dayi get out."

"Lalle bature beyi k'arya ba daya ce love can make you do weird things yau amininka kake kora kaman kashi daga office akan mace?" Mik'ewa Afzal yayi a fusace "Tashi ka fita I'm damn serious." Ganin yadda Afzal ya fusata sosai Sultan yayi shiru ya shiga basa hak'uri yana mai da maganan wasa, "Yi hak'uri ni wasa nake da Allah."

"Ka fita nace ko sena sa securities sunyi waje da kai?"

"Idiot kai shikenan baka san wasa ba? I said I'm sorry."

"Iskanci kawai mtsww" komawa yayi ya zauna "Ya office yau?"

"Lafiya bazaka ci abinci bane yau?"

"I'm not hungry yanzun nasha coffee I'm good."

"Toh nikam bari in k'arisa I'm starving" fad'in Sultan sarai yasan inda Afzal ze nufa so yake ya biya ya d'auki Amal suje suci abincin su biyu. Yana ficewa ba da jimawa ba kuwa Afzal ya d'aga waya ya kira Amal ta wayan Mami da kusan kullum tana zuwa school da shi saboda security reasons. "Halo Lily?"

"Na'am Yaya ina yini?"

"Lafiya ya lectures?"

"Alhamdulillah yanzu ma ya k'are sauran na 3 kuma."

"Inzo muje muci abinci?"

"Beyi maka nisa ba Yaya?"

"Not at all inzo?"

"Yaya har seka tambayeni izini ne? Se kazo ina jiranka" da haka sukayi sallama in less than 30 minutes Afzal ya iso ya d'auketa. A farko yaso su ci abincin ma a makaranta a cikin unimaid garden amman tuna achan Nazeefah ke cin abinci yasa suka fito suka nemi wani gun daban. Kaman kullum haka yata d'aukanta unexpected pictures tun tana hanasa har tagaji ta miyar da hankalinta ga abincinta kawai. Suna gama ci ya mai da ita school ya koma office.

A haka har su Amal suka samu wata d'aya a makaranta, sosai lectures yayi zafi har ya zammana bata samun time na karatun mahadiyya sosai amman dukda hakan ranan da bata gaji lis ba tana tashi cikin dare tayita bita ko hadda. Yau Asabar bayan sallan Azahar Amal ta shirya ta wuce cafe don yin assignment nata kasancewar bata da smartphone irin na zamani na Mami kuwa baida internet. Ana cikin mata assignment d'inne Afzal ya kirata dake ta fita da wayan Mami ta samu ta d'aga "Halo Yaya ina yini?"

"Lafiya Lily ya kike?"

"Lafiya k'alau ya weekends?"

"Alhamdulillah ya lectures ko yau baki fita ba?"

"Wallahi."

"Why?" Yayi saurin tambaya a tunaninsa gabad'aya bata da lafiya ne. "Lafiya dai ko?"

"Assignments aka bamu senazo cafe kuma zan samu inyi."

"Geez Lily I'm sorry."

"What for Yaya?"

"Gabad'aya na manta bamu sai miki waya ba."

"Kai Yaya kai kam kashe kud'i baya baka wuya, gashi Allah ya kawo sauk'i akwai cafe kota ina a unguwa mey amfanin wayan?"

"Amman ai still stress ne, har yaushe zaki na fita cafe kullum kina yin assignments?"

"It is worth the stress ai Yaya karka damu please."

"Toh shikenan dama baki kira ba yau nace lemmi call up inji ko lafiya"

"Wallahi lafiya kuma kana raina nima."

"Alright toh a gama assignment lafiya I'm hanging up."

"Alright take care" da haka sukayi sallama. Washegari da yamma ya shirya tsaf cikin wasu k'ananun kaya da suka mugun amsansa ya feffeshe da turare sannan ya fito parlour inda Nazeefah ke zaune tana yin assignment nata, a two seater ya ajiye wata ledar dake hannunsa sannan ya k'arisa dining space d'auko ruwa. Cikin wannan lokaci Nazeefah ta tashi ta bud'e ledar inda taga sabuwar iphone 6s dal cikin ledar. Mumunar fad'i gabanta yayi, take gun ta yanke hukuncin kaiwa budurwarsa zeyi, wani irin wawan kishi ne taji ya tokareta bata kaiga motsawa gun ba Afzal ya k'ariso ya k'wace ledan daga hannunta.

"Ina kuma zakaje?" ta tambayesa lokacinda yake duba cikin ledan don tabbatar da cewa bata ta6a abu aciki ba. Shiru ya mata ya kama hanyan tafiya yayinda tasha gabansa "Yanzu kana ganin abinda kakeyi ka kyauta kenan? Kana ganin kana min adalci kenan a gidan nan? Wallahi ka cigaba Allah na kallonka."

"Kaman yadda yake kallonki ba, tell me mey kika ta6a nema a gidan nan kika rasa dukda rashin hankalin da kike min ban ta6a tauye miki hak'k'inki ba duk abinda kikeso shi kikeyi a gidan nan without getting questioned what else do you need?"

"What else do I need?" Ta nanata da mmaki tana kallonsa "Your attention and for you stop flirting around taya da aurenka zaka tsaya kana bin 'yan mata a waje? Do you deny wannan wayar ba wa budurwarka zaka kaiwa ba?"

"I don't have time for this, na sha fad'a miki ni banida budurwa a waje idan ma ina dashi ba abinda ya shafeki bane I'm a husband to four wives so learn to stay in your lane."

"Abinda zaka fad'a min kenan Afzal? Dududu auren namu watanni nawa ne har zaka soma kula 'yan matan waje?"

"Ko nayi ina da laifi ne? Never once did you ever regard me as your husband inba wai buk'atunki sun tashi ba, a tsammaninki kina da right na min magana ne?"

"In girki ne kakeso naji na yarda zan fara yi maka girki."

"Ni bance ina son girkin ki ba, keep it to your self abu d'aya nakeso da ke learn to mind your business kaman yadda kike duk abinda ranki yaga dama a gidan nan ba wanda ke miki magana nima haka nake da 'yanci ko fiye da hakan ma because this is my house and I do only what pleases me."

"Wallahi Allah ze sak'a min."

"Tare ze mana sakyyan kuma kidena had'ani da Allah" yana kaiwa nan ya wuceta ya fice. Kuka kawai tasa a wajen da k'yar tayi shiru taja mayafinta se gida. Mummy na ganinta ta gaskata zancen akwai matsala a k'asa don haka ta jata d'aki ta shiga jero mata tambayoyi hajiyarku kam ba se kuka ba mutum na iya cewa wani gaggarumin laifi ne Afzal ya mata har Mummy ta soma tunanin ma ko dukanta Afzal d'in yayi. Da k'yar de ta samu Nazeefar tayi shiru sannan ta fad'a mata halin da ake ciki na cewa Afzal na shirin yi mata kishiya ne. Da Mummy ta tambayeta hujja kuwa bata da ko d'aya banda iphone 6 data ga cikin leda se kuma ce mata da yayi wai shi miji ga mata hud'u ne.

"Ke shikenan don kinga ya sai sabon waya seki ce wa budurwa ze kaiwa?"

"Wallahi Mummy wa budurwa ne" ta fad'a tan share hawayenta sau dayawa ina jinsa yana waya da ita kuma ranan ma k'awata tace ta gansa da wata a school."

"Toh ai koma meye Afzal d'in yayi banga laifinsa ba se naki inda kin bashi girmanshi kin rik'e shi da mutunci da amana kina kula dashi a matsayinsa na mijinki wallahi nasan Afzal baze fara gaggawan k'aro aure ba ko baki fad'a ba Nazeefah nasan baki kula da Afzal a gidan can da k'yar ma idan kina basa girmansa as mijinki wanda kike k'rk'ashinsa, kin musanta?" Shiru Nazeefah tayi tabbas ba k'arya cikin kalamun Mummy ko d'aya. "Dake fa nake? Nayi k'arya?" Shiru tayi chan ta kad'a kai.

"Tell me meyasa bazeyi tunanin sake yin aure ba tunda baki kula dashi baki basa muhimmanci?"

"Toh Mummy shi yana nunawa ya damu dani ne? Tafiya nayi gabad'aya don ban sanar dashi ba ko kira na yayi min na isa lafiya beyi ba."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un Nazeefah!" Mummy ta dafe k'irji "Yanzu har kiyi tafiya bazaki sanar da yaron nan ba? Yau kin fallasheni ni Fatsuma shin tarbiyyan dana baki kenan? Yanzu har kiyi tafiya bazaki sanar da mijinki ba? A tunaninki zaman kanki kike ne a gidan, Iyyeh? Kodan kinga bayi magana ne?" Shirun da Nazeefah tayi ya bata daman cigaba da magana "Da ke fa nike!"

"Toh ai na tuba bazan sake ba ni kawai ki kirashi kice mishi ya dena neman wannan yarinyar da yake."

"Saboda gani uwar banza ko? Lallai ya tabbata bakida hankali to ki bud'e wannan kunnuwan k'ashin naki wallahi ki saurareni, in ke bakida hankali ni ina da shi kuma muddin baki zubda wannan banzayen halayen nan naki ba haka kinaji kina gani Afzal ze k'aro aure matar ta k'wace miki shi kina ji kina gani kuma ba abinda zaki iya k'arshe yaga dama ma ya sakoki."

"Dan Allah Mummy ki kirashi ki bashi hak'uri wallahi zan dena rashin hankalin da nakeyi zan shiryu."

"Kar ma kiyi mana karma is coming for you."

"Mummy dan Allah kiyi hak'uri."

"Sani fa ya rage wa me shiga rijiya ko ki canza ko ki sha mamaki."

"Toh Mummy ya zanyi in karkato da hankalinsa a gareni? Wallahi bazan iya rayuwa da kishiya ba."

"Kidena rashin ji, bari na bari- yi na yi, kina tsaftace kanki da muhallinki, girki kar ya ta6a wuceki, shin ina kika kai hud'uban dana miki kap kafin in kaiki gidanshi Nazeefah? A ina kika zubar dasu?"

"I'm sorry" ta furta tana turo baki.

"Amman har me kike masa yasa sa wannan gaggawa? Dududu auren naku wata nawa ne?"

"Ni ba abinda nake masa."

"Oh bazaki bud'e baki kimin magana ba sena kira Daddy'nkunna k'irga mai komi tukun?"

"Mummy dan Allah na tuba, wallahi komi ma na mishi Mummy ko girki ban ta6a mishi ba amman daga yau zan fara ni banason ya sake yin aure."

"Innalillahi wa inna ilaihi raji'un ai kuwa aure ki k'addara a ranki an riga an d'aura believe me idan da nine Afzal d'in wallahi tun auren naku na sati biyu zan kawo amaryata, wannan rashin hankalin da me yayi kama? Kina nufin for morethan five months yaron nan kullum siyan abinci yakeyi a waje? Where is my phone wallahi sena k'irga wa Daddy'nku."

"Dan Allah Mummy kiyi hak'uri" ta fad'a da sauri tare da janye wayan kafin Mummy ta d'aga.

"Bani wayata sakariya kawai bani!"

"Mummy kiyi min rai wallahi Daddy yaji kasheni zeyi I'm sorry please don't call him." Fad'a sosai Mummy tayi mata Nazeefah se kuka, bayan nan tayi mata nasiha sannan ta tura ta gida.

Ta d'ayan 6angaren kuwa, Afzal tun fitansa ya zarce gidansu Amal acikin mota ta k'ariso ta samesa suka gaisa bayan d'an hiran da suka ta6a kad'an ya mik'a mata ledar.

"Toh kuma mey aciki Yaya?"

"Amsa ki duba" ba gardama ta bud'e thunderstrucked taga sabuwar waya pil aciki wayan da ko a mafarki bata ta6a kawowa kusa da tunanin ta zata rik'e irinshi a kwanakin kusa ba. Dan mamaki da murna ta ma kasa magana se chan baya ta shiga tambayansa dagaske wayan nata ne kode wasa yake mata. Godiya sosai tayi masa, sam ta kasa 6oye farin cikinta a rayuwa batasan ya zatayi ba idan ba Afzal yanzu shikenan zata nayin assignments nata cikin sauk'i ba seta je cafe ba 'yan iskan samari nan suna bin mutum da kallo da kalamun soyayya. Sabon sim daya sai mata yasa mata a ciki ya nuna mata yadda zatayi charging wayar idan ta shiga ciki sannan ya mik'a mata ya kuma ce mata duk abinda bata gane ba she shoud feel free to call and ask him. Godiya mara adadi Amal ta tayi masa har zuwa lokacinda ya tafi. A hankali ya bud'e mata account a WhatsApp, Instagram da Snapchat dukda cewa ita bata wani damu da su bama, dama-dama WhatsApp d'inne take d'anyi dake anyi adding nata a group na 'yan class nasu ta na kuma samun informative messages ta wajen.

A hankali a hankali kan Amal ke wayewa har ta soma amfani dasu snapchat tazo ta bud'e Twitter account da kanta, yarinya tana wayewa tana k'ara kyau da k'warjini. Tuni samari suka fara yi mata chaa sede dake tasan daraja da k'imarta kota kansu batayi duk wanda ya tsareta ce masa take akwai tambayan wani a kanta. A haka har suka shak'u da wata coursemate nata Maamah, yarinyar nada hankali sosai kuma ba k'aramin son Amal take ba. Suna da kud'i amman hakan besa ta rasa tarbiyya ba yawancin kullum
DOWNLOAD
DOWNLOAD

Please Login or Register in order to submit comment